Skip to main content

DANGI 'DAYA - HAUSA NOVELS


 

*❣️DANGI 'DAYA❣️*


_{Romance & Friendship luv}_


Writing by Amnah El Yaqoub


_Marubuciyar:_

```DANA SANI```
_{Ahmad & Feenah}_

```BURINAH```
_{Amal & Daddy}_

```WAZAN ZABA?```
_{Iman & Aliyu}_

```SHALELAN BABA```
_{Haneef & Haneefa}_

```NI DA KE```
_{Mk & Baby}_

_And now!_
               👇
             *_DANGI 'DAYA_*


*_Bissmillahir-rahmanirraheem_*

_Ina qara godia ga Allah daya bani damar rubuta wannan littafi, ya Allah ka haneni rubuta abinda yake sharri ne da kuma abinda bai kamata ba, Allah kabamu ikon yin amfani da abinda yake Mai kyau ne, kasa muyi watsi da marar kyau._

_Littafin *DANGI DAYA* qirqirarran labari ne, saide ina fatan idan yayi daidai da  Rayuwar ki wadda kika tsinci kanki aciki yanzu kisamu solution acikin wannan littafin._

_Idan labarin DANGI DAYA yayi miki dad'i inaso duk lokacin dakika tuna Dani kiyimin Addu'ah._

_Daga qarshe, duk wani masoyin *Amnah El Yaqoub*, na sadaukar da wannan page din agareshi🥰._


"NIHLA! lokacin tafiyar ki makaranta fa yayi, kitashi haka kada ki makara"

Cikin jin dadin baccin tayi juyi tabawa wadda take yimata magana baya,hakan yabawa dogon gashin kanta Wanda duk ya cukurkude damar rufe mata fuska, cikin magagin bacci tace "Diddi Allah ni baccin bai isheniba"

Dan qaramin tsaki taja, tasa hannu tadauketa cancak, bata ajiyeta ako'inaba sai afilin Dan qaramin tsakar gidansu na qasa Wanda yake ashare tas
Tsugunnawa tayi daidai Tsawon yarinyar tace "dan ubanki bude idonki, idan kika makara dukanki zasuyi "

Jin maganar duka yasa ta wartsake lokaci daya, ganin tatashi sarai yasa mahaifiyarta rabuwa da ita, takoma cikin dakin tad'auko mata d'an qaramin brush dinta, tabata, sannan tadauki baho tafara hada Ruwan Mai d'an d'umi.
Ruwan wankan data hada tad'auko takawoshi gaban yarinyar, sannan tadauko kwandon wanka Wanda yake d'aukeda soson wanka Mai laushi, da alama na yarinyar ne, ta tsugunna a gabanta "wai bazaki hanzarta kigama wanke bakin ba?"

Cikin sauri yarinyar ta wanke bakinta, ta ajiye brush din akan wata yaluwar jarka ta OKEY wadda take cikeda ruwa, bakin ma bai wani fita sosai ba, haka tahaqura tace "Diddi nagama, afara wankan"

Hannunta tasa ta tattare gashin kan yarinyar, Wanda yakeda tsawo sosai, cikar batada yawa, ta d'aureshi waje d'aya, sannan tafara yimata wankan

Idanunta a runtse tace" Diddi baza'a wanke kanba? "

"Nihla idan aka wanke wannan kan naki shi kad'ai ma zaisa ki makara kafin ya bushe, kibari idan za'a miki wanka da yamma saiki siyo omo awanke miki"

Tace "to Diddi"

Tsaf tagama yiwa yarinyar wankan anan filin tsakar gidan nasu sannan tasata tayi alwala , kasancewar akwai rairayi kad'an agidan hakan yasa qasar wajan ta shanye Ruwan, lokaci d'aya farar fatar yarinyar tasake futowa, wani zanin atamfa taja akan igiyar tsakar gidan nasu, tarufa a jikinta  sannan tashige d'akinsu da gudu.

Itama bayan yarinyar tabi zuwa d'aki, ta goge mata jikinta, sannan tashafa mata Mai Vaseline na Habiba, tasa ta tafara sallah, dukda yarinya ce qarama, tayi kokari wajan yin sallar saide gyara 'yan kad'an

Hijabin datayi sallar dashi tacire, tad'auki mataji tabawa mamanta tace"Diddi gashi "

Batare da tace komai ba ta karbi matajin, tafara tajewa yarinyar gashin kanta, me mugun tsawo sosai, tad'aure matashi da ribom sannan tatufke mata sauran, zanin atamfar data goge mata jikinta dashi tad'auka ta goge mata fuskarta, saboda maiqo, sannan tasaka mata d'an qaramin hijabinta fari me hula, kasancewar hijabin d'an qarami ne hakan yabawa jelar gashinta damar futowa ta qasan hijabin, takalmin ta tasaka silifas, sannan tace "Diddi natafi"

"to Muje wajan babanki kikarbi kud'in karyawa"

Wani d'aki suka shiga Wanda yake kusada Wanda suka shirya, tana tsaye abakin kofar d'akin ta doka sallama, radion dayakeji yarage sautinta, sannan ya amsa mata, ko ina kwana Babu tace masa "Baba kudin karyawa"

Murmushi yayi, yadauki nera goma acikin aljihun rigarsa yabata, takarba tafuto, ta kalli Diddi dake tsaye abarandar gidan nasu tace "Diddi natafi"

"to Nihla saikin dawo, banda wasa ahanya kinji ko"

"to Diddi, idan anyi tara nataho gida ko?"

"Haba Nihla, mezakiyi idan kinzo?ba ana baku abinci a makaranta ba? Kiyi zamanki sai antashi, nisan ai yayi yawa"

Cikin shagwaba tace "to Diddi idan basu bamu bafa?"

"tome amfanin nera goman da aka baki? Saiki siya wani abun kici"

Tace "to natafi"

Itama tace "to Allah yakiyaye, banda wasa de kinji ko"

Tace "to" tareda ficewa daga gidan
Ita kuma Diddi tad'auki albasa yan madaidaita guda uku tafara Yankawa, amma abin mamakin shine hancinta yana gab da albasar datake Yankawa tana shaqar yajin albasar Kamar batajin zafi


Kamar kullum tana futowa daga gida adede lokacin shima megadin gidansu ya wangale musu get, kallo d'aya tayiwa motar qirar Mercedes Benz tadauke kanta, ta gabanta motar tazo tawuce, tana d'ago kanta taganshi shi kad'ai a bayan motar ana jansa, shima uniform ne ajikinsa amma ba irin nataba, da alama na private school ne nasa, cikin sauri yajuyo ta glass din bayan motar yafara d'aga mata hannu yanayi mata bye-bye,sarai taganshi, amma taqi yimasa bye-bye din, sai murmushi datayi masa har dimple d'inta suka futo gaba d'aya biyun

Juyawa yayi yadena Kallanta, yabude school bag dinsa yayi rubutu ya cukwikwiye yasaukar da glass din gefensa, ya wulla mata takardar, sannan Yarufe glass din yana daria, baisake Kallanta ba

Itama tana kallan motarsu, har sukai mata nisa, takardar dataga ya wullo mata tad'auka, ahankali ta bude takardar   "You're my friend"
Shine abinda tagani ajiki, bata fahimci komai ba, Dan haka tayagata ta watsar awajan 😃
Taci gaba da tafiya tana ball da duk abinda tagani agabanta


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

"Abubakar"

"na'am Hajiya"

Wata takarda tabashi doguwa alinke, sannan tasake kallansa tace "riqe wannan takardar"

Karba yayi yariqe fuskarsa cikeda mamaki, bai iya boye mamakinsa ba yadubeta yana qoqarin bude takardar "Hajiya wannan takardar mecece?"

Cikin sauri tace masa "karka kuskura kabud'e wannan takardar Abubakar, abinda yake cikin ta Sirri ne tsakanin nida mahaifinka da mahaifiyar ka wato abokiyar zamana"

Kallanta yasakeyi sosai"to Hajiya meza'ai da'ita? "

" yauwa Tun farko abinda yakamata ka tambayeni kenan, Abubakar wannan takardar wasiyya ce da mahaifinka yabari ahannun mahaifiyarka Tun kafin yabar duniya, ita kuma tad'auka tabani kafin itama Allah yayi mata rasuwa, ni kaina inaji ajikina ba lalle naqara shekara d'ayaba nan gaba, shiyasa nima na damqa maka wannan wasiyyar ahannunka amatsayin ka na babba acikin MAZAWAJE FAMILY,"

" haba hajiya, meyasa zaki dinga yimin irin wannan maganar? Ke kad'ai ce kika rage mana, sannan ke kad'ai muke gani muji dadi, kinasa jikina yanayin sanyi sosai "

" Kayya, Abubakar kenan, shekara tamanin da biyu ba nan bace Abubakar, gara inyi abinda yakamata Tun kafin lokaci ya quremin, mutuwa bata sallama "

Shiru yayi, kansa a sunkuye, maganar hajiya tasa jikinsa yayi mugun sanyi, bata taba nuna masa banbanci da 'ya'yanta ba duk da ba'itace ta haifeshi ba, kishiyar mahaifiyarsa ce, idan itama tatafi tabarsu yaya zasuyi? 🤔
lokaci d'aya Idanunsa yakad'a yayi jajir, yadago yadubeta "Hajiya yanzu yaya zanyi da wannan takardar?"

Hannunta ta miqa masa tace "bani takardar Abubakar"

Takardar yasaka mata cikin hannun ta, yana Kallanta ta bude wata qaramar akwati agefenta tasaka takardar aciki, sannan tasaka key tarufe akwatin, tamaida Kallanta gareshi tace "Wannan takardar zataci gaba da zama acikin wannan akwatin har Tsawon shekara goma"

Cikin sauri yad'ago kansa yadubeta "Hajiya shekara gomafa ba wata goma bane, mu kanmu bamuda tabbacin zamu iya kaiwa wannan shekarun dakika ambata"

"Abubakar kenan, kullum addu'armu itace Allah yaraya mana ku, nasan zaka iya amatsayin ka na babba Mai fada aji acikin yan'uwansa shiyasa nabaka wannan takardar, kuma har gobe ina fatan gaba d'ayanku kukai wannan lokacin"

Cikin sanyin jiki yace "to Hajiya Allah yasa"

Tace "Amin Abubakar, Allah yayi maka albarka, mukullin dazai bude muku wannan akwatin zaku iya samunsa awajan Alhaji mamuda, Wato aminin mahaifin ku idan shima lokaci bai cikaba, sannan abu na qarshe dazanyima kashedi akansa shine daga rana irinta yau kada asake taro kowanne irine acikin MAZAWAJE FAMILY, idan anyi haihuwa asakawa yaron suna kawai, maganar taro na biki shima daga kan masu shekaru irinna FAROUQ zuwa qasa kada abari kowa yayi, idan so Samu nema kubarsu su girma kowa ya mallaki hankalin kansa tukunna kafin ku aurar dasu"

Wannan karon kam gumi ne yajiqe masa fuska, wannan wanne irin sharad'i ne? 🤔
Kallanta yayi" Amma hajiya... "

Cikin sauri ta d'aga masa hannu" dakata Abubakar, wannan umarni nane, banaso kace komai akan haka, Yaya maganar takardar filaye na yara?"

Daqyar yace" Hajiya angama yankawa kowa nasa, dukkan yaran maza kowa angama sama masa nasa filin, takardun ma sunzama ready"

"to idan kowa acikinsu ya tasa, kad'auka da kanka kabawa kowa nasa, Wanda ya wulakanta nasa shiya jiyo, idan mutum yanason zama acikin gida na family shikkenan, idan baya buqata saiya gina filinsa"

Cikin ladabi yace "to hajiya, insha Allah zanyi kokari inga nacika umarninki, nizan wuce gida su Rahma suna jirana itada yara zasu tafi jigawa suyi kwana biyu"

"meyasa kai ba zakaje ba Abubakar?"

Shiru yayi, bai tanka mataba, Dan haka tayi Murmushinsu na tsofaffi tace "Ayi hakuri haka Abubakar, abinda yafaru yariga yafaru, Aisha qanwar ka ce dakuka futo ciki d'aya, bayan 'ya'yana bakada Wanda yafita duk duniya,kaida Aisha duka DANGI 'DAYA kuka futo,sannan ba ita kad'aice Mai irin wannan laifin ba, kamanta da abinda yafaru abaya kajiko?"

Yace "to hajiya insha Allah, mungode sosai da sosai da irin ruqon dakika mana, Allah yaqara girma"

Cikin rashin damuwa tace"Amin Abubakar, Allah yayi maka albarka, ya albarkaci mazawaje family "

Yace" Amin hajiya"daga nan yatashi yafita


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️
Tunda yadawo gida yarasa meyake masa dadi, idan yatunada maganar dasukai shida hajiya duk sai yaji wani iri, wannan ba qaramar magana bace, amatsayin sa na babba acikin family dole abin zai dame shi, to yanzu ita hajiya data d'ora masa wannan nauyin tana da tabbacin zata rigashi mutuwa ne? Idan kuma shi yarigata mutuwa fa? Wannan ba maganar 'boye-'boye bace, dole zai kira yan'uwansa gaba dayansu yafad'a musu komai, saisu sake tattaunawa akan batun, duk Wanda Allah yayi masa Tsawon rai acikinsu haryakai lokacin da hajiya ta ambata, saiya zartar da hukuncin, bazai iyu yabarshi aransa shi kad'aiba, zai hada meeting akan hakan dole

"Alhaji tunanin mekake haka tun d'azu nashigo inata sallama bakajini ba?"

Ajiyar zuciya yasauke yakai dubansa zuwa ga matar da tashigo cikin d'akin nasa, kallo d'aya zaka mata ka hango hutu da jin dadi atare da ita, yace"Rahma banji shigowar ki bane, ina yaran suke? Kun gama shiryawa ne?"

Shiru tayi masa tanemi waje ta zauna a gefensa sannan takama hannayensa tace"Alhaji meyake faruwa? Yanayin ka ya sauya bayan qalau kafita, kafadamin meyake damunka?"

Kallanta yayi "wallahi Rahma hajiya ce tadauramin wani Babban nauyi akaina,tabani wasiyya ne, sannan maganganun nata duk sun sanyaya min jiki, tanamin magana Kamar bazata qara kwana d'aya aduniya ba"

Cikin mamaki tace "wasiyya kuma?"

Yace "qwarai kuwa" nan take ya labarta mata abinda yafaru tsakaninsa da hajiya

Ajiyar zuciya tasaki tace "Alhaji, tunda kaga tanemeka kunyi wannan maganar da'ita haqiqa ta yarda dakai ne,tunda duk cikin yaranta bata nemi d'aya daga cikin su ba saikai, kayi kokari kaga kacika umarnin datama, amma gaskiya kasamesu kuyi maganar shi ne yafi, dukda nasan ma wasiyyar bazata wuce maganar hadin kanku ba "

" nima abinda nake tunani kenan Rahma, saide kuma idan hakanne me yakawo maganar taro da za'ace bandashi? "

" ka kwantar da hankalin ka Alhaji, insha Allah Babu abinda zai biyo baya sai alkhaairi "

" to Allah yasa, kwana nawa zakuyi idan kunje? "

" Kamar dai yanda mukai maganar dakai Alhaji, kwana biyu zamuyi insha Allah "

" to saikun dawo, Allah yakiyaye hanya, ki kulamin da yarana "

Murmushi tayi" Alhaji kenan, kanaji da wannan samarin naka, ni kuwa suna sakani ciwon kai, shikkenan za'a kula dasu "

Yace" to asauka lafiya "

Tashi tayi zatabar d'akin, harta fara tafiya Tajuyo tace masa"Alhaji banji kace na gaida Aisha ba "

" fad'ar gaisuwa ta a gareta ai batada amfani Rahma, tunda nina shirya muku tafiyar ai yakamata kisan cewa inaso ki ganomin ita ne"

Murmushi tayi tareda girgiza kanta, cikin ranta tace "Alhaji kenan" 🤣
Amma afili sai tace masa "to shikkenan zanfad'a mata yayanta yana gaishe ta kuma yana cikin kewarta akoda yaushe"

"kudin hannun ku zai isheku ko?"
shine abinda ya tambayeta a memakon yabata amsa akan maganar datayi masa, sai itama ta basar, tace "zasu isa, mungode,"

Tafuto daga d'akin batare data sake cemasa uffan ba, kai tsaye compound ta nufa, driver na ganinta yataho Dasauri ya karbi handbag d'inta, sannan yabude mata gaban motar ta shiga

❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Tunda tataho daga makaranta take kalle-kalle tana waige ko yauma zataganshi and'aukoshi daga makaranta Kamar kullum, saide ko alamun tayar motarsu bata ganiba, afili tace "inajin yauma yarigani dawowa , ko meyasa baya jirana?"

Takardar daya wullo mata d'azu dasafe tatuna tasaki dariya tasake cewa "kome ya rubuta oho masa, DANA SANI na nunawa Diddi"

Tana tafe tana waige har Allah yakawota gida, Tun daga bakin kofar gidan ta d'aga murya tace "Diddi nadawo " sannan ta qarasa shigowa cikin gidan, turus tayi ta tsaya waje d'aya ganin baqin fuska  agidan nasu, maza ne harsu hud'u reras, guda uku suna tsaye suna buga ball atsakaninsu, gaba d'aya wandone ajikinsu three quater, sai guda d'ayan dayake zaune kusa Diddinta ko d'ago kansa baiyiba bare ya kalleta

d'aya daga cikin masu buga ball d'inne ya kalleta dakyau yace "fine girl"

'Dago kai Diddi tayi ta kalleta tace "Alhamdulillah kinga 'yar halak, Nihla zonan,"

Kallan uniform d'in jikinta tayi sosai, tasan fad'an Diddi baya wuce anbata kayan makaranta, Dan haka tace "Diddi ki kalli kayana Allah yau ban batasu ba"

Diddi ta kalli matar datake kusata ita wadda taketa zubawa Nihla murmushi tace"Anty Rahma kinji 'yartaki harta fad'i d'aya daga cikin halin ta ko? "

Matar da aka kira da Anty Rahma tayi daria tace" Nihla zonan, ina kika tsaya baki dawo gidaba har biyu tawuce?"

Qarasowa cikin rumfar tasu tayi, jin Diddi takirata da anty Rahma yasa itama tace " Anty ina wuni "

damuwa ce ta baiyana a fuskar matar, Dan haka tace" Nihla Anty kuma? Momy zakice kinji ko? "

d'aga mata kai tayi, ta zauna awajan tareda cire d'an qaramin hijabinta, doguwar sumar kanta ta baiyana, Diddi tasake Kallanta tace" A'ina kika tsaya? Kintsaya kad'ar tsamiya ko? "

Tace" a a Diddi, qara nakai wata yarinya wajan malamin mu, kullum saita dinga tsokanata tana cemin 'yarme fad'in gira "🤣
Daria sukasa gaba dayansu harda yaran dasuke tsaye suna buga ball, amma shi Wanda yake zaune agefen Diddi ko murmushi baiyi ba bare dariya

Diddi tace" to Allah ya kyauta, aisaikiyi haquri, wataran zata daina tsokanar ki"

Mazan dasuke ball ne suka fara musu atsakaninsu, momy tace, "Farouq, Usman, Aliyu, kudena mana, banasan shirme "

Ta kalli diddi tace "shiyasa fa banasan tafiya da maza wallahi"

Daria Diddi tayi tace "toya zakiyi tunda mazan Allah yabaki?"

Dena buga ball din sukayi, suka dawo cikin rumfar, suka zauna Nihla tabisu da kallo, dukansu farare ne Kamar ita, Wanda ke kusa da Diddi ne kadai wankan tarwad'a, bekaisu haske ba

Momy ta dubesu tace "Usman ga qanwar ku Nihla,"

Cikin wasa Farouq yace "taso nakoya miki ball my sister"
Daria kawai Nihla tayi batace masa komai ba

Momy ta kalli na gefen Diddi tace "ABBA, bakaga Nihla bane?qanwarka cefa, yarinyar Diddinka"

Sai a lokacin yakai Kallansa gareta, sau daya yakalli fuskarta, duk a tunanin su ita yake kallo, amma azahiri ba fuskar tata yake kallo ba, hankalinsa yana kan dogon gashinta, ahankali Kamar me koyon magana yace "na gan ta"

Dan Baqin ciki Momy ko kulashi batayi ba, ta dubi Diddi tace "nikam Aisha anan wajan ku Babu malamai ne masu addu'ah, irin masu roqon Allah d'innan?"

Cikin mamaki Diddi tace "malamai kuma anty Rahma? Me zakiyi awajan malamai?"

Momy tace "zuwa zanyi nayi musu bayani su temaka su tayani da Addu'ah akan Abba,😂 inma rubutu ne suyi masa saiya dinga sha, Aisha idan Abba Yazauna awaje bazakiji maganarsa ba, idan ma zaiyi magana saide kiji yanayi daqyar Kamar anyi masa dole kokuma wani d'an sarki, bayan Babu Inda muka had'a dangi da sarauta, idan kinga Abba yazage yana miki surutu da Fara'ah to yaga jirgin sama ne, shi ala dole yanaso yazama matuqin jirgin sama"



D
A-Abba
N-Nihla
G
I
D
A
Y
A



*FAN'S ya bayan saduwa?🤪*
_please ta hanyar Comments d'inku ne zaisa nagane cewa labarin ya karbu, harma inci gaba da turowa 🙏🏻_




Amnah El Yaqoub ✍🏻[6/13, 11:26 PM] El Yaqoub: ❣️DANGI DAYA❣️

 _{Romance & Friendship luv}_

Writing by Amnah El Yaqoub


Like my page On facebook
 
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493/



3&4


Murmushi Diddi tayi "haba dai Anty Rahma, basai kinje wajan kowaba, kiyi hakuri kibarshi yanda yake, kinsan kowa da irin yanayin sa, haka Allah yayishi, hakan ai kwarjini yake qara masa, mazantakar kenan, yanzu kinga Nihla idan tafara zuba miki surutu saikin gaji, kowa da irin yanayin sa "

Momy tace" to shikkenan Aisha tunda haka kikace, Allah yaqara shirya mana zuria "

Tace" Amin Anty Rahma "

Hankalinta ta maida kan Nihla tace"ke tashi kije kicire kayanki kiyi sallah saikizo kici abinci "

Tace "to Diddi" sannan tatashi tayi cikin d'akin datake kwana aciki, anan taci karo da kayan abinci da katan katan d'in lemuka, lokaci d'aya wani farin ciki yakamata, saida taje ta tattaba su sannan tafara cire kayan nata

Usman Wanda shine babba acikinsu yakalli Diddi yace "Amma Diddi idan zamu tafi tareda Nihla zamu tafi ko, saiki bawa Momy ita"

Shima Aliyu Wanda yake binsa yace "eh wallahi, kinga bamuda qanwa mace, mu kadai ne, Diddi kibamu ita Dan Allah"

Abba yakalli Usman harya gama magana, Aliyu ma yana farawa yasake maida kallansa kan Aliyu, saikuma farouq Wanda yake bin Aliyu yace "Diddi, idan kika bamu ita kinga tazama qanwar mu, komai mune zamu dinga yimata, munasan Baby amma Babu agidan mu, saisu dinga tafiya makaranta itada Abba"

Momy ta kalli Abba dayakebin yayun nasa da kallo tace "Abba nah bakace komai ba, kanaji duk brothers d'inka sunyi magana, kaima kanaso abamu Nihla saiku dinga wasa tare ko?"

Ataqaice yace mata "Eh"

Girgiza kanta tayi sannan ta kalli Diddi tace "Aisha, kinsan lokacin bikina da yayanki, duk yaran nan da hankalin ki aka haifesu, Tun kafin Allah yabani haihuwa nakeso Allah yasa nahaifi mace, amma Allah da ikonsa bai baniba, saide maza, Aisha Dan Allah kibani Nihla wallahi inason yarinyar sosai, bazan iya kwatanta miki yanda nake santaba, "

Daria Diddi tayi"yanzu Anty Rahma banda rigimarku idan na baku ita nikuma fa?"

Cikin sauri momy tace " Sai Allah yabaki wata, may be ke Allah yayi mata zaki dinga haifa shikuma yayanki maza"

"A a Anty Rahma, kuyi hakuri amma bazan iya baku ba, 'yar tawa ita kad'ai jal Zan dauka naqara miki, sun zama su biyar fa kenan, nikuma Babu ko daya"

"idan kika bani ita saikiga Allah yabaki wata"

"Anty Rahma, Allah hakuri zakuyi, amma kyauta kacokam, inaaa"

Cikin sanyin jiki Momy tace "to shikkenan Aisha, Tun farkoma dana sani Mai hakuri na yiwa maganar ba keba, nasan shi bazai min musu ba,"

Diddi tace "zata dinga zuwa muku hutu dai, shima ai yayi"

Momy tace "Aisha irin wannan soyaiya idan zakiyi auren ta yaya zaki yi?"

"ni kaina bansaniba Anty Rahma, amma banason rabuwa da 'yata"

Murmushi kawai momy tayi, tana Jinjina irin wannan qauna da Diddi takeyiwa Nihla, saide anata bangaren kawai jinta take,banda de itace ta haifi Nihla dazata iya cewa  duk duniya banda ita Babu Wanda yakai ta son yarinyar, jitake Kamar ta d'auketa gaba daya

Diddi ta dubeta tace "Anty Rahma ban tambayekiba, yaya labarin matar yaya Basiru kuwa? Tasauya ko halin ta yana nan?"

Ajiyar zuciya tayi "Aisha ai wannan baiwar Allah halin ta bazai sauya ba sai wani ikon Allah, gaba d'ayafa nema take ta lalata tarbiyar yaranta, shi Fawaz nema yakema yafi qarfin iyayen, abokan banza yake kulawa, idan su Abba zasu tafi school bayason binsu sai anyi da gaske,gaba d'aya sunansa yabace, idan zaki wuni kina cewa fawaz bazai amsaba, saide gaye 🤣, ita kuma Aysha takwararki tace bazata sake zuwa makaranta ba saide afitar da'ita qasar waje, Acan zatayi🤣, ita kuma qanwarta Ilham tana nan tana zuba rashin kunya, bata barwa kowaba, yara qanana sai rashin kunya "

"Amma yaya Basiru yana gani yazuba musu ido yana kallan su?"

"to yaya zai musu Aisha?🤔Kinsan hali dai, dama yayanki ne Mai tsawatarwa, to shima yayi shiru yazuba musu ido, yace lokacin dazaiyi auren ai baiyi shawara dashiba"

"to ina Diyana da Dida, su Aslam da Adam?"

Momy tace "wallahi kowa yana lafiya,"

Haka sukaci gaba da firarsu, Diddi tana Tambayar Momy labarin gida, ita kuma tana fada mata, har yamma tayi liss
Diddi ta dubi Nihla data baje kayan wasan 'yar tsana tanayi tace "Nihla tashi kidauki nera hamsin agefen katifar nan kije shagon bashari kisiyo omo naduka"

Tace "to Diddi"
Sannan ta kalli Abba daya zubawa kayan wasan nata ido tace masa "zakaje?"

Girgiza mata kai yayi, alamun bazashi ba, saida ta harareshi sannan tace "karkaje d'in" 🤣
Ta d'auki kud'in tayi ficewarta

Momy tayi daria tace"walllahi kuwa,yasha zamansa kema kin huta abinki, "

Ta kalli Abba tace" kaide akan wannan halin naka na miskilanci bakada ranar samun matar aure, Dan babu wacce zata soka ahaka "

Diddi tace" Haba Anty Rahma, meyasa kike fad'ar haka, tayaya zai rasa matar aure? Abba nefa, ABUBAKAR SADIQ, me sunan mahaifina sannan kuma me sunan yayana, nida kaina Zan samo masa matar dazai aura muna nan dake "

Daria yayi, sosai kuma dariyar tayi masa kyau yace"Diddi Zan kaiki umarah"

Cikin farinciki tace "Umarah Abba!"

Yace "harda Hajji"

"Alhamdulillah yau haihuwa tayi rana, Yaya bekaini ba gashi Abba zaikaini"

Momy tace "inde Abba ne zamu ganku arana"

Dariya sukayi gaba dayansu

"Diddi ga omon" cewar Nihla data shigo yanzu

Karbar omon tayi, tace "jeki zuba ruwa inzo na wanke miki kanki, saina miki wanka ma gaba d'aya"

Ruwan tazuba tadawo ta zauna agaban Diddi kusa da Abba, sannan ta d'ora kanta akan cinyar Diddin, hannu tasa ta warware mata gashin kanta, daga Momy har yaran nata duk kallan yawan gashin yarinyar suke,
Saida tagama warware mata sannan tace "Muje na wanke miki to"

"Diddi Zan wanke mata"

Cikeda mamaki kowa yake kallansa, musanman Momy, cikin ranta tace tabd'i
Amma a fili sai tace, "lalle Nihla kin ciri tuta"

Diddi tayi daria tace"lalle yau haihuwa tanamin rana sosai"

 takai Kallanta ga Nihla tace " ke tashi kije yayanki ya wanke miki kanki "

Babu musu tatashi ta cire kayan jikinta, daga ita sai pant tabishi suka futo tsakar gidan ta tsugunna, shima tsugunnawa yayi  sannan yafara zuba mata ruwa akan, ba komai yasa yace zai wanke mata kanba, saidan yanaso yataba gashin yaji, omon yad'auka yazuba mata akan sannan yafara wankewa yana dirzawa da duka hannunsa biyu
Momy dasuke zaune a rumfa kallansu take tanajin d'ad'i aranta, ashe Abban nata ya'iya wankin kai,🤣 shikuwa Usman hannu yasa a aljihun jeans d'insa yad'auko wayarsa yana musu photo

Kannata yafita sosaai amma haka yaita wasa da gashin sannan yadena zuba mata Ruwan, ya kalleta Ahankali yace "kicire wandon nayi miki wanka"

Hannu tasa ta goge Ruwan daya zubo mata a fuskarta ta d'aga murya tace "Diddi wai yamin wanka?"

Cikin rashin damuwa tace "Eh yayi miki mana"
Ahankali tatashi ta cire wandon sannan ta tsugunna, babu bata lokaci yafara yimata wankan, saida ya wanke mata jikinta tass sannan yacemata "tashi kije"

Bata damu da yanda yayi mata maganar Kamar bayaso ba, tatashi tatafi d'aki da gudu

Da yamma  Usman da Aliyu da Farouq suka fice yawo ganin gari
Nihla kuwa tunda Abba yayi mata wanka ta shiga d'aki tasaka wata 'yar qaramar riga marar hannu tashan iska, ta kwanta tana wasa tana surutun ta ita kad'ai anan bacci ya dauke ta

Diddi ta kalli Abba da Idanunsa suke lumshe wa tace"me sunan yaya nah, kai ba zakaje yawon kaga gari ba? "

Hamma yayi yace" Diddi bacci nakeji "

" to tashi ka shiga d'aki mana, jeka kwanta kahuta, dama ai akwai gajiya kunsha hanya "

Yana shiga d'aki yaga Nihla na bacci, katifar tanada girma sosai, shima ya kwanta agefenta, nan da nan kuwa yayi bacci

Saida Momy ta leqo d'akin taga sunyi bacci dukansu sannan ta kalli Diddi tace" Aisha kin tambayeni kowa amma baki tambayi yayanki ba, "

Lokaci d'aya yanayin Diddi ya sauya," Anty Rahma yaya bayasona yanzu, wannan shine dalilin dayasa bazan iya baki Nihla ba, qiyaiyar dayakemin bakan kowa zata komaba sai kan 'yata,nikuma ina son yata, banasan wani abu yasameta, yanzu haka tsoron irin amsar dazaki bani ne yasa ban tambayeki shiba, saboda nasan ba zanji amsa Mai d'ad'i ba "

hawaye ne suka zubo mata, wasa wasa Tun ta nayi marar sauti harta dawo tana kuka sosai Kamar qaramar yarinya

Ajiyar zuciya Momy tayi, ta dafata  "Aisha yayanki baya fishi dake yanzu, idan ma yanayi to kad'anne,kisaki ranki kidena damuwa, wai Aisha ke kadai kikai wannan laifin ne? Baga Basiru nanba, ganin yarane yasa banyi miki fada ba, ki kalli jikin ki aisha kin kasa kwantar da hankalin ki duk kin rame, meyasa hakan Aisha "

Cikin kuka tace" dole zanyi kuka Anty Rahma, ki kalli irin Rayuwar danake nida 'yata, Yaya yana dashi bazai tallafamin ba, uwarmu d'aya ubanmu d'aya, wacce irin qiyaiya ce wannan? "

"Aisha idan kika sake zancen qiyaiyar nan tsakanin keda yayanki ranki zai baci yanzun nan, yanzu haka yayanki ne ya shirya mana wannan tafiyar, kiyi hakuri ki kwantar da hankalin ki, watarana komai zaizo qarshe"

Jakarta ta bude tadauko kudi masu yawa ta miqa mata, Diddi tasa hannu takarba,sannan tasake dauko mata wata sarqa ta gold tabata, sannan tace "ki ajiye wannan sarqar awajan ki, dakaina nasiyo miki ita, tanada tsada, duk lokacin dakika buqaci kudi idan babu ahannun ki kije kasuwa kisiyar kiyi amfani da kudin, shikuma wannan kudin dubu hamsin ne,yayanki yace akawo miki"

Hawaye masu d'umi suka zubo wa Diddi, taji dadin kyautar amma wani bangare na zuciyarta ya kasa yarda cewa yayanta ne ya aiko mata da kudin, ta kalli Momy tace "nagode sosai Anty Rahma, Allah yasaka da alkhaairi"

Momy ba tace komaiba tajata jikinta tana bubbuga bayanta alamar rarrashi, saida taga ta daina kukan tasaki ranta, sannan suka tashi suka fara shirye-shiryen had'a Abincin dare


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Cikin bacci taji anajan gashin girarta, zafi taji, lokaci d'aya tabude idonta, dashi tafara yin tozali yana kwance agefenta yazuba mata ido, tace "kai meyasa kakejamin girata, Allah Zan fadawa Diddi"

"to sai bacci kike kitashi mana, tashi natayaki wasa"

Kafada ta maqale masa "bazanyi wasa dakai ba,saboda d'azu kaine kaqi rakani shago nasiyo omo"

Kansa ya nuna da hannunsa yace "nid'in? bana wanke miki kanki ba?"

Daria tasaka, gefen kumatunta duka biyun suka lotsa, ahankali ya d'ora hannunsa awajan, itama hannunta tasaka ta janye nasa hannun daga fuskarta tace "eh natuna, kamin wanka, to mun shirya, meyasa kai baka magana? Anty tace baka magana"

"inayi mana, gashi ina magana dake"

Gyara kwanciyar ta tayi Tajuyo tana fuskantarsa, kusancin yayi kusanci Kamar zata shige jikinsa, tace"meyasa to kakeyi Dani?"

" because You're my friend "

Girgiza kanta tayi tace " niban gane me kace ba"

"Zan fad'amiki"

"yaran Momy kun tashi daga baccin kenan" Dagowa sukai dukansu suka kalleta, Dasauri Nihla tace "yawwa Anty, me You're my friend take nufi?"

"Nihla Anty, Anty, nahanaki cewa Antyn nan kinqi ji, to zamu bata dake, kutashi ku futo kuyi shirin sallah, magrib takusa,"

tana fadar haka tafice daga d'akin, itama Nihla tashi tayi tafice tabar Abba shi kad'ai


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️



Da daddare dukansu suka baje a tsakar gidan akan tabarma, Nihla ta liqewa Usman tana ganin game a wayarsa, gama cin Abincin su kenan, sai lemuka dasuke ajiye agefe Wanda suka sha sukabar sauran

Baba ya kalli Momy yace "Amma hajiya ai zakuyi mana sati d'aya ko"

Momy tace "sati Ibrahim! Haba Mai hakuri, sati ai yayi yawa, jibi jibin nan zamu tafi insha Allah, kwana biyu zamuyi muku, saboda yara suna zuwa school, yanzu ma saida muka sanar a makaranta sannan muka Taho dasu"

Yace "to hajiya, ai hakanma kunyi kokari sosai, su Alhajin de duk suna lafiya ko?"

"lafiya kalau alhmdlh"

"to yaya wajan su hajiya Farida da yaran nata su Dida da Diyana?"

Wannan karan saida Momy tayi Murmushi, saboda tasan duk cikin mazawaje family baya shiri da kowa Kamar hajiya Farida, tace masa "suma suna nan kalau"

Yace "to madallah, Allah yasaka da alkhaairi Hajiya, Aisha duk ta nunamin abin arziqi"

Murmushi Momy tayi ba tace komaiba, suna nan zaune suna taba hira har dare yayi, suka nemi makwanci, Usman da Aliyu da farouq sukabi baba d'akinsa, Momy da Diddi da Abba da Nihla suka tafi dayan d'akin suma, Momy ce ta gyara musu shimfida daga nan taja Nihla jikinta suka kwanta, yanda tasata a gabanta Kamar wani zai qwace mata ita, har Diddi nayi musu daria


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Washe gari bayan sallar asuba yaran duk bacci suka koma, sai Diddi da Momy ne kawai suke fira sama-sama, gari nayin haske suka fara had'a abin karya wa, zuwa tayi d'aki tataso Nihla tashiryata tsaf sannan tabata nera ashirin tace ta tatafi makaranta
Yauma tana fita kofar gida taga gate din gidansu abude,direban gidan yana goge Mota, shikuma yana tsaye da lunch box ahannun sa, lokaci d'aya farin ciki ya kamata, yau itace da kanta tafara d'aga masa hannu, cikin sauri ya ajiye Abincin nasa aqasa yafuto da gudu, direban yana kiransa amma ko waiwayowa baiyi ba, qyaleshi yayi amma de yabishi da kallo yanaso yaga Inda zaije
Kusa da ita yaje ya kalleta "meyasa jiya ban ganki ahanya ba da aka tashi daga school?"

Zaro ido tayi "laaaa ashe kaima kana nemana, nima inata kallan hanya banganka ba"

Zuba mata ido yayi yace "yaya sunanki?"

Tace "Nihla Ibrahim Mai hakuri, kaifa?"

Cikin farin ciki yace "Yusif Isma'eeil,"

Hannun ta yaja yafara tafiya "zomuje direba yakaimu school tare"

Qwace hannunta tayi tace "um um Babu ruwana Diddi zata dakeni, tace karna tsaya ako'ina"
Tana fadar haka taqwace hannunta tatafi da gudu, shima Kallanta yake yana daria, sannan ya juya ya koma cikin gidansu

Da azahar ana tashinsu daga makaranta bata tsaya wasaba tataho gida, tana hanya bataga motarsu ba, saida ta kusa qarasawa gida sannan ta hangi motarsu suna shiga gida

 Bayan sallar la'asar dukansu suna zaune suna fira, Nihla tana kwance akan tabarma Momy tajata ta d'ora mata kanta akan cinyarta 🤣
Sukuma mazan suna buga ball Ahankali kasancewar gidan akwai d'an fad'i kad'an yau harda Abba akeyi, yana sanye da qananun kaya riga me Jan duhu da wandon jeans amma ya tattare wandon daga qasa ya maidashi Kamar three quater
 Saida sukayi suka gaji sannan kowa Yazauna, wayar Usman Abba ya karba yafara game, Nihla tanajin qaran game tatashi takoma wajansa tana gani, qasa-qasa tayi muryarta tace masa "zomuje yawo"

Shiru yayi ya qyaleta, tasake cewa "kaji"

Kallanta yayi becemata komaiba ya kashe game din yasaka wayar a aljihunsa yatashi yace mata "Muje"

Daria tayi itama tatashi, takama hannunsa suka fara tafiya ya kalle Momy yace "Momy munfita"

Cikin farin-ciki tace "to Abba na, amma Karku d'ad'e naga garin akwai hadari"

Basuce mata komaiba suka fice daga gidan ita kuwa Nihla takama hannunsa ta riqe sosai
Suna fita suka dinga zaga garin, sai surutu take masa amma amsar datake samu kad'ance daga wajansa

Kallanta yayi "ina zamuje?"

Tace "zakaje rafi innuna ma ruwa dayawa muyi wasa saimu dawo?"

"akwai ruwa sosai?"

Tace "eh akwai sosai baka ganiba harda kwale-kwale"

Yace "to Muje mu"

Tafiya sukayi me nisa sosai, Yakalleta yana haki yace "kewai bamuzo bane?"

"to idan munzo ai zakaga Ruwan ko? Kaide kataho kawai"

Bece da'ita komaiba suka cigaba da tafiya har sukazo wajan, hannunsa tasaki tatafi wajan Ruwan da gudu tana daria, abaki bakin Ruwan ta tsaya, sannan tasaka hannunta tad'ebo Ruwan ta watsa masa

Firgigit yayi, yadawo hankalinsa daga kallan yawan Ruwan wajan, yace "kika jiqani?"

Kafin tabashi amsa ya qaraso wajan shima yad'iba ya watsa mata, bata damuba, dariya ma tayi tasake diban wani tajiqashi, shima yasake ramawa, haka duk suka jiqa jikinsu shima ya biyemata sai daria suke cikin farin-ciki

Hijabin jikinta ta cire tana wullashi sama, tana cafewa, sai tsalle take tanata farin ciki, wayar Usman yadauko acikin aljihun wandon sa ya tsaya yanayi mata photo, gani tayi yana binta da waya ta tsaya tace "photo kakemin?"

"eh"  shine kawai amsar daya bata

Tace "to tsaya na gyara"

Tsayuwa ta gyara, yanata yimata photon iri iri, ya shagala yanayi mata pictures din, ta tsugunna ta d'ebi yashin dayake wajan ta zuba masa ajikinsa

Wandonsa ya kalla yanda tazuba masa yashi,memakon ransa yabaci saiyayi murmushi yabiyota da gudu, tana gudu tana waiwayensa har tazo wajanda aka tara wani yashin da yawa, tana zuwa wajan tafad'i

Shima yana qarasowa wajan yariqe gashin kanta yace  "wana kama?"

Daria tayi tace "nadena, Allah nadena"
Rabuwa yayi da ita ya kwanta anan gefenta akan yashin, sai haki suke maidawa kowa yana kallan Dan'uwansa, wayar hannunsa yadaga yayi musu pic suna daga kwancen

'Dis taji an d'iso mata ruwa, Dasauri tatashi duk yashi yabata mata gashin kanta tace,"ABBA ruwa"

Hannunta ya fizgo tadawo ta kwanta yanda take da, yace "me kikace?"

"Abba" tabashi amsa kai tsaye

Girgiza kansa yayi yace "Yaya Abba zakice"

Daga masa kai tayi, kafin tace wani abu sukaji Saukar ruwa akansu, cikin sauri suka tashi, tadauki hijabinta, yariqe hannunta suka tafi qasan wata bishiya da gudu, suka tsaya anan, Tun ana yayyafi aka dawo ana shara ruwa da karfi, duk tsoro yakamata, ta rikice, shikuwa Babu wani tsoro atare dashi, iskar da akeyi ne yasa bishiyar dasuke qasanta kad'awa, nan take ruwa yajiqe musu jikinsu jagab,kallan gashin kanta yayi, gaba d'aya yajiqe ya kwanta sosai yana sheqi Kamar Wanda ake saka masa Mai, hijabin jikinta ya karba Yarufe mata Kannata dashi, sannan yajata yasakata ajikinsa yace "kidena tsoro"

Bata iya cemasa komaiba, ahaka suka tsaya har aka qare Ruwan tas, Inda Allah yarufa Asiri ba'a dauki lokaci ana Ruwan ba

Ana gama Ruwan yasaketa, cikin tsoro tace "mutafi gida"

Bece mata komai ba yariqe hannun ta suka fara tafiya, mutane kowa yafuto yanata harkar gabansa
Sunzo wucewa ta wata bishiya su kaga mutane suna gudu ana cewa Zuma! Zuma!! Zuma!!!
Kallansa tayi tace "la'ila, wallahi mugudu karya cijemu"

Nan take suka fara gudu duk yanda sukaso kaucewa saida zuman yacijeshi awuyansa, kafin ya farga wani yashiga cikin hancinsa, lokaci d'aya ya rikice ya tsaya yadena gudun, hannunta yasaki, yarasa yaya zaiyi yafitar, wani me machine ne yazo wucewa ya gansu, ita yagane yace "subhanallah Nihla, me yakawo ku nan wajan?"

Kafin tace wani abu yacacimi Abba yasakashi akan machine din, ita kuma yasakata agaba, be tsaya ko'inaba sai Dan qaramin asbitin garin (Nuhu Alfa Hospital)

Saida ya danqasu ahannun likita, yaga sun fara duba Abba sannan yace musu zaije gidansu yasanar


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Acan gida kuwa duk sun fito kofar gida, gaba dayansu har mahaifin Nihla, sunyi neman duniya sun rasa Abba da Nihla 😂
Me machine yana zuwa kofar gidan yafaka, suka gaisa da mahaifin Nihla, nan take ya sanar dasu komai, cikin tashin hankali suka nufi asbitin baki d'ayansu




Waye yusif? Menene yake tsakanin Aisha da yayanta Abubakar? Wacce irin wasiyya iyayen su suka rubuta? Duk Ku biyoni



Sharhi please 🙏






Mrs Usman ce ✍️
[6/14, 10:40 PM] El Yaqoub: ❣️DANGI DAYA❣️

{ Romance & Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub


Like my page On facebook

https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493


5&6


Suna zuwa asbitin sukaga Abba Akwance Idanunsa yayi jajir, Nihla tana zaune agadon kusada qafafunsa, sai likitan daya dubashi a tsaye
Momy tace "subhanallah, sannu Abba,"
Sannan ta kalli likitan tace "doctor Babu dai wata matsala ko?"

"Babu komai hajiya, ai anyi masa allura ma, zaku iya tafiya, saide a kiyaye gaba"

Diddi tace "insha Allah likita, yanzu ma nemansu mukai muka rasa, amma insha Allah za'a kiyaye"

Takai Kallanta ga Abba tace "Sannu Abba, kanajin zafi yanzu?"

Girgiza mata kai yayi, Bece komai ba

Momy tasa hannu ta kamashi yasauko daga gadon, su Usman suka riqoshi suka futo daga asibitin
Suna hanya yadaga kai yakalli momy yace "Momy"

Kallansa tayi, "na'am Abba"

Yace "Momy nasha wahala bazan sake dawowa garin nanba"

Murmushi Momy tayi "a a Abba karka ce haka mana, kaida nakeso duk wata kana zuwa kana duba Nihla" 🤣

Nihla ta kalleshi tasaka daria, shima Kallanta yayi yadauke kansa, amma baiyi mata ko murmushi ba

Suna zuwa kofar gidansu Nihla tasake saka daria, Abba yajuyo ya kalleta, su kuwa su Momy da Diddi rabuwa sukai dasu suka shige gida
Yace "me kikewa daria?"

Saida tasake yimasa daria sannan ta kwaikwayi maganarsa tace "Momy nasha wahala bazan sake dawowa garin nanba"

Haushi tabashi sosai,beyi wata wataba yasa hannu ya tureta tafadi aqasa

Da gudu ya qaraso wajan, tun daga nesa yake kallansu, shima yana qaraso wa yasa hannu yabige Abba yace "me tayima zaka bigeta?"

Cikin bacin rai Abba yace "menene ya shafeka? Qanwarkace ko qanwata?"

"bansaniba, amma idan kasake tureta, saina rama mata" yana fadar haka ya tsugunnawa yadaga Nihla tatashi tsaye

Cikin fishi Abba yasa hannu ya fizge hannunta yace "cika mata hannu!"

Shima dayan cikin tsawa yace "bazan cika ba!"

Lokaci daya ransa yaqara baci, ya kalli Nihla batare dayace mata komaiba ya shige gida

Itama dayan ta kalla tace "yusif..."

Kafin taqarasa maganar da zatayi yace "karkiyi kuka, idan yadakeki ki fadamin Zan rama miki kinji?"

Daga masa kai tayi, sannan tashige gida

Tana shiga taga Diddi tana ha'bo, Abba yana zuba mata ruwa abuta, bata wani damuba saboda tasaba ganinta ta nayi, rana d'ai'dai ne Diddi bazatai ha'bo ba, Dan haka hauka irinna yarinta dakuma gani yauda kullum yasa bata damu sosai ba, wajan Momy ta nufa tafada jikinta tace "Antyyy" 🤣Girgiza kai Momy tayi, har cikin ranta bataso antyn nan da Nihla take fada, sotake tadinga kiranta Momy Kamar yanda sauran yaranta suke fada, har zatayi mata magana saita fasa

Diddi nagama wanke fuskarta suka dawo tabarma suka zauna, Abba yace "Sannu Diddi, idan na girma Zan kaiki asbiti"

Daria Momy tayi, "wannan girma wannan girma, zamu gani dai, ga umara ga hajji, yau kuma anqara da asbiti 🤣"

Diddi na goge fuskarta da gefen zaninta tace "kuma insha Allahu duk saiya cikasu"

Momy tayi daria tace "muma haka mukeso aisha, wai dama har yanzu kina wannan ha'bon naki? Aisha yakamata kije asibiti fa kiga Babban likita akan haka, kina zubar da jini dayawa"

Murmushi Diddi tayi "Anty Rahma kenan, to Tun muna yara mukeyi nida yaya, saide ni nafishi yi, kuma Tun umman mu tanada rai muke zuwa asibiti, maganin dai dayane ake bamu, kuma anan ma inashan irinsa, amma bandainaba, shiyasa nake yanka albasa ina shaqar qamshin nata, shima yana maganin ha'bo sosai"

Farouq najin haka yace "to Diddi bari na yanka miki yanzu ma, yatashi yadauki wuqa yanufi wajan da take ajiye albasa"

Nihla ta kwaikwayi Abba tace "Sannu Diddi" 🤣

Kallanta yayi yasakar mata harara, yadauke kansa, Momy tana kallansa, cikin ranta tace to da alama sunyi fada 😃
Saita kalli Diddi tace "to Allah yasawaqe aisha, amma Zan sake yiwa yayanki maganar gaskiya,abin yayi yawa"

Babu musu Diddi tace to, Dan itama abin yana damunta, wani lokacin tana bacci zataji jini yana futowa daga hancin ta

Har dare, Abba Yaqi kula Nihla, da niyya take tsokanar sa amma saiya shareta, idan ya tuna abinda yafaru dazu a kofar gida shida wannan gayan sai yaji haushi ya kamashi 🙊
Shiyasa itama yarabu da ita, da daddare ma ko kallan Inda take baiyiba, ita kuwa bata fasa tsokanar saba, har sukayi bacci

Washe gari da yamma sunata shirin tafiya, Nihla duk tayi shiru bataso sutafi, har direba yazo yagama zuba musu komai nasu amota, kowa yayi wanka ya shirya, dukansu qananun kaya suka saka

Momy ta kalli Diddi, "to Aisha zamu tafi"

"to Anty Rahma Allah yakaiku lafiya, idan kinje ki gaida kowa,"

Momy tace "to yayanki fa?"

Daria Diddi tayi, "harda shi Anty Rahma, ki qara yimasa godia, ki gaishe shi sosai"

Tace "to zaiji, yanzu Aisha Allah bazaki bani Nihla ba?"

"Anty Rahma rigima, sokike na zauna nikadai agidan de" 🤣

Momy da taga alamar Aisha bazata iya rabuwa da Nihla ba, sai tayi shiru kawai, suka futo, har kofar gida suka rakosu itada Nihla, suka tsaya daga bakin kofa suna kallansu
Yaran kowa yashiga Mota, Nihla tanata kallan Abba, shima ita yake kallo, lokaci daya idonta yayi rau-rau, tasaka kuka tace "Diddi zasu tafi"

Hannu Diddi tasa tashare mata hawaye, jikin Abba ne yayi sanyi, Dasauri yabude motar yafuto, duk 'yan uwansa suna kallansa, har gaban Diddi yaje, ya tsugunna agaban Nihla yace" kiyi shiru, kefa qawata ce, You're my friend "

Kallansa tayi ta daga masa kai alamun to
Saida ya kalli Diddi, sanan yamatso da fuskarsa daidai tata, yasakar mata kiss akumatu

Zaro ido 😳Nihla tayi tana kallonshi, kafin tayi magana yajuya ya shige motarsu da gudu
Qamewa Diddi tayi a tsaye, Abba datake ganinsa shiru shiru shine yayiwa Nihla haka? 🤔
Momy kuwa murmushi tayi, tace "Allah ya kyauta" 🤣
Sannan tayiwa direba umarni yaja motar sutafi


Cikin gida Diddi tajuya tashige, tana tunanin wani abu aranta
Nihla kuwa qin shiga gidan tayi, tazauna akofar gidansu tana wasa, Kamar daga sama taji maganarsa "Nihla, mekike yi anan kinyi shiru?"

Kallansa tayi, lokaci daya tasaki murmushi, "yayunane suka tafi, nikuma banaso sutafi "

"haba? Yaushe suka tafi? Kinsan garin da suka tafi?"

Girgiza kai tayi, "nima bansan garin su ba"

Hannunta yariqe yace "zomuje gidanmu muyi wasa"

Gidan dayake kallan nasu gidan ta kalla, hadaddan gida ne daya gama haduwa, harda beni, tace "to Muje"

Janta yayi suka shige cikin gidan, har falonsu suka shiga Nihla sai kalle kalle take, mamansa tana zaune tana kallo, falon ya tsaru iya tsaruwa
Kamannin Ibrahim Mai hakuri da tagani a fuskar yarinyar hakan ya tabbatar mata da cewa yarinyar Diddi ce

Wajan ta suka qarasa yace"Ummah kinga qawata, sunanta Nihla, Acan gidan take naje na kirata zamuyi wasa "

Murmushi tayi, tashafa kan Nihla tace" a a masha Allah yanmata, to kuje kuyi wasan, banda fada kunji ko "

Dakinsa yakai ta, nan taga kayaiyakin wasa iri iri, nan take suka fara wasansu, yana koya mata abinda bata iyaba

❣️❣️❣️   ❣️❣️❣️

Har bayan sallar isha'i Nihla bata dawo gidaba, Diddi tayi neman ta harta gaji, haka ta tsaya akofar gida tana Tambayar duk Wanda taga yazo wucewa ko yaga Nihla, amma Babu Wanda yace yaganta

Umman yusif tazo rufe window tana daga saman beni, hango Diddi a tsaye akofar gida
Saukowa tayi tafuto wajan ta sameta, Diddi tace "a a Hajiya, ina gajiya,"

Tace "lafiya kalau, da alama de Nihla kike nema"

Dasauri Diddi tace"wallahi ita nake nema hajiya, Tun yamma ban ganta ba, "

Murmushi tayi tace" ai tana gidana, sunata wasa da yusif Yarona, yanzu kam nayi musu shimfida ma sunyi bacci "

" to bari naje nadauko ta hajiya, kar babanta yadawo begantaba "

" haba Diddin, ki barta mana, dasafe sai akawo ta "

Murmushi Diddi tayi, cikin ranta tace nagode Allah, kowa yana qaunar 'yata, afili tace" Hajiya ai wataran zata kwana, ina Ruwan yara "🤣

Badan tasoba, suka shiga gidan, Diddi tanata yaba haduwar gidan, Dan bashiga takeba, amma gashi yau wannan yarinya takawo ta

Baccinsu suke hankali kwance, ga esi nan yana sanyaya musu jiki, haka Diddi tasa hannu tadauketa, suka tafi gida, tanata yiwa Maman yusif din godia






(idan naga ana Comments Zan qara yawan page d'in)

WhatsApp readers, ina qara godia sosai yanda kuka bani hadin kai, kuka bani lokacin ku wajan karatu da kuma sharhi, ana mugun tare🤪










Amnah El Yaqoub ✍️
[6/15, 2:27 PM] El Yaqoub: ❣️DANGI 'DAYA❣️

{Romance & Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub


Like my page On facebook

https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493


7&8


Zaune suke acikin Babban falonsa dayake tarbar baqi, Babban falo ne daya hada komai da Komai najin dadin rayuwa, tsaki yasaki yakalli Agogon hannunsa fuskarsa Babu alamun wasa yace "me Basiru yakeyi ne har yanzu baizoba, bayan Tun jiya nasanar dashi da kaina cewa akwai meeting karfe tara nasafe"

Kafin sauran biyun su bashi amsa aka turo kofar falon aka shigo, kana ganinsa kaga cikakken magidanci, fuskarsa adaure yadubeshi "mekake yi bakazo a lokacin dana sanar dakai ba?"

Yace "yaya Abubakar ai lokacin yayi, gani kuma nazo akan lokaci" 🤣

Kai tsaye yace dashi "duba agogo karfe nawa?"

Kallan Agogon dakin yayi "goma da rabi"

Fuskarsa adaure yace "kuma karfe nawa nace kazo?"

"karfe tara kace, aini to inajin agogo nane yasamu matsala, karfe tara ya nunamin wallahi, inajin matsala yasamu, duba kagani" ya qarasa maganar yana nuna masa hannunsa

Harara ya watsa masa yace "lusari, Wanda mace tagama shanye shi"

Shiru falon yasakeyi, ba qaramin girma suke bawa Babban yayan nasuba, hakan yasa Wanda aka kira da lusari baice komai ba, yanemi waje Yazauna

Gyaran murya yayi yace "munyi magana da hajiya dangane da wani abu Mai girma Wanda ni kaina bansan menene ba,...." nan take ya sanar dasu yanda sukai, sannan yaqara cewa "nasanar daku ne saboda nima korai zaiyi halin sa,"

Hajiya Farida datake zaune, wadda ita kadai ce mace acikinsu tace "Amma yaya Abubakar meyasa ba'a fadawa Aisha ba? Itama fa tanada 'ya, kuma  'yarta tana daya daga cikin wannan family, Kamar yanda Iyayenmu suka bada wasiyyar dabamusan kota mecece ba akan yaranmu, ai yakamata ace tasani"

Kallanta yayi fuskarsa adaure "da Aisha da abin data haifa duk suna qarqashin iko nane,"

Jinjina kanta tayi, sannan tasake cewa "to amma yaya ai yakamata ace munjata ajikin mu, Kamar yanda aka fadawa yaya Basiru itama..."

Kafin ta qarasa magana yadaga mata hannu tareda fadin "Farida!!!"

Lokaci d'aya ta nutsu Kamar ba itace take zuba surutu ba, kallansu yayi yace "daga yanzu kuma daga rana irinta yau, doka zata fara," yana fada musu haka yatashi yafice, yabar kowa da tarin tambayoyi, Alhaji Baqir yatashi yana gyara Babbar rigar jikinsa yace "koma menene bazai wuce maganar rabon gado ba, ni wannan bata gabana," shima yafice daga falon 🤣

Hajiya Farida ta kalli Agogon hannun Basiru dayake zaune kusada ita batare daya saniba, taga karfe tara da kwata, ta kalli Agogon dake manne afalon taga goma da arba'in da biyar, tasaki daria tasan sarai aikin matar sa ne wannan, wadda ya Auro musu ita tazame musu baragurbi acikin family, Kallanta yayi "me kikewa dariya?"

Tace "yaya Basiru Babu komai, nina wuce gida sai anjima" 🤣

Daganan shima yatashi yadoru a bayanta yana darurar sanar da matar sa abinda yaya Abubakar yace

❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Labarinsu

Mazawaje family Babban family ne dayake da tarin mutane dayawa, Abubakar shine jigo na wannan family yanada mata biyu Hauwa'u dakuma Fatima

Hajiya fatima itace babba, tanada yara biyu, Babban danta shine Yaci sunan babansa Wato Abubakar, sai qanwarsa Aisha, sun taso sunasan junansu sosai da sasai

Sai Hajiya Hauwa'u, wadda suke kira da hajiya sak, tana da yara uku, Baqir shine Babban danta, sai Basiru da kuma qaramar su Farida

Abubakar yayi aure ya auri daya daga cikin family dinsa na uwa, maisuna Rahma, suna zaune lafiya saide murdaddan halin sa datake hakuri dashi wani lokacin, sunada yara hudu, Usman shine babba, sai Aliyu,Sai farouq, Sannan Abubakar Wanda yaci sunan kakansa suna kiransa da Abba,

Alhaji Baqir kuwa yaransa biyu, Aslam da kuma Adam

Sai Alhaji Basiru, yanada yara uku, Fawaz shine dansa na farko, bayajin magana kokadan, ga kula abokan banza, sai Aisha qanwarsa wadda aka saka mata sunan Diddi, tanada hankali da nutsuwa, sannan ta fannin kamanni suna kamada Nihla sosai Kamar yan gida daya, sai qaramar Ilham, ita kuma ilham rashin kunya, kowa yasan batada kunya yarinyar

Sai hajiya Farida Mai yara biyu Dida, dakuma Diyana

Qa'idar familyn nasu shine tunda suke Babu wani Wanda yake auren bare, saide ka nema a family ka aura, kowa yabi wannan dokar, kwatsam sai Alhaji Basiru yagano wata wadda bata cikin family yace ita yakeso zai aura, adede lokacin itama Aisha Wato Diddi tace tanada saurayi wani bafulatanin yalleman dake jihar jigawa, tace shi takeso, al'amarin yakawo rigima sosai a tsakanin wannan family, har hakan ya haifar musu da rabuwar kai, wasu suna ganin aiba laifi bane hakan tunda ba haramun bane, wasu kuwa suna ganin cewa bedace ba, tunda dokace ta family, cikin su kuwa harda Abubakar, saida aka kai ruwa rana sannan aka rabu dasu sukai auren, da sharadin duk abinda yabiyo baya su sukaja amma kada su nemi kowa
Babu Wanda yakai Abubakar bacin rai akan hakan, ganin idon qanwarsa Yarufe akan soyaiya, hakanne yasa ya tattara ta yawatsar, yadena shiga cikin al'amarin ta, amma cikin qasan ransa yana qaunar qanwarsa, ita kuma matar Basiru hajiya Abida tunda tashigo family din taga basa sonta saita shanye mijin nata da kissa iri iri, idan tasa doka bai isa ya qetare ba, haka kawai kuma Allah yadora mata kaunar Diddi aranta, tana son Aisha sosai, shiyasa tana haifar yarta qanwar fawaz tace Aisha za'a sakawa yarinyar, babu musu mijin nata yayarda🤣

Aisha Wato Diddi tana zaune lafiya da mijinta Mai Suna Ibrahim, amma ana kiransa da Mai hakuri kasancewar mutum ne shi Mai mugun hakuri, dukda halin rashin dayake dashi bata taba nuna masa ba, haihuwar ta ta farko tahaifi mace Mai kama da babanta sak, suka sakawa yarinyar suna fatima, Wato sunan kakarta, amma suna kiranta da Nihla (kyauta)

Wannan shine labarin Mazawaje family


❣️❣️❣️   ❣️❣️❣️

"Diddi tunda su yaya Abba suka tafi ko, kullum sai nayi mafarkin su"

Dasauri ta kalli yarta ta taga hankalinta yana kan wasa ma Kamar ba itace tayi magana ba, "suwa kike mafarki Nihla?"

Kallanta tayi cikeda qosawa tace "Diddi nace miki su yaya Abba, nayi mafarki shima munata wasa dashi"

Diddi tace "shi Abban ne ya koma yaya Abba?"

"eh Diddi, ai shine yace nadena cemasa Abba, saide yaya Abba"

Diddi ta Jinjina kanta tace "to suma sauran ai yayunki ne, dukansu haka zaki dinga fada musu"

Tace "to Diddi, yaushe zamuje wajansu?"

Daria Diddi tayi tace "kinason zuwa wajansu ne?"

"eh inaso naje, wai a wanne garin suke Diddi?"

"Suna kano, Nihla, kibari idan akai muku hutu saina kaiki, kiga qawayenki su Aisha, da ilham, da Dida, su Diyana"

"Diddi duk agidan suke suma?"

Diddi tace "duk suna gidan Nihla, idan mukaje zaki gani, gidane babba sosai, kowa aciki yake, amma kowa yana part dinsa, kuma akwai nisa atsakani, amma duk gidanmu daya dasu"

Cikin murna tace "to yaushe zamu tafi Diddi?"

Cikin sauri qosawa da maganar ta tace "nace miki idan anyi muku hutu"

Tace "to Diddi"

❣️❣️❣️   ❣️❣️❣️

Haka Rayuwar taci gaba da tafiya, yara naqara girma, kuma har zuwa wannan lokacin Diddi bataje gidaba, kuma bata taba kai Nihla cikin yan'uwanta sun gantaba, kullum tayi mata maganar Abba saita shashantar da zancen

Zuwa wannan lokacin Abba yayi candy, Har Alhaji Abubakar yafitar dasu qasar Germany karatu shida Aslam, Dan gidan Alhaji Baqir, tunda yalura hankalin yaron ya karkata akan jirgi 🤣, shiyasa yadage yanaso yacika wa dansa burinsa na ganin yazama cikakken pilot

Yayinda Aslam hankalinsa yafi karkata kan harkar kasuwanci

Bayan shekara biyu Allah yayiwa hajiya rasuwa, mutuwar tataba kowa, wannan family sun shiga damuwa sosai, kowa kaga fuskarsa zaka ganshi dauke da damuwa, Su Abba sunso suzo, amma Alhaji Baqir mahaifin Aslam yahanasu zuwa, yace kawai suyi mata addu'ah, Momy ce takira Diddi tafada mata, a lokacin Nihla tana makaranta, bata jira dawowar ta ba tatafi, shikuma Ibrahim Mai hakuri yace bazai iyu su tafi dukansu subar Nihla ba, idan tadawo ranar uku shi sai yaje

Kowa yaganta a family din yasan ta rame, shi kansa yayan nata daya ganta, saida jikinsa yayi sanyi, gaba daya ta sauya Kamar ba itaba

Bayan angama sutura suka koma part din su Momy, anan takejin labarin tafiyar Abba da Aslam karatu germany, duk yaran gidan sunzo sun gaishe ta, Aisha ce kawai bata ganiba, anan Momy take fada mata cewa tana India tana karatu agidan wani abokin Alhaji, saboda ita tadage bazatai karatu anan ba 🤣

Murmushi kawai Diddi tayi, tace "Allah ya kyauta," suna wannan firar Alhaji yashigo, shima zama yayi, Diddi tasake gaida shi, a mamakinta saitaga ya amsa mata cikin sakin fuska, yana murmushi yace "meyasa baki Taho da mamana ba, Tun tana qarama ban sake ganinta ba"

Diddi tace "Nihla tana makaranta yaya, yanzu ma batasan nataho ba, ashe su Abba suntafi germany"

"wallahi su Abba suntafi, shekarar su biyu kenan, sunaso suzo gida ma nahanasu, nace su bari sai sun gama komai tukunna, aide kuna zaune lafiya ko?"

Mamaki yagama kashe Diddi, tace "yaya lafiya kalau,"

"to alhmdlh, idan kin koma sai kiyi harama hajjin bana dake za'a tafi insha Allah, daga nan sai Rahma tarakaki Dubai kisiyo kayaiyaki kifara business ko"

Saboda murna Diddi harda kukan ta, takasa cewa komai, ahankali shima yatashi ya shige ciki, yanaji kukan ta yana taba ransa, to yaya zaiyi tunda auren de bazata rabu dashi ba, gashi harda Rabon yarinya a tsakani, gara yayi hakuri yaja qanwarsa jikinsa


❣️❣️❣️   ❣️❣️❣️


After 8 year's

Da gudu tashigo gidansu cikin murna tace "Diddiyyy"
Sannan tafada jikinta ta rungumeta

"Nihla ke kadai ma zaki karyani kihuta"

"to Diddi ai ina murna ne, kinga result din nawa"

Karba Diddi tayi cikeda murna tace "a a masha Allah, Allah yamiki albarka Nihla, Allah ya albarkaci ilminki, neco tayi kyau waec tayi kyau, saura jamb insha Allah"

Fari tayi da idonta tace"Diddi, wannan karan da kinaso, da bakyaso Diddi sainaje kano, inaso naga su Anty "

" A a Nihla kede kice kinaso kiga Abba, to ai Abban bai dawoba, saide kije kiga su Antyn Kamar yanda kika min qarya daga farko "🤣

Ajiyar zuciya tasauke, ta cire dogon hijabin jikinta, kanta Babu dankwali qananun kalbar da akayi mata tazubo agadon bayanta, ta zubawa waje daya ido tana kallo batare data cewa Diddi komai ba

Kallanta Diddin tayi cikin murmushi" to yanmatan Diddi, me kuma ake tunani? "

" Diddi, Yaya Abba yana germany har yanzu bai dawoba, Yaya yusif yatafi china shima Yaqi yadawo, duk qawayena basa nan, basusan nayi Candy ba, dama suna nan Diddi, shi yaya Yusif naje umma tabani number sa amma kullum na kirashi bata shiga, saura yaya Abba Dan Allah Diddi kicewa Anty taturo miki number sa na kirashi "

Diddi tace" a a babu ruwana, keda kikace zakije kanon da kanki? Idan kinje sai Antyn tabaki "

" shikkenan Diddi, idan naje Zan dauki wayarta da kaina na dauki number sa na kirashi "

Diddi tace" keni kin dameni da zancen wannan mutanan naki 😂, tashi kije kisiyomin maganin zazzabi, zazzabi nakeji "

"to Diddi"
Kudin tadauka agefenta tafice daga gidan

Gidansu Nihla kenan, Diddi ta manyan ta, bakinta manne da haqorin makkah, Nihla taqara girma, kyanta yana nan sai abinda yaqaru, tazama budurwa, idan ka kalleta saika sake kallonta, surutun ta yana nan yanda yake

Maganin takawo mata tasha, da yamma tagyara gidan tsaf, tayi wanka ta shirya cikin riga da siket, hips dinta yafuto acikinsu siket din sosai, 'yan madedetan breast dinta ma haka, dukda basu cika girma sosai ba, amma kana kallansu zaka tabbatar a tsaye suke sosai

Kusada Diddi tadawo tazauna tace "Diddi ko zazzabin ne? Naga kinyi shiru kina tunani"

Ajiyar zuciya tasauke tace "tashi kidaukomin wayata inkira yaya na,"

Saida tayi daria sannan tadauko mata wayar tana cewa "hajiya Diddi kinaji da wannan yayan naki,kuma ni Diddi banga alamun ma yanada Fara'ah ba wallahi"

"zakici ubanki Nihla, yayan nawa kike fadawa haka?"

Shiru Nihla tayi tana daria, Diddi takira yayan nata, bugu yadauka "Aisha kina lafiya ko"

"lafiya kalau yaya, Ya wajansu Abba kuwa? Sai yaushe zasu dawo ne yaya?"

Cikin mamaki yace "Abba sun kusa dawowa, amma Lafiya Aisha?"

"lafiya kalau yaya, kawai na matsu yadawo ne naganshi,"

Saida yayi Murmushi Wanda saika dade kafin ka ganshi yayi sannan yace "Zai dawo insha Allah, idan zai dawo ai zanturo driver yazo yadauke ki insha Allah"

"to yaya Allah yakaimu, Tokai yaushe zakazo yaya?"

Cikin mamaki yace "Aisha wai kalau kike kuwa?"

Saida tayi Murmushi tace "yaya lafiya ta kalau fa, kawai inaso naganka ne"

Jikinsa ne yayi sanyi, me yarinyar nan take nufi ne? Anya kalau take kuwa? Haka yake ta fada cikin ransa afili sai yace mata "inde nine Zan shirya gobe nazo kiganni Aisha, shikkenan?"

"eh yaya shikkenan, ka gaida Anty Rahma, ga Nihla ma tana gaishe ka,"

Yace "toki shafa min kanta" sannan ya kashe wayar, Diddi kuwa maganarsa dariya tabata, wai ashafa masa kanta Kamar wata 'yar yarinya

Da magrib baba yadawo daga kasuwa, suna zaune sunata fira, zazzabin datake ji ma Babu yatafi, sallama akayi akofar gidan, baba yace su shigo, samari ne guda uku suka shigo da kaya niqi-niqi ahannu, kwalin taliya da macaroni sai doya Mai yawa, sukace Alhaji isma'eeil mahaifin Yusif ne yace akawo musu yayi zakkah ne

Godia sukayi musu, baba yanata yabon kirkin mutumin, duk unguwar kowa yana yana yabonsa

Har dare yayi suna zaune suna fira, sannan sukaje suka kwanta, Diddi yau a dakin Nihla ta kwanta, Nihla ta dade dayin bacci, ahankali Diddi ta matsa kusada ita ta rungumeta a jikinta, sannan tayi musu addu'ah itama ta kwanta

Da asuba Nihla ce tafara tashi, kallan Diddi tayi agefenta tace "Diddi asuba tayi"

Bata jira amsarta ba tatashi taje tayi alwala tazo tatada sallah, harta idar Diddi bata tashi ba
Addu'ah tashafa, takama kafarta tace "Diddi asubafa tayi"
Taji shiru, hijabin jikinta ta cire tace "a a Diddi lafiya kuwa?"

Takoma kanta tana tashin ta, amma Diddi ko motsi batayi ba, gabanta ne yayi muguwar faduwa, tafara ja da baya Ahankali, harta futo tsakar gidansu, adede lokacin baba yadawo daga masallaci hannunsa dauke da carbi yanaja

Cikin tashin hankali tafara nuna masa d'akin da hannun ta, tace "Baba Diddi!"

Yace "Diddi kuma? Me yasameta? Ko zazzabin ne?"

Bata iya bashi amsaba, duk jikinta rawa yake kawai tana nuna masa dakin da hannu, Dasauri yashiga, itama ta doru abayansa
Yana zuwa yasa hannu ya tallafo Diddi jikinsa yace

 "Aisha!"

Yaji shiru, gabansa ne yafadi yaduddubata, lokaci daya jikinsa yayi sanyi baisan lokacin daya zauna ba

"Innalillahi wa inna ilaihir raju'un, Innalillahi wa inna ilaihir raju'un, Aisha, haba Aisha, meyasa zaki tafi kibamu, me.. Yas..sa Aisha" ya qarasa maganar yana kuka wiwi, sake rungumeta yayi yana fadin "Innalillahi wa inna ilaihir raju'un, yanzu Aisha dama tafiya zakiyi kibarmu?"

Cikeda tashin hankali tafara girgiza kanta "A a baba, Diddi bata mutuba, lafiya fa muka kwanta, baba Diddi na bata mutu ba kadena cewa tamutu baba"

Cikin kuka Kamar ba babanta ba yadago kansa ya kalleta yace "Nihla Aisha tamutu, Aisha tatafi ta barmu"😭



(sannu sannu bata hana zuwa saide adade ba'a jeba, dafatan kun gane)







Amnah El Yaqoub ✍️
[6/16, 11:52 PM] El Yaqoub: ❣️ DANGI 'DAYA❣️

{Romance & Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub


Like my page On facebook 👇🏻
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493/

9&10


Kuka take sosai Kamar ranta zai fita, wai gawar Diddi ce a gabanta Akwance haka, akan idonta makotansu da wasu daga cikin yan'uwan babanta sukayi mata wanka, bata taba tunanin zataci gaba da rayuwa batare da Diddi ba, babu me iya bata hakuri saboda kowa yasan yanda tashaqu da mahaifiyarta, gara abarta tayi kukan ko zataji sassauci

Dole saida aka jinkirta jana'izarta har saida yan kano suka qaraso, dirin motar da sukaji ne ya tabbatar musu da cewa sun qaraso, gaba dayansu sunzo yara da manya, Momy tana kuka tashigo gidan, duk hankalin mutane ya koma kanta, cikin dakin tashige, tana ganin Diddi Akwance anrufeta da farin mayafi tasake sakin kuka tana cewa "Innalillahi wa inna ilaihir raju'un, Allah yaji qanki Aisha"
Nihla ta kalla datake zaune agefe idonta ya kumbura gashi sunyi jajir, Dasauri ta rungumeta, tana bubbuga bayanta "Nihla kidena kuka kinji, kidena kuka bakiyi rashin uwaba, kina damu kinji yata, kidena kuka"

Duk dakin saida suka sakasu kuka, Alhaji ne yashigo Wato yayan Diddi taredasu Alhaji Baqir gaba dayansu, tsugunnawa yayi agaban gawar, yasaka hannu yabude fuskarta, duk jajircewa irinta Alhaji, saida yayi kuka, yasaka dayan hannunsa Yarufe fuskarsa yana kuka sosai, yakasa magana, yadade yana tsugunne a gabanta, Alhaji Baqir da Alhaji Basiru suka jashi, suka fita dashi, sannan sukayi mata addu'ah, aka qarasa shirya ta, ana daukanta za'a fita da ita waje domin sallah Nihla tasaka kuka ta qanqame Momy tace "Anty zasu tafi da ita"

Kasa magana Momy tayi,domin itama wani irin d'aci takeji aranta

Babu yanda suka iya, haka aka sallaci Diddi aka kaita gidanta na gaskiya, saide muce idan tamu tazo Allah yasa mucika da imani

Ranar da akai sadakar uku data bakwai, da yamma lis yan kano sukai shirin tafiya gida, Momy tana zaune da carbi ahannun ta, wayarta ce tayi qara, wayar tana ajiye kusada Nihla, daukar wayar tayi taga ansa Daddyn Abba hakan ya tabbatar da cewa yayan Diddi ne yake kira, meqa mata wayar tayi tace "Anty Daddy yana kiranki"

Karbar wayar Momy tayi, Cikin ranta tace Daddy.., taji dadin yanda Nihla tace Daddy, amma ita Anty 🤦🏻‍♀️, batasan meyasa Nihla take kiranta da Anty ba, kokuma har yanzu bata bata matsayin uwa bane a gareta?

Kawar da tunanin tayi aranta tadauki wayar "ki dauko Nihla kufuto mutafi"

Abinda yace da ita kenan, tace "to" tareda kashe wayar, farin ciki yakamata, ta kalli Nihla tace "Nihla tashi ki sauya hijabi mutafi, tare dake zamu wuce"

Batayi tunanin komai ba ta shiga daki ta sauya hijabin jikinta, sannan tadauki wasu kayan acikin jaka sukayi sallama da sauran yan'uwan babanta suka futo

Motoci  uku suna jere akofar gidan, suka nufi daya daga ciki, hannunta yana cikin na Momy, Daddy yatashi yayiwa sauran mutanan wajan sallama, amma kokadan baiyiwa Baba magana akan Nihla ba, kawai de yace musu su suntafi, baba yakasa magana, yayi shiru yana kallansu har suka shiga Mota, akan idonsa aka tafi da Nihla, amma bai nuna komai ko akan fuskarsa ba


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Sai dare suka qarasa kano, agate din gidan sukai Parking gaba dayan motocin, zubawa gate din ido tayi, shi kadai ma abin kallone
Ana bude musu gate suka shiga gidan
Anan taga Inda duniya take, Kamar gidan turawa,part hudu ne manya manya agidan, saide akwai nisa sosai a tsakanin kowanne parta, ga kuma Parking space dayake cikeda manyan motoci

Futowa sukai daga motar, kowa yanufi hanyar part dinsa, Alhaji Basiru yace "Nihla sai gobe yan'uwan ki zasuzo ki gansu kinji?"

Daga masa kai kawai tayi, Momy taja hannunta suka nufi nasu part din, suna shiga taga falon yahadu, komai ya tsaru yanda yakamata

Zama sukai dukansu afalon,Usman ya kalleta yanaso yaja hankalinta tadan sake tadena tunani yace "to yar'qauye tazo birni sai kalle kalle take, Momy wannan yarinyar fa sakina rufe mata ido wani lokacin" 🤣

Murmushi Momy tayi "eh lalle Usman bakason auren naga alama, karfa kazo kana kuka nabaka ita"

Daria sukasa gaba dayansu harda Nihla, Aliyu yace "haba Momy, kirasa wazaki bawa sai yaya Usman? Ai yayi mana tsufa Momy"

Dasauri farouq yace "eh dama ai kasan Nihla tawace, ni Momy zata bawa ko Momy?" ya qarasa maganar yana kallan Momy

Tace "duk ba Wanda Zan bawa, ni mijin yata saiya kasance Mai tsananin sonta kunji ko, bazan badata a araha ba"

Alhaji ne yashigo dauke da sallama, dukansu lokaci daya suka nutsu, yakalli Momy yace "Hajiya nina shiga daki, akula da wannan yarinyar"

Saida Momy tayi Murmushi sannan tace "to Alhaji"

Farouq yace"momy nizan wuce gida, nagaji sosai "

Aliyu yace" yes amarya tana jira "

Daria yayi yace" bakada dama yaya Aliyu, "yakalli Nihla yace" my Sister Zan gudu gida, kinsan momynki ta dade da bawa wata ni, idan kin gama hutawa sosai agidan, ki dauki wayar Momy kisaka number ta, ki kirani Muje nakaiki yawo kiga gari, sannan muyi shopping kinji ko? "

Saida tayi Murmushi Mai kyau dimple dinta suka futo sannan tace" to yaya farouq "
Usman yace" eh lalle farouq da alama wani zaiyi kishi dakai idan yadawo "🤣

Nihla bata fahimci komai ba akan maganar Usman, Momy de ta fahimta Dan haka tayi Murmushi

Aliyu ma yayi daria yace" saide ayi Yaqi, ba zamu qi kyautatawa yar qanwar mu ba, "
Yamaida kallansa ga Nihla yace" Nihla  kina jina ko?, nima idan kin gama hutawa ki kirani nazo da kaina nadauke ki Muje wajan telan mata ta yayi dinki masu kyau "

Usman yace" to nikam Babu ruwana, zanyi rabiya a tsakani, kada naje nashiga ciki wataran Pilot Yaqi ragemin hanya zuwa Saudia "🤣

Momy tace" Usman baka isaba, bawani rabiya da zakayi, nagane ka, Wato wayo ko? "
Yace  " Momy kinsan de halin mutumin naki ko,?amma shikkenan nima idan tagama hutawa zanzo gidan sai abinda tace tanaso da kanta insha Allah "

Momy tace" eh naji "

Daga nan sukai musu sallama kowa yatafi gidansa, Momy tana qara jin dadin yanda kan yaranta yahadu sosai, kuma tasan ba komai yasa sukewa Nihla wannan wasan ba sai don tasake dasu ne ta kuma kwantar da hankalin ta.

Kallan Momy tayi tace" Anty wai duk sunyi aure ne? "

" sunyi aure Nihla, ni kadai ce agidan yanzu, saikuma ke dakika dawo, shi Abba yadade da gama karatu harma yafara aiki, shida Aslam, basu saka ranar dawowa bane, yanzu haka Alhaji yahana afada musu wannan mutuwar amma da yanzu kin ganshi "

Tace" to Anty Allah yabasu zaman lafiya "

" Amin Nihla, tashi Muje kiyi wanka kici abinci saiki kwanta ko? "

Babu musu tatashi, kai tsaye dakin Momy suka tafi, tayi wanka sannan taci abinci, Momy tasa ta ta kwanta, ta qara mata karfin esi sannan takashe mata wutar dakin tafita zuwa wajan Daddy


❣️❣️❣️   ❣️❣️❣️

Washe gari daqyar tasamu taci abinci, idan tatuna Diddi saitaji wani irin abu yatokare mata maqoshi, daqyar taci kadan ahakan ma saboda Momy ta tsareta ne

Cikin murna  tashigo part din nasu da gudu tana kwalawa Momy kira "Momy! Momy!! Momy!!!"

Cikin sauri Momy ta kalli wadda tashigo part din nasu, kafin tayi mata magana  yarinyar tace "Jiya Ummah tah tace Nihla tazo, Momy tana ina?"

Murmushi Momy tayi "ilham, Nihla tana dakina, jeki sameta"

Dasauri tashige dakin Momy, a lokacin Nihla tana kwance tana tunanin Diddi, sai jin mutum tayi a jikinta, Dasauri ta kalli wadda tashigo din, kyakykyawa ce sosai wadda ake kira da choculate beauty, ahankali tatashi zaune tana cewa "wash Allah, zaki karyani"

Cikin murna dayar tace "to murna nake ance kinzo, duk bamu sanki ba, kema baki sanmu ba, nide sunana ilham, dama ummah na tana cewa kina kama da yayata Aisha, me sunan Diddi, kuma yau nagani, wallahi kina kama sosai da ita"

Murmushi Nihla tayi "dama kece ilham? Ai duk Diddi tana bani labarin ku, ina Aishan take?"

"tana India, amma ta kusa dawowa, meyasa kika zauna a daki ke kadai bakya tsoron kiyi tunani?,"

Ajiyar zuciya tasaki "nayi karatu ne kuma nagaji, shine nake Dan hutawa, ya karatu?"

Fari ilham tayi da idonta "ai nayi candy, ke dukanmu munyi candy, saide tagaba insha Allah"

"nima nayi candy har na karbi result dina,"

Kafin ilham tayi magana Momy tashigo dakin tace "Nihla tunda ga ilham tazo kuje ta tayaki ki gyara dakin naki ko?"

Ilham tace "eh wallahi zomuje"

Dakin dayaji furnitures da Komai launin green suka fara gyara wa, ilham tafara wanke mata toilet, sannan suka goge kayan dakin, tareda yin moppinga, Nihla tanata yabon halin ilham cikin ranta, babu ruwanta faram faram

Dasuka gama gyara wa zama sukai anan kowa tadau wayarta suka hau Xender suna tura abubuwa

Sallama sukayi suka shigo dakin susu biyu, kana ganin su kasan gidansu daya saboda kama dasuke da juna, daya tana sanye da riga da wando dasuka kamata sosai, gata da uban hips masha Allah,dayar kuwa norml kayane a jikinta, kana ganinta kasan silent ce, me riga da wandon ce ta d'akawa Ilham duka abaya
Sannan tazauna

Ilham tace "haba Diyana, irin wannan daukan ai saiki budamin qirjina"

Zama sukayi suma akan gadon, wadda aka kira da Diyana ta kalli Nihla "haba haba Nihla, wannan hijabin fa, Kamar bakyajin zafin duniyar nan? Kinci wani uban hijabi Kamar matar liman haba be wise mana"

Murmushi nihila tayi tana kallanta, yanda taci wannan riga da wando aidole tayi fada akan hijabi 🤣
Wadda batayi maganar ba tace "Nihla sannu da zuwa kinji, kirabu da Diyana, idan kina neman mace Mai shegen son maza to Diyana ce" 🙆🏻‍♀️

Kallanta Diyana tayi "to Dida idan banso maza ba mata zanso?🤣

Dida tace "kide rage wallahi, ai a yimaka shedar arziki ma abu ne Mai kyau"

Tashi tayi tsaye, batama kalli yar'uwar tata datayi mata magana ba, tace "Nihla, natafi, saina sake dawowa kokuma inkin shigo, ai zaki zo ko?"

Nihla tace "Zan shigo Diyana, nagode "

Ilham ta kalleta, "sai ina kenan?"

Kai tsaye batare da tantamaba tace "wallahi unguwa zamuje nida wani cika 🙆🏻‍♀️, yanaso zaiyi birthday zamuje mufara shirin komai, danya takura ne ma wallahi banso zuwaba"

Nihla ta kalleta cikeda mamaki anya kuwa Diyana kalau take? 🤔

Dida tace "ke dince zakice antakuraki? Keda yawo? To idan baki bishi ba ina zakije?"

Babu alamun damuwa tacewa qanwar tata "Dida nadade kema kinsan dadade banje nigh Club ba 😳, wallahi nan nakeso naje"

Wannan karan kam Nihla daria tasaka 🤣
Al'amarin Diyana akwai kallo, kuma duk maganar datake yi hankalin ta kwance, zuciyarta daya take magana

"Ilham tace" to saikin dawo, idan Nihla zatazo Zan rakota masha fira "

Tace musu  " ok"   sannan tafice

Dida ta kalli Nihla tace "haka take wallahi, Karki yi mamaki 🤣, mune yaran Anty Farida, itace babba ninake binta, kuma wallahi Mom dinmu tasani amma tazuba mata ido, tana zama idan ta tsarata shikkenan sai kiji shiru"

Murmushi Nihla tayi, tace "Diyana kenan" sannan sukaci gaba sa firarsu gwanin sha'awa

❣️❣️❣️   ❣️❣️❣️

Washe gari Ilham ce tasake dawowa taja Nihla zasuje ta nuna mata kowanne part na gidan, part dinsu suka fara zuwa
Hajiya Abida tana ganinta ta karbeta hannu bibiyu, tana tausayin yarinyar sosai, taso Aisha Wato Diddi, hakanne yasa ta sakawa yarta suna Aisha, kuma ganin Nihla tana kama da Aishanta saitaji dadi, sai nan nan take da ita, sun dade sannan suka futo
Ji tayi taci karo da mutum, Dasauri tadago kanta taganshi a tsaye abakin kofar part din shima zai shigo, dogo ne fari, saide bakinsa dayayi baqi, alamun yana shan wani abun🤔,yaraba gashin kansa biyu yasakawa Rabin colour Mai launin yallow, dayan gefen kuma yabarshi yanda yake, hatta Dan gemun daya tara irinna samari yan gayu shima yasaka masa kala,ga wani uban bluetooth daya toshe kunnuwansa dashi, da alama waqa yakeji, kana ganinsa kaga tantiri na gaske, ahankali tace masa "ina wuni?"

Yace "normal ne, Nihla ko?"

Tanajin irin Tambayar dayayi mata jikinta yayi sanyi, ahankali ta daga masa kai kawai

Yace "okey kihuta"
Yana fadar haka ya shige ciki 🤣

Ilham taja hannun ta suka futo ta kalleta sannan tace "wannan shine yaya fawaz, shine Babban yayanmu, dagashi sai Aisha saini, Tun suna yara yake kula abokan banza har suka koya masa shaye-shaye, babu irin qwayar da baya sha, Tun su ummah suna fada har sun gaji sunyi shiru

Nikuma kinga banaso naga abinda akeyi nayi shiru, kokuma ban shiga sabgarka ba ka shiga tawa, to Zan rama ne, shiyasa Tun muna qanana ake cewa nafi kowa rashin kunya.

Nihla tace "kai wannan gida kuna abinda kukeso wallahi" 🤣

Part dinsu Alhaji Baqir sukaje "hajiya na'ila ta amsa musu cikin sakin fuska, amma aboye hararar Ilham take, saboda yarinyar batayi mata ba kwata kwata 😎

Daga cikin dakin hajiyan yafuto da car key ahannun sa, yana sanye da manyan kaya riga da wando na wani yadi, ya kalli hajiyan yace" mama zanje school inada lacture da yamma "

Tace" to adam saika dawo "

Ilham tace" yaya adam ina wuni"

Sai lokacin yakula dasu, cikin farin ciki yace "a a Kamar Nihlan Diddi"

Daria sukayi, Nihla tace "nice wallahi"

"A a masha Allah, sannu da zuwa"

Tace "yawwa"

Fita yayi daga falon, basu jimaba suma suka fice, Ilham tace "wannan shine yaya Adam,duk Mazawaje family shine ustazi, idan kina neman alaramma kikazo wajansa to kingama samu🤣, lacturer ne, yana koyarwa a yusuf maitama, Wato northwerst, yayansa yana germany shida yaya Abba Wato Aslam, su biyu ne a part dinsu

Nihla tace "Allah sarki, aikuwa Babu ruwansa bawan Allah" 🤣

Part din qarshe sukaje kafin su shiga Ilham tace "wannan shine part dinsu Diyana da Dida, maman su tana auren dan'uwanmu ne na family shiyasa taci gaba da zama agidan nan, basu bar family house ba, tana son yaranta sosai, batasan abinda zai tabasu
Kuma ayanda ummah take fada mana hajiya Farida Maman su Dida tana shiri da baban ki sosai"

Nihla tace "hakane kam, nima nasani Ilham"

Part din suka shiga, nanma Babu laifi sunsha fira da Dida, Dan Diyana bata nan 🤣, sannan suka futo kowa ya koma part dinsu


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Watan ta d'aya agidan tafara sakewa, kuma tagama gane halin kowa, nacinda Ilham take mata ne yasa suka saba da ita sosai, Dida da Diyana ma suna zuwa, saide Dida tafita zuwa saboda Diyana kullum tana wajan yawo, yawon ma bada yan'uwanta mata ba, maza!

Su yaya Usman da Aliyu fa farouq sosai suke nuna mata gata, Aliyu yakai ta anyi mata dinku na masu kyau amma kullum tana cikin hijabi, da wahala ka ganta tazauna haka Babu hijabi, haka yaya farouq yakai ta shopping tasiyo kayan kwalliya ta jeresu agaban mirrow din dakin nata, Yaya Usman kuwa Sabuwar waya yasiya mata qirar iphone Mai tsadar gaske.
Rayuwar ta take hankali kwance, saide tunda Diddi tarasu wata nutsuwa tasake shigar ta, abu dayane yake damunta, tunda tabar jigawa kullum takira wayar Baba baya dauka, tarasa dalili, lafiya lafiya zata kira yan'uwansa su gaisa da ita amma shi idan takira baya dauka, idan tayi masa text baya reply, amma tasan koma menene zai iya neman ta daga baya, tasan Baba da wahala yayi fishi da ita Babu dalili.

Hisnul Muslim din hannunta datake karantawa ta ajiye tafuto falo, babu kowa da alama Momy ma tana daki, zama tayi acikin kujerun falon tana kallan tashar aljazeera

Wayar Momy dake gefenta ce tafara qara, Ahankali takai hannu tadauki wayar, sunan dake yawo a screen din wayar ta kallah taga ansa Abba nah, haka kawai ta tsinci kanta da faduwar gaba, cikin ranta ta furta "Yaya Abba"

Wayar tana gab da katsewa tayi picking call din tace  "Hello"

Shiru yayi anasa bangaren, Idanunsa a lumshe, yana kwance akan katifar robar nan ta cikin ruwa, acikin swimming pool din gidansu, babu riga ajikinsa dagashi sai gajeren wando, gashi Mai yawa kwance akan qirjinsa, cikin ransa ya furta "Sweet Voice"

Shirun dataji anyi ne yasa tasake cewa "Hello"  still aka sake yin shiru, hakan yasa takashe wayar ta ajiye ta

Sake qara wayar tayi akaro na biyu, adede lokacin kuma Momy tazo falon tazauna tareda amsa wayar  "Abba nah"

"Momy shikkenan ni duk kinmanta Dani ko nemana bakyayi, babu wanda yake missing dina"
ya qarasa maganar cikin shagwaba

Murmushi tayi "Abba kacika rigima wallahi, idan nakiraka kuna aiki kace baka kusa, idan naqi kira kace bana nemanka"

Shiru yayi Bece mata komai ba, baisan mezai cemata ba,itama tasan hali Dan haka tace "yaya aiki, ina Aslam?"

"Momy Aslam baya nan yaje Indonesia,"

"haka kuka iya dai, yau wannan qasa gobe wannan, amma banda Nigeria"

Yasan sarai abinda take nufi Wato sunqi dawowa gida, Dan haka yayi Murmushi cikin aji yace "Momy toki shirya next week zamu dawo"

Cikin farin ciki tace "Alhamdulillah, Allah abin godia, da gaske Abba nah?"

"yes serious Momy, i will call you back"  dif ya kashe wayar batare daya tambyeta wadda ta d'aga wayar tasa da farko ba











pls Karku Manta da Comments da sharhi 🙏🏻






Amnah El Yaqoub ✍️[6/18, 12:36 AM] El Yaqoub: ❣️ DANGI 'DAYA❣️
 
{Romance &Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub


Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493


11&12


"Anty dawowa zaiyi?"
Nihla tayiwa Momy wannan Tambayar

Zama Momy tayi cikin farin ciki "Nihla Abba zai dawo next week"

Lokaci daya farin ciki yakamata, finally yaya Abba zai dawo, cikin murna tace "Tome za'a shirya na tarbar su Anty? Medame yaya Abba yafiso?"

Hannayenta Momy takama Kamar qawarta 🤣tace "Yanzu de kije daki ki dauko memo saimu zauna narubuta miki abubuwan da zamu iya buqata, sai kuje keda driver kusiyo, abinci za'a hada Mai yawa yanda zai ishi kowa nacikin gidan nan"

Cikin murna tatafi dakin tadawo dauke da memo da biro tazauna kusa Momy, nan take Momy tafara rubuta mata abubuwan dasuke buqata, duk irin kalar Abincin da Abba yafiso saida Momy ta zayyanewa Nihla tas🤣

"to Anty naje nayi wanka saimu tafi?"

"A a kibari sai gobe, sai kuje gobe da safe kidawo da wuri"

"to Anty"

Murmushi Momy tayi Wanda yayi kama da yaqe tatashi tace"zanje sauran part din na sanar dasu "

Hankalinta ya koma kan tv, Dan haka ta cewa Momy" to Anty "

Fita Momy tayi cikin sanyin jiki, sai yaushe ne yarinyar nan zata dinga kiranta da Momy Kamar kowa? Anya kuwa Nihla tasan yanda take jinta aranta kuwa? Yanzu idan tayi baqi tana murna ta nuna musu ita cewa ga 'yarta kai tsaye sukaji takirata da Anty zataji dadi? Me zatayi wa Nihla danta dauke ta amatsayin uwa?

Da wannan tunanin tafara zuwa part din hajiya Na'ila, da sallama ta shiga, hajiya na zaune itada Adam da Alqur'ani a hannunsa yana dubawa🤣
Gaisawa sukayi, shima ya gaida ta ciki girmama wa

Ta kalli hajiya Na'ila, "Hajiya munyi waya da Abba yanzu, yacemin suna nan zuwa Next week insha Allah"

Hajiya Na'ila tayi farin ciki, amma meyasa ita nata Dan bai kirata yafada mataba sai abakin facala zataji? Dama a family ana rad'e rad'in cewa angama shanye mata yaro, andauke mata shi ankai shi wata uwa duniya da sunan karatu gashinan Yaqi dawowa, nan take ta nuna bacin rai a fuskarta, Murya ciki ciki ta dubi Momy, "Allah yakawo su lafiya, nagode"

Jikin Momy yayi sanyi, tatashi tace "to sai anjima"

Tana fita Adam ya dubeta, "haba Dan Allah mama, meyasa kike hakane?" mutanan nafa sunyi mana komai, mijinta yayi muku kara yatura dansa da danki karatu, gashi nima nagama karatu na ina aiki na mallaki komai, to menene yayi saura awajan ki bayan godiyar Allah mama? "

" aikai dama ba dan agida na haifeka ba Adam to tabbas zan'iya cewa ansauya min kaine, da anfara magana zaka fara kawo aya da hadisi, Allah yace, annabi yace, tashi kabani waje, d'an kare me macacciyar zuciya Kamar ta ubansa "🙊

Tashi Adam yayi yace" nina tafi masallaci "🤣

Tsaki tasaki tace" haka de"

Washe gari Nihla ta shirya sukaje kasuwa itada driver da Dida, lafiya sukaje suka siyo komai suka dawo, saboda Dida Babu laifi akwai nutsuwa sosai duk family kowa yayi mata wannan shedar

❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Bayan kwana bakwai wannan family ya haukace da hidima, kowa kaganshi yana cikin farin ciki sosai, part din Momy yacika da qamshi anata girke girke, Nihla da kanta ta shiga kitchen tace Momy tayi zamanta itace zata yiwa yaya Abba girki, Momy taji dadi sosai, Dan haka tatafi wajan ma'aikatan gidan domin ta sanar dasu suje su gyara wa Abba dakinsa, a bangaren hajiya Na'ila itama tanacan tana ta hidima

Diyana da Ilham da Dida ne suka shigo part din, dukansu kitchen din suka shige suka kama mata aikin
Sosai Nihla taji dadin zuwan su

Ilham tace "Nihla duk kinyi kaca-kaca a kitchen gaskiya kinaji da yaya Abba"

Nihla tace "ke kuwa qawana guda zai dawo ba dole ba"

Diyana taja kujera ta zauna "nikam nagaji wallahi, kugama nazuba naci" 🤣
Ta kalli Nihla tace "Kekuma Nihla yaya Abba ne qawanki?, lalle baki samu qawaba wallahi,aini dakika ganni nan gabana faduwa yake da dawowar su, saboda takura tadawo, harna fara blocking numbers din gayu, saboda idan sukazo gida Babu shakka wataran koshi ko yaya Aslam wani zai iya dukana"

Ilham tayi Murmushi tace "baki Manta marinda yaya Abba yayi mikiba ashe"

Nihla tace "au shi yaya Abban haka ya koma? Meyasa toni be taba nunamin ba?"

Diyana tace"inaaa ai zama ne beyi zamaba Nihla,😃 shiyasa, amma kowa yasan halin yaya Abba a family dinnan, babu wasa, kwata kwata bayasan raini dagashi har yaya Aslam, shiyasa ma jinin su yafi haduwa"

Jinjina kai Nihla tayi, wadannan karfa su saka mata tsoronsa

Dida ta wanke hannun ta yace"nikam duk family dinnan ko wallahi yaya Adam ne yake birgeni, babu ruwansa shiru shiru dashi, gashi kyakykyawa inason manyan idonsa wallahi irinna hajiya Na'ila "🤣

Daria sukasa gaba dayansu Diyana tadubi qanwar tata" toke dama ai bakisan luv ba, yanda kike shiru shiru ai dole kiso alaramma, to bari kiji kokin aure shi wallahi nasiha kawai zaki samu, ko kiss bazai mikiba, kirasa wazakiso sai ustaz tirr"🤦🏻‍♀️ta qarasa maganar tana dafe kanta🤣

Ajiyar zuciya Ilham tayi "gaskiya de Dida kinyi kokari, ni banga laifin yaya Adam ba amma gaskiya banason maman su, hajiya Na'ila masifarta tayi yawa, danni da ace ita suruka tace ko, wallahi saide ayita taqare bazan raga mataba" 🙆🏻‍♀️

Nihla tace "inama ace yaya adam din yazo yace yanason ki Ilham, muga yanda zaku kwashe keda hajiya Na'ila 🤣,"

Dasauri Ilham tace "wa? Allah yasawaqe, Dida ce take sonsa,danni kona aure shi idan mamansa tamin ramawa zanyi saide yasake ni aranar, shiyasa duk family dinnan Babu Wanda nakeso, gara kowa yayi harkar sa karma mufara soyaiya kayimin fada in rama azo ana cewa nacika rashin kunya"

Dariya Diyana tayi "aini yaya fawaz yana birgeni, akwai hutu da gayu, danni duk Inda gayu yake ina nan" 🤣

Ilham ta kalleta da mamaki tace "kirasa wazakiso sai Mashayi?" 😳

Nihla tace "Ilham yayan naki kike cewa Mashayi?"

"to Nihla kowa yasan yaya fawaz mashayi ne, Dan qwaya, Dan yana yayana sainaqi fadar gaskya?shiyasa ai ake ganin laifi na ace inada rashin kunya, bayan gaskiya nafada"


Diyana tace "keni can ta matse muku, anata zancen aure aure inma Allah yakawo mazajan auren yazo haka za'ayi shi sulu, wannan tsohuwar dukta hana komai" 🤦🏻‍♀️

Dariya suka saka dukansu, suna wannan firar suna aiki ahaka suka gama suka adana komai Inda yadace sannan suka dawo falo suna kallo, Momy ce tazo tabawa Nihla key "Nihla riqe wannan key din na dakin Abba ne,nasa masu aiki sun gyara, amma kije kiduba kigani idan akwai abinda baiyiba saiki gyara" karbar key din Nihla tayi, ita kuma Momy tayi ciki

Dida tace "Allah sarki Momy, dukta hana kanta sukuni saboda Dan autanta zai dawo"

Ilham tace "ai yanzu saide yayi hakuri dan Nihla ta qwace kujerar" 🤣
Tana fadar haka tamiqe tace "natafi nayi wanka na shirya, berage awa dayaba jirginsu yasauka"

Suma su Dida da Diyana tafiya sukai domin shirya wa, ita kuma Nihla tawuce dakin da'aka nuna mata tun farkon zuwan ta gidan cewar na Abba ne, key tasaka tabude dakin, ahankali ta tura ta shiga

Qamshin Air freshner ne yadaki hancinta, ta lumshe idonta sanan tabude, shigewa tayi ciki, dakin yayi kyau komai yaji, daga kan labulen dakin har komai da Komai naciki duk launin blue ne, gadon da aka lailaye ta kalla tasaki murmushi tareda fadawa kai, juyawa tayi tana kare wa dakin kallo, anan taga pictures dinsa manya manya guda biyu, cikin sauri tatashi ta qarasa wajan photon, zuba masa ido tayi, haka yaya Abba yakoma? Photon yayi kyau sosaai, daya ya dauka da qananun kaya, sun karbi jikinsa sosai, shagala tayi da kallan pictures din tanajin wani irin dadi da batasan dalilin sa ba, gyara zamanta tayi awajan kawai tana qare masa kallo, kira Momy ta qwala mata hakan yasa tatashi Dasauri ta gyara gadon sannan tafuto

"kin gama ganin komai yayi? ''

" eh Anty komai yayi "

" to shikkenan kije kiyi wanka kishirya, su Alhaji sun tafi su dauko su"

Cikin murna tace "to Anty" sannan tayi cikin daki

Wanka tashige, tana qalqale jikinta Kamar ba gobe, ta dade tana wankan sannan tafuto

❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Acan filin jirgin Aminu kano kuwa, zaratan samarin gidanne sukaje dauko 'yan'uwansu

Usman, farouq, Aliyu, Fawaz, da kuma Adam

Basu dauki lokaci wajan jiran su ba, jiriginsu yasauka
Farouq ne yafara hango su yace "yawwa gasu nan" nan yafara daga musu hannu

Gaba dayansu hankalinsu suka maida wajansu, Sunqara kyau, fatarsu ta goge, kana ganin jikinsu kasan hutu Yazauna

Suna qarasowa wajansu suka saki ihun murna duk suka rungumesu, hankalin mutane yadawo kansu gaba daya, mutanan wajan suka fara kallansu

Usman ya kallesu yace "Aliyu, yarafa sun girma, babu abinda zamu jira saide kowa yakawo matar dayake so, musha biki"

Cikin aji Abba yadubi Usman "Aure kuma yaya?"

Dasauri farouq yace "aikai banda kai, nadade da yima mata, yanzu saura Aslam da, Fawaz, dakuma Adam"

Daria Fawaz yayi, shida arayuwarsa mace ma bata gabansa, harkar qwayarsa kawai yasa agaba, yaushe zaiyi wani aure, ahankali yace "Aure, Aure tab"

Aslam ya kalleshi yace "Guy yatake ne? Kaida nayi tunanin ma kafin mudawo har anwuce wajan?"

Kafin Fawaz yabashi amsa Adam yace "kun Manta da wasiyyar kaka kenan, ba taron biki ba taron suna" 🤣

Daria suka sake sakawa gaba dayansu, Aliyu yace "tome muke jira? Muje gida kawai"

Motocin dasuka zo dasu guda biyu suka bude suka shiga, har sukaje gida suna ta surutu da raha a motar, bakin Abba nede gim baya tofa albarkacin bakinsa

Suna qarasawa gida kuwa sukaga komai ya canja, anqara gyara gidan Kamar ba gidansu ba, gaba daya 'yangidan suna tsaye a compound kowa yana jira sufuto amma banda Nihla,
Aikuwa suna futowa waje yakaure da ihun murna, Abba yana ganin Momy yaje ya rungumeta, cikin shagwaba yace "Momy i miss you"

Daria suka fara yimasa, Momy tace "gidanku Abba, bakasan ka girma bane yanzu?"

Dariya akeyi musu, Daddy yanata farinciki yayi gaba, sannan kowa yayi part dinsa cikin murna

❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Hayaniyar dataji afalo ne yasa gabanta yafadi, kode har sun zo? Kafin tasamu amsar ta Tajuyo muryar yaya Usman yana cewa "Pilot, Pilot Shagwaba de tana nan "

"to waye kuma pilot?" ta tambayi kanta, kafada ta daga taci gaba da kwalliya

Gaba dayansu dining suka wuce, Daddy, Momy, Usman, Aliyu, farouq, Abba, abinci zasu faraci, Usman yace "Momy banga 'yarki ba, ko ita muke jira?"

Daddy yayi Murmushi yace "ai tunda tayi  'ya takafa mana doka agidan bazamu ci abinci ba kome take sai anjirata"

Aliyu yayi Murmushi "gaskiya ne Abba zaiyi kishi an qwace masa fadar sa"

Duk maganganun dasuke yana jinsu, Wacece suke magana akanta? Shida yadawo daga wata qasa ba'a jirashi ba sai ita, Wacece ita?

Tunanin sane ya tsaya jin Momy ta daga murya tace "Nihla! Nihla!!

Cikin zazzakar muryarta tace "na'am Anty, gani zuwa"

"Nihla"   ya furta hakan cikin ransa, lokaci daya ya zubawa kofar dakin dayake tunanin daga ciki zata futo ido

Usman yazuba masa ido yanaso yagano yanayin sa, yayinda Aliyu yake murmushi

Ahankali tafuto daga cikin dakin, tana sanye da doguwar riga ta atamfa, daya daga cikin dinkin da ya Aliyu yayi mata, tayi kyau sosai acikin kayan, daurin dankwalin datayi ya baiyanar da dogon gashin kanta, dukda ta daureshi , yan madedetan Breast dinta shape dinsu yafuto sosai ta cikin breast cup din rigar

Dashi tafara tozali, numfashinta ne yakusa tsayawa cak, saboda wani irin mugun kyau daya qara, ya girma yazama Babban mutum, ga fatarsa taqara wani gogewa

Shima a nasa bangaren hakan take, idanu yazuba mata yana qare mata kallo,

Cikin ransa ya furta "tad'an girma kad'an, but still yarinya ce qarama "

"oyoyo ya Abba"

Maganar ta ce tadawo dashi daga tunanin daya tafi,
Usman yagama kallansa tsaf yasaki murmushi

Kai tsaye wajansa tanufa, taja kujerar datake gefensa ta zauna ta kalleshi dakyau
 " Ya Abba sannu da zuwa, mekake cine haka, kaga yanda ka sauya kayi fari ka qara kyau kuwa?"

Murmushin kefen baki yasakar mata "kema haka"

Abinda yace kenan

Murmushi tayi "haba de ya Abba wace ni? Gashinan kana nema ka kamoni fari"

 tafadi haka tana matso da hannunta me dauke da dogayen yatsu kusa da nashi hannun, Dan yagani ya ban bance

Bin farar fatar hannun nata yayi da kallo, d'an siriri dashi, Wanda yake tunanin idan yayi mata kyakykyawan riqo zai iya karya ta 😳🙆🏻‍♀️

Kafin yace mata wani abu, Daddy yayi gyaran murya ganin suna nema su Manta dasu awajan "Am yata zuba mana Abincin ko?"🤣

Tashi tayi tabude Abincin, babu kunya tafara Jan flet din gaban Abba tazuba masa, sannan tadauki na Daddy😃

farouq, Usman, da Aliyu gaba daya suka koma yan kallo awajan, Aliyu cikin ransa yace anya idan Nihla da Abba suka fara soyaiya Momy zata iya bude idonta? 🤔

Saida tagama zuba musu sanan tazuba nata Dan kadan, sannan kowa yafaraci

abinci takeci amma hankalinta yana kansa, tana kallan yanda yake cin Abincin cikeda nutsuwa, Miqewa tayi tsaye Ahankali, tadauki just din dake gaban ya Usman ta tsiyaya a glass cup sannan ta tura wa ya Abba agabansa, takoma tazauna tanaci gaba da cin abinci, Aliyu da farouq suka hada ido tareda Jinjina kai 🤣
Gaba daya Babu wata damuwa aranta take nuna masa kulawa, sai tarairayarsa take Kamar Dan qaramin Baby

Tsawon lokaci suka dauka kafin su Gama, falo suka dawo suna kallo, su Usman sai tsokanarta suke suna janta da fira, ahankali yatashi ya kalli Momy "Momy zanje nayi wanka nahuta"

"to Abba nah,"

Wani irin kallo yayiwa Nihla Wanda ni kaina nakasa fassara shi, amma tabbas za'a sami matsala idan aka yiwa mutumin daya dade yana cikin soyaiyar ka "ina Diddi? Why bakizo da itaba?"


Gaba daya falon shiru sukayi, kowa yakasa bashi amsa
Shikuma ya tsareta da Idanunsa, dago kanta tayi ta kalle shi takasa magana, karkata kansa yayi alamun yana jiran amsa yace "uhm inajin ki"

Idanunta ne suka cika da qwallah, Ahankali ta dago kanta ta dubeshi "Diddi tarasu ya Abba"


"what?"

Dasauri ya kalli Momy yace "Momy, me yarinyar nan take fada haka?"

Jijjiga kai Momy tayi, alamun da gaske ne, Lokaci daya mutuwar Diddi ta dawowa Nihla sabuwa, da gudu tatafi daki tana kuka 😭

Lokaci daya jikinsa yayi sanyi "Innalillahi wa inna ilaihir raju'un, Diddi tarasu, Momy meyasa baku fadamin ba? Haba Momy, meyasa? Innalillah..."
Yadafe kansa da hannunsa🤦🏻‍♂️ya koma kan kujera Yazauna jagwab

Dafashi Momy tayi "kayi hakuri Abba, Aisha ta rasu Sanadin zazzabi na kwana daya, Daddynku ne yace kada afada muku, hankalin ka zai tashi, addu'ah take buqata idan kuka dawo sai kuyi mata"

"Momy yanzu Diddi tarasu?ashe ganin qarshe nayi mata?"

Su Aliyu dake zaune jiki a sanyaye, sune suka fara bashi hakuri, sannan ita kuma Momy tabi bayan Nihla daki



Zuwa dare ta ware, tadan kwantar da hankalin ta tadena kuka a dalilin nasihar Momy, tana kwance agadon dakinta tana daddana wayarta, yauma takira ya yusif yafi sau biyar amma wayar taqi shiga, ko a wanne hali yake?
ta duba Agogon dakin karfe tara da arba'in da bakwai, Dasauri ta furta "kaiiii goma saura"

Dasauri taduro daga gadon tafuto falo, kitchen tashige tafara hada coffee Mai Dan karan dadi
Momy ce taji motsinta, ta furta alhmdlh aranta, tunda tasaki ranta harta futo falo

Kitchen din ta shiga taganta tana aiki "Nihla me kike hada mana ne da wannan daren?"

"Anty bafa mu nake hadawa ba, Ya Abba nake hadawa coffee, nasan zaiji dadinsa"

 ha'ba Momy ta riqe, "to Allah ya temaka, nima kallo zanyi shine naji motsinki na futo"
Tana fadar haka tajuya zuwa falo

Itama Nihla tana gama hadawa tadauka adan qaramin tire, tazo tawuce tagaban Momy tashige dakin nasa, saura kadan tasaki farantin dake hannunta, saboda yanda taganshi dagashi sai gajeren wando 😳, babu riga ajikinsa,gashi kwance a qirjinsa, yana kwance yana waya qasa qasa, batasan dawa yake wayar ba

Qamewa tayi a tsaye, takasa qaraso wa ciki, tayi dana sanin shigowa dakin nan nasa batare da nocking ba

 shi kansa baiyi tunanin shigowar taba, futowarsa kenan daga wanka yasaka Dan gajeren wandon, ko shirya wa baiyi ba aka kira wayarsa shine yad'an kishingid'a yana wayar

cikin ransa ya furta "yasalam! Yarinyar nan kada ta raina shi fa" ahankali yatashi zaune tareda zubo qafafunsa zuwa qasa

Ya tsareta da ido Bece mata komai ba, hannunta ne yafara rawa, duk ta rikice, wanne irin qirji ne dashi haka me fadi? Duk Ta diririce tarasa me zatayi

Shima ya lura da yanayin data shiga, ko menene ya tsoratata take karkarwa haka? 🤔 🤣
Ya tambayi kansa.

Cikin in-ina tafara magana "Am dama... dama coffee..."

"zoki ajiye"
Abinda yace da ita kenan

Ahankali ta taka ta qarasa wajansa, sai kawar dakai take, takasa kallansa, ta tsugunna ta ajiye masa agabansa tafuto da sauri

Binta yayi da kallo, to menene abin tsoro ajikinsa ? To kodan ta ganshi haka ne dukta tsorata? Tabe bakinsa yayi, sannan ya kalli wayar tasa yaga anma kashe, shima bai sake kiraba yayi wulli da wayar yadauki coffee din data kawo masa

Tana futowa daga dakin tazauna afalo kusa da Momy suna kallo, amma gaba daya hankalinta bayakan kallan, 🤣


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Tsawon satin su biyu da zuwansu , koda yaushe da irin kulawar da Nihla takewa Abba, zuwan yanzu kam, kowa yasan cewa Nihla nason Abba, Shidinne de suka rasa gane Inda yadosa

Alhaji ne yashigo falon nasu dawowar sa kenan daga wata tafiya dayayi, Momy tanayi masa sannu da zuwa, ya amsa mata, yana zama akan kujera, "ina ya rannan ne?"

"Nihla bata nan taje wajan Ilham, Abba kuma ni Tun safe ma banganshi ba "

Wayarsa yadauka ya kira Abban
" kazo kaida Aslam ku sameni agida yanzu, kokuma ka turomin shi "
Yana fada masa haka ya kashe wayar

Basuda dauki lokaci ba sai gasu sun shigo shida Aslam din, cikin ladabi suka tsugunna agabansa bayan sun gaida shi,Alhaji ya dubesu " Aslam inaso ka shirya kaje India ka dauko Aisha daga makaranta, munyi magana da abokina cewa harma tarafa university, to Zan turoma adress din gidan, saika shirya kaje kutaho tare "

Momy ta kalleshi tace  " Amma Alhaji lafiya kuwa? "

" lafiya kalau Alhamdulillah, kawai de lokacin karanta wasiyyar hajiya ne yayi, tunda Allah yayi mana Tsawon rai, gara intara kan kowa na family a karanta wasiyyar agabansa "

Momy ta Jinjina kai, tace" hakane, Allah Mai iko, kwanci tashi kenan "

Beyi mata magana ba, yadubi Aslam din yace   " shine kiran dama, ka shirya katafi, ka tabbatar kun dawo akan lokaci "


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

" gaskiya Ilham akwai matsala "

" matsala kuma Nihla? Allah yarabamu da matsala, 🤣
Meyake faruwa? "

" Ilham ina tunanin son yaya Abba nake wallahi, shikuma naga Kamar hankalinsa baya kaina, ina yawan tunanin sa, sannan ni Tun ina qarama nakasa mantashi a raina, Ilham ina tsoro kar yaya Abba Yaqi saurara ta "

" soyaiya Nihla? Kuma ma da yaya Abba? Anya baki debo da zafi ba Nihla? "

" nima abinda nake tsoro kenan Ilham, bansan ya zanyi ba wallahi "

" kinga ki kwantar da hankalin ki, shima nasan Babu yanda za'ai yaganki amma baiji aransa cewa yana sonki ba,Nihla Allah yamiki kyau, sannan kuma ke dashi duka DANGI 'DAYA ne, bazai qikiba, dan'uwanki ne, tunda duk cikin mu Babu Wanda yake sakewa da'ita Kamar ke, amma idan zaki iya to kiyi masa maganar mana "

Kai tsaye tace" bazan iyaba Ilham, yanamin mugun kwarjini wallahi, kullum naganshi agabana ma gabana tsananta faduwa yake, sannan yana cikamin ido, koba wannan bama bazan iya tunkarar namiji da wannan maganar ba "

Ilham tayi ajiyar zuciya," hakane kam,gaskiya gara shiya fara furta miki, amma mezai hana cikin siyasa kifara nuna masa? "

" to ta wacce hanya kenan Ilham? "

" kulawa, kidinga bashi kulawa yanda yadace "

" Ilham duk Wanda Yazauna a part dinmu zaisan cewa ina bawa ya Abba kulawa ta gaske, saboda haka kicire kulawa a lissafi"

Girgiza kanta tayi tace "gaskiya ne wannan, nima shedace, ke kinga mudena bata lokacinmu akan wannan tunanin, duk miskilancinsa qarya yake ya juyawa mace Kamar ki baya Nihla"

 tace" da gaske kike Ilham? "

Girgizakai Ilham tayi," da gaske nake "

Cikin farin ciki ta rungume Ilham







(to ko yaya zata kasance?ko yaya bayanin wasiyya? Fatana kuci gaba da kasancewa Dani)




Kada amanta da sharhi da Comments 🙏🏻






Amnah El Yaqoub ✍️
[6/19, 12:52 AM] El Yaqoub: ❣️DANGI 'DAYA❣️

{Romance & Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub


Like my page On facebook 👇

https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493


13&14


Bayan kwana biyu Aslam ya shirya yatafi India domin tahowa da Aisha, yaso sutafi tareda Abba amma sai Abban Yaqi
Yana sauka a Airport yakira number da Daddy ne yaturo masa amma wayar taqi shiga, haka yadinga tsaki shi kadai
Daga qarshe saiya kira Daddy yafada masa, a lokacin Daddy yasa Alhaji Basiru yatura masa number Aisha

Aslam na ganin number nan take yakirata, amma yakira yakai sau hudu bata daga wayar ba, haka yasake kiran Daddy ya sanar masa, daga qarshe de sai Daddy ne yayi masa kwatancen gidan da kansa, shikuma yahau taxi suka tafi, daqyar ma me taxi din yagane abinda Aslam din yake nufi, saboda shi Babu turanci, shikuma Aslam Babu yaran hindi 🤣

Sunyi tafiya Mai nisa sannan yasauke Aslam ya nuna masa bus din dazai shiga, zata kaishi har kofar gida

Dole saida dala yayi amfani wajan sallamar me taxi din, sannan yafara jiran zuwan bus
Yanayin garin yake kalla da dan hadari kadan, Kamar wasa kuwa aka fara yayyafi, mutane dasukasan kan garinsu kowa sai yake baza lema, Aslam kuwa sai kare ruwa yake da hannu amma abin ba riba🤣

Ruwan yafara jiqa masa kayansa saiga bus din tazo ta tsaya awajan, gani yayi mutane suna shiga, shima yace ai ko ba ita bace wallahi shiga zaiyi, sukaishi koma ina ne 🤣

Duk kujerun motar ma sun cika, sai wata yarinya datake zaune gefenta akwai kujera daya, kallo daya yayi mata yagane cewa Babbar arniyace, shigar ta kadai zaka kalla kagane hakan

Riga da wando ne a jikinta kayan ya kamata sosai, sannan gashinta awaje sai Dan qaramin mayafi data dora akai Wanda dashi da Babu duk daya
Itama kallansa tayi, taganshi a tsaye yariqe karfen Mota, kayan jikinsa sunyi masa kyau sosai, da yaren India tace masa yazo yazauna, taga ko Kallanta ma baiyiba alamun baima san dashi takeba
Dan haka tace "hi"

Sai lokacin ya juyo

Tace "please come and sit"

Kallanta yasakeyi ya yatsina fuska, "no, thank you"  yafada mata haka yana yatsina fuska
Hankalinta ta maida kan window bata qarabi ta kansa ba

Wayarsa yaciro yaciro daga Aljihun jeans d'insa yakira Abba, Abba yana dauka Aslam yafara zuba "Abokina kasan me? Wallahi gara da Allah yasa baka biyoni ba, gani nan muna tafe awata bus tana tafiya yanda kasan hawainiya, ni a tsaye ma nake narasa wajan zama"

Abba yace "Kamar ya?"

"to gashinan de kowa yana zaune, babu kujera sai guda daya, ita kuma wata qatuwar arniyace azaune nake fadama 🙊, inani ina zama kusa da manyan arna😳
Shegiya harda cewa wai in zauna, d'an iska neni, ina zama zata liqemin daga nan kuma ta addabi rayuwata"

Murmushi Abba yayi, yasan halin Aslam sarai, "to kayi hakuri mana, insha Allah zakuje lafiya"

Wani uban birki aka taka, hakan yasa Aslam yayi gaba yasake dawowa baya, nan take yakashe wayar yasake riqe karfen 🤣

Mutum uku ne suka fita, kujerar datake gaban yarinyar Babu kowa, nan yakoma Yazauna, yarinyar tanata kallansa

Kafin su qarasa Inda zaije motar ta lalace, kowa yafuto, wasu suka fara tare Mota, wasu kuma suka tsaya, kiran sallah yaji anayi awani masallaci, Dan haka yaje wani dan case agefen su yasiyo ruwa, yadawo wajan motar ya tsugunna yafara daura alwala

Yarinyar tana tsaye a gefensa, duk tana kallansa, ajiyar zuciya tayi, tataka Ahankali ta qaraso wajansa cikin yaren hausa tace masa "bawan Allah Dan Allah idan kayi sauran ruwan inaso nima zanyi sallah, kudin hannuna baida yawa bazai isheniba"🤣

Shiruuu Aslam yayi Kamar an kwada masa sanda🙆🏻‍♀️
Kasa Dagowa yayi, bare yahada ido da ita 🤣

Tasake cemasa "dan Allah, kaji"

Sai a lokacin yadago kansa, cikin kuskurin kunya yace "yanzu ke, dama kinsan kina jin hausa kika barni inata zuba?"

Murmushi tayi batare datayi magana ba, Ruwan ya miqa mata yace "gashi inde ruwa ne, ai ruwa baya had'a fad'a, shi musulmi ai dan'uwan musulmi ne" 🤣

Hannunta ta meqo zata karbi gorar Ruwan idonsa yasauka akan wani abun hannunta irin Wanda yan gayu suke daurawa maza da mata, amma nata anrubuta mata MAZAWAJE da manyan harufa 😃

Fasa bata Ruwan yayi, ya tsaya yakalli fuskarta dakyau, aishi sai yanzu nema yaga yarinyar tanayi masa kama da Nihla sosai, saide tafi Nihla cika dakuma 'yar qiba, yayi ajiyar zuciya yace "ke fadamin, Yaya sunanki?"

Murmushi tayi tace "Aysha Basiru Abubakar Mazawaje" 🙆🏻‍♀️
Cikin ransa yace tabd'i, dara tasake cin gida kenan, yatsunsa biyar ya nuna mata yace "uwaki" 🤣

Yaci gaba da cewa "to a qasar nan qafata qafarki dake Zan koma Nigeria, Aslam ne Dan gidan Alhaji Baqir yayan babanki"

Cikin sauri tace "yaya Aslam, Innalillah..., ya akai nakasa ganeka?"

"aikokin ganeni, ko baki ganeniba, daga nan, babu Inda zan barki kije,wuce Muje muhau wata motar kikaini gidan"

"toka bari muyi sallah mana, bani Ruwan nayi alwala ni"

"da wannan shigar zakiyi sallah? Haba, haba, wannan kam baki isaba, ina wayarki ina kira baki dagaba?"

Jakar hannunta ta duba tace "kaganta acikin jaka, niban saniba"

Yace "yayi kyau, to wuce Muje gidan" 🤣

Daga nan tajuya sukayi bakin titi domin tare wata motar


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Kallanta yayi idonsa akan manyan qirjinta yace "gaskiya naji dadin rawar nan, gashi gayu sunzo dayawa, club din yacika sosai, Ina alfahri dake Diyana kin iya rawa ba qarya"

Murmushi tayi tace "najjashi kenan, ai mutum ya mori yarintarsa, yayi amfani da lokacin sa kafin yaqure masa, nan gaba idan natara yara ai bazanyi ba"

Yace "wannan gaskiya, toga kazar taki, nasan kinason kaza shiyasa nasiyo miki ita, zakiji dadin ta"
Yafadi haka yana miqa mata ledar kaza

Hannu tasa ta karba tace "to najjashi nagode, kaga dare yayi, sha d'aya saura, Zan shiga gida"

Idanunsa ya lumshe sannan yabude su, ahankali yadora hannunsa akan qirjinta, kafin ta farga yafara murzawa,😳🙆🏻‍♀️
Cikin kasalalliyar murya yace"to yanzu ya za'ai kenan? "

Da qarfi kuma cikin fishi ta bige hannunsa, bacin rai ya baiyana akan fuskarta qarara, ta kalleshi dakyau tace" najjashi bude min Mota nafita kafin na tsinka maka mari anan, anfada maka ni 'yar' iska ce? Saboda ina yawo club club bashi yake nuna jikina nake kaiwa ana amfani da niba, "

Runtse idonta tayi cikin tsananin bacin rai taci gaba da fadin " najjashi nace kabudemin kofa kafin inbude idona "

Dariyar yaqe yayi, yayi tunanin zai samu abinda yakeso awajan ta, yayi tunanin itadin yar hannu ce,koda yaushe yanaso ya gwada sa'arsa akan Diyana ko zai dace, amma abin ya faskara,
cikin borin kunya yace  " dama fa gwadaki zanyi, 🤣
Kuma kinci Interview"

Cikin fishi tace "uwar Interview, nace kabudemin kofa," ta qarasa maganar cikin tsawa, babu musu yabude mata kofa, tawullo masa ledar kazar tafice daga cikin motar

Adede lokacin Adam yadawo daga wajan meeting din dasukai a Makaranta, qare mata kallo yayi tana sanye da riga da wando, duk shape dinta yafuto, babu wani namiji Mai cikakkiyar lafiya dazai ganta ya qyaleta

Yakalli Agogon motar yaga shadaya saura, yana Kallanta tashige cikin gidan, sannan najjashi yaja motar sa yabar kofar gidan, shima Adam din yayi horn megadi yabude masa, cikin ransa yana fadin Allah ya shirya, yarinya kam tagama lalace wa saide addu'ah 😭, Dan nasiha bazata karbuba adede wannan lokacin 🤣

Tana zuwa part dinsu taga Babu kowa afalon danhaka tashige cikin dakin su itada Dida, tana shiga ta gansu azaune dukansu, Ilham, Nihla, da Dida

Zama tayi akan gadon tana sakin tsaki, dukansu suka kalleta, Nihla tace "meyake faruwa ne Diyana?"

Cikin bacin rai tace "wallahi daga club nake, wani gaye ya ajiye ni abakin gate d'an iska jiyake nima irinsa ce shine yasa hannu yana tabamin nono"

Gaba dayansu suka hada baki suna fadin "Nono" 😳

Kallansu tayi, "to miye abin hada baki anan? Ku daga anbaku labari zaku nemi ku ta rawa mutum jama'ah"

Nihla tace "tab, ai abinne da nauyi, kema Diyana kidena wannan yawon, wannan shigar dakike duk bai kamata ba"

Ilham ma tace "ato shikuwa gaye ina ruwansa yaga abubuwa asarari ai dole ya gwada ko zai dace" 🤣

Dida tace "gara de ku fada mata ko zataji," sannan ta maida Kallanta ga yayar tata tace "gara ma wallahi, gaba kya sake fita" 🤣

Diyana de tayi shiru tana jinsu, amma tabbas yaukam najjashi ya nuna mata cewa ita yar'qaramar 'yar club ce


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Aslam yasamu tarba sosai daga wajan abokin daddy, cikin kwana biyun dayayi a qasar ya fahimci halin Aysha, tanada nutsuwa sosai da sosai, bako Mai ne yake qara birgeshi da yarinyar ba sai Kallanta, duk lokacin data daga ido ta kalleshi sai yaji wani abu ya soki zuciyarsa
Haka nan ya tsinci kansa dajin dadin kasancewar su tare da yarinyar, kwata-kwata ya Manta da maganar Daddy dayace kada su dauki lokaci Mai tsawo basu dawoba

Yau kuwa Tun safe Daddy ya kirashi yace sukamo hanya su Taho gida, Dan haka washe gari sukai shiri suka Taho shida ita
Acikin jirgi ma tana gefensa, sau uku tana kamashi yana Kallanta
Tace "yaya Aslam lafiya kuwa?"

"akwai abinda yake damuna qanwata"

Kokarin saka belt take saboda sanarwar da ake cewa jirgi zai tashi
 "meyake faruwa?, meyake damunka?"

Yace "kece, kece damuwata Aysha, narasa yanda zanyi da soyaiyar ki"

Sakin belt din Hannunta tayi ta rufe fuskarta cikeda kunya 🙈

Dab da ita ya matso yadauki belt din zai saka mata, tanajin sa akusa da ita, Kamar zai maida ta jikinsa

Harya saka mata belt din bata bude fuskarta ba

"kibude fuskar ki mana"

Cikin kunya tabude fuskar tata

Hannunsa yadora akan nata yariqe yace "Aysha kimin alqawari duk rintsi bazaki rabu da niba"

Wani iri takeji yanda yakama mata hannu, danta taqaita maganar tace masa "insha Allah yaya Aslam, nayima alqawari"

Ajiyar zuciya yasauke, sannan yasaki hannunta yana jin farin ciki naqara ratsashi

❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Tsaye suke a Airport, Fawaz, Adam da Abba
Suna jiran jirginsu Aslam ya sauka, Fawaz yace "guy's kunsan menene, ni arayuwata kwata kwata mata basa gabana wallahi, amma tunda nayi karo da'ita take nema ta addabi nan d'ina"
Yaqarasa maganar yana dora hannunsa asetin zuciyarsa

Da mamaki Abba da Adam suka kalleshi, Adam yace "Wacece?"

Ahankali yace "Nihla"

Dasauri Abba ya kalleshi, haka nan yaji haushin maganar Fawaz din, yayi shiru baice komai ba, Adam yace "Babu laifi tanada hankali, yarinyar akwai Face, duk family dinnan idan kana neman kyau kazo wajanta kagama Alhaji"

Fawaz yace"no ni bawai  kyanta ne yajani ba, ina tunanin idan na aure ta bazata damu da halaiyataba, zata barni insha abinda raina yakeso "

Wannan karon Abba kasa hakuri yayi yadubi Fawaz din yace masa   "Nihla?"

Hankali kwance Fawaz yace "yes"

Adam yace "nikam gaskiya idan Zabi za'a bani ko to Zan Zabi Dida, najima ina son yarinyar but narasa yanda Zan fuskanceta in fada mata, bazan iya zuwa wajanta da girmana ina qaramar murya akan tasoni ba, amma gaskiya sosai nake sonta, dama inka dauke Nihla da Dida da Aysha, tofa sauran biyun sai Ahankali, Ilham rashin kunya, Diyana kuwa Hmm karma kasata acikin lissafi, Dan rannan ma wani gaye nagani yasauketa amota "🤣

" dan Allah kundameni da maganar wannan yaran, ku yanzu ko kunya bakwaji kuzauna kuna cewa qannan bayan ku kukeso? Ahaifi yaran agabanku amma kudinga wannan maganar? "
Cewar Abba

Fawaz yadafa kafadarsa
" zamu ga yarinyar da zaka Aura Abba "

Suna wannan maganar su Aslam suka futo, shine yake riqe da jakar ayshan, Tana ganin Fawaz ta qarasa ta rungumeshi tace
" yaya Fawaz "

Cikin farin ciki yace " Sannu da zuwa qanwata, "

Su Adam ta gaisar, gaba daya sun sauya mata, in akan hanya ta gansu ba lalle taganesu ba, shima Fawaz din dan kullum suna gaisawa dasu ne ta cht

Hannun ta yaja yabude mata Mota ta shiga, Adam ma yashiga, shikuma Aslam zasu tafi shida Abba

Ta glass din motar ya leqo kansa yace "my dear shikkenan sai munyi waya ko?"

Kunya ta kama Aysha, shi yaya Aslam ko kunyar qaninsa Adam dayake wajan bayayi zai yi mata wannan maganar?
Ahankali ta daga kanta, Fawaz ya kalli Adam suka hada ido 🤣
Basu cemusu komai ba, sukaja motar suka tafi

Shima Aslam ya shige ta Abba suka tafi

❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Bayan dawowar Aysha da kwana biyu Aslam yazo part din su Abba, suna zaune agefen gado da takardu agabansu suna tsara yanda zasu gina wani sabon kamfanin dasuke son budewa tare
Suna gama tattaunawa Aslam ya ajiye file din a gefensa yakalli Abba "Abokina gaskiya inason yarinyar nan, Aysha tagama tafiya da nutsuwa ta, zan jira agama wannan meeting din da Daddy yace za'ayi bayan angama Zan sanar dasu kawai ayi mana aure, inyaso saita dawo nan taci gaba da karatun ta tunda yanzu tafara"

Kallansa Abba yayi "Aslam kuna bani mamaki yanda kuka dage akan wannan qananun yaran"

"Abba karka renamin hankali, haka kakeso muyi ta zama ne? Ko kana tunanin muna germany bana sane da irin juyin dakake cikin dare kakasa bacci?" 🤣

"Malam ni bana wani juyi cikin dare"cewar Abba

"qarya kake Abba, to lemon tsamin danake gani cikin dozbin fa?ni bazan kashe kaina ba, aure nakeso kawai"

"to karka min kuka" inji Abba

Adede lokacin taturo kofar dakin tashigo, bakinta dauke da sallama, tana riqeda flet me dauke  da meat pie

Kallansa tayi "ya Abba ga meat pie nayima,"

Agajarce yace mata "Ok"

Ta kalli Aslam tace "Barka da wannan lokaci ya Aslam"

Cikin sakin fuska yace"yawwa Nihla, mungode sosai "

Murmushi tayi tajuya tafice daga dakin

Aslam na ganin fitarta ya kalli Abba "Abokina yarinyar nanfa nagama lura tana sonka, irin yanda take kula dakai zaisa kowa yagane hakan"

Kallan Aslam yayi  "wacce irin magana kake haka Aslam? Yaushe Nihla ta girma dahar zatasan wani soyaiya? She's 17 year's fa"

"to menene aciki?"

Hannu yadaga masa "no, no, dakata Aslam, kafi kowa sanin nafisan na Auri mace babba, wadda ta waye, me ilmi, ta mallaki duk abinda nakeso ajikin mace, sannan me hankali, amma Nihla renonta kawai zanyi, Aslam nasan kaina inada tsananin sha'awa, kuma ni kadai nasan yanda nakeji, wannan yarinyar zan'iya kakkaryata Tun a daren farko idan ma ta nuna kenan, bare ma yanzu dabata nunaba "

" dan Allah ka dakata Abba, wannan yarinyar fa qanwar ka ce, menene aciki idan ka aure ta? Meka dauki mace Abba? Kana maganar nuna ai kaine zaka maida ta hakan "

" dan Allah kadena min wannan maganar Aslam, nafadama bazan iyaba, nafisan mace me tarin ilmi, wadda tahada komai, amma Nihla amatsayin qanwata nake ganinta "

Aslam yace" nasan dalilin dayasa kake wannan maganar, kuma kasan hakan ba qaramin kuskure bane idan ka aikata shi, ba kuma ranka ne kadai zai baci ba harda namu baki daya, inaso ka tuna halin da Diddi ta shiga itada baba Basiru akan hakan "

Yana fadar haka yayi wulli da file din dasukai magana akansa yafice daga dakin cikin fishi

❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

"wayyo Allah ummah cikina ciwo, zan mutu ummah, ummah Dan Allah kiyafemin, kicewa Abbanmu shima yayafemin"

Hajiya abida tashare hawayen idonta "Aysha kidena maganar mutuwa, ba zaki mutu ba, 'yata bazaki tafi kibarni ba"

Ilham idanunta sunyi jajir tace "Anty Aysha kiyi shiru Dan Allah, bazaki mutuba, zaki tashi mu rayu tare"

Hannun Ilham ta riqe tace"ilham kicewa yaya Aslam ina sonsa, bazan tashi ba Ilham ni nasan yanda nakeji, nadade ina wannan ciwon cikin, amma nayau dabanne ilham "

Alhaji Basiru ne yasa hannu da kansa yadauketa suka futo daga cikin motar suka shiga cikin asibitin dasuka qaraso

Likitoci ne suka karbi aysha, nan take suka shiga bata temakon gaggawa, Alhaji Basiru Yazauna awajan yayi tagumi

Daga baya yan gidan gaba dayansu suka qaraso asbitin, Aslam yafi kowa shiga tashin hankali, Daddy ya kalli Alhaji Basiru yace "wai dama batada lafiya ne?"

"wallahi yaya Abubakar kwana mukai bamuyi bacci ba, cikin ta yana ciwo, bayan wani dan lokaci saiya lafa, shine muka Taho Asbiti yanzu"

Alhaji Baqir yace "subhanallah, Allah yabata lafiya"

Gaba dayansu sukace amin, haka suka zauna jugum jugum, babu wanda yankewa dan'uwansa magana, har likitocin suka futo

Gaba dayansu sukai kansu da tambaya, Likitan ya goge gumin fuskarsa yace "Alhaji saide kuyi hakuri, Allah yayi mata cikawa, munyi iya kokarin mu ganin mun ceto Rayuwar ta, amma hakan ya gagara sakamakon ciwon Hanta datake dauke dashi, hantarta tariga ta lalace, kuyi hakuri"

Ilham najin haka ta yanke jiki tafadi, yaran kuwa kowa kuka yake, Aslam ya sulale Yazauna aqasa yana maimaita kalmar Innalillahi wa inna ilaihir raju'un acikin ransa

Gaba daya waje ya kaure da koke koke, babu me lallashin wani, haka suka dauki gawar Aysha suka tafi gida, akai mata sutura aka kaita gidanta na gaskiya, Aslam kuka Kamar mace, duk yafita a hayyacinsa, saide muce Allah yaji qanta, idan tamu tazo Allah yasa mucika da imani


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Tunda akai wannan mutuwa gidan yadawo shiru, Diyana kuwa kullum tana cikin hijabi🤣
tunda taga aysha qiri-qiri tamutu da quruciyarta, sosai mutuwar tataba matasan gidan, saboda basu taba kawowa kowa mutuwa acikinsu ba
Ranar ukunta yayi daidai da ranar da Daddy ya sanar za'ai meeting, amma ganin anyi musu rashi yasa aka sanarwa kowa sai bayan sati biyu akwai gagarumin family meeting.
Hakan ce kuwa ta kasance,ranarda sati biyu tacika kowa yatafi Babban dakin taro nacikin gidan mata da maza manya da yara, Usman shida matar sa da yaransa biyu, sai Aliyu shima yazo da matar sa da dansa daya namiji, farouq kuwa matar sa ko haihuwa batayi ba
kowa yazo  yanaso yaji abinda wannan wasiyya ta qunsa
Samarin ne awaje kawai basu shiga ciki ba suna jira saisu Daddy sun qaraso

Sunata fira kadan kadan amma Aslam baya magana, Adam kuwa gabansa ne yake ta faduwa harya kasa boyewa yace "nifa gaskiya meeting dinnan danya zama dole ne amma gaskiya da bazan zoba, yau inada lacture, sannan gabana faduwa yake narasa dalili"

Fawaz kallansa yayi bai tankaba, Abba ma shiru yayi, Aslam kuwa daja tunda aysha tarasu suka kasa gane kansa

Kallansu yayi yace"wai badaku nake bane duk kunmin shiru?" 🤔

Ajiyar zuciya Fawaz yasauke yace" kai sai yanzu kakeji,? ni Tun jiya gabana yake faduwa, Kamar akwai abinda yake san faruwa Dani, amma koma menene Allah yasa ya sameni ni kadai banda Nihla "🤣
Kallansa Aslam yayi cikin mamaki, to kode Fawaz nason Nihla ne? 🤔

Kafin wani yace wani abu su Daddy suka qaraso wajan, shida Alhaji Baqir da Alhaji Basiru
Dakin taron suka shiga, sannan suma samarin suka bisu abaya

Wajan meeting din yayi kyau an qawata shi da lemuka da ruwa domin baqi 😃

Nihla tana kusada Momy, yayinda Ilham ma take gaban ummanta hajiya abida, suma su Dida itada Diyana suna gaban maman su hajiya Farida

Su daddy suna zama hall din yayi shiru, Kamar ruwa ya cinyesu, megadin gidanne yaqaraso dauke da akwatin da aka rufe takardar wasiyya aciki ya ajiye yajuya yafita 🤣

Daddy dakansa yatashi yabude, kowa yazuba masa na mujiya, yadauko takardar Yazauna sannan ya'ajiyeta agabansa

Yakai dubansa wajan samarin sun zauna waje daya gaba dayansu, Adam ya kalla yace "Adam taso kabude mana taro da Addu'ah"

Babu musu yatashi yadinga kwararo musu addu'ah, sannan aka shafa

Daddy yayi gyaran murya, yafara magana "Alhamdulillah, muna qara yiwa Allah godia akan Tsawon rai dayayi mana har muka kawo wannan lokaci cikin kwanciyar hankali, wadanda suka rasu acikin wannan family Aisha, da takwararta Aysha, muna yi musu addu'ah Allah yaji qan su"
Gaba daya aka amsa masa da  "Amin"
Sannan yaci gaba da fadin
"insha Allah yanzu zamuji dalilin daya taramu anan wajan "

hall yaqara yin tsit, Daddy yabude takardar yayi tozali da rubutun Ajami, yadaga kansa yasake duban Adam yace"da Ajami sukayi rubutun, Adam kaine malami zoka karanta mana"

Hajiya na'ila tafara karkad'a kafarta tana hura hanci , jin ansake kiran dannata akaro na biyu

Jikin Adam a sanyaye yaje gaban iyayen nasa ya karbi takardar yafara karanta wa :Assalamu alaikum jama'ar wannan dangi Mai albarka, ni Abubakar Mazawaje mun zauna tareda matana guda biyu mun rubuta wannan wasiyya badan komai ba saidon hadin kan wannan zuri'a,mun yanke shawarar hada jikokinmu aure domin zumunci yaqara qullu wa,...

Adam yana zuwa nan yaji gabansa yafadi, jikinsa yafara rawa, hannunsa sai karkarwa yake yaji maganar akansu ne Wato jikoki

Cikin daure fuska Alhaji Baqir ya kalleshi "kai menene haka? Cigaba mana"

Muryar Adam na rawa Kamar ba namiji ba yaci gaba da karatun

"Duk mazan da suke cikin wannan family an mallaka wa kowa filin dazai gina,duk Wanda yayi aure acikin wadannan yara dazamu ambata, to lalle lalle ya tabbatar yasake wani auren yacika namu Burin

 munyanke shawara tareda umarnin cewa Ilham 'yar gidan Basiru zata auri Aslam Dan Alhaji Baqir

Dida yar gidan Farida zata auri Fawaz yaron Alhaji Basiru

 sannan Adam yaron Alhaji Baqir zai auri Diyana, yarinyar hajiya Farida

 saikuma na qarshe takwarana Abubakar Wato Abba, zai auri Aisha yar  gidan Alhaji Basiru tareda Nihla yarinyar Aisha "

Wannan dalilin ne yasa mukayi muku hani akan duk wani taro acikin family, na suna kona aure, saboda gagarumin taron dazaku hada na auren jikokinmu, muna yiwa kowa fatan alkhaairi "

Takardar ya ajiye, saboda jiri-jiri dayake gani 😃

Cikin fishi hajiya Na'ila ta miqe tsaye tace "wallahi bazata sa'buba, kowa yasan kaf family dinan yarana sunada hankali, babu wanda yakai Adam sanin Allah yace, annabi yace, 😃
amma arasa  yarinyar da za'a liqa masa sai Diyana, yarinyar dakowa yasan tagama tambad'ewa atiti, shikuma Aslam wai Ilham, da rashin kunyar ta zaiji koda aikin gabansa "

Hajiya Farida cikin sauri itama tatashi tsaye ta maida wa hajiya Na'ila martani,
" ke saurara hajiya Na'ila, dakike cewa 'yata tagama tambadewa ambawa danki jinake yata Dida aka hada da qungurumin Mashayi 🙆🏻‍♀️, ni nace wani abu ne? Saike me bakin magana?"

Hajiya abia tayi shiru, tabbas taji haushin furucinsu akan yayanta, sai yau take dana sani akan halin Fawaz na shaye shaye, ta kalli hajiya Farida tace
" Farida Karki sake danganta min dana da sunan shaye shaye, "

Hajiya Farida tace  " besha bane? Jinake Tun yana yaro kika gama lalata masa tarbiya, antashi an Auro mana baragurbi cikin family"

Gaba daya hall din ya kaure da surutu, da hayania, Aslam yayi shiru yana tunani, tayaya zai iya Rayuwar aure da qanwar Aysha? Yanzu kenan da ace tana raye ma Abba zata aura? Innalillah...wannan wacce mahaukaciyar wasiyya ce?

Momy kuwa hamdala take cikin ranta, shikkenan Abbanta zai auri nihila

Adam kuwa me karanta wasiyya yana ganin Ance Diyana zai aura yatuna lokacin data futo daga motar wani qato

Shikuwa Fawaz tunani yafara wai A'ina yakejin Dida ne? 🤔 Wacece Dida ne acikin yaran?

Daddy yayi shiru yana kallan kowa, matan sai hayaniya suke, Alhaji Baqir ne yatashi yadaka musu tsawa sannan suka nutsu kowa takoma wajan zamanta tazauna

Cikin ransa yafara magana, mata biyu!! amma wad'annan tsofaffin sunfi kowa cimasa mutunci, to aishi guda d'ayanma bayajin zai iya zama da ita, Dan haka yadago kansa Ahankali ya kalli Daddy yace

 "  I'am sorry Daddy, amma i can't marry her, Daddy bazan iya auren taba, inada wadda nakeso"

Gaban Nihla yayanke yafadi, ita yaya Abba yake cewa bazai aura ba agaban jama'a?
 Lokaci daya hawaye suka wanke mata fuska, babu wanda yafado mata sai Diddi, tabbas sai kayi rashin uwa zakasan wani bangaren na rayuwa

Momy ta kalli Abba da sauri tanaso ta gaskata abinda kunnanta sukaji, ba ita kadai ba hatta Usman, Aliyu, farouq, shi suke kallo cikin tsananin mamaki

Daddy kansa maganar Abba tadaki ransa, amma saiya basar bai nuna ba ya kalli Abban yace "Amma kasan cewa yanda 'ya'yan wasu sukabi umarni bazai iyu d'anda nahaifa acikina yaqibiba ko? Tunda kace baka sonta tokaje kanemo son aduk inda yake, idan kuma kanakan bakanka har yanzu to kasa aranka cewa, qin auren Nihla dede yake da fitarka daga cikin Mazawaje family,sannan ni kaina nacireka acikin  'ya'yana, Zabi na gareka, koka amince kokuma daga nan katashi kafita baka cikin Mazawaje family "

Hall yasakeyin tsit, maganar Daddy ta daki kowa, tabbas yanda yayanke wannan hukunci akan d'ansa nacikin sa tofa bazaiji kunyar yankewa Dan wani ba

Babu musu Abba yamiqe, yafuto daga cikin Hall din

Momy tafara kuka wiwi, tace" Innalillahi wa inna ilaihir raju'un, meyake shirin faruwa damune?"

Ta kalli Abba dayake dab dabarin cikin hall din ta qwala masa kira tace  "Abba!!!"

Amma ko juyowa baiyiba







(wai ina labarin yusif ne,?🤔Yaje China ya maqale)

(tab bari na fece kar masu dukan Abba sudawo kaina 🤪}

Mutara zuwa gobe🙏🏻






Kada ku Manta da sharhi, Comments, dakuma share, please










Amnah El Yaqoub ✍️
[6/19, 10:55 PM] El Yaqoub: ❣️DANGI 'DAYA❣️

{Romance & Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub

Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493



15&16


Baqin ciki yakama Momy, batasan lokacin data rungume Nihla ba suna kuka tare, Nihla kukan abu uku takeyi, na farko yanda ta dauki Abba aranta, take jinsa na daban acikin zuciyarta Tun tana qarama, amma karshe ga irin abinda yamata, na biyu Diddi, ta tabbatar da ace tana raye, zataji Dan sauqi acikin zuciyarta, na uku mafi munin yanda yafadi kalmar baya sonta acikin bainar jama'ah

Momy kam Baqin ciki yahanata magana tama kasa Dagowa ta kalli idon kowa saboda abin kunyar da d'ansu ya aikata

Hajiya Farida bataji dadin abinda akaiwa Nihla ba, yanda take shiri da Mai Hakuri bataso wannan abu yafaru akan yarsa ba, kowa yasan cewa yaran Babu Wanda yakeso, amma dukda haka ai basuyi magana ba

Hajiya Abida mahaifiyar Ilham tayi shiru abun duniya yayi mata yawa, wannan abin takaici da yanzu harda Ayshanta za'ace baza'a iya aura ba


Ran Daddy yayi mutuqar baci akan abinda Abba yayi, haqiqa ya kunya tasu agaban mutane, ya nuna musu cewa ba'a isa dashi ba

Ahankali yadago kansa ya kalli al'umar dake gabansa yace "amatsayina na babba acikin wannan family daga ranar yau, na yankewa wannan yara ranar aure, nanda wata daya Mai zuwa"

Ahankali Momy tatashi taja hannun Nihla suka futo daga cikon hall din, qafar Nihla sai hard'ewa take saboda yanda ake Kallanta
Suna fita shima Usman yatashi yayi gaba ransa abace, Aliyu ma ya biyo bayansa, yayinda farouq shima yaga to zaman me zaiyi? Yatashi yabiyo bayan 'yan uwansa

Sai ajiyar zuciya Nihla take ja saboda yanda taci kuka, ta kalli Momy tace  "Anty inajin zazzabi" daga haka tashige cikin dakinta tafada kan gado tana sakin sabon kuka

Momy ma ta doru abayanta,tana zuwa taganta tana kuka, tasa hannu tadagota ta rungumeta tana bubbuga bayanta alamar rarrashi, saida taji ta rage kukan sannan tadagota tana kallan idonta tace "Nihla, zaki iya rabuwa da Abba? Ki cireshi gaba daya daga cikin zuciyarki?"

Hawaye ne yazubo mata tace "Anty inason ya Abba sosai, bazan iyaba Anty"

Momy tace "zaki iya Nihla"

Girgizakai tayi alamun a a, sannan ta koma kan gado tarufe idonta da fillo tana kuka
Jikin Momy yayi sanyi, taso ace Nihla zata iya rabuwa da Abba, dasai ta nunawa Abba Dan hakin daka raina Shike tsone maka ido, to amma yaya zatayi tunda yarinyar ta dage akan tana sonshi? Dole shi zatayi wa dole akan saiya amince da wannan auren
Tana gama wannan tunanin tafuto daga dakin domin zuwa wajan Abba, dasu Usman tafara cin karo afalon azaune, kowa ransa Babu dadi

Batace dasu komai ba tashige dakin Abba, suma sukabi bayanta dukansu

Suna shiga dakin suka sameshi yana zuba kayansa acikin jaka, Momy ta kalleshi tace "ina zakaje?"

Fuskarsa atamke yace "Momy already hutu na yaqare Zan koma bakin aikina"

Usman yace "Abba kanada hankali kuwa? Kasan abinda ka aikata zakayi dana sanin sa agaba ko?"

"bana tunanin haka yaya Usman, wai meyasa kuka kasa fahimta tane? Saboda me Zan boye mata gaskiyar abinda yake raina?"

Cikin zafi Aliyu yace "to Dan uwarka baka isaba,  wacce yarinya kakeso dazaka Wulaqanta Nihla akanta? Wacece?"

Kai tsaye yace "sunanta Nadiya, tana Abuja, tare mukai karatu da ita a germany"

Momy tace "Abba,yarinyar nanfa marainiya ce, agabanka mahaifiyar ta tace idan ka girma da kanta zata samo maka matar aure, kana tunanin tanada wadda zata samo makane bayan Nihla? Ashe yanzu da ace Aisha tana raye a gabanta zaka watsawa yarta barkono a'ido? Banasan abinda zakazo kana dana Dani akansa nan gaba "

Shiru yayi Bece komai ba, farouq kam me raguwar zuciya hawaye yake sharewa yakasa cewa komai tunda suka shigo dakin, sai yanzu yadago kansa cikin hawaye yace  " Momy nizan aure ta"

Kallansa Abba yayi jin irin furucin dayayi, yarasa meyasa duk suka damu kansu akan Nihla, shima yanaso yaga ya faranta ransu ta hanyar amince wa to amma Nadiya fa?

Aliyu yace "farouq bazaka aure taba, shidin shine dai zai auri yarinyar, da yanaso da bayaso"

Momy ta kallesu tace "ya'isa haka,"

Taci gaba da cewa "Abba idan na isa dakai, amatsayina na mahaifiyar ka to inama umarni akan ka auri Nihla, nide amatsayina na wadda tayi renon cikin ka Nihla tafi kwanta min a raina, idan kuma nima zaka nunamin ban'isa dakai bane shikkenan katafi kabar Mazawaje family din Kamar yanda mahaifin ka yace, su Usman ma sun isheni "
Dasauri tafice daga cikin dakin saboda wani sabon kuka daya Taho mata

Farouq ya kalleshi yace  " danma kasamu yarinyar tana sonka, duk tarasa wazata so acikin mu saikai, kaje kayi tayi, kada Allah yasa ka amince, bazata rasa masoya ba"
Yatashi yafice daga dakin, su Aliyu suka mara masa baya suka Barshi shi kadai a dakin

Ahankali Yazauna yadafe kansa 🤦🏻‍♂️
Meyasa kowa yakasa fahimtar sane?

❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Daddy tunda yadawo daga wajan taro Yazauna afalon nasa yayi shiru yana tunani, yanda Aisha tatafi tabarshi ai dole ya kyautatawa yarta, yanajin Nihla aransa sosai, duk lokacin daya bude ido yaganta yanajin dadi, bayasan abinda zai rabashi da yarinyar kokadan,
Su Usman suna zaune afalon suma, ya kallesu fuskarsa Kamar Babu damuwa yace "kume kuke jira anan ne? Tunda angama ai yakamata kutafi gida ko?"

Babu musu suka tashi, amma farouq kansa har ciwo yake saboda yanda yayi kuka
Momy ce tafuto tafon taga Daddy azaune shi kadai, tazauna kusa dashi tace "Sannu da zuwa Alhaji"

"yawwa Rahma sannu, ina wannan yarinyar take?"

"tana daki, zazzabi ne yadan rufeta, amma na bata magani tasha, nabarta tahuta"

Jinjina kansa yayi batare dayace komai ba, itace tasake kallansa tace "Alhaji nasamu Abba munyi magana dashi, ya amince da auren, yana cikin dakinsa baitafi ko'inaba, kayi hakuri akan abinda yafaru"

Ajiyar zuciya yayi "ai nayi tunanin yatafi wajan wadda yakeso din, da saide yanemi wani uban, amma baniba"

Itama Jinjina kanta tayi, tace "yana ciki, kayi hakuri Allah yahuci zuciyarka"

Batare dayace mata komaiba yatashi yayi cikin dakinsa

Awannan rana haka Nihla tawuni adaki ko falon bata futoba, gaba daya family din Babu mejin dadi aransa

Acikin yammatan ma Babu wadda taje wajan kowa, ko wacce tana part dinsu tanaji da abinda yadameta

Bayan sati biyu tana zaune a dakinta, yammatan suka zo wajan ta, kullum tana zaune adaki, abincima saide Momy takawo mata, kunyar ma hada ido take da Abba saboda yanda take shishishige masa amma yayi watsi da'ita

Ilham ta kalleta tace "Nihla har yanzu kinqi sakin ranki, yakamata ki Manta da abinda yafaru fa, duk kin rame"

Dida tace "wallahi kuwa, ni bazan d'orawa kaina ba, muma nan dukanmu hakuri mukayi, dama yaya Adam naso, kuma yanzu anbawa Diyana shi"

Tsaki Diyana tayi tace "ni wallahi Dida kina qara ba tamin raina idan kina hadani da wannan mutumin, arasa Wanda za'a bani sai malami, ni kunyar fita ma nake wallahi, adinga nunaka ana ga matar Malam" 🤦🏻‍♀️

Ilham tace "nide bansan yaya Zan zauna da yaya Aslam ba, agabana Anty aysha take wayar soyaiya dashi amma wai ace shi Zan aura, haba aida kunya, amma Zan bashi girman sa yanda yakamata, renin hankali ne bazan daukaba, idan ya min wallahi ramawa zanyi, Dan dagashi har Hajiya Na'ila bazan dauki renin wayonsu ba "

Ta kalli Dida tace" kekuma Dida wannan shiru shirun naki wallahi saikin Barshi, bar ganin yaya Fawaz yaya nane wallahi idan yamiki kicire kunya kirama "

Ahankali tace" inani ina shi Ilham, bazan iya bama, kowa yayi sabgar gabansa "

Diyana ta kalli Nihla tace" ke ya batun yaya Abba kuwa?"

Tace" bansani ba Diyana, Tun lokacin da abin yafaru ban qara haduwa dashiba, banyi tunanin zaimin hakaba, abin takaicin ma shine yanda nakasa cireshi a raina, har yanzu ina nan ina jinsa acikin raina, abinda yake bani tsoro Diyana shine idan na kwanta bacci kullum sainayi mafarkin sa, dana kwanta dashi a raina daban kwanta dashi a raina ba "

Gaba dayansu sun tausaya mata, Dida tace" kiyi hakuri Nihla, lokaci ne "

❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Tsaye suke a compound din gidan shida Abba, Aslam ya dubeshi yace  "Abba biki yanata matsowa bamu gayyaci kowaba"

"nifa Aslam mantawa nake da wannan auren, babu wanda Zan gayyata, tunda sundage saina aure ta, ayi bikin kawai, naji haushin wasiyyar nan, akan wannan qullin nasu suka hana wannan family yin taron komai, wai saboda sun tanadar mana Babban taro agaba, mutsw "
ya qarasa maganar dajan tsaki

Aslam yace" to aikai Dasauqi Abba tunda Nihla zaka aura, amma nifa, qanwar budurwa ta fa, gata da rashin kunya yarinyar "

" idan tayi maka rashin kunya ka zaneta kawai ka wullota waje karufe gidanka "🤣
Cewar Abba

Ajiyar zuciya Aslam yayi" Abba duk cikin mu kaida Fawaz ne kukai sa'ah, Nihla tana sonka sosai "
 
" So, so, so, maganar kenan dai, Aslam narasa gane meyasa qananun yara suke daukar kulawa amatsayin soyaiya, kaga mubar wannan maganar dai, na turawa wajan aikina takarda inaso su yimin transfer nadawo gida "

" hakanma yayi Abba, kaga zamufi samun damar kammala abubuwan damuke buqata na company "



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

"my son, kacika rigima dayawa, idan kazo gidan me zakayi? Mami d'inka tana nan lafiya, saini nikuma kana ganina idan nazo"

Shiru yayi yana sauraron yaron nasa, saida yagama jin abinda yace sannan yace "to shikkenan naji, idan kazo ma bazan barka ka kadede ba zaka koma, Allah yakaimu next week din, Yaya batun kayaiyakin da nace katuro? Katuro kuwa?"

Cikin muryarsa Mai cikeda Aji yace "anturo su, zuwa jibi zasu qaraso"

"Ok to, to, ba laifi, zan fadawa mami dinnaka zuwan ka"
 daga haka suka yanke wayar, yana juyowa bayansa yaga Ibrahim Mai hakuri, nan take ya fadada fara'arsa yace "a a mai hakuri, kace kana tafe"

Baba yace "ina nan wallahi Alhaji, ai nazo na tarar kana waya, shine nace bari naqyaleka kagama tukunna"

Cikin murmushi yace "eh wallahi ina waya da yusif ne Dan wajena, yadage yanaso nabarshi yazo gida yaga maminsa"

Baba yayi Murmushi yace "to Alhaji abarshi mana, aiya dade yayi kokari ma, daga karatu anzarce harkar canji ai yaro yayi hankali saide muce Allah yaraya mana"

Yace "hakane kam, Mai hakuri abinda yasa nakiraka shine dama nayanke shawara zamu koma Abuja da zama nida Mai dakina, saboda harkokin nawa sunfi yawa Acan, shine nakeso kaima ka shirya akwai wani aiki na canji danake so na doraka akai, idan Babu damuwa inason mutafi gaba dayanmu harkai, mu koma can gaba daya "

Cikin tsananin murna baba yafara yiwa alhaji isma'eeil godia, Alhaji yace" Babu damuwa, sai ka fara shiri, wani satin idan Yarona yadawo, zamu wuce insha Allah "

Cikin tsananin murna baba yace zai shirya, haka suka rabu da maqocinnasa cikin farin ciki

Yana shiga gida yafara hada kayaiyakin gidan yanata farin-ciki, wayarsa ce tayi qara, yana dubawa yaga hajiya Farida ce mutuniyar tasa, cikin farin ciki yadaga wayar "Barka da wannan lokaci hajiya Farida"

Itama anata bangaren "tace yawwa Mai hakuri, mu munata shirye shirye, amma banga yan yalleman sunzo ba"

"shirin me kuke hajiya?"

Tace "Ah Mai hakuri karka cemin bakasan ansawa yaranmu ranar aure ba? Kuma danaga harda Nihla shiyasa nace bari nakiraka naji yaushe zakuzo"🤣

Cikin mamaki yace "ranar aure kuma hajiya Farida?"

"qwarai kuwa, wani satin ma aure idan Allah yakaimu"

Yace "subhanallah wallahi bansaniba hajiya, banida labari, waye ne Nihla zata aura?"

Tace "Abba aka bata, saboda anbi tsarin wasiyya ne da iyayen mu suka bari, shine sukace ahadata da Abba, abin takaicin ma shine yaron baya sonta, acikin bainan Nasi yafuto qarara yace bayaso"

"subhanallah, subhnllh, banida labari hajiya, Allah yakiyaye gaba,"

Tace "amin Ibrahim to sai anjima"

Shima yace mata "to hajiya Farida nagode sosai"

Wayarta takashe tana tunani aranta, anya kuwa Mai hakuri Babu abinda yake damunsa? Afada maka wannan maganar amma kace Allah yakiyaye gaba,? lalle kuwa in hakane ya tabbata Mai hakuri 🤣

Shiru yayi yariqe wayar a hannunsa, me Alhaji Abubakar yakeji da shine? Za'ayi bikin yarsa ta cikin sa amma bashida ikon da za'a kirashi Afada masa amatsayin sa na ubanta? 🤔 Wannan wanne irin iko ne?


❣️❣️❣️     ❣️❣️❣️

Zaune suke a part dinsu, shida Momy, yasaka qananun kaya, farin wandon jeans, sai riga marar hannu, yana zaune afalon suna kallo shida Momy, gaba daya tamanta dashi awajan, harkar gabanta kawai takeyi, Dan wani irin haushi takeji aqasan ranta, yana Kallanta Tun dazu take ta hada wani abu da madara, daga gani zai yi dadi sosai 🤣
Nihla ce tafuto, jikinta sanye da kayan bacci amma ta dora Babban hijabi akai,dogo ne sosai Tsawon sa har qasa, daqyar kake gano qarshan wandon jikinta saboda tsayin hijabin 🤣
Tana ganinsa afalo tayi turus, nan da nan gabanta yafara faduwa, ahankali ta qaraso cikin falon itama tazauna, tunda akai meeting dinnan sai yau taganshi

Tunda tafuto yake Kallanta, cikin ransa yake cewa kullum tana cikin hijabi, yarasa metake boye wa, yarinya qarama ta d'orawa kanta wahala 😂, kullum ka takura kanka acikin hijabi kome zata boye masa bayan yagama yimata wanka? 🤔 🤣

Ahankali ta dago kanta, karaf suka hada ido, cikin sauri yakawar da kansa gefe, Kamar ba shiba
Ajiyar zuciya tayi tace "Ya Abba ina kwana?"

Ataiqaice yace   "lafiya"

Haushi yakama Momy, taso ace Nihla tayi banza dashi wallahi, domin kawar da bacin ranta yasa tadau cup din maganin tsumin data hada mata tace "Nihla ungo wannan kisha"

Dasauri ya kallesu, yayi tunanin shi zata bawa yasha ashe wannan yarinyar take hadawa? Kona menene oho musu

Dauka tayi tafara sha, abin yanada dadi Dan haka Babu musu ta shanye shi tsaf

Yana ganin ta shanye cikin ransa yace gaskiya ne, yanzu Momy bata sonsa 🤣, kowa dakowa Nihla Nihla Kamar abin sihiri 🤦🏻‍♂️

Kallanta yayi Babu ko d'ar yace mata "Am Zan'iya samun coffee?"

Ba Nihla kadai ba, hatta Momy saida tayi mamakin qarfin halin Abba
Batare da tace komai ba tatashi taje kitchen tahado takawo masa, daga nan tawuce daki, bata qara dawowa falon ba, Dan ganinsa ma zai iya qara mata wata soyaiyar tasa acikin zuciyarta


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

"umma Tun safe gashi har yamma tayi amma yaya Fawaz yana dakinsa yana bacci, saikace me baccin mutuwa"

Hajiya Abida tace "Ilham kenan, zai wuce qwaya yasha ne? Jiya idona biyu har karfe biyu Fawaz bai dawo gidaba, sai wajan biyu da kwata yadawo shima ina Tambayar sa daga ina yake yafara min magana cikin maye alamun wajan abokansa yaje suka sha tare, nasan shine yasa har yanzu bai tashi ba"

"to amma ummah meyasa yaya Fawaz bazai daina halinsa ba? Kayi ta bankawa cikinka kayan maye baka tsoro suma illa? Gashi ko sallah baiyi ba"

"Hmm Ilham ni kaina al'amarin Fawaz yana bani mamaki, kinga babanku yayi masa maganar aiki yafara zuwa office amma Fawaz yayi biris, inajin haushin yanda ake kiran dana Mashayi, Allah ya shirya minshi kawai"

"Ilham tace" amin ummah, gabana yana faduwa idan natuna da ranar bikin nan ummah "

" kiyi hakuri, insha Allah komai zaizo da sauqi, kitashi kije gidan safara'u sister na, tamin maganar gyaran jiki "

Haushi yakama Ilham, wai gyaran jiki, tarasa wa zata gyara wa jiki sai saurayin yayarta🤦🏻‍♀️

Suma su Dida haka hajiya Farida tasasu agaba tahada musu kaza kowa dai-dai,
 Diyana kuwa tafi bata maganin matsi, saboda ita kanta batasan adadin mazanda yarta takula ba🙆🏻‍♀️🤣

Haka akaci gaba da hidimar biki kowanne bangaren Babu maiso, har Allah yakawo satin biki


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Rana bata qarya, ayaune aketa hada-hadar daura aure, iyaye maza kowa ka kalli fuskarsa zaka ganshi yana farin ciki, amma iyaye mata kowa da abinda ya isheta
Tun karfe goma mutane suke ta tururuwar zuwa wajan daurin auren, saboda iyayen maza sun sanar, su kuwa yaran a tsakanin su ko walima Babu Wanda yahada

Angwaye kowa yayi kyau da fararen shaddodin da Alhaji Basiru ya dinka musu, Kamar ka sacesu ka gudu

Kowa ya hallara acikin Babban masallacin unguwar domin daurin auren, liman ya gyara zama da nad'in rawanin kansa, yace "to Alhamdulillah , wanne za'a fara daurawa?"

Alhaji Baqir yabashi sunayen yaran a rubuce kowa da matar sa agaban sunansa

Adam -maryam(Diyana)
Fawaz-Khadija (Dida)
Aslam - Ilham
Abubakar - Fatima (Nihla)

❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Tun safe yafuto daga gida yanaso yaqaraso gidan  amma matsalar go slow tasa ya makara, mutanan daya gani a masallacin unguwar ya tabbatar masa da cewa anan ake daurin auren, kai tsaye yatafi masallacin shima,
Kutsawa yake cikin dandazon jama'ar wajan har ya qarasa cikin masallacin

Adede lokacin liman yake cewa "yawwa Alhamdulillah saura na mutum daya kenan,"🤣

Ladan yace "eh saura na Abubakar da Nihla"

Qarewa mutanan wajan kallo yayi, Alhaji Baqir, Daddy, Alhaji Basiru, da Alhaji habib mijin hajiya Farida, dakuma mazan family din baki dayansu su Usman dasu Aslam Wato Angwaye

Dasauri yadaga hannu yace "A dakata!!"

Gaba daya idanu suka dawo kansa, Daddy cikin ransa yace "Mai hakuri"

Amma afili baice dashi komai ba, yazuba masa ido yana kallansa

Baba ya kalli liman yace "ala gafarta Malam, nine mahaifin Nihla, amatsayina na ubanta ban yarda adaura wannan aure ba, yarinya ta kawai nazo dauka, ita nake buqata"

Ko kallan Inda su Daddy suke baiyi ba, bare gaisuwa ta hada su, yajuyo yafice daga cikon masallacin, yanaji ta cikin Speaker anata salati 🤣🤣

Daga nan baba ya koma gidan,ya tsaya abakin get, yasa maigadi yashiga gidan yakira masa Nihla, ace inji babanta tazo

Maigadi kai tsaye yatafi part din Momy, jama'a sun taru anata hidimar biki, gaba dayansu yanmatan suna zaune a dakin Nihla, Mai kwalliya tana tsantsara mata

Diyana ce tafuto falo tana amsa wayar wani saurayinta 🤣
Maigadi yana ganinta yace "yawwa Diyana, kicewa Nihla babanta yana kiranta, yana can abakin get"

Ta amsa masa sannan ta amsa wayarta tajuya dakin tace "Nihla babanki yana bakin get, yace kije"

Yanda ta dade tana kiran wayarsa Yaqi ya amsa, tana tura masa saqo Yaqi yayi reply, hakanne yasa ta naji ance babanta tatashi tace "Baba nah!!!"

Sannan ta kalli maiyin kwalliyar tace "ina zuwa, bari naje nashigo da babana ciki"

Futowa tayi, Momy bata lura da ita ba tanata baqi
Kai tsaye Nihla tafuto bakin get din ko mayafi Babu🤣

Tana zuwa taganshi fuska Babu Rahma tace "Baba!!!"

"wuce mutafi gida" abinda yace da ita kenan

Mamaki yakamata, bata taba ganin baba cikin fishi irin wannan ba, tace "Amma baba Anty...."

"Kiwuce mutafi gida nace!!!"

Yadaka mata tsawa

Tace "To baba Babu ban dauko hijabi..."
Kafin ta qarasa yaja hannunta, suka fara tafiya, sai dankwalin da aka nad'a mata akanta ta ware tayafa a jikinta 🤣

Suna zuwa bakin titi yatare musu adedeta suka shiga, gaba daya tarasa gane kan baban nata, tashar Mota sukaje, daga nan suka wuce jigawa

Awa biyu ce ta kaisu gida, kuma har lokacin Bece da'ita uffan ba, suna zuwa kofar gida sukaci karo da motar Alhaji Isma'eeil qirar Range rover

Alhaji Isma'eeil yace "Mai hakuri ina ka shiga Tun dazu angama zuba kaya amota kai muke jira?"

Baba yace "Alhaji wallahi kano naje Tun safe, yarinya ta za'ayi wa aure batare da iznina ba, shine naje nadauko ta"

Adede lokacin yafuto daga gidansu shida mami, karaf maganar tasauka acikin kunnansa, Dasauri yakai kallansa kan yarinyar da ake magana akai
"Nihla my friend" yafadi sunan cikin ransa, fuskarta ya qarewa kallo har yanzu kyanta yana nan saima qaruwa dayayi

Cikin mamaki yakalli baba yace "Baba wai wannan yarinyar za'ayi wa aure?"

Ko a mafarki taji wannan muryar bazata taba mantawa da ita ba, kallansa tayi tafara magana cikin ranta "yaya Yusif! Innalillah.. Yaushe yadawo? 🤔

Alhaji isma'iel yayi Murmushi yace" Mai hakuri, hakuri yaqare kenan "🤣

Mami da baba sukai daria, Nihla tayi shiru, ga tashin hankalin rabuwarta da yan kano ga kuma mamakin ganin yaya Yusif

Handbag din mami ce a hannunsa, ahankali ya matsa ya wullawa Nihla jakar yace  "ke riqe wannan "

Dasauri ta cafe jakar, saboda karta fadi qasa

Alhaji isma'eeil yakalli Yusif yace "nasa Mai gadi yadauko kayan Mai hakuri ansaka amota, bani key naja motar da kaina, ban yarda da driving dinka ba na ganganci, idan kuka samu titi kuna gudu Kamar bakwa son ranku" 🤣

Sumar kansa ya sosa,sannan yabashi car key din

Sai a lokacin Nihla tagaidasu, mami da Alhaji Isma'eeil suka amsa mata cikeda kulawa

Alhaji ne yabude motar yashiga, shima baba yashiga gaba, mamy da Nihla suka shiga baya, sannan shima Yusif yashiga bayan daga daya bangaren, Yazauna agefen mamy

Mamy ta kalli Nihla cikin kulawa tace "Nihla kinsha hanya sosai ko 'yata, nasan kin gaji, zoki kwanta kihuta" 🤣

Taja Nihla jikinta sannan ta dora kanta akan cinyarta tana bubbuga bayanta Kamar wata qaramar yarinya

Shikuwa Kallanta yake, Wato bazatayi masa magana bako? It means batayi missing dinsa ba,koda yake yaushe zatayi masa magana tunda ta Manta dashi harta samu wani zata Aura (tofa🤔)

Ahankali Alhaji isma'eeil yatada motar, suka dauki hanyar Abuja.













To Alhamdulillah anan na kawo qarshen labarin DANGI DAYA, zan Dakatar da typing dinsa badan komai ba saidon Comments din readers da ban gamsu dashi ba, sharhi yayi qaranci, idan akwai wadda na batawa rai Sanadin wannan labari to tayi Hakuri 🙏🏻


WhatsApp readers banida bakin dazan gode muku, kunyi min komai akan wannan littafi
 masu yimin sharhi daga cikinku nayi saving number dinsu insha Allah zansakaku asabon group dina, mudinga gaisawa












Yaya labarin Mazawaje family?

 Wanne hali Momy zata shiga dangane da tafiyar Nihla?

Yaya Rayuwar Nihla zata kasance a Abuja?

Ina labarin amare masu shirin shiga daka ciki?🤣























Amnah El Yaqoub ✍️
[6/21, 1:40 AM] El Yaqoub: ❣️DANGI 'DAYA❣️

{Romance&Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub

Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493





Tabbas hakane, laifin wani baya shafar wani, amma kuma Babu dadi kayi rubutu a karanta ma bayan ansan kanason Comments a share ka, danku nake wannan rubutun, be kamata agani ayi shiru ba, masu kirana, masu min private text, masuyi min magana ta group, da Wanda suka min ta page d'ina, duk naji maganganunku, nagode da soyaiyar dakuke nunamin, insha Allah zanci gaba da typing, daga qarshe wannan page din na sadaukar dashi ga dukkanin masoyan Amnah El Yaqoub 💋

'yan labe ina kuke? 🤔 To Allah yasa ku d'ore dayin Comments ehe😚😚


17&18


Liman ya kalli Alhaji Abubakar kozaice wani abu tunda shi ne babba, amma tashin hankalin da Alhaji Baqir ya hango a fuskar Daddy ne yasa shi yayi magana dasu yace "ala gafarta Malam mungode, mungode sosai,"
Yadauko kudi a aljihunsa masu yawa ya ajiye musu, Sannan yakama hannun Daddy suka futo daga masallacin, Alhaji Kabeer kuma shine yake sanarwa da mutane ansoke daya daurin auren, daga nan yaci gaba da godia ga jama'ar dasuka gayyata

Uban gayya kuwa fuskarsa Babu yabo Babu fallasa Wato Abba
Angwaye dukda dama can suna cikin bacin rai, sai abin yasake qaruwa
Usman yadafe kansa, meyasa baba Ibrahim zai musu haka? Amma aida yayi hakuri anbi komai Ahankali ko, amma abu acikin taron mutanen da sukazo daurin aure

Dan haka yayiwa su Aliyu alama da ido, nan danan suka futo gaba dayansu sukabi bayan Daddy

Su Daddy kuwa saida sukaje bakin get sannan Alhaji Baqir yasaki hannunsa yace "Alhaji kayi hakuri, nasan yanda kake ji acikin ranka, kayi hakuri" ya qarasa maganar yana bubbuga kafadarsa

Su Usman ne suka qaraso, Aliyu yajashi hannun Daddy yace "Daddy Muje ciki"

Alhaji Baqir yawuce part dinsa jiki a sanyaye

Suma sukaja hannun Daddy suka tafi, mutane baqi anata hidima, dasuka shigo kowa sai gaida su yake amma su Usman ne masu amsawa, suna shiga dakin Daddy gaba dayansu suka zauna Babu me magana acikinsu, farouq yafuto daga dakin yayi wajan Momy

Yana zuwa yakama hannun yace "Momy zokiji"

Kallansa tayi tace "jarababbe, farouq Dan Allah kabarni nahuta yau ana bikinma bazaka rabu Dani kaima kaje wajan mutanan ku ba"

Yace "Momy kitaho please"

Fuskarsa ta kalla taga Babu wani wasa ko Fara'ah, mamaki ya kamata, Dan haka kai tsaye tabishi zuwa dakin Daddy

Kujera ta nema tazauna, tace "yanaganku haka jiki a sanyaye? Meyake faruwa ne?"

Daddy yayi shiru har lokacin Bece komai ba, Aliyu ne yafara magana "Momy Wallahi fa ansamu matsala, anfasa auren Nihla da Abba"

Cikin mamaki tace "me kace Aliyu?"

Usman yace "hakane Momy, baba Ibrahim yazo yadauketa, suntafi"

Adede lokacin Abba yashigo dakin, yanemi waje Yazauna, duk Babu Wanda ya kulashi

Momy ta kalli Daddy tace "to Alhaji meyasa zakayi shiru? Yanzu de ka kirashi kafada masa Dan Allah ni yadawo min da yarinya" 🤣

Ajiyar zuciya Daddy yayi, sai a lokacin yayi magana "Ibrahim ya nunamin yafini iko akan Nihla ne, yanda na nuna masa iko da farko, shine yazo har gida ya nunamin yafini iko akanta"

Tace "mekake nufi Alhaji, bangane maganganun ka ba"

Yace "Rahma bayan rasuwar Aisha nashiga tashin hankalin da ban taba fuskantaba, Nihla kadai Zan gani naji dadi, ita kadai Zan gani yarinyar inji Kamar Aisha tace akusa Dani, hakan yasa lokacin dazamu dawo gida kai tsaye nace ku fito mutafi, saboda ina tsoron inyiwa Mai hakuri magana yace bazai ban itaba, nasan shima yaji mutuwar Aysha, Awannan lokacin bazai taba yarda yarabu da 'yarsa ba, nikuma Rahma bazan iya tahowa nabar jinin Aisha Awannan wajan ba, shiyasa nadauko ta muka Taho batare da iznin mahaifin ta ba "

Momy tace "Innalillahi wa inna ilaihir raju'un,"

Dukda taji gaskiyar magana a bakinsu, wani bangaren na zuciyarta bai yardaba, wayarta tadauka takira layin Nihla, Adayan bangaren wayar tana hannun Dida tana ganin sunan Anty tasan cewa Momy ce, saboda ita kadai Nihla take cewa Anty

Ta daga wayar tace "Momy Nihla tafita bakin get, wai babanta yazo"

Kashe wayar Momy tayi tace "Innalillah... Yanzu Alhaji shikkenan Nihla tatafi? Inaji ina gani anrabani da 'yata..." Sai kuka

Su farouq suka dawo gefenta suna bata hakuri, takalli Abba tace "duk abinda yafaru, laifin ka ne, Inda ace baka nunawa yarsa qiyayya ba, babu abinda zaisa Ibrahim yazo yatafi da ita, idan ma akan antaho da ita batare da sanin sabane to danaka laifin, na tabbatar labari yaj...j...ji" numfashi tane yafara sama

Anan maganar ta tsaya, numfashinta yana qara yin sama, cikin tashin hankali Abba yataso yacire Babbar rigar jikinsa yayi wulli da ita 🤣
Ya cacimeta yana kiran "Momy! Momy!!,"

Amma inaaaa, numfashinta ne kawai yake sama, qirjinta sai Dagowa yake, lokaci daya kuma, jikinta yasaki

Cak Abba yadauketa yadawo da ita kan gadon Daddy, farouq yadauko ruwa a fridge ya shafa mata, Usman kuma yafara kiran number family doctor nasu yace gashinan zuwa

Saida tadauki lokaci kafin ta farfado, tana bude idonta tafara kuka, Daddy yanaga yashiga tashin hankali ashe duk abinda yakeji Rahma tafi shi 🤣
Mamaki yagama kashe Abba, yanzu duk saboda Nihla suke wannan abun? Lalle ba qaramin so suke mataba

❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Sai yamma liss suka sauka, saboda Alhaji Isma'iel bayasan gudu, futowa sukai daga ciki motar, Yusif yasaki miqa yana fadin "wash Allah" idonsa akan Nihla

Mami tace "Yusif banasan wannan san jikin fa, to yanmata de basason rago, oya bude boot ka dauki kaya mushiga"

Yace "yanzu ni dinne rago?"

Murmushi tayi, ta kalli Nihla data shagala wajan kallan hadadden gidan, yanzu itace zatayi rayuwa acikin wannan gidan? Duniya kenan
Mami tace "Muje ciki Nihla"

Fuskarta Babu yabo ba fallasa tace "bari nadauki wata jakar mami"

Kusadashi taje ta tsaya, shi beyi mata magana ba itama haka, haushi yaqara kama Yusif, duk murnar dayake zaizo yaganta yaga yanda takoma amma shine tashareshi, 🤣
Cikin fishi yadauki jaka guda daya yamiqe zaiyi ciki
Dasauri ta tareshi tareda miqa hannu zata karbi jakar tace masa "kawo jakar"
Lokaci daya hannunsu yahadu dana juna, kallan hannunta yayi zanen qunshin da akayi mata yayi kyau sosai, Dasauri ya fizge jakar yace "no Barshi kawai"

Daga haka yayi ciki, sai wata tadauka acikin boot din tabiyosu ciki

Dakinda zata zauna mami ta nuna mata, sannan tashige ciki, anan taga babanta yana ciki, yana futo mata da kayaiyakinta na sakawa daga cikin jakarsa, cikin ranta tace dama de baba yagama shirya komai

Jakar yadauka yatafi Inda akayi masa masauqi daga can baya

Yana fita taga wayarsa ya mantata, Dasauri tadauka tasaka number Momy tafara kira


Acan kano kuwa gida duk ya hargitse yanmata duk sun shiga damuwa saboda labarin tafiyar Nihla, Ilham tafi kowa Baqin ciki saboda Babu abokiyar shawara antafi, Dan dole ake saka su abu su yi, yanzu ma wanka akasa ko wacce tayi domin anjima kadan za'akai kowa dakin mijinta

Apart din Momy kuwa kowa sai neman ta yake yarasa, tunda tashiga dakin Daddy bayan doctor yazo yagama dubata bata sake futowa ba, wayartace data Nihla  a gefenta, adede lokacin wayarta tafara qara, Dasauri ta dauka tace "Ibrahim Dan Allah kayi hakuri, munsan munyi maka laifi amma kayi hakuri kadawo min da yarinyar nan" hawaye yazubo mata tasa hannu tashare

Kuka Nihla tafara tace "Anty kidena kuka nice"

Dasauri tace "Nihla kece? Kina ina, gida kuka koma?"

"Anty gida baba yadawo Dani, amma yanzu muna Abuja, mun tafi Abuja gaba daya da zama Anty"

Momy tace "Innalillah...Nihla banji dadi ba, banji dadin tafiyarki ba yata, kiyafemana kinji?"

Tace "Anty kidena neman yafiyata ba kiyimin komaiba, kedin Kamar mahaifiyata ce"

Momy tace "to ai kinji Nihla, kema kikace kama, ba kama nakeso nayi da mahaifiyar ki ba Nihla, sonake ki daukeni amatsayin mahaifiyar ki, ki kirani da Momy Kamar yanda 'ya'yan cikina suke fadamin, ke dasu bakuda banbanci a wajena"

Jikin Nihla yayi sanyi sosai, bata taba sanin cewa Momy batasan Antyn datake fada mataba sai yau, ashe haka Momy take kaunarta? Wannan wacce irin soyaiya ce? Kasa magana tayi sai kuka datake sosai abaiyane

Alokacin baba yashigo yadawo daga masallaci kenan, tana ganinsa takwashe wayar, idonta jajir, tana share hawaye

Zama yayi agefenta ransa abace yafara magana "ke saboda rashin hankali, da hauka dayake damunki zaki zauna kinawa mutumin dabai damu dake ba kuka,? idan akayi muku auren waye zai wahala bayan ke?
Anayi wa mace auren dole kuma tayi hakuri tazauna din, amma namiji karkiyi tunanin lokaci daya zai hakura Yazauna dake amatsayin matar sa, yaron yafuto yace bayasonki to kema ki cireshi aranki, sannan daga yau ko awaya ne ban yarda ki nemesuba, "

Yana fadin haka yafice yabar mata dakin

Innalillahi... Baba bai taba fishi irin wannan ba, dama ance ka kiyayi fishin mutum Mai hakuri
Wai ita ta d'orawa kanta soyaiyar yaya Abba ne? Yaya zatayi da Rayuwar ta? Yanzu yaya Yusif yadawo amma ta gagara yimasa magana, ba kuma komai ne yasa hakanba sai tunanin datayi akan Abba, yadawo daga wata qasa tabi ta shishshige masa, daga qarshe ya Wulaqantata, tana tsoron shima tayi masa magana daga qarshe yayi mata Wulaqanci, itada shigewa maza har abada, ya Abba ya koya mata Hankali 🤣


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Shadaya da rabi kowa ya watse daga gidan amare anbarsu su kadai, mayafin da'aka lullube mata kai dashi ta cire tayi wulli dashi tafara fada "ina dalili Zan takura kaina akan wannan malamin, kun wani rufeni da mayafi ai zafi sai yamin illa" 🤣

Saukowa tayi daga gadon, tafara cire kayan ta, daga ita sai under wear a jikinta, tadauki towel tashige wanka, da ruwa Mai Dan dumi tayi wankan saboda gajiyar biki

Tana futowa daga wanka tadawo gaban mirrow tafara shafe jikinta da turare, ko kayan bacci bata nemaba ta kashe wutar dakin ta kwanta bacci
🤣
Shikuwa Ango Adam sai wajan sha biyu yashigo gidan, hakanan gabansa yake faduwa saboda baisan mezai tarar ba
Falon yashigo da sallama, yaga Babu kowa, wucewa yayi zai shige dakinsa amma wata zuciyar tace yakamata kaje kaduba yarinyar nan, haqqinta yana kanka

Dan qaramin tsaki yaja Kamar anyi masa dole, yakoma baya sannan yabude dakin nata yaga duhu, zuciyarsa daya yakunna wutar dakin, lokaci daya yayi arba da santala santalan cinyoyinta, baccinta take hankali kwance, magana yafara cikin ransa, to yanzu wannan tayaya zakai tunanin yimata maganar sallar da akeyi raka'a biyu ga sababbin aure? 🤔
Kallanta yasakeyi sosai, Diyana tanada komai da d'anamiji yakeso awajan mace but ba yarinyar kirki bace, kuma may be hakanne yasa take tallar jikinta awajan sauran maza

Bata son haske inde tana bacci, ko yaya taga haske tofa zata farka, yanzu ma cikin magagin bacci tabude idonta taganshi a tsaye yana qare mata kallo 🙈
Cikin ranta tace jikinnan dai haka za'a ganshi abarmin kayana
Tashi tayi zaune, har towel din yana kwance wa kana iya hango nashanunta takalleshi tace "Yawwa nace ba, idan kagama kallon ka kashe min wutar dakin please, banasan haske idan ina bacci" 🤣

Tana fadar haka tayi juyi ta rufe idonta, Adam kuwa kunya ce ta kamashi, karfa yarinyar nan tayi tunanin neman wani abu yazo wajan ta, tsaki yaja, yafice daga dakin ko kashe wutar baiyi ba

❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Ilham kuwa tunanin Nihla take tayi, tayi shiru ita kadai agidan, gashi kowa yatafi Babu kowa, tashi tayi tarage kayan jikinta tafuto falo ta kunna kallo ko Allah zaisa ta daina tunanin, gashi tabar wayarta agida bare ta kirata

Tana kwance akan kujera tana kallo har bacci yayi awon gaba da'ita
Angon nata kuwa yana can awajan Abba Yaqi yataho gidan, daqyar yataho gida ganin karfe daya tana neman yi, harda ledar kaza a hannunsa 🤣
Yana shigowa falon yaji qaran tv, falon yakalla tsarin komai yayi masa yanda yadace
Can yahangota tana bacci akan kujera, 'yan qananun kitson da aka mata yayi mata kyau kuma yafuto mata da goshinta, sai fuskarta tayi fayau

Ahankali yataka yaje kanta ya tsaya, kayan baccin dake jikinta ya kallah kana iya hango yanda qirjinta yake azahiri, haushi ya kamashi, ya za'ai wannan yarinyar tasaka wannan kayan tazauna haka tsabar rashin kunya amatsayin sa na saurayin yayarta 🙆🏻‍♀️

Saida yasami dede cinyarta sannan ya d'aka mata duka, cikin firgita tatashi tace "subhanallah,"

Tabude idonta sosai taganshi a tsaye akanta, cikin bacin rai tace "ya Aslam lafiya zakamin irin wannan dukan Kamar agidan kurame? Kira daya idan kamin ai Zan tashi"

"Ok ke saboda tsabar rashin kunya nizaki koyawa yanda Zan tasheki daga bacci?"

Tayi shiru tana jinsa, sosai taji zafin dukan, ledar hannunsa ta kaza ya wullo mata jikinta yace "gashinan kici, idan kuma ba zakici ba shikkenan kinyi wa kanki"

Hararar ledar daya wullo mata tayi, tawurgar da ita awajan tayi cikin dakinta tabarshi awajan a tsaye

Shikuwa da kallo yabita yace "Dani kike zancen"


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

"mami bade kinfara bacci ba"

"wallahi nafara bacci Yusif, ina ka tsaya ne baka dawoba?"

"mami naje wani waje ne, ga Ice-cream nataho muku dashi ko zakusha"
Dukda tana bacci hakan bai hanata murmushi ba, wai ga ice-cream yakawo musu, ita da girman ta ina ita ina wani ice-cream, kawai de yace ga ice-cream na kawowa Nihla 🤣
Kokarin tashi take tace "nikam na qoshi Yusif saide Nihla, bari nakai mata"

Cikin sauri ya Dakatar da ita yace "a a a a, mami aikin fara bacci, kiyi baccinki bari nakai mata"

Tace masa "to saida safe"

Daga dakin yafuto kai tsaye yayi dakin da aka bawa Nihla, abin mamaki a zaune ya taddata tana kallan saman dakin tana hawaye, tana tausayawa Rayuwar ta sosai
Kallanta yayi ya girgiza kansa, sannan yaqaraso cikin dakin
Cikin sauri ta goge hawayen fuskarta tace "Sannu da zuwa yaya Yusif"

Yaji dadin yanda takira sunansa Tsawon shekaru

Zama yayi agefenta kan bedside drower, yakalli abinci agefenta alamun bataci komai ba

Fuska Babu alamun wasa yace "sauko kici abinci"

Babu musu ta sauko, tazauna aqasa, shikuwa be motsa daga Inda yakeba yazuba mata ido yana Kallanta
Abincin ta dauka tafaraci amma wani irin daci takeji acikin ranta, daqyar take tura abincin, idonta yayi rau-rau Kamar zatayi kuka, kafin kace me tuni hawaye sun zubo mata, saikuma tasaki kuka sosai, daga qarshe ma saita saka kanta akan gwiwar ta taci gaba da kuka

Ajiyar zuciya yasauke yadawo kusa da ita Yazauna har tana iya juyo hucin numfashinsa akusa da ita

Haushi ya kamashi, yace "kuka kike akan mijin naki ne?"

Cikin sauri tadago kanta ta kalleshi, sai ganinsa tayi dab da ita Kamar zai sakata cikin jikinsa, nan take yayi mata kwarjini, ta girgiza masa kai tace "a a Anty"

Ajiyar zuciya yasauke, yace "to kici Abincin Karki zauna da yunwa"

Abincin tafara ci amma hannunta sai karkarwa yake, gashi Yazauna dab da ita, duk atakure take tarasa yaya zatayi
Shikuwa ganin haka yasa yakai hannunsa kan nata hannun yariqe, sannan yadauki spoon din da daya hannun yafara bata abaki, babu musu take karba tanaci, cikin zuciyar ta fal tunani, kulawar da dan'uwanta ya Abba yakamata yabata, bebataba amma gashi wani bare yanayi mata

Saida ya tabbatar taqoshi sannan yabata ledar ice cream din daya shigo da ita yace "ga wannan, idan bazaki iyasha yanzu ba, ga fridge nan kisaka gobe sai kisha"

Daga masa kai tayi, yatashi tsaye yace "saida safe"

Daga nan yafice Yarufe mata dakin


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Tun tana jiran zuwan Ango harta daina tahaqura, girman gidan yasa takejin tsoro sosai, gashi bakajin qaran komai, shiru garin, haka tatakure waje daya afalo cikin kujera har bacci yadauketa

Shikuwa fauwaz yanacan mashaya, da temakon Allah da temakon wani abokinsa da sukasha tare yadawo gida, dirin motar da taji ne yasa tatashi afirgice, Agogon falon ta kalla karfe biyu da rabi, tashi tayi tsaye cikeda tsoro
Yana tangadi irinna yan maye yashigo cikin falon, gabanta yafadi, tunda take bata taba ganin mutum murararan cikin maye hakaba sai yau, gadan-gadan yataho wajanta tana ja da baya, har yazo gab da ita, cikin muryar maye yace "keeeee..uban waye yakawo ki nan eh?"

Girgiza masa kai tafara tace "yaya Fawaz Dan Allah kayi hakuri"

Idanunsa yake son budewa sosai amma yakasa, yayi tangal-tangal zai fadi qasa tayi sauri tariqeshi aikuwa saiya dawo kanta gaba dayansa, dagashi har ita sukai baya suka fada kan kujera,  shine akanta ita kuma tana qasa, tureshi tafara kokarin yi amma yamata nauyi sosai, shikuwa jinshi Akwance yasa nan take yafara bacci, kansa ta kalla taga yadora shi akan qirjinta, nan tafara ture masa kansa, amma saiyayi juyi ma yaci gaba da baccin sa
Haka ta hakura ta zubawa sarautar Allah ido, wai ita Dida itace qato Akwance akanta, wannan Baqin ciki da yawa yake 🤣

❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Da asubar fari yafarka daga baccin da yake, amma Idanunsa a lumshe bai budesuba, qamshin turaren dayake shaqa Mai dadi ne yasa cikin sauri yabude idonsa, da fuskarta yafara tozali, mamaki ya kamashi, laushin dayaji akansa ne yasa cikin zabura yadaga mata qirjinta
Tashi yayi tsaye yana qarewa yarinyar kallo, gaba daya kunya ta kamashi, yaushe ya aikata hakan? Yarinyar nan shi tunda yake ko kallo bata isheshi ba ko a family house dinsu, amma tayaya zaizo cikin maye ya kwanta a qirjin yar mutane d'ame d'ame?😳
Cikin borin kunya ya wanka mata mari

Azabure tatashi ta dafe kumatunta, qwallah tacika idonta, cikin tsananin mamaki tace "ya Fawaz menama?"

Yace "ashe dama ke ana ganinki shiru shiru ke 'yar iska ce bansaniba? Ni zakizo ki kwantawa a jiki?"

Hawaye ne suka zubo mata tace "ya Fawaz kaine fa kaz..."
Kafin ta qarasa magana yace "waye yayan naki? Amma kuwa bakiyi sa'ar yaya ba, ki kirani guy, bawani fauwaz kingane ko?"

 cikin dakinsa ya shige fuuuuu, yana zuwa ya zauna akan gado  yadafe kansa,🤦🏻‍♂️ Allah ya soshi ya qwaci kansa awajan yarinyar nan 🤣

❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

"Ibrahim tunda auren yarinyar nan bai iyuba ai bekamata tazauna hakaba ko, yakama ace takoma makaranta"

Baba yadubi Alhaji Isma'iel "to Alhaji wacce makaranta zatayi, kawai tazauna haka har Allah yakawo mata miji tayi aure,"

"A a Ibrahim ba za'ayi hakaba, yarinya zata fara karatu idan Allah yakawo mijin sai tayi aure, akwai maqocina me wannan gidan na hannun damana, already nayi magana dashi, yana aiki a university, yanzu kaje ka dauko min takardun yarinyar Zan bashi, saiya nema mata admission takoma school kawai "

Baba yayi shiruuu, sai can yace" Alhaji da wanne baki Zan gode maka? Alhaji kayimin kayiwa yata? "

" kada kadamu Ibrahim, ai anzama daya "

Alokacin baba yaje ya bincika kayansa yadauko takardun Nihla, yakawo masa, adede lokacin akayi wa Alhaji Isma'iel din kiran gaggawa daga office dinsa,Dan haka yakira wayar mamy yace taturo masa da Nihla, a lokacin suna kitchen suna aiki tare, har Nihla tafara sakin jiki da mamy saboda yanda take janta da fira
Tana fadawa Nihla, tadauki hijabinta dogo tafuto compound din gidan wajansu
Har qasa ta tsugunna tace "gani baba"

Alhaji Isma'iel ya kalleta yace "yawwa yata, kije nan gidan kikaiwa matar gidan takardun ki kice inji ni, tabawa mijinta su"

Cikin ladabi ta karbi takardun tafita

Tana fita taga unguwar shiru Kamar Babu kowa, kowa yana gidansa yana sabgar gabansa
Ilham ce tafad'o mata arai, cikin ranta tace Allah sarki Ilham ko ya take yanzu?


"kaga Mazawaje, nagaji da wannan halin naka, saina dinga kiran wayarka amma kashareni?"

 karo sukayi da juna, har wayar dake hannun wadda take wayar tafadi qasa
Matar tace "subhanallah, qanwata me kike tunani haka har kina bigeni? Bakya kallan gabanki ne?"

Nihla de tayi shiru tana tunani, inde ba kunnuwanta ne suka jiye mata qarya ba, to tabbas taji wannan matar tace Mazawaje, to dawa take waya acikin family dinsu? Dawa take waya acikin samarin dake Mazawaje family? Koda yake may be da d'an wani family din take wayar

Ganin matar ta girmeta yasa tace "kiyi hakuri Anty, wallahi ban kula bane"

Ita kuma matar jin angirmama ta ance mata Anty yasa lokaci daya taji yarinyar ta shiga ranta

Tayi murmushi, tadafata tace "kada ki damu qanwata, kema anan layin kike ne?"

Nihla tace "eh, bamu dade da dawowa ba, kinga gidan mu can"

Matar tace "laaa ai nasan gidanma, to dafatan de zamu dinga zumunci, menene sunanki?"

Tace "sunana Nihla"

Itama tace "ayya suna Mai
dadi, nikuma sunana NADIYA"😳






tofa wata sabuwa, anya wannan zumunci zai dore kuwa?

Shin Nihla ta gane Wacece Nadiya kuwa?


Duk kuci gaba da bibiyata, nagode 🙏🏻
















Amnah El Yaqoub ✍️
[6/22, 1:47 AM] El Yaqoub: ❣️DANGI 'DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub

Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493

19&20

Murmushi Nihla tayi "Allah sarki Anty Nadiya, nagode, bari inje an akenine"

Gidan tawuce zata shiga Nadiya tace "to ai gidanmu ne, Dan haka tare zamu shiga"

Daria sukayi gaba dayansu, sannan suka shige gidan

Nadiya ta lura yarinyar akwai abinda yake damunta, tabbas akwai damuwa a atattare da ita, amma zata jata a jikinta har taji damuwarta, Dan ita kam haka kawai taji yarinyar ta kwanta mata, Kamar qanwarta kasancewar batada qanwa mace sai namiji

Nihla tabawa maman su Nadiya takardun, cikin murmushi takarba tace idan yadawo zata bashi, daga nan Nihla tayi musu sallama tafuto, amma fafur Nadiya tahanata tafiya, qarshe ma dakinta tajata suna fira kadan kadan, Nihla ta lura Nadiya Babu ruwanta, gata da son mutane, Tun tana dari-dari da ita harta sake sukayi  ta fira Kamar sun saba

❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Zaune suke su uku Sunayin break fast, mamy tadubi Alhaji Isma'iel tace "Alhaji Nihla fa batada kayan sakawa sosai, sannan Babu waya ahannun ta irinta 'yanmata,kuma ace wannan kyakykyawar yartawa Babu waya Alhaji, yanzu idan tafita ta samomin siriki wacce number zata bashi?"

Yusif yana jinta, ahankali ya kalleta, yamaida hankalinsa kan Abincin dayake ci

Alhaji Isma'iel yayi Murmushi, yaga alama hajiya tanaso ta maida yarinyar tata Babbar yarinya yace"to hajiya ai ga yayanta nan, suje su siyo duk abinda takeso, idan sun kawo kinga akwai abinda babu saikiyimin magana asiyo mata "

Dadi yakama Nihla ta kalleshi tace"Nagode Dad"

"Babu godia a tsakanin mu Nihla, sannan ga albishir ki shirya zuwa next week zaki fara zuwa makaranta, saide kuma zaki bar mamynki da kewa"
Daria sukayi gaba dayansu

Suna gama cin Abincin suka tafi shopping ita dashi, suna tafiya ahanya Babu Wanda yakewa dan'uwansa magana, shi har yanzu maganar mamy ce take masa yawo a zuciya, wai saboda tabawa samari number Hmm

Ita kuma Nihla ganin Yaqi bata fuska akan maganar yasa itama tayi shiru

Har sukaje super market din ataqaice yace mata "Futo"

Babu musu kuwa tafuto, sukayi ciki

Dogayen riguna suka diba, masu shegen kyau, saida suka duba Wanda sukayi mata dai dai sannan suka dauka, inde yaga kalar riga zata karbi fatar jikinta saiya dauka yaqara musu, har mamaki yake bata
Da sukaje wajan kayan kwalliya komai Set yake dauka
Kallansa tayi "yaya Yusif sunyi yawa fa"

Yace "zaki dade kina amfani dasu"

Daga haka bata qara magana ba, suka koma wajan perfume dakuma inner wears, Kallanta yayi, yanzu kam bashida damar dazai zaba mata, yace "dauki mutafi"

Kunya ce ta kamata, haka ta matsa taba zaba, da yaga tana kunyar sa saiya kauce yabar wajan

Atamfofi kuwa sun kwashe su sosai, sannan suka tafi shagon saida wayoyi

Anan ma Kallanta yayi yace "wacce iri kikeso?"

Tace "irin tawa tada, iphone ce"

Haka nan yaji zuciyarsa tana zargin cewa mijinda zata aura ada ne yasiyamata wayar, cikin kishi yace "dole sai irinta?"

Itama da taga fuska ad'aure Babu alamun wasa sai tace "A a, ko wacce ma asiya inaso" 🤣

Babu musu yasiya mata Babbar waya Qirar Huawei

Sannan suka dawo gida da kaya niqi-niqi

Mamy suka samu afalo tana ganin su tare taji dadi, harga Allah tanason Yusif da Nihla, anan Nihla tabata kayan itama tana gani

❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Cikin satin mahaifin Nadiya yanema mata admission a wata private university, Base university, yayan manya ne acikin makarantar kowa tanajin kanta ita watace, gayu kuwa ba'a magana, ko wacce mace tanaji da tata wayewar
Direban gidan zai kaita yadawo da ita, saide kawai zuwa take, amma bata gane komai, damuwar datake ciki ma ta isheta, gashi babu wanda zatai sharing damuwarta dashi bare ta cire maganar datake ranta abata shawara ko zataji dadi baba yahanata kiran kowa na kano
Ahankali sabon su da Nadiya yake qaruwa harta kai kowa yana ziyartar kowa acikinsu

Yauma bayan tadawo daga makaranta tana daki tana duba hand out, Nadiya ta kirata awaya suka gaisa sannan sukai sallama, dena karatun tayi tafuto falo, anan taga mamy tana zuba danbun nama dayawa acikin wata roba, tace "mamy wannan ina za'a kai?"

"Na yayanki ne, zai tafi dashi yanzu"

"mamy ina yaya yusif din zaije?"

Murmushi tayi, ganin yanda Nihla tayi mata Tambayar cikin sauri haka, tace "china zai tafi, akwai aikin dayake son yayi"

Jikinta ne yayi sanyi, ahankali ta karba tace "to mamy kawo nazuba masa"

Bar mata tayi, tazuba masa sannan tace "mamy bari nakai masa"
Bata jira amsar mamynba tayi hanyar dakinsa, akaro na farko Tun zuwan su gidan

Turawa tayi ta shiga dakin nasa da sallama, yana zaune yana hada kayansa acikin truly
Ya amsa mata batare daya kalli Inda takeba, zama tayi akusa dashi tace "ya Yusif gashi inji mamy"

"ajiye anan" abinda yace mata kenan

Ta ajiye masa, zuciyarta tana karyewa Kamar zatayi kuka, duk sai shamata kunu yake tunda yadawo, wai ita ya sukeso tayi ne?

Dauka yayi yasaka acikin jakar tasa sannan yatashi tsaye yace "idan kinsamu time kuje keda Nadiya abude miki account  idan kina buqatar kudi saiki kirani ki fadamin, zan tafi yanzu, may be nadawo dawuri"

Yana fada mata haka bakowa ne yafado mata araiba sai ya Abba, duk alamomi sai yanzu suke nuna mata cewa dama ya Abba baya santa, itace takasa gane hakan soyaiyar sa ta rufe mata ido, duk su ya Usman Babu abinda basuyi mata lokacin data dawo kano, kowa yana nan nan da ita, amma shi ya Abba itace take nan nan dashi, 😃
Gashi shima ya Yusif yadawo amma bata bashi kulawar komai ba sai shine yake hidimta mata, batasan lokacin da hawaye yazubo mataba, ahankali ta miqe tsaye tafada jikinsa tana sakin wani irin kuka abaiyane

Qam Yusif yaqame a tsaye, shibe tureta ajikinsa ba, shikuma bai saka hannu ya rungumeta ba 🤔
Kuka take sosai har hawaye yana d'isa agaban rigarsa

Wata irin ajiyar zuciya yasaki, sannan yasaka hannu ya rungumeta gaba daya, yana bubbuga bayanta, wani irin yanayi ya tsinci kansa aciki, Wanda bai tabajin irinsa ba, cikin kasalalliyar murya yace"kiyi hakuri mana kiyi shiru, menene na kukan? Me aka miki?kokuma Wanda zaki aura kika tuna? "

Girgiza kanta tayi, tace" dan Allah kayi hakuri, kadena fishi "

Yaga alama idan akaci gaba da tsaiwa ahaka to yarinyar nan zatasa yayi mata ba daidai ba, Dan haka ya janye tadaga jikinsa, yace" ya'isa to, ni bana fishi dake, kuma kece yakamata nabawa hakuri, tunda kina ganina kika share ni, saboda kin samu wani"

Wasa tafara da yatsun hannunta tace "kayi hakuri, kuma ba kullum saina kiraka ba, amma wayar taqi shiga"
Tafadi haka cikin shagwaba

Murmushi yayi "to naji, komai yawuce, yanzu Muje ki raka yaya Yusif zai tafi kada yayi missing flight, but banda bawa samari number, kinji ko?"

Daga masa kai tayi, tace "to"

Sannan ta janyo masa jakar suka futo daga dakin, mamy bata falon, kai tsaye dakinta suka nufa domin yayi mata sallama

❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Dawowar sa kenan daga makaranta duk yagaji, ga yunwa dayakeji yaji Kamar ana buga get din gidan
Tsaki yaja sannan yatashi yafita, yana budewa yaga samari su uku dukansu yarane bazasu wuce 27 ba, gaba dayansu sun tsuke cikin qananun kaya, kallansu yayi dakyau yace "samari lafiya kuwa? Ko wani gida kuke nema?"

Daya daga cikin su yace "dama munzo wajan qawarmu ne, munyi waya da ita, so tace mana tadawo nan gidan dazama"

Cikin mamaki yace "qawarku kuma? Inaga kunyi batan hanya ne, ba nan bane"

Na biyun yace "bawan Allah ya zakace mana ba nan bane, bayan nan gidan tayi mana kwatance?"

Yace "Wacece qawar taku?"

Na ukun yace "Diyana"

Tsayuwarsa ya gyara yace "Ok ai sai yanzu nagane ku, ashe wajan aminiyarku kukazo, to bismillah, kushigo mana"

Wanda yace wajan Diyana sukazo yakalli Adam dakyau, anya kuwa zai shiga? Da alama fa wannan yayan tane, karfa su shiga yamusu shegen duka 🤔

Saiya girgizakai yace "no, Barshi kawai,"

Ya kalli sauran yace "Baba kuzo mu ware kawai" 🤣

Sukuma biyun suka dage sai sun shigo, Adam yana tsaye cikin zuciyarsa yana addu'ah su shigo gidan, ysce"ku qaraso mana, tana ciki fa maryam din "

Sunfara shigowa gidan kenan sai daya yalura da yanda Adam yake tattare hannun rigarsa aboye 🤣, sai yaja dan'uwansa ya tsaya

Adam yajuyo ya gansu sun tsaya yace" me kuka tsaya yine? Rakaku zanyi "

Adede lokacin tafuto daga cikin dakinta zuwa compound din gidan, tunda aka kawota gidan yaune kawai Adam yaganta da atamfa a jikinta dinkin riga da Zani, kuma sai kayan yayi mata kyau sosai

Tana ganin mazan tasaki murmushi tace" guy's, ya garin? Yakuka tsaya daga nan? "

Murmushi sukayi, atare sukace" zamu dawo, Karki damu zamu dawo next time "daga nan suka fice da sauri

Itama tajuya cikin gidan ko kallan Adam batayi ba, shikuwa binta yayi da kallo yace" Allah ya shirye ki "

❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Da yamma suna zaune afalo shida ita, kanta ko dankwali Babu dana daddana wayarta, shikuma yana can kujerar qarshe yana cike wasu takardu daya karbo awajan Abba
Tun safe rabonsa da abinci, Dan haka yana gama cike takardun yadago kansa ya kalleta
Besan meyasa yarinyar nan take san zama kai Babu dankwali ba, amatsayinsa na saurayin yayarta ai yadace ace tana shiga ta kamala, amma kullum kai Babu dankwali, wani lokacin ma shigar da zatayi idan yaganta daqyar zai dauke idonsa akanta 🙈
Badan yana ganinta amatsayin qanwar budurwar sa ba ai zata iya saka shi awani hali  

Ajiyar zuciya yayi yadaga murya yanda zata jiyoshi, saboda basa zama waje daya yace "ke tashi kikawomin abinci"

Hankalinta yana kan waya tace "banajin yunwa banyi abinci ba"

Yace "Wato Ilham na lura kanki yana rawa acikin gidannan, rashin kunyar ki tafara kaini bango, Karki qureni kuma"

"to yanzu yaya Aslam girki akace nazo nayi kome? Ni wallahi bazan iyaba, saikace wata jaka"

Yace "okey Wato nida nake nemowa na kawo gidan na ajiye nine jaki, 🤣
To bari kiji Dan Allah ki yarda nasake yimiki maganar abinci acikin gidannan"

Yana fada mata haka yatashi yafice ransa abace, wannan qaddararran auren yafara isarsa, haba!


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

"A'a, yanmatan Yusif, kece atafe kenan"

Ajiyar zuciya tayi "wallahi nice Anty Nadiya, mamy tafita unguwa, saini kadai agidan shiru, shine nace bari nataho wajan ki kawai" cewar Nihla

Nadiya tace "hakane kam, kin kyauta masha fira, gashi saurayin naki ma yagudu china"

Murmushi Nihla tayi "wai yaya Yusif, aiba saurayina bane Anty Nadiya, Yaya Yusif yaya nane, yayi min abinda dan'uwana yakasa min, inajin sa a raina tamkar yayana da muka futo ciki daya"

Gyara zama Nadiya tayi tace "waye dan'uwan naki?"

Kai tsaye tace "yaya Abba"

"yaya Abba kuma? Kifuto fili kimin bayani Nihla, NI DAKE, munzama Kamar yaya da qanwa, yakamata kibani labarin ki, menene yake yawan sakaki tunani, har kike bige mutum ahanya batare dakin saniba?" 🤣

Nihla tace "Anty Nadiya, labarins yana cike da abin tausayi, nida iyayena natashi, mahaifina ne qaramin qarfi ne, bayan na girma mamana ta rasu, nakoma gidan yayanta da zama har Allah yadawo dashi daga qasar waje"

Nadiya tace "wakenan? Kici Gaba mana"

Hawaye ne yataru a'idonta, tace "yaya Abba, Tun muna yara nasaba dashi, har na girma da tunanin sa acikin qwaqwalwata,ganin irin sabon damukai dashi muna yara yasa ya daya dawo daga qasar waje nake kula dashi, yanda nake masa zaki dauka ansaka mana ranar aure ne, ashe shi ba haka bane acikin ransa, yanada budurwa, ranar da akace anhadamu aure acikin mutane yace bayasona, akwai wadda yakeso, ahaka iyayen sa zasuyi mana auren bayan an lallabashi ya amince, sai ranar auren babana yaje yadauko ni, muka Taho nan garin ta dalilin baban yaya Yusif, wannan dalilin ne yasa naje ganinsa Kamar yayana uwa daya uba daya, Yaya Yusif yamin abinda yaya Abba yakasa min shi "tana gama bata labari tashare hawayen idonta taci gaba da cewa" bansani ba ko bankai yasonin bane kokuma banida abin dazai gani a wajena yasoni "

Kai tsaye Nadiya tace" qwarai kuwa bakidashi Nihla "
Da sauri Nihla ta kalli Nadiya cikeda mamaki

Nadiya tace"Nihla Dafarko ki kalli Hijabin dayake jikinki, ki kalli irin atamfar datake jikinki, wallahi idan ni kika bawa wannan atamfar taki saina tambayeki dalili, saina zaunar dake nace Dan Allah meyasa kika bani wannan kayan? A a kin renamin hankali ne kokuma tsabar kin maidani yar qauye ne yasa kika banisu? 🤣🤣
Nihla samarin wannan zamanin fa saida dabara, na farko namiji yanason mace Mai aji, Nihla kinje kina zubda ajinki agabansa abanza, wasu mazan zakiga duk wata mace Mai yi musu biyyaiya to zakiga hankalinsu baya kanta, idonsu yanacan wani waje, Nihla tunda nake dake bantaba ganinki Babu hijabi ba, kullum kina cikin hijabi, tayaya zaiga kwalliyarki har wani abu yaja hankalinsa yaji yana sonki? 🤔
ni macece 'yar'uwar ki amma tabbas na yabawa kyanki, kinada kyau Dan kyau, amma awajan wani na mijin hankalinsa bayakan kyau kokadan, hankalinsa yafi karkata kan abubuwan more rayuwa, kuma ke bakidasu"

Nihla tayi shiru tanajin maganganun Nadiya, acikin maganar ta Babu ta qarya

Nadiya ta dafata tace " babanki yamiki gata daya dauko ki,saboda dakin aure shi ma wahala kawai zakisha, sannan kuma ki godewa Allah dakika hadu Dani, domin kuwa komai yazo qarshe, zan temaka miki, kishigo gari Kamar ko wacce budurwa da takeji da kanta, ta yanda Abba kikace kowa? Bashi kadai ba kowanne namiji ma idan yaganki, saiya sake kallan ki, amma bazai iyuba saikin kwantar da hankalin ki, kin cire shi aranki "

Nihla ta kalli Nadiya tace " gaskiya Anty Nadiya inason ya Abba "🤣

Murmushi Nadiya tayi tace" matsalar ku kenan yara, saiku dauki soyaiya kusa aranku Tun bakuje ko'inaba, kinganni nan Nihla, babu na mijin dazan zauna ya renamin hankali,
Idan naga take takenka agu Zan tattaraka na ajiye agefe, akwai wani saurayina SADIQ MAZAWAJE, naje germany karatu anan muka hadu, shida kansa ya nuna yana sona kuma na amince, sai daga baya nagane cewa nayi kuskure danake saurarensa, na farko bayamin kalaman soyaiya, sannan bayasan kirana nice nake ta kiransa, ke qarshe ma kwanaki dana kirashi muna waya kawai naji yana magana da wata mace agefe, naji yana cewa zoki ajiye anan, wallahi Nihla tunda nakashe wayata ban sake nemansa ba sai rannan, amma ni Inda yake birgeni akwai riqe alqawari, munyi alqawari dashi zamuyi aure, amma gaskiya Nihla nagaji, ko wacce mace tanason kulawa, amma ni bana samu awajansa, aikinsa kawai yasa agaba,tunda nagane haka saina saka shi awani bangaren daban na ajiye, naci gaba da kula samarina masu bani kulawa, (😳)
To kinga ko rabuwa mukai dashi bazanji wani haushi ba, bari kiga pic dinsa "
Wayarta tadauka tadubo pic dinsa, tadorawa Nihla data zama mutum mutumi wayar akan cinya, tace "bari in shiga toilet na futo"

Batare data lura da yanayin Nihla ba tashige toilet

dak! dak! Gaban Nihla yake faduwa, cikin ranta ta furta yaya Abba!!!
Gaskya ne, Sadiq yana nufin Abubakar kenan, yanzu dama yaya Abba shine saurayin Anty Nadiya? Saboda Anty Nadiya yaqita?
Kallan pic din tayi, karon farko data taba ganinsa cikin kakinsu na pilot Mai launin fari da baqi, yayi bala'in yin kyau a pic din, yana zaune akan kujera wajan da'ake tuqa jirgi

Wato ita da yakeso harta samu pic dinsa, amma ita batakai wannan matsayin ba

Jikinta har rawa yafara saboda tsananin firgita, abin yabata mamaki sosai, dole dole tasan abinyi

Nadiya ce tafuto daga toilet tace "kin ganshi?"

Cikin in'ina tace "eh na.. naganshi Anty Nadiya, amma yayi kyau"

Nadiya tace "ke rabu da wannan kyan yarinya, kyau Babu kulawa ina wani kyau, idan na aure shi kyan zanci ko kulawar zanfi buqata, shareshi kawai" 🤣

Hausawa sukace naka nakane, hakanan taji bataji dadin furucin Nadiya ba, meyasa zata fadawa dan'uwanta haka?

Nadiya tace, kishirya gobe zamuje kasuwa akwai abubuwan dazamu siyo, sannan kincemin akwai atamfofin da Yusif yasiyo miki basuda dinki, zamuje wajan telana ya gwada ki yayi miki dinki nagani nafada, Sanna wannan kan naki zamuje wajan saloon awanke shi, wani satin kuma sai Muje wajan gyaran jiki ayi miki, sonake qanwata ta sauya ta yanda Babu wani na mijin dazai qara rena miki hankali "

Murmushin yaqe Nihla tayi" tace  " to Anty Nadiya, Allah yakaimu, dama akwai kudin dayamin saura irin Wanda ya Yusif yake bani, saimu hada dashi"

Nadiya tace "Karki damu nima akwai kudi a wajena,"

Washe gari Tun safe suka yiwa many sallama suka tafi wajan tela, Nadiya ce ta karbi tif din da kanta ta aunata, kuma itace tabasu irin Style din datake so ayi mata, daga nan kasuwa suka wuce suka sai :

Alkama
Shinkafa
Gyada
Ridi
Dawa
Hulba
Gero
Aya
Zogale
Kanumfari
Waken soya


Sannan suka dawo gida,Nadiya tace" Sai gobe kuma zamuje wajan saloon,da wankin qafa, "

Nihla tayi shiru ta kalli kayan dasuka siyo tace" yanzu Anty Nadiya me za'ayi da wannan hadin? "

Murmushi tayi tace" kece zaki dinga sha kullum safe, da dare, idan zaki iyama har rana, zakisa ka ruwa kadan ya tafasa saiki debi garin wannan maganin kidamashi a cup dadan kauri, saiki zuba acikin Ruwan zafin nan nakan wuta kina juyawa har yayi kauri saiki juye kidinga sha da madara ko nono kindirmo, Nihla nabaki wata uku cikakke qirjinki zai qara cikowa sosai, Sannan hips dinki ma zasu sake budewa "

(yanmata masu buqata da matan aure zaku iya gwadawa yanayi sosai, shine de ake zuba mukushi aroba azo asiyar muku shi dubu uku uku, dukansu zaki hadesu waje daya ki soya su sama-sama, saiki kai aniqa miki, ki tankade kidinga damawa kinasha 🙏🏻)


Jikin Nihla yayi sanyi, jiki a sanyaye tayi mata godia ta tafi gida dashi,da daddare tana zaune agadon ta har sha biyu na dare takasa bacci, tunanin Nadiya kawai take, dame zata sakawa Anty Nadiya? Yazama dole ta cire ya Abba daga cikin zuciyarta kodan Anty Nadiya,dole zata dage da addu'ah akan Allah ya yaye mata, afili ta furta   " insha daga yau nahakura dakai ya Abba, koda sanka zaimin illa insha Allah daga ranar yau, nahakura da kai, saide yamin illlar"















(kunga laifin Nihla? 🤔)



Ina godia sosai da sosai masoyana, yan group din DANGI DAYA  kuna sani nishadi, wallahi sharhinku yana bani dariya 😃 oh Abba ma yaga takansa 😚















Amnah El Yaqoub ✍️[6/22, 11:41 PM] El Yaqoub: ❣️DANGI 'DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub

Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493



21&22




Tunani taci gaba dayi, mahaifin ta bashi dashi Mai qaramin qarfi ne, meyasa ma Tun farko hankalinta Yaqi karkata kan karatu? Wata zuciyar tace saboda soyaiyar Abba
Juyi tasakeyi, gashi wadda yaqita saboda itanma bawani sonsa takeba, ita kuma yafuto bainar jama'ah yace baya sonta, gara ta hakura itama dashi, idan taci gaba da sonsa har Anty Nadiya tagano gaskiya haqiqa zatace ta munafurceta, to gara Tun wuri ta tsaida Rayuwar ta waje daya, itama ta haqura dashi dukda tasan abune Mai wahala amma dole zata kamanta , tsaki tasaki afili, tayi juyi tareda addu'ah tarufe idonta

Washe gari suka tafi wajan saloon bayan tadawo daga makaranta,ba Nadiya kadai ba, hatta masu shagon tsayawa sukai ganin yanda gashinta yaqara tsawo, gashi Kamar ba 'yar hausawa ba, ita kanta wata irin iska takeji tana shigar ta

Duk lokacin data ga Anty Nadiya saita tuno da ya Abba, amma tana kokarin kawar da tunanin sa acikin zuciyarta

Sati na zagayowa sukaje wajan gyaran jiki, Nihla saita koma Kamar wata amarya, mamy de tanata Kallanta tana wannan bidiri, saide tayi Murmushi kawai, taga take taken Nihla qarfi dayaji sotake ta sauya

Sosai ta maida hankalinta akan karatu, babu ruwanta da kowa a makarantar, kawai karatun ta tasa agaba,dinkunanta da sukaje suka karbo shi tafara sakawa, babu meyi mata kallan raini, bata shiga harkar kowa bama bare ta fuskanci wani bacin rai

Kamar yauma tana zaune awaje daya cikin makarantar, littafi ne a hannunta tana dubawa, taji anyi mata sallama, dago kanta tayi ta dubeshi, batare data ce komai ba, shima yayi Murmushi Yazauna dab da ita yace "baki ganeni ba ko?"

Tace "eh, bangane kaba"

Yayi Murmushi yace "qanin Anty Nadiya nefa Abdallah, anan makarantar nake nima, tacemin kullum kina shigowa shine taturo min number ki tace nanemeki, to nakira taqi shiga sai ita nakira tafadamin Inda zan sameki"

Lokaci daya tayi Murmushi tace "ashe kaine, ai inajin labarin ka awajanta,amma ban taba ganinka ba, ya gari?"

"wallahi ina wajan friend dinane, kawo natayaki karatun"

Yaja littafin ta yana gani, itama da taga yanada kokari saita fara Tambayar sa abinda bata saniba


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️
Yau Tun safe take shiri zataje wajan biki, wanka ta dauka taci kwalliya Kamar me, sannan ta shirya tsaf tafice batare data kalli ko Inda dakinsa yakeba, shima daya shirya yafuto zai tafi makaranta bai gantaba, kuma beyi tunanin neman Inda tatafiba, Yarufe gidan yayi tafiyar sa

Tun azahar yagama abinda yake amma saiya zauna baidawoba sai yamma, daya dawo gidanma abin mamaki bata nan, yayi shiru yana tunani, yarinyar nan tunda akai aurensu gaisuwa ma bata Hadashi da ita, ga mu'amula datake da samari awaje duk yana sane da ita, me zaiyi mata ne yaja hankalin ta ta daina abinda take?
Dariyar dayaji ne yasa yadago kansa da sauri ya kalleta, wani shegen mayafi tayafa ga kayan datasa dinkin irin dede da itan nanne, ta kalleshi taci gaba da wayarta tana cewa "ashe pictures sunyi kyau, kaima kagani ashe,"
Ta saki dariya tashige dakinta

Adam yabita da kallo, yanzu idan Diyana zata fita bekai tafada masa Inda zataje ba? Anya yarinyar nan kuwa tasan me ake nufi da aure? 🤔

Binta yayi cikin dakin tana zaune tana cire Dan kunnanta, yace" daga ina kike? "

Hankali kwance tace "daga gidan bikin wata qawata"

"ke ba'a isa da keba kenan, kindauki qyale qyalen duniya kinsa aranki, maza suna kawo miki ziyara, kinada aure akanki kina waya da wasu qartin banza, to Karki Manta de da aure na akanki, kuma duk abinda kika aikata zunubi kike kwasa akanki"

Kallansa tayi tace "zunubi?"

Takaici yakama Adam, tabbas idan yaci gaba da kula yarinyar nan, zai iya yimata dukan tsiya, kuma yasan hakan a addinance Babu kyau, cikin bacin rai yafice yayi dakinsa

❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Kalau yadawo gidan yau yana cikin nutsuwarsa,yana sanye da qananun kaya sunyi masa kyau sosai, kayan kallo take gogewa tadago taganshi taci gaba da abinda take, beyi mata sallama ba yaqaraso falon Yazauna yana ganin yanda take komai cikin nutsuwa, itama ko kallan Inda yake batayiba, harta gama tashige kitchen

Bayanta yabi da kallo kenan shi yarinyar nan saboda bata daukeshi a mijiba ko gaida shi ba zatayi ba bare sannu da zuwa
Ajiyar zuciya yasaki yatashi ya shige d'akinsa, Dan qaramin fridge din dakin nasa yabude yadauko magungunan maye ya ajiyesu a gefensa, Yazauna agefen gadon yabude kowanne yasha, sannan ya koma gadon ya kwanta yana lumshe idonsa

Acan kitchen kuwa Dida lemon Kankana tahada Mai dadi tahada da Abincin datayi tazuba masa sannan tafuto zata kawo masa, tana zuwa falon taga baya nan, Dan haka kai tsaye tashige dakin da Abincin

Tana zuwa gabanta yafadi ganin uban kwalaben dake gabansa shikuma gashinan Akwance yana bacci ko takalma bai cire ba

Girgiza kai tayi ta ajiye Abincin agefe ta tsugunna tadauke kwalaben, karantawa tayi, afili ta furta "Benalyn, Codein,Emzolynn, 🙆🏻‍♀️tabdi harda su Emzolynn acikin kayan mayen?"

Karaf maganar ta shiga kunnansa, a lokacin bacci yafara fizgarsa

Dida kuwa kwashe shu tayi, ta ajiye masa agefe,kafarsa takama tafara kokarin cire masa takalmin, tana cirewa ta zubawa kafarsa ido tana gani, kafar me kyau kuwa, saide Mai kafar bashida kyan hali, ahankali tatashi zatabar wajan yasa kafarsa yabigeta, lokaci daya ta'iyo kansa tafada Kirjinsa, sai jin mutum yayi akan Kirjinsa, Dasauri yabude idonsa yazuba mata ido yana Kallanta

Dida kuwa idonta yana kan bakinsa, meyasa yana shan kayan maye amma lips dinsa beyi baqi ba?

❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Kasancewar yasan Babu me shigo masa daki yasa daya futo daga wanka yana daure da towel iya qugunsa yanufi cikin kayansa yadauko manyan kaya, saboda baqi dazasu gani shida Abba akan shirye shiryen bude campany nsu.
Kayan yadauko ya ajiye sannan yagama shafe shafensa yadawo zai saka kayan, gajeren wando yadauko, ya cire towel din ya wulllashi kan gado, zai saka kenan sai gata taturo kofar dakin tashigo 🙆🏻‍♀️
Tana ganinsa haka tasaki qara tafuto aguje, gabanta sai faduwa yake, Innalillahi..😳,meyakaita dakin yaya Aslam?

Shikuwa Aslam yana jin qaranta ya tabbatar yarinyar taganshi, qarasa saka wandon yayi Yazauna agefen gadon yadafe kansa 🤦🏻‍♂️, shikkenan girmansa yazube a'idon qanwar budurwarsa, zance yaqare taga komai

Haka yatashi ransa abace yagama shirya wa yafuto, tana ganinsa futowarsa takwasa aguje tayi dakinta, shikuwa Aslam ko Kallanta beyiba yawuce zai fice daga falon, ta kalli bayansa tasaka dariya, tashige dakinta

Sarai yana jinta yayi fuska ya shareta, toba dole tayi masa dariya ba, duk yanda yake kare mutuncinsa saida yarinyar nan taga komai, wallahi yanda yakeji aransa idan ta kuskura yadawo tayi masa dariya wallahi sai jikinta yayi tsami 😃

Bayan sun gama ganawa da baqin harma suntafi, sun tsaida ranar dazasu shirya bude campany, Aslam yayi shiru yana tunani, Abba ya kalleshi yace "meke damunka"

Ajiyar zuciya yayi yace "wallahi Abba akwai damuwa"

"wacce irin damuwa?"

"Abba kaga tunda akai auren nan, yarinyar nan ko abinci bata min, kullum ina wajan cin abinci, idan na yi mata magana tafadamin ba dadi"

"Aslam wannan ne dalilin dayasa nake fada muku kudena kula qananun yara, amma bakwa ganewa,"

Ajiyar zuciya yayi yace "yanzu de abinda nake fadama yarinyar nan fa taga komai, koda nayi mata fada bama lalle taji ni ba"

Abba yace "Kamar ya, mekake nufi"

Cikin haushi Aslam yace "kagane mana, saina futo fili nama bayani ne"

Dariya takama Abba, sosai yake dariya yana kallan Aslam

Aslam yace "tomiye kuma abin dariya, miye hakan, wallahi Zan huce akanka"

Abba yace "maida wuqar abokina, kaima saika rama abinda tama, kaga shikkenan kunyi 50 50, babu wanda zaiyi wa wani dariya"

Kallan Abba yayi yace "Kamar ya Abba? Ma kake nufi?"

Abba yakama Kunnan Aslam yayi masa rada
Lokaci daya sukasa dariya, Aslam yace "kai Abba wallahi bakada dama, natafi, yanzu yanzu zanje nasiyo, sai munyi waya"

Daga nan kowa yayi gida


Aslam bai zarce ko'inaba sai wani super market da ake saida kayaiyakin wasan yara, daga nan yayi gida, lokacin yamma liss, yana shiga falon yaji qamshin abinci yadaki hancinsa, ahankali yaleqa kitchen yaganta tana girki tana waqa hankali kwance, cikin sand'a yadawo da baya yashige cikin dakinta, yabude toilet dinta yadauko lizard cikin aljihunsa yasaka mata shi dede Inda yaga tana shanya panties dinta, cikin sauri yafuto Yarufe dakin Ahankali ya koma falon Yazauna yadora kafa daya kan daya yana jijjigata


Agabansa tafuto daga kitchen din, ta kalleshi tayi Murmushi, tazauna tazuba Abincin ta ita kadai tanaci tana murmushi
Kallanta yayi yasan sarai dashi take, sotake yamata magana tafada masa marar dadi, Dan haka yayi shiru yaqyaleta, suna zaune ana kallan kallo har dare yayi, bega tatashi ta shiga dakiba, shikuwa sallah yake zuwa yadawo falon Yazauna, daga qarshe ma bayan sallar ishsha'i wanka yayi yadawo falon Yazauna yana kallo, abin harya fara bata mamaki, yatsina fuska tayi tashige daki, zuciyarta daya tazage ta shiga wanka, cikin nishadi tasha wankan ta tas, ta janyo towel zata daura kenan tayi ido biyu da qadangare, tsaro ido tayi😳

Cikin faduwar gaba tace  " Innalillahi wa inna ilaihir raju'un, nashiga uku me yakawomin masifa cikin toilet" dagudu tafuto towel ahannu

Shikuwa yana zaune yana kallo yana shan lemo, yana jin salati yace "lokaci yayi kenan" 🤣 Ahankali yatashi yayi hanyar dakin, yana zuwa bakin qofa sukai karo, jikinta yana karkarwa ta kamashi ta riqe, cikin tsoro tace "yaya Aslam qadangare a toilet dina, wallahi yana ciki, Muje ka ganshi"

Aslam kuwa gunki yazama a tsaye, magana take masa amma yadade da shagala yana kallan surar jikinta, ashe haka yarinyar nan take?

Jijjigashi tayi tace "yaya Aslam!!!"

Firgigit yadawo cikin duniyar mu 🤪
Yanayin sa yadan sauya kadan, ya kwashe da dariya yace "to daura towel din"

Sai a lokacin talura da towel din dayake hannunta, kunya ta kamata, cikin sauri taja tarufe jikinta, amma takasa kallan idonsa 🙈

Futowa yayi yabarmata dakin, tabiyo bayansa, yana dauke kafa tana maidawa, yajuyo ya kalleta yace "wai menene?"

Cikin shagwaba tace "to Muje kacire min shi mana, haka kawai saika tafi kabarni"

Banza yayi da ita ya kashe kayan kallo yadauki wayarsa yayi hanyar dakinsa, itama ta doru abayansa 🤣

Dakinsa yashiga, yafara cire kayansa,cikin sauri tajuya masa baya, Kallanta yayi yanda tajuya bata kalleshi ba, ya zubawa cinyarta ido daga baya, yadauki jallabiya yasaka, yahau gadon ya kwanta

Tanajin ya kwanta tataho kansa ta tsaya tana share hawaye, yanajinta ya qyaleta, ita kuwa daga ta haka saita qara gunjin kuka, tsaki yayi yatashi yafuto yabar mata dakin, itama tasake futowa, cikin ransa yace yau naga ta kaina 🤣
Hanyar fita daga falon yanufa tabiyoshi, yajuyo ya kalleta "ina zakije ahaka?"

Cikin kuka tace "Allah bazaka fita kabarni ba"

Yace "abinci nakeso naje nasiyo, banaso dare yamin"

Tace "to baga abinci can a kitchen ba, basai kaje kaciba"

Cikin sauri yace "ni? A a riqe abinki, Abincin da ba'abanishi Dan dadi ba saidon wuya?"

Yana fadin haka ya juya zai fice, tasa hannu ta riqe gefen jallabiyarsa
Yuyowa yayi ya kalleta ya girgiza kai sannan yadawo falon Yazauna, itama tadawo tazauna akusa da qafafunsa 🤣


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Computer datake gabansa Yarufe ya ajiye ta agefe, sannan yadauki coffee din da Adala Sabuwar Mai aikin Momy takawo masa
Yana kai coffee din bakinsa ya runtse idonsa, zaqi yayi yawa, shikuma bayason zaqi, ga shi kansa coffee din har wani d'aci-d'aci yakeyi

Tsaki yaja, yadauko cup din yafuto falo yana kwalawa Momy kira "Momy! Momy!!"

Momy dake kallo afalo tadago idonta ta kalleshi, tace "Abba nah menene?"

Cikin damuwa yace "Momy waye yahada wannan coffee din?"

Tace "waye zai hadama coffee Abba bayan Adalaiye? "

Tamkar qaramin yaro haka yafara yimata shagwaba "Momy wallahi Babu dadi, zaqi yayi yawa, kuma ni kwata kwata ma bayamin dadi abakina Kamar yanda yarinyar nan take min, duk Babu teste"

Momy tayi shiru tana kallansa, Wato Nihla ce bazai fad'aba saide yarinyar nan,ai already Nihla tagama bata Abba da wannan shegen coffee Kamar qa'ida, Tun bayan barinta gidan komai yaci yadinga mita kenan shi Babu dadi 🤔

ajiyar zuciya tayi afili tace "Abba Tun yanzu?"












Ko'ina masu lizard zasu kwana yau? 🤔

Oga me coffee ko yaya abin zaici gaba da kasancewa🤣?








Amnah El Yaqoub ✍️
[6/23, 11:31 PM] El Yaqoub: ❣️DANGI 'DAYA❣️

{Romance&Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub


Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493


Wannan page din na'yan la'be ne🤪
kawai sonake yau kuma ku futo kuce wani abu



23&24

Yace "Momy me kike nufi?"

"A a, babu komai Abba, zanyi mata magana saita gyara"

Ajiye cup din yayi "no kibarta Momy, kawai de daga yau karta sake min"

Haka ya juya cikin dakinsa ransa duk ajagule, zama yayi yadauki wayarsa yafara kiran number Nadiya, but number busy, cikeda mamaki yakalli agogo "to Dawa take waya Awannan lokacin ?"

Babu me bashi amsa, Dan haka yayi wulli da wayar ya kwanta


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Har sha biyu suna zaune jugum jugum afalo, Aslam sai hamma yake yanaso yaje ya kwanta, gashi wannan yarinya ta hanashi sakat, tazo tasa shi agaba da wannan shegen towel din nata Wanda dashi ma gara Babu
Ahankali yatashi yayi dakinsa, tatashi tabishi, Bece mata komai ba yahaye gadonsa ya kwanta, kujerar datake dakin nasa tahau ta kwanta itama, saide atakure take
Yakalleta yace "kitashi kibarmin dakina"

Ilham kuwa tana jinsa tayi banza ta qyaleshi
Wai akan masifa ta sameta yake korarta, Hmm zata rama ne, da haka tayi addu'ah sannan tayi bacci, shikuwa kasa baccin yayi yazuba mata ido yana Kallanta dukda ta juya masa baya, daqyar yasamu yayi bacci bayan fama da juye juye dayake, idan Yarufe idonsa, surarta kawai yake gani

Tun kafin tatashi daga bacci asubar fari yatashi yaje toilet dinta ya cire lizard din sannan yatafi masallaci

❣️❣️❣️    ❣️ ❣️ ❣️

Yau daga makaranta gida yawuce, yadade agida sannan yakamo hanyar gidansa
Tun kafin yasako qafarsa cikin falon ya ganshi kaca-kaca, yariqe qugu ya tsaya yana qarewa falon kallo, fillow's din dake kan kujera duk wasu aqasa, matsawa yayi yaje wajan kayan kallo yasaka hannu yataba, yana duba hannunsa yaga qura

Daga murya yayi yafara qwala mata kira "maryam! Maryam!!"

Cikin sauri tafuto daga dakinta,fuskarta cikeda kwalliya, riga da wando ne a jikinta, rigar nan takamata kyam ajiki, wandon kuwa tacika abin ta, Dan qaramin mayafi ne a hannunta tana kokarin nad'ashi akanta tace "gani"

"yanzu maryam abinda kike acikin gidannan yadace kenan? Bakisan mukwana dake acikin gidannan kibudi baki kice Dani ina kwana ba, idan zaki fita unguwa bankai matsayin dazaki tambayeni ba,bakisan kidafawa mijinki abinci ba, now kalli gidannan, kina nema kibar min gida ya lalace, kalli, kalli Dan Allah cikin falon nan "

Yaqarasa magana yana nuna mata cikin falon


Kallansa tayi  " yanzu ya Adam duk kokarin danake dannaga na zauna dakai lafiya baka gani? Auren nanfa baso nake ba, sannan kana maganar abinci aikai malami ne kasani, haqqinka ne kaci Dani sannan kashayar Dani, ni bazan iyaba!, bazan iyaba!! Bazan takura kaina ba, in tashi dasafe, inyi wanka, inyi kwalliya, inyi kokarin hadawa kaina abinci, sannan kuma inzo ingyarama gida, na maka girki, saboda samu ma inyi mopping,inturara gida da turaren wuta, saikace a novel? Aljanar inace nida Zan yi wannan aikin kullum? 🤣
To kaga ni gaskya ko agaban iyayena Babu me takuramin ehe! "

Tana fadar haka tajuya takoma cikin dakinta, jagwab Adam Yazauna akan kujera tareda dafe kansa 🤦🏻‍♂️maryam zata haukatashi

Yadade azaune sannan yatashi yatattare hannun rigarsa yadauki tsintsiya yafara share gidan, takan dakinsa yafara sannan kitchen, sai kuma falo, mopper yadauko ya goge falon tas, sannan ya goge kayan kallan yadauko qur'ani adaki yadawo falon yana karantawa


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Tunda taga ya Fawaz har gida yake shigowa da kayan maye yasaka acikin fridge ta shiga damuwa, ya Fawaz koshi ba dan'uwanta bane yakamata tafara nuna masa abinda yake ba daidai bane, balle ma shidin mijinta ne, haqqin kula dashi yana kanta
Jiya tatuno saida yagama qarewa fuskarta kallo sannan wai ta d'agashi tunda dama tasaba 🤣

Ahankali tatashi tashige cikin dakinsa, ta gyara masa dakin tas, ta lailaye masa gadon tsaf, fridge din dakin tabude kwalaben maganin maye dana mura gasunan birjik, shiru tayi tana tunani, tarasa mafita Dan haka tadau wayarta takira yayarta, bugu daya ta dauka tace "Diyana kinga dakin ya Fawaz nake gyara wa bakiga kayan maye ba, nikuma banaso yanasha wallahi, Yaya zanyi dasu ne?"

Diyana tace "um lalle Dida agaisheki, ke har gyaran dakinsa ma kike, tab!"

Dida tace "toya zanyi Diyana, mijina ne ko mahaukaci ne shi dole Zan kula dashi ahaka"

Batare da tunanin komai ba Diyana tace "kidebesu kizubar kawai"

Dida tace "to shikkenan nagode Diyana" daga haka takashe wayar, takwashe duka magungunan tafitar dasu waje ta tsiyayar dasu sannan tayi watsi da kwalaben
Tadawo ta goge fridge din, ta dauko lemuka a kitchen da ruwa tazuba masa su sannan tafuto daga dakin

Abinci taje tadafa musu bayan tagama tayi wanka tadawo falon tazauna tana game a wayarta
Ta dade azaune awajan sannan yashigo gidan, yau yayi mata sallama, cikin ladabi ta amsa masa, tace "a kawo ma abinci ne?"

Yatsina fuska yayi "no kibarshi kawai, ke kidena dafa abinci Ma Dani, kiyi rayuwarki kawai"

Batare data ce masa komai ba ta kwanta taci gaba da abin datake

Yana shiga dakin ya ganshi yasha gyara sai qamshi yake, zama yayi agefen gadon afili yace "wannan yarinyar da naci take wallahi"

Fridge dinsa yabude nan yaga Babu komai, cikin bacin rai yace "kan ubannan!!!"

Belt din jikinsa ya cire yafuto falon afusace, Dida tanayin game kawai sai Saukar belt din taji a jikinta, cikin sauri tatashi tana sosa wajan, be tausaya mata ba yaci gaba da dukanta, tatashi tana kuka sosai tana bashi hakuri, yana binta da duka tanayin baya har sukaje bangon falon ta tsugunna aqasa tana kuka sosai, cikin hucin bacin rai yace "ke Dan uwarki nizaki renawa hankali eh ? Okey wato saboda na sakar miki fuska acikin gidannan kina abinda kikaga dama shine zaki nemi ki takurawa rayuwa ta ko?, to bari kiji duk lokacin dana sake ajiye kayana cikin fridge tsautsayi yasa kika dauke min, saikin yabawa aya zaqin ta "
Yayi wulli da belt din awajan ya koma dakinsa, Dida kuwa kanta yana cikin qafafunta tana kuka, Dagowa tayi ta kalli jikinta, gefen hannunta harya shata



(Allah karabamu da mazaje masu dukan iyalinsu 🙏🏻)

❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Nihla karatu yayi nisa, alhmdlh tafara kwantar da hankalinta, saide damuwarta daya ya Abba, yana nan daram acikin ranta, amma alqawarin data daukar wa kanta yana nan Babu shi Babu ita,fatanta daya tasamu miji nagari Wanda zai nuna mata soyaiyar dazatasa ta Manta da Abba kwata-kwata, tana fatan samun wannan mijin

Gefe daya kuma shaquwa Mai qarfi tashiga tsakaninta da abdallah, kullum suna tare, tana karatun ta cikin kwanciyar hankali, abdallah yazame mata tamkar aboki, gashi yanada abin dariya, idan suna tare dole nema saiya bata dariya, shiyasa take ganinsa Kamar qawanta, gashi duk abinda bata ganeba yana temaka sosai harsai tagane, fatarta kadai zaka kalla a yanzu kasan cewa lalle tasamu canji, Anty Nadiya tayi mata komai a rayuwa


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Bayan tagama gasa jikinta tabawa megadi kudi yasiyo mata magani tasha sannan ta kwanta, amma hawaye take sharewa, kanta har ciwo yake saboda kuka, yakamata tabarwa yaya Fawaz gidansa, Tun ranar da aka kawota gidan nan tafara cin karo da mari, to tunda yafara duka bazai dainaba gara tafara tunanin barin gidan Tun wuri,kuma yazo ya kwanta a jikinta yace itace, bayan duka ga sharri, inaaaa! Da sake


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Yau agajiye yadawo gida,gashi ya Manta bai siyo abinci ba awaje, tsaki yasaki yafara qwala mata kira "Ilham"

Daga kitchen tafuto, ya kalleta daga ita sai wata qaramar riga da bata wuce gwiwarta ba
Ya Girgiza kai, yarinyar nan bazata dena halin ta ba, batada kunya, batasan shigar kamala 🤣
Yace "jeki kawomin abinci"

Babu musu tajuya takoma kitchen, Aslam yabita da kallan mamaki, yau shine yace wa Ilham tabashi abinci Babu musu Babu rashin kunya tajuya zata kawo masa? Lalle yau za'ayi ruwa da qanqara

Ilham kuwa tana shiga kitchen tazuba masa Abincin, sannan tad'ebo gishiri Mai uban yawa tazuba masa aciki, tasa spoon ta jujjuya Sanna tadauko takawo masa, zuciyarsa daya yadebi Abincin yakai bakinsa, lokaci daya ya yatsina fuska, gaba daya gishiri yahade masa baki, daqyar ya iya hadiyewa, yadauko Abincin yakawo mata gabanta ya ajiye, tadago kai ta kalleshi dariya ta nasan kamata, cikin fishi yace "Ashe ke zero ce bansaniba?"

Ran Ilham yabaci, ita ya Aslam zai kalla yace mata zero? Itama cikin bacin rai tace masa "To sannu 1"

Tas kakeji yadauketa da mari, yace "Ilham idan kinaji da rashin kunyar ki kiyi abinki ke kadai, tayaya Zan kashe kudi na kawo miki abinci gida na ajiye, banda damar dazaki dafamin, Sannan yanzu nace kikawo min abinci zaki zuba min gishiri aciki?to gashinan zauna tas saikin cinye shi"

Hawaye ne yazubo mata, tasa hannu tashare tana magana cikin kuka "Allah bazanci Abincin nanba"

Yace "nikuma kika sakamin naci namutu, baki damuba, zauna saikin cinye Abincin nan"

Haka Ilham tasa hannu acikin Abincin nan tanaci tana hawaye, fakar idonsa tayi tatafi dakinta dagudu tana kuka, Kallanta yayi yafara fada cikin ransa, haba yarinya sai Jan magana da rashin kunya, in banda yana mata kallan qanwar budurwarsa yau dasai ta cinye Abincin nan tas


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Futowa tayi tatafi dakinsa kanta tsaye, shi kansa yayi mamakin ganinta a dakin, saboda ba kulashi takeba, agefen gadon tazauna "yaya Adam inason kudi zanyi amfani dashi, banda kudi"

Kallanta yayi yace "banda shi"

"yanzu yaya Adam kaine zakace bakada kudi? Idan ban tambayeka kudi ba wazan tambaya?"

Yace "Allah masani"

Tace "Ok to sata zanje inyi insamu kenan?"

Yace "maryam koma menene kije kiyi, amma nide bazan dauki kudina nabaki kitafi yawon banza ba, kokuma kisa kati ki kira samari, qarya haram!"

"Ok haka kace?"

"yes haka nace maryam, kije kiyi duk abinda kikaga dama"

Tashi tayi tafuto tabar masa dakinsa
Tunani tafara maranta ciwo yake, A'ina zata samu kudin dazata siyo pad, shikuma besiyo mataba sannan yahanata kudin, haka takoma daki ta kwanta ga ciwo  da takeji sosai, Tun tanaji kadan-kadan harta faraji dayawa, daga qarshe ma zazzabi me zafi Yarufe ta


Washe gari dasafe ya shirya zai tafi makaranta saboda yanada lacture, yayi kyau sosai cikin farin yadi sai qamshi yake
Har zai shiga Mota ya tuna yarinyar nanfa Tun jiya beji motsinta ba, Dan haka ya koma ciki kai tsaye yashiga dakinta, tozali yayi da ita akan gado tana cikin blanket amma karkarwar sanyi take


Cikin sauri ya qarasa wajanta yace "subhanallah... Maryam!"

Bargon ya janye saiga Diyana tana kuka sosai, yace "bakida lafiya ne?"

Bata iya bashi amsa ba sai kuka, dagota yayi yatasheta zaune sai riyamm tafada jikinsa, kanta yana kan qirjinsa amma tana iya jiyo bugun zuciyarsa,wannan shine karo na farko da mace tahada jiki dashi, sai yaji abin wani iri, goshinta ya shafa yaji zafi sosai, lokaci daya yashiga damuwa, yace "Sannu, sannu kinji, bari nahada miki ruwa kiyi wanka sai Muje asbiti"

Dagota yafara yi daga jikin sa amma taqi tashi, ya sassauta muryar sa cikin sigar lallashi yace "kiyi hakuri, zaki denajin zazzabin insha Allah, kinji ko?"

Ahankali ya maida ta ya kwantar da ita, Sannan yashige toilet dinta yahada mata ruwa, yadawo yakamata zai tasheta, ta miqe kenan taji zuciyarta tana tashi, lokaci daya taji amai, cikin sauri zata shige toilet yatareta zai kamata suje, aikuwa sai amai ajikinsa, farar rigar yadin daya saka ya kalla, gaba daya tabata su da amai, tayi tunanin zataji Saukar duka, amma abin mamaki sai yace mata "Sannu, sannu kinji,"

Daga masa kai tayi, yadaga hannunsa ya cire rigar jikinsa, yadawo daga vest sai dogon wandon jikinsa

Kamata yayi suka shige toilet din, sannan yafuto yabarta aciki, dakin ya gyara tsaf, yasake gyara mata gadon, sannan yabude kayan ta yana dubawa kozaiga Mai Dan sauqin sakawa, amma gaba daya da riga da wanduna yayi ar'ba

Wata atamfa yagani yajanyota, ya ajiye mata akan gadon, shikuma ya juya ya koma dakinsa yasake shirya wa  sannan yadawo dakin nata

Bude toilet din tayi tafuto, taganshi yasaka qananun kaya, cikin ranta tace ashe yana saka qananun kaya,kayan kuwa sun karbi jikinsa, Kallanta yayi sau daya yakawar da kansa cikin sauri, yace "ga kaya nan kisa, saimu tafi asbiti yanzu"

Yadauki wayarsa yayi kira "hello monitor ki fadawa kowa cewa bazan samu damar zuwaba, matata batajin dadi"

Dasauri Diyana ta kalleshi, yanzu saboda ita yaya Adam zai fasa zuwa wajan aikinsa?
Fita zaiyi daga dakin tace "ya Adam"

Juyowa yayi Bece da ita komai ba tace "banda pad, kuma inaso zanyi amfani dashi"

"idan mun fita sai asiyo" yana fadar haka yafice daga dakin, yaga alamar Diyana batasan cewa bayasan ya zauna da ita Awannan halin datake ba, kokuma kallan dutse take masa waya sani, ita kuwa ko a jikinta

Kalau ta shirya suka tafi asbitin aka dubata aka bata magunguna Sannan sukaje suka siyo pad din, suka dawo gida
A sauqaqe yadafa mata indomie da dafaffan qwai 😃saboda bazai iya soyawa ba, yadoro spoon akai tareda gorar ruwa, sai ganinsa tayi yashigo dakin da abinci, karon farko da taji Tausayinsa ya kamata, meyasa take masa Wulaqanci? Tabbas sai kana jinya zaka zaka gane masoyinka na gaskiya

Zama yayi akusa da'ita, yace "maryam tashi kici abinci kisha magani saiki kwanta"

Ahankali tatashi tasa hannu zata karbi flet din, yace "A a, ai naga jikin naki Babu qarfi, kibari nabaki"

Ta Girgiza kanta tace "zan'iya ci ya Adam"

"maryam banason musu fa"

Shiru tayi, takasa yimasa gardama, ahankali ya matsa kusada ita har jikinshi na gugar nata, yafara bata indomie din abaki, saida yaga ta qoshi sannan yabata maganin tasha, yace "ki kwanta kihuta, Allah yasawaqe"

Tace "amin" idonta akansa, tashi yayi daga kan gadon Yazauna akan bedside drower yayi shiru, itama haka Babu me magana acikinsu, saide cikin ranta tabbas ta Jinjina wa ya Adam, saika zauna da mutum sannan zakasan halinsa 🤣

❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Yau Tun safe ya shirya yabi jirgi zuwa Abuja, yakamata yaude yaje yaga Nadiya yaji A'ina suka tsaya akan maganar aurensu, yanaso kawai yaturo iyayen sa agama maganar komai

Baisha wahala ba daga Airport kai tsaye wani abokinsa dayake tuqin jirgi amma bangaren state, yadauko shi a motarsa suka qaraso gidan nasu Nadiya,akofar gidan sukai Parking ,suka futo daga cikin motar yakira wayarta nan take tashiga
Tana dauka cikin muryar sa Mai cikeda aji yace "Nadiya gani agidan ku"

Cikin mamaki tace "gidanmu kuma?"

"eh, nazo ne muyi magana dake Mai muhimmanci, koda yaushe kina tambayata yaushe zanzo yaushe zanzo, banda lokacin ki, banida kirki, to yaude gani"

Tace "ayya, gashi kuma wallahi bana nan, naje lagos gidan Antynmu, munata shirin biki"

Be tambayeta bikin waba, sannan Beyi tunanin komai ba yace "okey, to shikkenan idan kindawo saiki sanar Dani, lokacin dana samu dama sainazo, but yanzu Zan turo miki 50k sai kiyi anko dashi"

Tace "to shikkenan Sadiq nagode"
Suna ajiye waya yatura mata kudin, sannan yadubi abokinsa yace "kaji batanan taje lagos, next time kawai"

Maigadi yaji dirin Mota abakin get kuma yaji shiru baiji ance yabudeba, Dan haka ya leqo, yana futowa yaga su Abba, nan take yagane shi
Cikin farin ciki yace "a a yallabai ashe kune kuke tafe, toku qaraso ciki mana"

Abba yace "A a sammani kada kadamu, ai munyi magana da ita ma yanzu tace taje lagos ko?"

Sammani maigadi yace "eh wannan gaskiya ne yallabai, ya hakuri kuma?"

Cikin mamaki Abba yace "wanne irin haquri kenan sammani?"

Yace "to yallabai Wanda yarasa mace Kamar Nadiya ai yayi Babban rashi dole a jajanta masa, ai lagos din data tafima sunje hado kayan lefenta ne itada mijinda zata aura 😳,
 bikinma yanzu haka saura sati uku" 🙆🏻‍♀️

Lokaci daya kansa yasara, cikin tsananin mamaki yace "sammani me kace?"

Sammani maigadi yace" wallahi gaskiyar kenan yallabai "

Lokaci daya yafara karanta kalmar Innalillahi wa inna ilaihir raju'un abaiyane, da abokinsa da sammani maigadi basu zataba kawai sai ganin Abba sukai aqasa🙆🏻‍♀️
Cikin sauri sukayi kansa suna kira, abokinsa yana cewa "Abba! Abba!!"

Shikuwa sammani yana kira "yallabai! Innalillahi..."

Daqyar suka cacimeshi suka saka amota, sannan abokin yaja cikin sauri, sukabar kofar gidan

Asbiti yakaishi, anan doctor yake tabbatar wa da abokin cewa kawai yaji abinda ya razanashi ne shiyasa ya suma, allura akayi masa, ba'a dauki lokaci Mai tsawo ba yafarka, amma yakasa cewa komai, abokin nasa yabashi hakuri, amma Abba bai iya cewa komai ba, daga qarshe ma tashi yayi ya cewa abokin yagode amma yanaso yabar garin yanzun nan, duk yanda abokin yaso hanashi tafiya abin ya gagara, dole sai Airport yakaishi yabi jirgin dazai tashi zuwa kano

Ikon Allah ne kawai yakai Abba gida, Momy tana zaune afalo sai ganin shigowar Abba tayi yana tafiya yana layi Kamar d'an maye, baima kalli Inda takeba yashige dakinsa da alama baima lura da'itaba

Fadawa yayi akan gadonsa, Baqin ciki yazame masa goma da ashirin, kenan kudin ankon aurenta yatura mata? 🤔
Lokaci daya yaji hawaye yana zubo masa, ga wani zazzabi dayakeji me mugun zafi, blanket dinsa yaja yashige ciki yana kuka, tabbas Nadiya taci amanar soyaiya

Momy taturo kofar dakin tashigo, ganinsa cikin bargo yasa ta qarasa da sauri tazauna a gefensa tace "subhanallah... Abba na lafiyarka kuwa?"

Dasauri yatashi yadora kansa a cinyar Momy cikin kuka yace "Momy Dan Allah kiyi hakuri, kuyafemin keda Daddy, bazan sake ba Momy"

Gaban Momy yafadi, bafa qaramin abu ne yakesa Abba kuka ba, anya kuwa kalau yake? Cikin tashin hankali tace "Abba meyake faruwa ne? Me kayi kake bada hakuri? Kayimin bayani"

Kuka yake harda Jan zuciya, yakasa fadawa Momy abinda yake faruwa, tayaya zai fada mata cewa yarinyar dayaso bijire musu, yaso Yaqi yi musu biyaiya akanta ta yaudareshi zata auri wani? Tayaya?dole ne yanemi yafiyar iyayen sa akan qin biyaiya dayaso ya musu

Momy tace "to shikkenan bari nafadawa Daddynka tunda ni bazaka fadamin ba"

Nan take takira Daddy, yana dauka tace "Alhaji takwaranka fa Babu lafiya, gashinan yazo yanata kuka wai nayi hakuri"

Daddy yace gashinan zuwa, Momy ta kalli Abba taga ko alamar dena kuka bayayi tace "to inaga addu'ah zanyi ma Abba, meyiwa gamo kayi" 🤣

Alokacin Daddy yashigo dakin, Abba yana jin shigowar Daddy yace "Daddy Dan Allah kayi hakuri, natuba Daddy wallahi bazan sakeba"






{Allah sarki Abba,😢Dani kabawa kudin ankon ma wallahi 🤣 🤣}









El Yaqoub ✍️
[6/24, 11:52 PM] El Yaqoub: ❣️DANGI DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub

Dedicated to DANGI DAYA GROUP 😃

Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493


25&26

Daddy yadubi Abba yace "yanzu Abubakar da girman ka kasamu agaba kana kuka kamar mace!, sannan mun tambayeka abinda yake damunka kayi shiru, sai hakuri kake bamu, to hakuri akan me?"

Shiru Abba yayi Bece dasu komai ba, shi ya'isa yafada musu gaskiya? Ai kaf family dinnan sai sunyi masa dariya wasu ma suce Allah yaqara
Dan haka yayi shiru yaqyalesu

Momy tace" Alhaji Abba fa ba magana zaiyi ba, nikam kaga tafiya ta "tasa hannu tadauke kan Abba dayake cinyarta tafuto daga dakin 😃
Shima Daddy yace" to ai shikkenan tunda haka kazaba "
Yafuto daga dakin, yaje wajan Momy yace"ko menene yake damunsa? Amma miskikanci ya hanashi magana?"

Momy tayi Murmushi tace "to awajan wa yadauko halin"

Shima murmushi kawai yayi, yashige dakinsa


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Tun bayan dukan dayayi mata ta tattara shi ta watsar, gaba daya tadena shiga sabgarsa, idan taji yashigo gidan ma tana falo cikin sauri take shigewa dakinta Tun kafin yashigo falon, abinci kuwa zatayi tabarshi anan, idan yaci shikkenan idan baici ba kansa yayiwa itade tasan cewa batada haqqin kowa akanta, koda rasuwa tayi tasan tafita haqqin sa saide nata haqqin dayake kansa
Tunanin abin datasa aranta yasa duk tafara ramewa, idanunta duk sun futo

Yauma shi kadai ne azaune afalon, Tun safe baije ko'inaba amma baiga futowarta ba, Kamar wasa saigata tafuto daga daki zataje kitchen, ta kalleshi ta watsar ko gaisuwa Babu, taje ta dauko ruwa tasake komawa dakin
Shikuwa Fawaz Yana binta da ido kawai
Yayi ajiyar zuciya yatashi yabita cikin dakin, yaune karon farko daya taba shigowa dakinnata, yanemi waje Yazauna yana Kallanta tanashan ruwa, saida tagama sannan yace "meyake damunki kika lalace haka?"

Shiru tayi masa, Dan renin hankali kawai, yagama dukanta yadawo yana Tambayar me yake damunta, idanunta sukai rau-rau zatayi kuka

Sassauta murya yayi yace "bazaki fadamin ba?"

Duk yanda Dida taso boye hawayen ta saida suka zubo, tasa hannu tashare tace "banasan abinda kake aikatawa ya Fawaz, kana dukana, kanashan kayan maye, nikuma banaso"
Tana qarasawa tasake fashewa da kuka

Fawaz yayi shiru yana tunani, Wato yau sabodashi ake kuka, yau saboda andamu da abinda yake aikatawa ake kuka yadena,nan take yarinyar tabashi tausayi
Kallanta yayi yace "to kiyi hakuri, dena kuka, insha Allah daga yau nadena"

Cikin mamaki ta kalleshi ido duk hawaye tace "da gaske?"

"yes da gaske nake"

"harda dukanma?"

Yasake cemata "nace miki nadena, kema saiki daina kukan ko? "

Aikuwa nan take tashare hawayen idonta

Yatashi tsaye yace "Zan fita, but banaso kina zaman dakinnan, kifuto falo ki zauna, kici Gaba da abinda kikeso kinji ko?"

Cikin murna Dida tace "to"


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Tunda Diyana tafara rashin lafiya Adam yake kula da'ita, kokadan baya barin ta tayi aikin komai
Yauma shida kansa yakawo mata abinci har daki, ya tarar tana gyara dakin, yace "maryam ga abinci"

Tace "ya Adam aina warke ma, nagode sosai da temakon dakamin, yau nice yakamata nadafa ma Abincin" 😳

Adam yayi Murmushi yace "nagode, amma ba yanzu ba,kici Abincin kishirya zamuje gida"

Cikin farin ciki Diyana ta rungumeshi tace "yawwa nagode ya Adam"

Cak jijiyoyin jikin Adam suka tsaya, yarinyar nanfa kada tasa yakasa aiwatar da abinda yayi niyya, cikin wata irin slow voice yace "Diyanaaah"  yaja sunan nata

Ahankali tadago daga jikinsa ta kalleshi yaune karon farko data tabaji yakirata da wannan sunan, koda yaushe maryam yake cewa, gashi  yanda yakira sunan nata ma kadai  ya'isa yasaka mutum cikin wani hali, ya'iya kiran sunan, tana gama wannan tunanin tayi fari da idonta tace "na'am"

Yace "kije kishirya mana, university nakesan wucewa daga gidan"

Murmushi tayi tace "to"
Sannan tasakeshi tashige toilet
Sai a lokacin yasaki wata irin ajiyar zuciya sannan yafuto daga dakin yadawo falo, abinda yake shirin yi shine daidai, dole zai nunawa Diyana kuskurenta, idan akaci gaba da zama ahaka to akwai matsala

Bata dauki Tsawon lokaci ba tafuto, ko hijabi bata sakaba kawai wani yalulun mayafi tayafa suka futo, shima Bece da ita komai ba, suna tafiya ahanya yana driving qira'ah tana tashi acikin motar
Har sukazo bakin get din gidan nasu Babu Wanda yace da dan'uwansa komai, amma Diyana tunanin Adam ne fal acikin zuciyarta, ashe haka yake da kirki? Babu ruwansa duk abinda take masa ko ajikinsa

Tsayawa ya kalleta yace "kishiga ciki, nizan wuce makaranta"

Cikin mamaki ta kalleshi tace "Kamar ya nashiga ciki, kai bazaka shigo ku gaisa ba?"

Fuskarsa Babu alamun wasa yace "kema ba gaisuwa nakawoki ba, gaba daya nadawo dake gida, kije saina nemeki"

Gaban Diyana yafadi, cikin rawar murya tace "ya.. ya.. Adam"

Cikin tsawa yace "yes abinda kikaji hakane, Maryam kitashi kifice min daga Mota kitafi gida saina nemeki"

Wani irin kuka ne yazo mata, Dasauri tabude motar tafuto da gudu tana kuka tayi cikin gidan
Kansa yadora akan sitiyarin motar idonsa yayi jajir, cikin kwana kin nan datayi batada lafiya tabbas yasan cewa yakamu dason yarinyar, saide bazai taba nuna mata hakanba, saita gane kuskuren data aikata abaya, shi aure ko wanne iri ne ba abin wasa bane


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️
Damuwa tayi masa yawa, gashi abin acikin ransa yarasa wazai fadawa yaji dadi aransa
Wayarsa ya janyo yakira Aslam "hello Aslam idan kasamu lokaci kazo gida inason ganinka, banda lafiya wallahi" 🤣

Aslam yace "subhanallah, to gani nan zuwa Abba"

Dama yana kan hanyar zuwa gida ne, Dan haka ya juya kan motarsa zuwa family house dinsu
Kai tsaye part dinsu Abba yaje, suka gaisa da Momy yashige dakin nasa

Akwance ya ganshi yana danna waya Yazauna yace "Abba da alama ka warke, tunda gashi wayace a hannunka"

Ajiye wayar yayi bayan yagama goge pictures din Nadiya da numbers dinta 🤣
Yace "banasan tunani yamin yawa ne''

Aslam yace" menene yake damunka? "

Abba shiru yana tunani, kode yafadawa Aslam ne? Kaiii wallahi Aslam ma sai yafi kowa yimasa dariya, Dan haka yace" kawai banajin dadin jikina ne "

" to Abba kaima kayi aure kaqi, ka zauna agaban Momy tuzuru dakai "🤣

" Aslam bana tunanin yin aure yanzu "😳🙆🏻‍♀️

"meyasa?" inji Aslam

Abba yace "haka nan, banda ra'ayin auren yanzu" 🤣

Ajiyar zuciya Aslam yayi "to shikkenan Allah yakaimu lokacin, daga campany nakefa kakirani, mungama tattara list din ma'aikatan da za'a dauka, yanzu kawai ina jiran kiran wayarsu ne, sunce zasu saka mana date din dasuke ganin shine yadace da bude campanyn, wallahi Abba banasan komawa gida, Ilham tacika rigima, yarinyar nan jiya gishiri tazuba min acikin abinci na, batajin magana "

Ran Abba yabaci  " meyasa zaka tsaya yarinya ta raina ka haka Aslam? "

Aslam yace" to Abba ba dole raini yashiga tsakanin muba, tunda taga tashigo dakina taganni haka "

Murmushi Abba yayi yace " Aslam ni aganina zancen boye boye yaqare atsakaninku, why not ka koya mata hankali sau daya, daga ranar zata dinga yima biyaiya, shikkenan anwuce wajan "

Dariya Aslam yayi yace" kai Abba, akwai shawara, toshknn Zan wuce gida, inaso nahuta kafin Baqin sukira wayata "

" to Aslam "

Aslam yafuto yatafi gida yana mamakin yanda suka shaqu da Abba, kowa yana fadawa kowa damuwar sa, gashi de bayasan magana amma inde da Aslam ne tofa zakaji maganar sa


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Da gudu ta qaraso part din nasu, cikin kuka tafada jikin mahaifiyarta tace "Mom ya Adam ya tsaneni"

Hajiya Farida ta dagota tace "ke kiyi shiru kimin bayani, meyake faruwa?"

Hawaye ta share tace "Mom cewa yayi natafi gida saiya nemeni, Allah Mom bazan zauna ba"

Hajiya Farida tafara salati "Innalillahi wa inna ilaihir raju'un... Diyana ki fadamin gaskiya me kika yi masa?"

"Allah Mom banyi masa komai ba, kuma saida yaga na haqura Zan zauna dashi zaice natafi gidanmu, Dan Allah Mom kibashi hakuri" 🤣

Hajiya Farida tace "yi shiru bari nakira babanku awaya,"

Alhaji habib takira, ta sanar dashi komai, nan take yazo gidan, yadubi Diyana datake zaune aqasa yace "ke maryam, fadamin gaskiya, me kika yimasa?"

Tace "Allah banyi masa komai ba, saide in wayar dayaji inayi da wasu maza ne yan ajinmu, kuma ni wallahi yan ajinmu ne, da rannan dana tafi biki ban fada masaba"

Alhaji habib yace "to ai kinji, haba maryam, da hankalin ki da girman ki tayaya zaki dinga waya da maza bayan da auren ki, ko qanwarki Dida bazata yi hakaba, ai shikkenan tunda kin kaso auren naki, saiki zo muzauna agida"

Cikin sauri tace "dan Allah, kubashi hakuri Mom Allah nadena, wallahi Zan dinga yimasa komai har girkin ma"

Zaro ido hajiya Farida tayi 😳"yanzu Diyana kina nufin har girki ma bakya yiwa wannan bawan Allah? Diyana me kikeso ki zama?"

Alhaji habib yace "to nide yaron nan yana ganina da mutunci, idan yaganni har qasa yake tsugunnawa ya gaishe ni, Dan haka ba zanje nabashi hakuri daga baya ki qara yin wani laifin yadena ganin girma naba"
Yatashi yafice daga falon nasu

Hajiya Farida tace "toke kinji, saiki haqura ki zauna, idan ya huce yazo yace kifuto kutafi saiki koma, tunda yace saiya nemeki"

Diyana tatashi tayafa mayafin ta tace "Allah Mom bazan zauna ba" daga nan tafice daga part din nasu tatafi part dinsu Adam wajan hajiya Na'ila🤣

Hajiya na zaune tanacin abinci taga Diyana tashigo tana kuka, Abincin hannunta ta ajiye tace "subhanallah, ke Diyana lafiya kike kuka? Me aka miki? Ko wani abu ne yasamu Adam din?" 🤣

Zama tayi akan kujera tace "Hajiya wai cewa yayi natafi gidanmu saiya nemeni"

Hajiya na'ila tahau salati "shi Adam dinne me yanke wannan hukuncin?" 🤔

Diyana ta daga kanta

"to kiyi hakuri, kidena kuka, zama na mutum biyu dole kowa yanada laifi, Zan kirashi gaba dayanku nayi muku fada, tashi kije daki ki zauna akawo miki abinci"

Diyana tatashi tana share hawayen idonta tace "to hajiya"

Hajiya na'ila tabita da kallo, Yaya zatayi tunda Allah yahada wannan aure, Diyana mace ce har mace, tasan cewa badan bibiyar maza da yarinyar takeba, Toda zatace tabbas danta yayi dacen mace
Tunda taji shiru dama tasan cewa to ko kalau kokuma akwai abinda yake faruwa agidan yaran, shima Aslam din Allah yakiyaye faruwar haka


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Zuciyarsa fes akan shawarar da Abba yabashi yashigo gidan da sallama

Tana zaune akujera tana jinsa tayi shiru, ya kalleta yace "Ilham ba kiji nayi miki sallama bane?"

Tadago kanta tace "naji, na amsa a zuciyata"

Jinjina kansa yayi, kowanne magidanci yanaso yadawo gida wajan iyalinsa amma banda shi, saboda idan yadawo ma bazai samu tarbar arziki ba
Dakinsa yashige ya cire kayansa yadaura towel zai shiga wanka

Dakin tashigo taje gabansa tace "ya Aslam inaso Zan fita, akwai Inda nakeso naje"

Kallanta yayi, eh lalle sai yanzu ya tabbatar cewa Ilham ta raina shi, har tazo gabansa ha ko ladabi Babu? Kai tsaye yace "bazakije ba"


Tace "ya Aslam gaskiya ni bakamin adalci agidan nan, haka kawai kai baka kaini ko'inaba, Sannan inaso nafita kace..... Dif tayi shiru sakamakon hade bakinsu dayayi waje daya, gaban Ilham yafadi, me ya Aslam yake mata haka? Cikin sauri tafara kokarin raba bakinta danasa, amma Yaqi bata damar hakan, kissing dinta yake sosai,tana tureshi daga jikinta shikuma yana qara riqeta, garin bige-bigen dasuke towel din jikinsa ya cire yayi qasa🙆🏻‍♀️

Cikin ransa yace shikkenan kin hutar Dani, cak yadauketa yadora ta akan gadon nasa, yafara nuna mata tsantsar soyaiya, kayan jikinta ya cire gaba daya, idanun Ilham suka raina fata, ganin da gaske yake ba qyaleta zaiyi ba, yasa tasakar masa kuka tana roqonsa yayi hakuri, amma Aslam ya shareta, kokadan baiji tausayin ta ba yashige ta kansa tsaye, Ilham tasaki qara tana dukansa, daga qarshe ma saiya hade bakinsa da nata yaci gaba da abinda yake, idanunta ya yi jajir saboda kuka, Aslam kuwa baya cikin duniyar, kawai cewa yake "Innalillah... Ilham... Meyasa bamuyi aure da wuri ba, Ilham ina sonki, wallahi ina sonki ilhma.... Tsawon lokaci yadauka sannan yasamu nutsuwa, yasa hannu ya rungumeta ajikinsa, yana jin wani irin farin ciki yana ratsashi, bed sheet din yaja yarufa musu idonsa akan qirjinta dasukai jajir

Tahada gumi jirgif, yasa hannu ya goge mata gumin fuskarta, yace "yi hakuri, kiyafemin kinji?"

Cikin takaici tace "mugu, azzalumi, wallahi sai Allah yasaka min abinda kamin" tafara kokarin tashi daga kan gadon, azabar da taji ne yasa tasaki qara cikin kuka takoma gadon ta kwanta

Murmushi yayi yace"ilham rigima, banace kiyi hakuri ba,? "kafin tace wani abu ya tura kansa cikin bedsheet din yayi kissing breast dinta, sannan yadago yace" i luv u Ilham," daga nan yadauketa suka shige toilet, Ruwan zafi yahada mata yasakata aciki, sannan tayi wankan tsarki, yadauketa yasakata ajikinsa, yanayi musu wani wankan, anan ma bai qyaletaba, breast dinta yana cikin hannunsa, hawaye kawai Ilham take banda azabar datake ji

Daqyar yabari suka futo daga toilet din yadaukota kai tsaye yakai ta dakinta, ya kwantar da ita saboda nasa dakin yariga ya lalace, hawaye tashare ta kalleshi tace "wallahi sai Allah yasa kamin abinda kamin"

Baiji dadin furucintaba, haka yafuto daga dakin jikinsa a sanyaye, dakinsa ya koma ya gyara, yana shiryawa, wayarsa tayi qara, yadauka aka sanar dashi ana nemansa cikin gaggawa, cikin sauri ya qarasa shiryawa, yafuto, ga Ilham batajin dadi, gashi ana kiransa, danhaka yakira number hajiya na'ila yace "mama kije gida Ilham batajin dadi, anyi min kiran gaggawa daga campany"

Gabanta yafadi, to sukuma ko lafiya? 🤔
Haka ta shirya tabar Diyana agida tataho gidan Aslam din


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Kokarin bude whtspp take da wayarta, saboda tadinga hawa kozai debe mata kewa

Saqo taji yashigo mata cikin wayar har guda biyu, tafuto ta duba, tabude guda daya taga alert ne yashigo mata, anturo mata 30k, tana duba sunan Wanda yaturo mata taga Yusif isma'eeil tayi Murmushi, Yaya Yusif kenan

Dayan tabude taga shima shine yaturo mata da number sa, nan take tafara karantawa:
Abinda nake mutuqar Burin ya kasance shi ne, nadinga kwana shimfid'e akan qirjinki , wani lokacin na yi bacci kwance a gefen ki, idan na runtse idanuwana na ganki cikin baccina, inaso naqara bayyana miki adadin yadda nake sonki, dakuma yanda nake Burin muyi aure mu kasance cikin inuwa guda daya, gida daya, daki daya, gado daya, fillo daya, blanket daya, kinajin numfashi na inajin naki, i luv u so much NIHLA"

Akwance take, amma tana gama karantawa tatashi zaune, Yaya Yusif ne kuwa anya? 🤔 Shine yaturo mata wannan kalaman? Kenan sonta yakeyi? Innalillah.. Meyasa ta rungume shi rannan? da tasan haka da bata aikata ba, wayyo wayyo, Dasauri takira wayar Anty Nadiya "hello Anty yaushe zaki dawo ne, shawara nake nema wallahi"

Nadiya tace "kai wannan qaramar qanwar tawa tacika takuramin kwana biyu, to gani agida, yanzun nan muka dawo"

Cikin murna tace "yeeee gani nan zuwa"

Mamy tayiwa sallama tatafi gidansu Nadiya, tana zuwa taganta da kayaiyaki agaba, itada mamanta suna dubawa, mamanta ta kalli Nihla tace "to Ga kayan lefe de sun qaraso, Nihla zauna ki gani kema"
Tatashi tafita, tabar musu dakin

Jikin Nihla yayi sanyi, ta kalli Nadiya "Anty Nadiya meyasa zakiqi aurensa?"

Cikin rashin damuwa Nadiya tace "kekam Nihla narasa irin zuciyarki, kin damu dayawa akan naqi auren Sadiq Mazawaje, saikace wani dan'uwanki?" 🤣

"ba haka bane Anty Nadiya, akwai tausayi dayawa, yana sonki sosai"

Nadiya tace "ya akai kika sani?"

"kawai alama nagani Anty Nadiya, amma Allah yabaku zaman lafiya"

Nadiya tace "yawwa qanwata haka nakeso naji, shawarar me kike nema?"

Nihla tabawa Nadiya wayarta tace "kinga abinda yaya Yusif yaturomin, harda kudi ra dubu talatin, Anty Nadiya kudin sunyi yawa me zanyi da kudi har dubu talatin?"

Nadiya tagama karanta text din duka tayi Murmushi tace "ai Nihla bakya buqatar shawara anan, kai tsaye ki amince, kina zaune lafiya da iyayen sa, shi yana sonki, kawai kicire wannan Abban daga ranki kisa Yusif, sannan kina maganar dubu talatin nawa dubu talatin din take awajan 'yan canji? Cemiki akai su suna jin kudi ne? Ki kwantar da hankalin ki kawai Nihla, kema ki tura masa cewa kin amince kuma kinga saqo kin gode "🤣

Cikin damuwa tace" Amma Anty Nadiya yaya Abba... "

Nadiya ta katseta" dan girman Allah Nihla ki rufamin Asiri da zancen Abban nan haba!!, tunda kika dawo Abuja da zama yataba nemanki ne? Inda ya damu dake zaizo har Inda kike ya nemeki"🤣 🤣

Tace" to shikkenan, nagode, dama shine shawarar, whtspp nake budewa natafi gida "

Murmushi Nadiya tayi tace" to sai anjima "


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Hajiya Na'ila tana shigowa gidan kai tsaye dakin Ilham tashige, ta tarar da'ita tana kuka sosai, cikin sauri ta qarasa gadon tace "subhanallahi, yanzu ke Ilham jinyar kikewa kuka saikace qaramar yarinya? Um to Allah ya kyauta, Aslam yamin waya tashi ki shirya Muje asbiti"

Hawayen idonta tashare, idanun nan yayi jajir, tatashi ta sauko daga gadon tanufi wajan kayan ta tana tafiya tana bude qafa, hajiya Na'ila tana ganin haka tafahinci komai, kuma ga yarinya daga sai daurin kirji, yanzu dama yaran nan haka suke zaune wata da watanni? 🤔

Afili tace "Allah ya kyauta, Kinshiga Ruwan zafi ne?"

Kuka Ilham ta fashe dashi ganin hajiya ta fahimci abinda yafaru, wallahi ya Aslam ya cuceta, fasa saka kayan tayi takoma gadon tazauna tana kuka sosai

Hajiya Na'ila tace "yau naji ta'bara, wai ni Ilham akanki aka fara karbar budurci ne?"

Ilham tasake jin wata kunyar, hajiya Na'ila kuwa tashi tayi tafara duba mata kayan dazata saka da kanta


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Tafiya yake yana driving amma tunani fal ransa, gaskiyar magana dayasan haka aure yake, da tuni yasauke girman kai ya lallaba yarinyar nan, yasaki murmushi Ahankali yace bazan iya Manta wannan ranar ba, maganganunta ne suke dawo masa, Mugu, Azzalumi, sai Allah yasaka min, yayi ajiyar zuciya yace oh Ilham tadauki abinnan da zafi, tunani yafara ko tana lafiya yanzu? Ko mama taje? Zuciyarsa tayi nisa a tunani saiji yayi yaci karo dawata motar, lokaci daya motar tasa tai gefe tadaki wani gini, mutanan dasuke wajan suka fara salati, aka tafi da gudu domin kai masa dauki
Daqyar suka zaroshi daga cikin motar kwata kwata Babu alamun rai atare dashi, wani daga cikin su yabude wayarsa domin sanar da yan'gida halin da ake ciki

Hajiya Na'ila takamo hannun Ilham suna tafe daqyar, sai mita take tana cewa zata hadu da Aslam din ne
Wayar hannunta tayi qara, cikin sauri tace "yawwa gashi nanma"

Ta daga wayar tace "kai gashinan muna hanyar zuwa Asbitin"

Daga daya bangaren akace "hajiya bashi bane, me wannan wayar yasamu hatsari yanzu nan, Allah yayi masa rasuwa"

Gaban hajiya Na'ila yayanke yafadi, tace "Innalillahi wa inna ilaihir raju'un, hatsari!!, yanzu Aslam dinne yamutu?yana ina yanzu? Ina zanga dana?

Kwatancen asbitin da'aka kaishi yayi mata, sannan ya kashe wayar

Kuka hajiya tace" shikkenan, Aslam yatafi yabar dan'uwansa Adam, yatafi yabarmu, Ilham Aslam yamutu "

Jin maganar hajiya take wani iri haka, wai wanne yaya Aslam din ake nufi? Girgiza kai tafara" A a, a a Hajiya, ni mijina be mutu ba, Yaya Aslam bazai tafi yabarmu ba, Anty Aysha tarasu, kidena cemin ya Aslam yamutu hajiya, yana nan da ransa... Sulalewa tayi tafadi awajan, hajiya Na'ila ta dora hannu aka tana kuka

Alhaji Baqir tayiwa waya, a lokacin su suna Asbitin ma, Abba yaji labari ya sanar dasu, shine yazo da kansa yasaka Ilham din amota sannan suka dauki hanyar Asbitin

Suna hanya Ilham tafarka, amma takasa gaskata abinda hajiya tafada mata, kuka take sosai, Alhaji Baqir dakansa shine yake bata haquri, amma abanza.

Suna zuwa Asbitin sukaga iyayen nasu duk sunje, Abba yafi kowa shiga tashin hankali, dazu-dazu Aslam yabar gidansu amma yanzu ace yana wannan halin,kwata-kwata yakasa zama sai zagaya wajan yake, Ilham tana ganin iyayen azaune tasake fashewa da kuka tafada jikin ummanta, Haushi yakama Abba, kasa boye bacin ransa yayi ya kalleta yace "koki rufewa mutane baki anan kokuma wanka miki mari yanzun nan, marar kunya kawai, koma menene bake kikaja ba?"

Alhaji Baqir mahaifin Aslam din yace "Abba! Kayi hakuri mana"

Likata ne yafuto daga dakin da aka kai Aslam din, gaba dayansu suka nufeshi, yace "Am Alhaji ku kwantar da hankalin ku, be mutu ba, yana nan da ransa saide yasamu karaya a hannunsa saikuma 'yan rauni dayaji, shima insha Allah zamuci gaba da bashi kulawa, zaku iya shiga ku ganshi amma Dan Allah banda surutu"

Ajiyar zuciya suka sauke gaba dayansu, domin kuwa dukansu kiransu akai awaya akace Aslam yamutu

Dakin suka shige, yana kwance yana bacci, ciwukan dayaji duk anyi masa aiki awajan, Ilham kam bataji kunyar kowaba tafada jikinsa tana kuka sosai, duk dakin Babu Wanda bata bawa tausayi ba

Haka suka wuni a asbitin, Ilham itace take masa komai duk da halin datake ciki itama, har Tsawon kwana biyar amma Aslam bai farka ba, Dafarko sun shiga damuwa, amma likitoci suka tabbatar musu da cewa Babu damuwa zai iya farkawa a kowanne lokaci, hakan ne, yasa hankalinsu yadan kwanta


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Kwance take akan gadon dakinta da Daddare, tunani take akan irin amsar dazata bawa yaya Yusif dangane da message din daya turo mata Tsawon lokaci
Idanfa ta amincewa yaya Yusif hakan yana nufin tabbas zata iya auren sa ne, wata zuciyar tace to Wanda kike haukan akansa shi baya sonki, kawai gara ki amince koshi din zai nuna miki tsantsar soyaiyar dazata ki Manta da Abba

Afili ta furta "yaya Abba, duk kaine kasani cikin wannan halin"

Amsa ta turawa Yusif din cewa ta amince, sannan tayi addu'ah Allah ya tabbatar musu da alkhaairi a tsakanin su sannan kuma ubangiji yayi mata Zabi nagari bawai son zuciyarta ba

Momy ce tafado mata arai, Allah sarki Momy haqiqa tana tsananin sona, ko yaya take yanzu? Tana kewarta sosai

Afili ta furta "i'm sorry Baba"

Tadau wayarta tafara saka number Momy, kasancewar ta riqe number

Adede lokacin Momy tana falo azaune tareda yaranta gaba dayansu, Usman, Aliyu, farouq, dakuma oga kwata-kwata Abba 🤣
taga Sabuwar number na kiranta,cikin nutsuwa tayi picking tace "Salamu Alaikum"

Abangaren Nihla kuwa tunani tafara, da wanne suna zata kirata? Tasan cewa Babu abinda Anty takeso Kamar takirata da Momy, Dan haka cikin farin ciki tace "Momyyyyy, i miss you Momy nah"

Shiru Momy tayi, ko a mafarki taji wannan muryar bazata Manta da ita ba, cikin farin ciki tace "Nihla!!!"

Gaba dayansu hankalinsu yadawo kan Momy jin sunan data ambata, Abba kuwa haka kawai ya tsinci kansa cikin farin-ciki baisan dalili ba

Momy tace "  'yata Nihla ina kika shige? Idan nakira Mai hakuri saiya cemin kina lafiya, kina lafiya ko 'yata?"

Murmushi tayi tace "ina nan lafiya Momy, karatu ne ya boyeni, baba ya maidani makaranta Momy, ina shirin gama level 1 ma"

Momy tace "Alhamdulillah, kice yata tazama yanmatan jami'ah, nasan yanzu samari suna nan buhu-buhu ko?"

Dariya tayi tace "um um Momy karatu na kawai nake, Momy ina Daddy da sauran yan gidan?"

"Daddynki yana nan kalau, yanzu ma yana masallaci Tun sallar ishsha'i bai dawoba, amma daya dawo Zan fada masa kin kira, sukuma yan gida dasu Dida kowa tana nan lafiya Nihla"

Tace "to Momy inasu yaya Usman?"

"Usman gashinan Nihla, duk yayunki sunzo yau suna tayani fira, ga farouq nan da Aliyu, dakuma yayanki Abba"

Gabanta ne yafadi jin an ambaci sunansa, amma saita share tace "Momy bawa yaya Usman wayar mugaisa"

Momy tabashi wayar tace "Usman ga qanwar ka tana magana"

Yana karba yace "da alama de wannan yar qauyen Dani takeyi yanzu, nine na gaban goshin, tunda nita fara nema"

Dariya tayi tace "ya Usman wallahi kamin tsufa yanzu, sai sabon jini"

Yace "aikuwa sainazo an goga Dani, yarinya tuni Zan daukeki daga Abujan nan kidawo kano"

Abba yakalli ya Usman yana mamaki, yaushe tatafi Abuja? Ya akayi besaniba? 🤔

Nihla kuwa dariya tayi tace "nide yanzu ya Usman Dan Allah bawa ya Aliyu mu gaisa"

Aliyu yabawa wayar, yace "qanwata yakike, dafatan kina lafiya"

"lafiya kalau ya Aliyu, yagida yayara"

Yace "duk suna lafiya,naji kincewa momynki kinkoma school to kidinga karatu sosai kinji ko? Banda kula samari"

"to ya Aliyu insha Allah nagode, ina ya farouq?"

Yace "farouq gashinan azaune yanaji Kamar ya qwace wayar" 🤣

Dariya tayi tace "to bashi"

Farouq na karbar wayar yace "Wato kin gudu kin barmu, kin lula birnin tarayya, to ki gama karatun kidawo, ina nan ina jiranki auren nan de yana jiranki sai andaura Dani" 🤣

Dariya tayi sosai tace "to yaya farouq aikai nawane, zan amince amma da sharadin makkah duk sati, yawon bude ido duk bayan wata daya" 🤣

Yace "inyeee wannan ai kora da hali ne, to bari kiji inde makkah ce saikin gaji, kullum Zan dinga kaiki, muda mukeda Pilot ai bakida matsala"

Sarai tagane Inda maganarsa ta dosa amma saita shareshi tace "to shikkenan, dakai din za'ayi, amma yanzu nide bawa Momy na waya zamuyi sallama"

Kai tsaye farouq yabawa Momy wayar, tana karba kuwa Nihla tayi mata saida safe akan wani lokacin zata sake kiranta, daga nan takashe wayar

Ba Momy kadai ba, hatta Usman, farouq, Aliyu saida mamaki yakama su, meyasa bata tambayi Abba ba? Ko bataji Momy tace suna tare ba?

Shikuwa jikinsa ne yayi sanyi, sai yaji murnar dayake takira waya duk tagushe, meyasa shi batace abata shiba? It means ta tsaneshi, batason jin voice dinsa








(kwana biyu zaku jini shiru, zanyi tafiya ne zuwa wajan wani biki, bazan samu damar typing ba, insha idan mungama zaku jini, nagode da soyaiyar dakuke min i luv u All 💋💋💋)



(ko yaya batun Diyana da Adam?)

(Aslam yabude taro da addu'ah 🙈ko waye zai biyo baya Kuma? 🤔 )


Game buqatar wannan littafin daga farko zuwa Inda muka tsaya, ya nemi wannan number  09039066577



Sharhi



Comments




Share please 🙏








Amnah El Yaqoub ✍️
[6/29, 11:18 PM] El Yaqoub: ❣️DANGI DAYA❣️

{Romance&Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub

Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493



Bayin Allah ya kwana biyu? Alhmdllh mungama biki lafiya, naji dadin yanda dayawa sukamin uzuri saboda sha'anin biki, masu yimin addu'ah nagode sosai, amarya tana godia.

Masu neman DANGI DAYA complt kuyi hakuri wallahi Nikaina banda shi complt a wajena, duk Wanda kukaga anyi muku posting dinsa arana, to wallahi aranar na rubutashi, ganda ma bazata barni narubuta cmplt lokaci dayaba

Masu tambaya sunason littafin gaba daya saboda sun matsu suga dramar Abba da Nihla suma suyi hakuri, sannu sannu bata hana zuwa, kuyi hakuri mu qarasa ahaka, bazai iyu na sauya tsarin labarin saboda Abba da Nihla ba, idan na sauya to komai zai iya lalace wa🤒

Sukuma masu cewa kona kudi ne sunaso nasiyar musu dashi complt to DANGI DAYA free ne, Tun farko nafada cewa idan labarin yamiki dadi kawai kimin addu'ah, Allah yabarmu tareda masoyan mu ameen👏🏻


27&28




Karan farko dayaji wani Baqin ciki ya kamashi, Ahankali yatashi tsaye ya kalli Momy "Momy Am tired, zanje nahuta" yana fadar haka yayi gaba

Momy ta kalleshi tace "to Abba"

Bayan yashiga daki ya Usman yace "Momy ran Abba fa yabaci, Kamar kishi yake"

Aliyu shi dama Babu wasa, kai tsaye yace "basai yayi ba, shiyasa ko sallama baiyi manaba yayi daki"

Farouq yayi dariya ya dauki wayarsa yace "anayi ina daga gefe ina smiling"

Momy tace "a a shide Abba baice hakaba, ni farin ciki ma naga yanayi" 🤣


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Dawowar sa kenan daga yawonsa, yashigo falon da sallama, yaji shiru, kai tsaye dakinta yashiga, a lokacin tana kwance tana bacci, daga ita sai d'an qaramin siket under wear shitaja har sama, hakan yasa cinyoyinta suka baiyana, hankalin ta kwance tana bacci bataji shigowar sa ba, yadade a tsaye yana Kallanta, shi sai yau nema ya qarewa yarinyar kallo san ransa, tana yanayi da Diyana sosai, ahankali yataka yaje gaban gadon ya tsugunna yaja qarewa fuskarta kallo, saida yagama ganinta tsaf, sannan yakai hannunsa ya shafa kanta Ahankali, Allah ya temakeshi bata farkaba,Inda tafarka ta kamashi da yaya zaiyi? Shida yake cewa itace take liqe masa
Ahankali yatashi yafuto yayi cikin dakinsa

Zama yayi agefen gadon tareda yin tagumi hannu bibbiyu, babu abinda yake masifar son yasha irin qwaya, gashi ya cewa wannan yarinyar yadena sha, amma a yanda yakeji yanzu idan bai shaba gaskiya akwai matsala, hannu yasa a aljihunsa yadauko su har guda biyu, yasha abinsa sosai yayi watsi da kwalaben anan, sannan ya kwanta yafara kokarin bacci, yasan cewa kafin ma tatashi daga bacci yatashi yayi wanka yafice


Dida kuwa ta dade tana bacci sannan tatashi tashige toilet tayi wanka, shaf ta shirya cikin atamfa dinkin riga da siket, tasan ya Fawaz bai dawoba Dan haka ta nufi kitchen domin dora musu abinda zasuci

Tafuto falon kenan zata shiga kitchen din taga kofar dakinsa abude, cikin mamaki tace "to lafiya?"

Dakin ta nufa tashiga kanta tsaye, ranta ne yayi mugun baci ganinsa kwance shame-shame yana bacci ga kwalaben kayan mayensa nan azube agefe, kenan sake sha yayi, haushi yaqara kamata, cikin takaici ta qarasa wajansa tana dukansa yatashi amma Fawaz ko gizau beyiba, awajan ta tsugunna ta dora kanta akan gadon setin kafafunsa tasaki wani irin kuka Mai cin rai, kuka take sosai tana tunanin Rayuwar ta, duk cikin 'yan'uwanta da aka musu aure tare ko wacce tana zaune gidan mijinta lafiya amma banda ita, ya Fawaz kullum shaye-shaye, ga duka, dago idonta tayi ta harareshi Kamar yana ganinta,garama tatashi Tun kafin yatashi Yarufe ta dawani dukan, shaye-shayen ma yace ya daina gashinan Akwance bai daina ba, to dukanma tasan cewa bazai fasa ba

Ahankali tatashi tafice daga dakin nasa, ko kallan kitchen din batayi ba tashige nata dakin tadauko mayafi da wayarta da jakar ta, tafuto daga gidan, saida ta kalli gidan hawaye yazubo mata sannan tasamu me napep tahau tayi masa kwatancen Inda zai kaita

Yana ajiyeta directly part dinsu tanufa, tana Jan jaka tana share hawaye
Hajiya Farida da Alhaji Habib suna zaune afalo suna tattaunawa akan maganar Diyana, kwata kwata Adam Yaqi zuwa gidanma bare ayi masa magana yadauketa su koma

Kawai sai ganin Dida sukai afalon tashigo tana kuka, gaban hajiya Farida yafadi, tace "nashiga uku Alhaji, meyake faruwa ne yara sai dawowa gida suke daya bayan daya?"

Kafin yabata amsa Dida ta qaraso dakin tazauna akan kujera tareda dora kanta akan cinyar uwar tana kuka sosai
Alhaji Habib yace "ke Dida, meyake faruwa? Kinshigo gida da jakar kayanki bakice mana komai ba"

Cikin kuka tace "Allah ni nagaji bazan koma ba"

"me yafaru?" cewar hajiya Farida

Dida tace "Mom kullum ya Fawaz saiya dinga shan kayan maye, nace yadena Yaqi ji, rannan yacemin yadena sha, shine yanzu ma naganshi yasha"

Alhaji Habib yayi ajiye zuciya, hajiya Farida tace "toke Dida waya fada miki ana kama maganar Mashayi? Ai yanzu zai zauna yadinga yimiki rantsuwa da Allah yadena amma ana jimawa zakiga yasha, waya kai Dan qwaya biyaiya? Idan gaisuwa ce har qasa zakiga yana gaida babba Kamar mutumin kirki, kuma yadinga yimiki rantsuwa shifa yadena shaye-shaye, amma hakan bazai sa anjima inde yaga qwaya yadauka yasha ba, kuma su masu shaye-shaye mace bata gabansu, bare ayi tunanin zataja hankalinsu harsu daina, da wahala kiga Mashayi wai yana kula yanmata, addu'ah daya zakiyi Dida Allah yasa Fawaz ya soki, to wannan kam idan yafara sonki duk abinda kikace zaiyi, amma a yanzu kam saide kiyi hakuri"

Ta kalli Alhaji Habib tace "Alhaji ba zama zakai ba7, tashi zakai kamaidata dakin mijinta"🤣

Dida najin haka ta qara volume din kuka tace "Mom Allah bazan koma ba, dukana fa yakeyi"

Hajiya Farida da Alhaji Habib suka hada baki wajan fadin "Duka!!"

Alhaji Habib yace "subhanallah"

Hajiya Farida tace "a a, to bazaki koma ba Dida, bazakije ya kashe minke ba, ina sonki, tashi ki shiga daki"

Dida tatashi taja jakar kayan ta tashige dakinta, hajiya Farida tayi tagumi tace "yau naga ta kaina, yarana har biyu agida,Allah ya hadani da sirikai biyu na arziki dana tsiya, shi na arzikin ya koro min 'yar tana gida, shina tsiyar matar tagudo tabarshi, kaiiii Allah ka sayaya mana"


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Qaran da wayarsa takene yasa yaji baccin duk ya'isheshi, daqyar yabude idonsa ya kalli Agogon hannunsa yaga magrib ta kusa, kaiii gaskiya yadau lokaci yana baccin nan, wani kiran ne yasake shigowa yadauka yana magana daqyar "hello ummah yane"

Ajiya Abida ta Girgiza kanta, Allah ya shirya mata Fawaz, wai ita yake cewa yane tace "naje Asibiti ne ganin mijin qanwar ka naga family kowa yana zuwa amma bangankaba"

Yace "Ummah meyasamu mijin Ilham din"

"wallahi Accident yayi, harya samu karayama, yakamata de kaje, narasa meyake damunka Fawaz, gaba daya baka cikin nutsuwarka, anyi ma fada kadena shan qwayar nan amma kaqi ji, tokaci gaba wataran saita haukatar dakai, yanzu ace mijin yar'uwarka ciki daya yayi rashin lafiya kusan sati amma ace kai baka saniba, ai shikkenan idan Baqin cikin ka ya kasheni "dif ta kashe wayarta

" kai ummah tanada damuwa wallahi, menene kuma na ambatar mutuwa? "cewar Fawaz, daga nan yatashi yashige toilet yayi wanka, tsaf ya shirya cikin qananun kaya, yafuto falon, ganin dakin Dida arufe yasa bai shigaba, yasan tana bacci itama

Kai tsaye Mota yashiga yakira wayar Ilham din tafada masa a asbitin dasuke, sannan ya kashe wayar yaci gaba da driving


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Zaune take agefen gadon akan kujera dede setin Inda kansa yake, Dan qaramin handkerchief ne a hanunta data jiqashi da ruwa tana goge masa kansa dashi, saboda taji kan nasa akwai zafi

Fawaz ne yashigo dakin shida wata nus datayi masa jagora, yana ganin halin da Aslam yake ciki jikinsa yayi sanyi, wannan hannu duk an nad'e masa shi, ga qananun ciwuka, tashi Ilham tayi tabashi kujerar Yazauna, anan yake tambayarta yamai jiki

Shiru sukayi na wani lokaci, Fawaz de jiki yayi sanyi, cikin ransa yake magana tabbas dan'adam ba abakin komai yakeba, kaduba kaga de halinsa Aslam yake ciki rai ahannun Allah shida bayama shan ko wacce irin qwaya, Allah ya jarabceshi da wannan qaddarar, to idan shine dayake aikata wannan mugun halin yaya nasa abin zai kasance kenan? 🤔
Tabbas dole ne yayiwa kansa fada ya shiryu Kamar sauran yan'uwansa, insha Allah yayi alqawarin daga yau yaraba hanya da kayan maye.
Jiki a sanyaye yayi mata sallama yatafi gida

Shiru Ilham tayi tana kallan Aslam, ita sai yanzu ne take ganin mugun kyansa, ya Aslam ya hadu ba qarya, amma da qiyaiya tahanata gani,Allah sarki, ko yaushe zai farka?.
Ahankali yafara bude idonsa, yasaukesu akanta, rufe idonsa yayi yana tunani nan take hatsarin dayayi yadawo masa cikin qwaqwalwar sa, bude idon yayi yaga tabbas Ilham yake gani a gefensa, meyasa tazo Inda yake? Ai yayi tunanin zatafi kowa murna
Farinciki ya rufe Ilham, cikin murna tace "Alhamdulillah, ya Aslam katashi? Sannu ya Aslam bari nakira Doc."

Cikin sauri tafice daga dakin yabi bayanta da kallo, menene ya sauya yarinyar nan haka lokaci daya?

Doc. ne yashigo dakin ya duddubashi tareda yimasa yan tambayoyi sannan yace yaci gaba da shan magunguna zuwa jibi za'a warware masa hannun nasa, sannan yafita

Ilham kuwa sai murna take bakinta Yaqi rufuwa, kujerar datake kai takoma ta zauna, ta dora hannunta akan goshinsa tace "ya Aslam sannu, ahadama Tea kasha ko?"

Dayan hannunsa da Babu ciwo yasa yakawar hannunta dake kansa yace "kidena tabani banaso, ai shikkenan tunda hankalinki ya kwanta, ba haka kike so kiganni ba"

Wani irin kuka ne yazo mata maicin rai, batasan lokacin data fada kansa ta rungumeshi ba, tana kuka, hawayenta yana d'isa agefen wuyansa, cikin kukan tace "ya Aslam Dan Allah kayi hakuri Allah nadena"

Aslam kuwa baisan lokacin daya lumshe idonsa ba jin nashanunta masu laushi akan qirjinsa, dama gwadat yake yaga tadena rashin kunyar kokuma de tarkonsa yakama shima tafara sonsa🤪

Adede lokacin Adam yashigo dakin, hannunsa dauke da ledojin fruits, murna yafara ganin idon dan'uwansa biyu yaude yafarka, adaya bangaren kuma kunya ce ta kamashi ganin yanda Ilham ta rungumeshi tana wani kuka qasa-qasa 🤣

Aslam yace "Adam sannu da zuwa"
Ya kalli Ilham dako niyyar tashi batayi yayi qasa da murya yace "qanina fa yashigo, zakisa ya renani" 🤣

Ahankali tatashi tana goge hawayen idonta tace"  ya Adam sannu da zuwa, ina wunin "

Adam yayi ajiyar zuciya yace" lafiya Ilham, ashe maigida ya miqe "

Murmushi tayi masa kawai, takama hannun Aslam din tariqe Kamar wani zai qwace mata shi.
Hajiya Na'ila ce tashigo dakin Diyana tana gefenta da abinci a hannunta

Da Adam tafara tozali acikin dakin, yana sanye da qananun kaya, saiyayi mata mugun kyau, ahankali tasauke idonta kasa, shikuwa Kallanta yake yana magana cikin ransa, Wato maryam dayace taje gida saiya nemeta wajansa mahaifiyarsa tatafi kenan 🤣, dama ai matsalar ka auri wadda kuke DANGI 'DAYA da'ita kenan, yanzu Inda bare ya aura ko hanyar gidansu bazata nemaba, Dan Allah kalli wannan shegen kayan data saka duk ya kamata hips dinta awaje, kuma mama tana gani shine suka futo ahaka

Cikin nutsuwa Diyana tace "ya Aslam ya jiki?"

Yace "jiki Dasauqi Diyana"

Ta kalli Adam dinma tace "ya Adam ina wuni ya aiki" 🤣

Shiru Adam yayi be amsa mata ba, haushi yakamata, Hmm zata rama ne

Hajiya Na'ila tace "kema de dabata yawun bakinki kike, kina gaidashi yana wani hura hanci, ajiye musu Abincin mutafi gida" 🤣

Diyana ta ajiye Abincin tafice daga dakin, hajiya ta kalli Adam tace "kasan abinda ka aikata ai, shiyasa idan na nemeka baka dagaba, to kazo gida ka sameni ina nemanka" tana fadar haka tafice daga dakin


Aslam yace "Adam kayi hakuri, kasan sha'anin mata sai Ahankali, dole sai kakai zuciyarka nesa, da niyya ma zasu dinga qin yiwa mutum biyaiya kasan... Su"

Maganar sace ta katse saboda mintsininsa da Ilham tayi ahannu🤣

Adam yayi Murmushi, shikam sun birgeshi, inama maryam zatazo ta koyi yanda ake kula da miji anan, yace "to insha Allah, nizan tafi, sai gobe idan Allah yakaimu"

Aslam yace "to shikkenan kakira Abba kafada masa natashi please"

Yace "okey"

Daga nan yaja musu kofar, Ilham tayi masa hararar wasa cikin shagwaba tace "shine zakake fada masa laifi na ko?"

Murmushi yayi yana Kallanta Kamar ba'itaba, Kamar an sauya masa qanwar budurwarsa🤣
Yace "ya jikinki? Yanzu de Babu kuka kin warke sosai ko?"

Kunya takama Ilham, tasa hannu ta rufe idonta tace "dan Allah ya Aslam katashi Muje kayi wanka" 🙈

Murmushi yayi, sannan yafara kokarin tashi, yana jin dayan hannun yana masa ciwon kadan-kadan




❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Jikinsa a sanyaye yadawo gida yana tunanin mutuwa, kai tsaye dakinsa yawuce yabude kayansa duk wata qwaya datake ciki saida ya dauko ta, nacikin fridge ma yadauko su yazuba acikin wani kwali yanufi dakin Dida dasu, yanaso ya tabbatar mata cewa yau yadena shan komai, yanaso yafara tabbatar wa matar sa cewa daga yau Babu me sake kiransa da Mashayi
Amma me, yana bude dakin yaga bata nan, qarasa shiga yayi yaga kofar toilet dinta abude, afili yace "a a, to ina yarinyar nan tatafi ne? Nasan duk Inda zataje tana tambayata ai"

Cikin sauri yafuto yadawo kitchen bata nan, yaduba compound bata nan, kwalin dake hannunsa yasaki yafadi qasa, yasake komawa cikin gidan da gudu, karon farko daya fara ambatar sunanta "Dida! Dida!! Dida!!!, ina kike ne?"

Wasa-wasa saida Fawaz yagama duba gidan tas yaga bata nan, Kamar mahaukaci haka ya koma dakinta ya kalli Inda akwatunanta suke yaga sunragu, anya kuwa Dida ba guduwa tayi tabarshi ba? Kode taganshi ne dazu bayan yasha maganin mayen nan? Tabbas yarinyar nan taganshi, awajan ya sulale yazube akan gwiwar sa tareda dafe kansa 🤦🏻‍♂️, ya zata masa haka?


Dasauri yatashi yafuto daga dakin yashige motarsa bai zarce ko'inaba sai gida

Kai tsaye part dinsu yatafi, hajiya Abida tana zaune tana kallo sai ganinsa tayi yashigo Kamar mahaukaci

Tace "subhanallah Fawaz lafiya?"

Yana daga tsaye yace "umma Dida batazo nan ba?"

Tace "Dida kuma? Aini rabona da Dida Tun bikinku Fawaz, kai baka taba hankalin dauko ta ka kawomin ita ko wuni ne muyi ba, itama batazo ba"

Gabansa ne yafadi, Yazauna aqasa kafet din falon jagwab, Idanunsa suka kada sukai jajir yace "Innalillahi wa inna ilaihir raju'un , Umma Dida tagudu tabarni" sai kuka 😭

Gaban hajiya Abida yafadi tace "kaini banason sakarci, yanzu Inda qannanka suna nanma haka zaka zauna kanamin kuka, kayi min bayani dalla-dalla meyake faruwa?"

Cikin kuka yace "umma...gani...ganina..tayi nasha wani magani shine... Shine...tagudu"

Tace "ahaf, ni nasan da walakin goro amiya, haba Fawaz, yarinyar nanfa tana kokari, aure kusan shekara biyu amma bata taba kawomin kararka ba, lokacin da akace anhadaka da'ita yarinyar nan ko uhm batace ba, duk family dinnan kowa yasan anfi qwararta akan sauran 'yan'uwanta, ai kai kamata yayi ma ace kayiwa yarinyar nan gata samada kowa acikin gidannan, kayi mata abinda takeso ka fifitata saboda ta rufama Asiri ta zauna dakai, yanzu ma dakace akan kasha wani magani tagudu bawani magani dazaka sha Fawaz bayan na maye "

Cikin kuka Fawaz yace" to umma kuma saita gudu tabarni "

Tace" a a, bamu bincikaba ba zamuce tagudu ba, tashi Muje wajan maigadi muji ko yaga shigowar ta gidan "

Tashi yayi yana goge hawaye yabi bayanta, suna zuwa wajan maigadi ya tabbatar musu da cewa tabbas yaga Dida Tun rana tashigo gidan, shine ma yabude mata get

Hajiya Abida tayi masa godia takoma part dinta, ta nemi kujera zata zauna kenan Fawaz yasa hannu yariqe rigarta yace "Ummah matata" 😭

Qwace rigarta tayi tazauna tace "tome Zan maka Fawaz? Bakaji da bakinka ance tazo gidaba? Ai kasan hanyar part dinsu"

Zama yayi agefen qafafunta yana kuka Kamar mace yace "Ummah Allah nide adawomin da matata, ya za'ai naje part dinsu bayan nasan mamanta bata sona" 🤣

Hajiya Abida tace "kaga Fawaz karufe min baki, ya zakazo kasani agaba kanamin kuka? Lokacin daka mata laifin kayi shawara Dani? To bari kaji, tunda akai auren ku har yau Babu Wanda yace uffan akan zaman aurenku, Dan haka ba zanje part din hajiya Farida tafadamin magana inqyale taba, wallahi saide kaje"

Bece da'ita komai ba, yatashi yafice daga part din, yayi nasu Dida, hankalin sa kwance yatura kofar falon, a lokacin kuwa Dida tana zaune itada Hajiya Farida suna kallo, kallo daya tayi masa tadauke kanta, cikin ransa yace tana nan kenan

Hajiya Farida tace "a a Fawaz kaine atafe, sannu da zuwa, shigo ka zauna"

Fawaz yanemi waje Yazauna yana mamakin yanda ta karbe shi hannu biyu, sai sunkuyarda kansa yake qasa dan karsu gano yasha kuka 🤣

Hajiya Farida ta miqe tsaye tace "Dida kawo masa ruwa mana" daga nan tayi cikin dakinta tabarsu su biyu, cikin ranta tace tasan bazai wuce biko Fawaz yazo ba, ita kuwa bada itaba, yaje su qarata atsakaninsu, tunda taga Dida tadawo gida tasan cewa qarshe yakai yarinyar shiyasa tayi fishi tataho gida, to ba zatayi mata dole akan takoma gidansa ba, Dan daga nanma zata iyayin wani gidan su nemeta su rasa, gara yanda tazo da qafarta, takoma da qafarta, amma bazata bakinta a sabgar yara ba


Daga kan kujerar yasauko yadawo kusa da ita har tanajin yanda numfashinshi yake sauka akan fuskarta yace "Dida"

Kallansa tayi, yaune karon farko data tabaji yakira sunanta, harara ta sakar masa tatashi ta nufi hanyar dakinsu, shima yatashi yabita, tana shiga dakin tarufo kofar, shikuma yakawo kansa zai shiga sai qumm tabige masa fuska

Kadan yarage Fawaz yayi hauka agidan surukai 🤣, haka yafuto jikinsa duk yayi sanya, ko kallan part dinsu baiyi ba yaja motarsa ya koma gida


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Yau Tun safe hajiya Na'ila bataga futowar Diyana ba, Dan futowar datake ta yataya aiki ma yau shiru 🤣

Tace "to wannan yarinya ko lafiya?" tashi tayi ta nufi dakin nata, tana zuwa ta risketa tana kuka adaki, hajiya tace "subhanallah Diyana menene kuma yafaru?"

Cikin kuka tace "Hajiya niso nake natafi gidanmu"

Hajiya tanemi waje tazauna agefen Diyana tace "ai dole kice zaki tafi gida Diyana, tunda shi yazo ya ajiye ki baya tunanin zuwa ya dauke ki, bansan yaushe Adam yakoyi taurin kaiba, nace yazo gida ya sameni Yaqi zuwa, nakira wayarsa kuma yadena dauka ma yanzu, inde baso yake na yiwa babansu maganar ba bansan yaya zanyi ba, hada kayanki ina zuwa "

Gyada kanta tayi, sannan tadauke komai nata na dakin itama ta shirya, hajiya ce tadawo dauke da cup ahannun ta da zuma aciki, tace "ki kalli abinda Zan hada miki kigani saiki dinga yi ,"

Diyana ta gyada kanta tana goge hawaye

Hajiya tazauna tana 'bare gyadar miya da qwai agaban Diyana tanayi tana sababi🤣"ba dole maza su dinga renaku ba, yaran zamani idan anyi muku aure shikkenan saiku zauna dagaku sai i love you, bazaku tashi tsaye akan mazajenku ba, ko wacce mace tanada sirrin ta, kuma ita tasan abinda mijinta yakeso, Inda kin kamashi ahannun ki datun ranar dayace kidawo gida saiya nemeki toko sati daya bazai iyaba zaizo har Inda kike yadauke ki "

Akan idon Diyana hajiya Na'ila tagama bare gyadar miya guda goma, da dafaffan qwai guda biyu sannan tazuba acikin cup din zuman nan tabata tace" karbi ki shanye duka "

Diyana datayi kasaqe tana kallan ikon Allah takarba ta shanye, zaqin zuman yasa harda saka hannu ta lashe kofin tass🤣
Cikin ranta tana mamakin hajiya, ko da wadannan abubuwan take amfani shiyasa duk masifar ta mijinta yakasa rabuwa da ita?

('yar uwa wanna sirri ne Mai mutuqar kyau wallahi, ko gwada zaki tabbatar da magana ta, wadda bata taba yiba zata samu gyadar miya, irin me qamshin nan, bafa gyada wadda ake gyada amaro da'itaba, a a gyadar miya zaki samu guda goma, kibareta kidaka tadaku sosai, saiki bare dafaffan qwanki guda biyu, ki yaiyanka akan gyadar miyar dakika daka, saiki zuba zuma cokali biyu aciki kijuya sosai, saiki shanye gaba daya, idan kuma kin tabayi to qwai daya zaki yaiyanka Karki sake kisa guda biyu, sirri ne Mai kyau, matan aure zasuji da dinsa sosai, ki jarraba yar'uwa🙏🏻)


Hajiya ta dubeta tace "to nan gaba saiki dinga saka qwai daya, kuma biyaiya kici Gaba dayi Diyana, yinayi bari nabari,kuma saikin ja ajinki dakyau, ki nuna masa kema kinada daraja, dan abubuwan Jan hankalin nan kidinga yimasa, yar kwalliyar nan ce duk ki masa" 🤣

Diyana tace "to hajiya, insha Allah"

Daga nan hajiya tace tasaka  mayafin ta sutafi, aikuwa cikin sauri Diyana tasaka suka futo, ahanya ma fada take qara mata, tana dada wayar mata da kai akan zaman aure har sukaje gidan nasa 🤣

Sabon maigadi suka gani azaune abakin get din, nan hajiya tafada masa kosu waye, aikuwa cikin ladabi yabarsu suka shiga, acikin ma saida hajiya tasake yimata fada sannan tayi mata sallama tatafi, hajiya na tafiya Diyana tatashi tahau gyaran gidan, dakinta tafara gyara wa da toilet Sanna tashige dakinsa, duk gadon nasa a hargitse, haka tahau gyaran dakin tasaka masa Air freshner, duk kayansa daya ajiye a'inda bai daceba ta gyara masa su, takardun dalibai yan jami'ah data gani Kamar ma text ne suma ta tattara masa su waje daya, sannan tafuto ta gyara falon, bata zauna ba tashige kitchen tahada masa abinci Sabon maigadi suka gani azaune abakin get din, nan hajiya tafada masa kosu waye, aikuwa cikin ladabi yabarsu suka shiga, acikin ma saida hajiya tasake yimata fada sannan tayi mata sallama tatafi, hajiya na tafiya Diyana tatashi tahau gyaran gidan, dakinta tafara gyara wa da toilet Sanna tashige dakinsa, duk gadon nasa a hargitse, haka tahau gyaran dakin tasaka masa Air freshner, duk kayansa daya ajiye a'inda bai daceba ta gyara masa su, takardun dalibai yan jami'ah data gani Kamar ma text ne suma ta tattara masa su waje daya, sannan tafuto ta gyara falon, bata zauna ba tashige kitchen tahada masa abinci
Sabon maigadi suka gani azaune abakin get din, nan hajiya tafada masa kosu waye, aikuwa cikin ladabi yabarsu suka shiga, acikin ma saida hajiya tasake yimata fada sannan tayi mata sallama tatafi, hajiya na tafiya Diyana tatashi tahau gyaran gidan, dakinta tafara gyara wa da toilet Sanna tashige dakinsa, duk gadon nasa a hargitse, haka tahau gyaran dakin tasaka masa Air freshner, duk kayansa daya ajiye a'inda bai daceba ta gyara masa su, takardun dalibai yan jami'ah data gani Kamar ma text ne suma ta tattara masa su waje daya, sannan tafuto ta gyara falon, bata zauna ba tashige kitchen tahada masa abinci, wainar shinkafa da miyar egusi da kuma lemon danyar citta, tasaka shi a fridge yana daukan sanyi

(yau Diyana anzama matar novel 🙊😀)

Wanka taje ta sheqo, ta shirya cikin wata 'yar bingilar riga, rigar batazo gwiwar taba, amma saura kadan ta qaraso gwiwar ta ,babu hannu ajikin rigar hakanne yasa lafiyaiyar fatar jikinta ta baiyana, Sanna tazo takunna tv tana sauraren karatun qur'ani

Tadauki wayarta tariqe ta, dora kafa daya kan daya tana jira yashigo taji dame yazo inyaso ayita taqare





















Taurari:

D-Diyana
A-Abba
N-Nihla
G-guy (Fawaz)
I-Ilham
D-Dida
A-Aslam
Y-Yusif
A-Adam










(idan naga Comments dayawa zan'iya yin Wanda yafi wannan yawa gobe, idan ban ganiba kuma gaskiya.... 🤒)








Amnah El Yaqoub ✍️
[7/1, 12:54 AM] El Yaqoub: ❣️DANGI DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}


Writing by Amnah El Yaqoub


Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493






29&30


Tun daga bakin get maigadi ya sanar masa cewa su hajiya sunzo, yana jin haka yasan cewa may be tare suke da Diyana, Parking yayi yafuto daga cikin motar, yana nufi cikin gidan yana magana cikin zuciyarsa, shida yace taje gida saiya nemeta meyasa zata dawo masa gida, kuma yasan sarai aikin mama ne

Yana dosar kofar falon yaji qamshin girki yana tashi, yace ikon Allah, sannan yatura yashiga,falon yabi da kallo yanda ya sauya kama Kamar bashi ba, ga wani qamshi dayake tashi, hakanne yasa ya lumshe idonsa.
Tana ganin shigowarsa falon ta miqe sai rangwada takeyi, taje kusa dashi da niyya ta matsa jikinsa sosai tace "Sannu da zuwa"

Dasauri yabude idonsa, sai ganinta yayi agabansa, kafin yabata amsa tasa hannu ta karbi Briefcase dinsa, shima da niyya tahana da hannunsa wajan karbar Briefcase din, tace "kawo jakar"

Babu musu yasakar mata,yana sakin ajiyar zuciya, sarai tajishi, tajuya tayi gaba da niyya take wata irin tafiya me daukan hankali, tayi cikin dakinsa da jakar

Shikuwa Adam sai satar Kallanta yakeyi, Yaqi yadago kansa ya kalleta sosai, saide ta qasan ido yake qare mata kallo, yanzu dama maryam ta'iya wannan gyaran gidan shine bata taba yiba?

Acikin kujerun falon Yazauna, yasake lumshe idonsa yana sauraron karatun qur'anin dayake tashi, ga wannan qamshin girkin yacika masa hanci, tabbas zaiso yaji dandanonsa

Yana nan zaune tafuto daga dakin, takalleshi taga yanda ya lumshe ido, tatuno yanda ya shareta a hospital, qasa qasa tace ai saina rama ne, qarasawa tayi tazauna ahannun kujerar dayake zaune, taja hannunsa guda daya tace "ya Adam Muje kayi wanka kaci abinci"

Cikin basarwa yace "no kibarshi kawai, nagode"

Wata irin harara ta zuba masa irin ta baka isa dinnan ba, ta qara jan hannunsa har wajan breast dinta, yanajin yanda hannunsa yake gogar breast dinta cikin ransa yace Innalillah...meyake damun maryam ne, Kallanta yayi, yaga sai sake tura hannunsa take awajan yace "shikkenan sakeni zanje nayi"

Murmushi tayi tasakar masa hannun, sannan yashige dakinsa, bata bishi dakin ba tayi kitchen tana kokarin hada masa Abincin, yau kam tasa aranta saitasa ya Adam yadau charge, barema hajiya tagama yimata huduba ai batada damuwa 🤣

Bayan yayi wankan tsaf ya shirya yafuto falon anan yaga irin girkin data hada masa, kokadan besaki fuskar saba, sai wani basarwa yake, yanemi kujera Yazauna yana sauya tasha, ta kalleshi tace zakayi bayani ne, afili tace "ya Adam ga abinci, ka sauko kaci"

Batare dayace komai ba yasakko Yazauna aqasan shima, yafara kokarin zuba Abincin da kansa, cikin sauri ta riqe masa hannu tace "kabari mana, yau nice zanyi feeding dinka, Kamar yanda kamin lokacin da banda lafiya"

Yace "Am maryam dakin bar..." Dasauri katseshi, tace "shiiiii"

Nan take yayi shiru, ta matsa kusadashi tazuba masa Abincin sannan tasa spoon tafara bashi, daqyar Adam yake cin Abincin saboda gaba daya tashige jikinsa, yanajin yanda take goga masa kirjinta ajikinsa, duk yarasa yaya zaiyi da ita, shi yana ganin Ilham da Aslam suna soyaiya a asbiti ashe idan Diyana ce saide arufe ido?
Ko yaya yayi motsi saiya gogi kirjinta, gashi ita abin nata masha Allah ba kadan ba, Danya rabata da jikinsa yasa yayi dabara cikin shagaggiyar murya yace "ke bazakici bane?"


Diyana tanajin yanda yayi mata maganar tasan cewa lalle tarkon ta yakama, cikin qasa-qasa da murya tace "um um, nafison kaide kafara qoshi tukunna"

Jiyayi jijiyoyin kansa suna nema su fara aiki, haka yayi shiru yakasa cemata komai, gaba daya saiya zame mata Kamar wani dolo, haka tadinga bashi Abincin shide sai santi yake aransa, domin kuwa ba qaramin dadi yamasa ba

Saida tagama bashi, sannan taci Dan kadan, yazuba mata ido yana Kallanta yanata mamaki, gaskiya duk Wanda ba'a zauna lafiya a gidansa ba to mata basu bashi hadin kai bane, amma inde mata sun bashi hadin kai, to za'a zauna lafiya, kalli de maryam, da ya'isa yayi mata maganar girki ma, amma yanzu shine ake bashi abinci abaki, yaji dadi sosai aransa, kuma yadena fishin shi ya dade da janyewa🤣

Ajiyar zuciya yayi, yace "Maryam girkin yayi dadi sosai"

Ajiye spoon din hannunta tayi tace "da gaske ya Adam yamaka dadi?"

Jinjina kansa yayi alamun qwarai kuwa

Beyi aune ba yaji takai masa wata irin runguma, tace"thnk you ya Adam "

Ahankali Adam yace
" yasalammm!"

Besan cewa sarai Diyana tajishi ba, itama sai tayi fuska Kamar bataji ba, tasake shi tace, "nima naqoshi, bari nakai kayan kitchen"

Adam yana ganin shigar ta kitchen ya lallaba yashige dakinsa, Dan idan yaci gaba da zama anan, maryam zata haukatashi da salonta


Bayan tafuto daga kitchen taga baya nan tayi Murmushi tace "ko'ina yakai fishin dayake oho?" 🤔


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Cikin nutsuwa take shirya musu kayansu, yau likita ya sallamesu, shikuwa Aslam yana kwance yana aikin Kallanta, har yau mamakin Ilham yakeyi, kulawar datake bashi ne yasa yaji bayason subar asbitin, duk'da gidan nasu ma su kadai ne, amma saiyake ganin Kamar idan sun koma gida zata dena, tsaf tagama shirya kayan Tajuyo ta kamashi yana Kallanta, yatsina fuska yayi alamun ciwo yace "wash Allah na"

Cikin sauri ta qaraso wajansa tace "Sannu ya Aslam, ko wani waje ne yakema ciwo?"

Yace "kad'an kad'an nakeji"

Jikinsa tafara tabawa tana cewa "ka tabbatar deko?bakajin komai"

Qirjinsa ya nuna masa yace "sai nan dina, setin zuciyata yana dan min ciwo kadan"

Wajan tasa hannunta tana shafa wa tace "Sannu ya Aslam, ze daina yima ciwon kaji"

Lumshe idonsa yayi, yanaji Kamar karta dauke hannunta awajan
Ahankali yabude idonsa yace "bafa nan baneba"

Cikin mamaki ta kalleshi tace "to'inane? Kode ma kira Doc.?"

Cikin sauri yace "um um, kinga irin nan ne fa"
Yakai hannunsa kan qirjinta yana shafa wa, wani irin zirrrr taji a jikinta, numfashinta yana sauya wa, gaba daya taji wani irin yanayi yana ziyartar ta, kuma takasa hanashi abinda yake, ganin saqon nasa yasamu karbuwa yasa ya janyota jikinsa gaba daya, babu musu ta dora kanta a Kirjinsa, shikuwa yatura hannunsa cikin rigarta, yana abinda yakeso, kansa yadora akan wuyanta yana kissing wajan, lokaci d'aya Ilham ta lumshe idonta, gaba dayansu nema suke su fita haiyacinsu Ahankali tadago kanta tace "Ya Aslam muna asbiti nefa, katashi mutafi"

Ajiyar zuciya yasauke yana Kallanta, sannan yakira number Abba, ko minti talatin basuyi ba kuwa yazo yadauke su, Ilham tana baya tanajin su suna firar kamfaninsu da zasuyi bikin budeshi gobe, ya Abba Babu wasa bayason raini, ko saka Ilham bayayi acikin maganar tasu, saide Aslam yanayi yana juyowa yana Kallanta ahaka har sukaje gida sannan ya juya, sukuma sukai ciki


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Wasa-wasa saida Fawaz yayi zarya awajan Dida harya gaji amma Dida ko kallansa batayi, gaba daya ya lalace, idan ya koma gida Babu abinda yake sai aikin tunanin ta, a yanzu kam shi kansa yasan cewa yana qaunar Dida, saide anata bangaren yanada tabbacin cewa Dida bata sonsa.
Abangaren Abba kuwa aiki yataru yayi masa yawa, ganasa aikin da yakeyi, ga kuma aikin campanynsu dasuka bude Wanda yake sarrafa kayaiyakin Furnitures, kuma Abban ne yake jagorantar komai tunda Aslam yana gida yana shan Honeymoon, shiyasa koda yaushe baya zama


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

"kiyi hakuri mana, kukan ya'isa haka"

Cikin shagwaba tace "toba saida nace ma akwai zafi ba, amma kai kullum saika dinga qyaleni" ta qarasa maganar cikin kuka

Jikinsa ya janyo ta, ya bubbuga bayanta yace "Ilham, toyi shiru mana hajiya ta, kiyi hakuri insha Allah zaki daina jin zafi, Nikaina nayi mamaki ace kusan wata daya kenan amma har yanzu kinajin zafi, but kiyi hakuri zaki dainaji kinji?" ya qarasa maganar cikin sigar sigar lallashi

Daga masa kai tayi, kafin tayi magana wani irin amai yataho mata, cikin sauri tatashi da gudu tayi cikin toilet, Aslam yabita da kallan mamaki


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️
Idan lissafin sa yayi daidai to yau watan Dida daya kenan agida, yau kam saide ayi Wacce za'ayi, amma inde yaje Babu Inda zai dawo saida matar sa, tsaf ya shirya yatafi gidan yaje kofar part dinsu Dida Yazauna, hajiya Farida tafuto falo zatayi kallo saitaga Kamar mutum awaje, tadaga labulen falon nasu kawai sai ganin Fawaz tayi azaune, Dasauri tasaki labulen Tun kafin yaganta, juyowa tayi tadawo cikin falon jikinta asanyaye, wannan yaro yanashan zarya, amma taga alamun Dida ko'ajikinta, Tun bata tausayin yaron harda dawo tana tausaya masa, gaba daya ya lalace wannan Jan lips nasa duk sun bushe 🤣

Haka tayi shiru tana fatan Allah ya hade kan yaran nasu gaba daya
Tun la'asar yake wajan, har magrib baije ko'inaba, saide idan ankira sallah yaje masallacin dayake cikin gidan yayi sallah yadawo, itama Dida da magrib din tafuto falo akan idonta yadawo daga masallaci yaci gaba da zama awajan

Amma saita nuna batasan ma yana wajan ba, hajiya Farida tana hankalce da'ita, tayi shiru tana kallan ikon Allah
Har karfe goma na dare Fawaz Yana wajan, kawai jira yake babanta yadawo yaje ya sameshi suyi magana abashi matarsa, adede lokacin kuma hadari Mai yawa yahadu, sai cida akeyi da walqiya alamun ana gab da yin Ruwan sama.

Iska aka fara amma Fawaz Yana zaune, har wajan shadaya na dare sannan ne aka fara sheqa ruwa kamar da bakin qwarya, Fawaz Yana nan zaune ruwa yana dukansa sai karkarwar sanyi yake, kayan jikinsa ya jiqe jalaf
Amma tsabar taurin kai yana wajan azaune, daga qarshe ma tashi yayi tsaye ya zubawa part din nasu ido yana kallo
Dida na cikin dakinta tana karanta littafi harta sauya kaya zuwa doguwar riga ta bacci, sai dan qaramin mayafi data daure kanta dashi, cikin ranta tace su Fawaz anace, Tun la'asar anzo an zaune, ai yanzu nasan dole yatafi, danni kam bazan koma gidansa yaci gaba da dukana Kamar yasamu jaka ba, littafin ta ajiye tatashi ta zuge window din dakinta taleqa, gabanta ne yafadi ganin Fawaz Acan gefe a tsaye yana karkarwar sanyi, ruwa sai dukansa yake, cikin tsananin mamaki tace "Innalillahi... Ya Fawaz"

Dasauri tafuto daga dakin zuwa falo, hajiya Farida taji alamun gudu, tace to Dida ko lafiya?

Dida kuwa kofar falon tabude tafuto wajansa tace "mekake yi hakane eh? Sai mura takamaka ko?, kawuce katafi gida"

Fawaz yanajinta yayi shiru, kuma still yana tsaye awajan bai motsa ba, Kamar marar gaskiya haka ta kalli gabas ta kalli yamma taga Babu kowa awajan saisu kadai, Sannan tafuto cikin Ruwan itama ta nufeshi, jikinsa tashiga girgizawa tana cewa "ya Fawaz katafi gida, kar zazzabi ya kamaka"

Wani irin dadi ne yakama Fawaz, ko banza yau Dida ta kula dashi, cikin sauri ya fusgota jikinsa ya rungumeta tareda hade bakinsu waje daya, tureshi tafarayi amma saiyasa dayan hannunsa yariqe waist dinta, dayan kuma yariqe kanta yana kissing lips dinta sosai


Hajiya Farida tafuto falo taga Babu kowa, cikin mamaki tace to waye kuwa yashigo naji Kamar ana gudu
Labulen falon ta janye tabude window anan idonta yasauka akan Dida da Fawaz da ruwa yagama jiqesu suna kiss, cikin sauri tarufe window din tana salati, da mema yakai ta dube dube? 🤔

Saida yagaji Dan kansa sannan yasaki bakinta yace "I'm sorry Dida, please forgive me, nayi miki alqawarin nadena komai, Allah da gaske"

Shiru tayi, takasa cemasa komai, ganin haka yasa yaja hannunta yace "zomu tafi gidanmu"

Hannunta ta fizge tajuya zata koma ciki, ganin abinda take shirin yi yasa yadauketa cak yayi wajanda motarsa take yasakata aciki sannan yashiga yatada motar, megadi yabude masa, yafice daga gidan


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Books ne agabansu masu yawa, duk na addini ne, yanayi mata bayanin su dalla dalla, littafin hannunsa na iziyya har sun danyi nisa aciki, yana sake yimata bayani dangane da hukunce-hukuncen tsarki da kuma abinda ya wajabta ayi tsarki, dagashi sai jallabiya amma tsabar yanda yadage yanayi mata bayani yasa jallabiyar ta tattare daga qasa kana ganin gajeren wandon dake jikinsa 🤣

Ita kanta dalibar tasa, wani shegun riga da wando ne a jikinta, gaban rigar abude kana iya hango albarkatun qirjinta awaje
Kallanta yayi yace "maryam kina ganewa kuwa?"

Matsowa tayi jikinsa ta leqa cikin littafin tace "eh ina ganewa"

Idonsa ne yasauka akan qirjinta yazuba musu ido yakasa daukewa, tana ganin haka tayi Murmushi cikin ranta
Afili tace "ya Adam!"

Firgigit yayi, yadawo haiyacinsa, yana sakin ajiyar zuciya yace "yawwa kina ganewa ko?"

Murmushi tayi tadan kwanta ajikinsa cikin dabara, tasaka hannunta akan littafin dake hannunsa tace "Amma nan wajan bangane fassarar saba ya Adam, kasake min bayani kaji"

Kallanta yayi yaga yanda ta kwanta ajikinsa, gashi ta dora masa qirjinta agefen nasa qirjin, yanaso yayi magana amma yakasa, hakanne yasa yayi shiru tare da lumshe idonsa, baiqi ace sun tabbata ahaka ba shida Maryam, tanada tarin baiwa dayawa yarinyar, dukda yasan cewa wasu gayun sun rigashi

Kallansa Diyana tayi cikin rada tace "ya Adam kawai ni nagaji ma abar karatun sai gobe, yanzu dare yayi sosai"

Idanunsa a lumshe bai iya bata amsa ba, sai kansa daya daga mata kawai

Mamaki yagama kashe Diyana, tarasa gane kan ya Adam, har yanzu Yaqi futowa fili ya nuna mata yanda yakejinta aransa, to kode har yanzu duk wannan Jan hankalin nasa datake yana nufin yace bai fara sonta ba?, ko yaya idan tahada jikinsu baida aiki saide ya lumshe ido amma har yau yakasa baiyana mata yanda yake sonta, aikuwa inde hakane tadinga gasa masa aya a hannunsa kenan harsai ya furta mata kalmar so, bazai iyu tadinga yin abu da jikinta da kalaman ta amma yanata basarwa ba, zataga qarshen basarwar tasa.

 idonta abude suke tana tunani tana kuma kallansa yanda ya lumshe ido, tana dariya qasa-qasa


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Tunda suka shigo gida take ta masa kuka ita yamaidata gida

Kujerar datake kai yazo ya tsugunna a gabanta, yadora hannunsa akan cinyarta yace "Baby Dida, rigima kikeji ko? Kinga fa ruwa ake, kibari gobe saina maida ke gidan kinji?"

Cikin kuka tace "ai nasan ba maidani zakayi ba"

Yace "a a, zan maida ke, bakisan banason abinda zaisa ranki yabaci ba?"

Dago kanta tayi tace "kuma shine kakeyi ba" sannan ta maida kanta qasa tana kuka

Murmushi yayi yace "to naji, kuma nadauki laifi na, inde shan kayan maye ne yakesa ranki yabaci ni wallahi nadena"

Tace "ai rannan ma haka kace"

Girgiza kansa yayi yace "Dida! Wallahi da gaske nake, idan kika sake kamani inasha nayarda ki dauki kowanne irin hukunci ne akaina amma banda yin nesa Dani, kinji?"

Daga masa kai tayi batare datayi magana ba

Yace "yawwa, to kokefa, tashi Muje kiyi wanka, kicire wannan kayan, kinga duk sun jiqe"


Tashi tayi batare da tace masa komai ba tashige dakinta, shikuma yabi bayanta da kallo yana ganin yanda surar jikinta tafuto acikin kayan sakamakon jiqewa dasukai, haqiqa ya yarda cewa a yanxu kam yanason Dida, tunda haryakejin yanayin jikinsa yana sauya wa akanta



Washe gari dasafe dakansa yadauki Dida suka tafi asbiti wajan wani doctor yayi masa bayanin matsalar sa

Likitan yabashi shawarwari akan yanda zaiyi Yaqi da shan miyagun qwayoyi, Sannan kuma ya dorashi akan wasu magungunan, Wanda zai dinga sha koda shaye-shayen dayayi abaya sunyi masa wata illar batare daya saniba


Haka suka dawo gida cikeda farin ciki, babu wanda yakai Dida murna, yau ya Fawaz yadena shaye-shaye, haka al'amarin yaci gaba da kasancewa, Inda kwanaki suka qara ja, lokaci yana qara wucewa


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Takardu ne a gabanta na handout, banda books manya manya dake jere a gabanta

Karatu take sosai, hankalinta kwance, dinkin doguwar riga ne a jikinta na atamfa, kanta Babu dankwali, hakan yasa dogon gashinta kwanciya agaban qirjinta kasancewar gaba tawatso shi

Turo dakin nata akayi a kashigo, amma bata daga kai ta kalli kofar ba, saboda tasan cewa Babu me shigo mata daki inba mamy ba

Saide kuka qamshin turaren dataji ne yasa tadago kanta Dasauri, Idanunsu ne suka hadu, lokaci daya murna ta baiyana a fuskarta

Tace "ya Yusif!, Dan Allah kaine? Yaushe kadawo?"

Murmushi yayi Yazauna agefen gadon, daga wajan qafafunta, yace "zanyi miki Surprice ne shiyasa nace kada afada miki yau zanzo qasar, but Dafarko dai ki sanar Dani me kikeci kika koma haka?, Nihla idan na ganki ahanya fa daqyar Zan iya gane ki, anya kece kuwa?"


Murmushi tayi tace "Allah ya Yusif kaganka ko? Nide bari na kawo ma ruwa"

Tana fadar haka tatashi daga kan gadon ta nufi fridge din dakin domin kawo masa ruwa, Yusif yabi bayanta da kallo yaga yanda hips dinta yake rawa acikin kayan, gaba daya Nihla ta sauya masa, acikin wannan 'yan shekarun takoma haka, kokuma danya dade baiganta bane? 🤔
Komai yaqaru ajikin yarinyar Kamar ba itaba, lalle dole yadinga kaffa-kaffa da'ita Tun kafin wani gayen yayi masa qafa 🤣

Yana wannan tunanin takawo masa ruwa da lemo ta ajiye masa, shide sai binta yake da kallo harta farajin kunyar kanta, zama tayi tace "ya Yusif ya hanya, Yaya kabaro china?"

"china tanacan Nihla, na kawo miki tsaraba Mai yawa harda kaya, but nasan may be suyi miki kadan, dannaga yanzu masha Allah, kinzama Babbar yarinya"

Murmushi tayi tace "a a fa ya Yusif, bawata Babbar yarinya nide"

Yace "kina zaune adaki ke kadai, ko tunani nama bakyayi ko"

Tace "ya Yusif kenan, tayaya Zan kasa tunaninka, kawai de karatu ne yamin yawa shiyasa, kaga munata shirye-shiryen rubuta exam din qarshe, yakamata na maida hankali akan karatu kozan samu sakamako Mai kyau, shiyasa duk nashiga damuwa ina zama adaki ina karatu"


Kallanta qaramin bakinta yake yanda take juyashi tana magana, baiso tadena yin maganar ba, gaba daya Nihla tabashi mamaki, nema take ta susutashi, wani irin kallan luv yayi mata tace "no kada kisake kirawa kanki damuwa inde kina tare dani, bakisan cewa ita kanta damuwar bata isa tazo wajan kyakykyawar mace Kamar kiba? Tana zuwa zanyi ball da'ita namaye miki gurbinta da tsananin farin-ciki"

Itama kallansa tayi tanajin dadin yanda yake sakata nishadi idan tana tare dashi, ko awaya yakirata bataso yace mata saida safe, bare kuma yanzu datake ganinsa azahiri





Masu buqatar DANGI DAYA daga farko su nemi wannan number 09039066577,kokuma kai tsaye suje suyi like na page dina zasu sameshi acan





Amnah El Yaqoub ✍️[7/2, 12:57 AM] El Yaqoub: ❣️DANGI DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub


Like my page On facebook 👇 https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493



🤒Mutane dayawa suna cewa a posting din danayi na shekaran jiya basu gane gyadar miya ba
 ba gyadar da'ake miyar taushe dasu amaro nake nufi ba, ita wannan gyadar miyar idan ki kaje wajan masu saida kayan qamshi na girki, ana hadawa da'ita, wasu suna sakata acikin miyar ja, tanada qamshi sosai, sannan jikinta baqi ne saikun fasa zakuga cikin ta da Jan duhu haka, amma wasu suna kiranta da Diyar miya, Wanda basu gane taba kuma suje wajan masu saida kayan qamshi irinsu citta da kanumfari suce abasu gyadar miya kokuma Diyar miya, insha Allah zasu samu , Allah yasa kun gane 🙏🏻




31&32




Tace "ya Yusif ga lemo nan baka shaba"

"baki zubamin ba ai"

Murmushi tayi tayi, tadauka ta tsiyaya masa lemon sannan tabashi, ya karba yasha Dan kadan ya ajiye "to bari nabarki, kici Gaba da karatun ki nima zanje nahuta, anjima sai musha fira ko"

Cikin kunya tace "to ya Yusif Allah yahuci gajia" bayan yafita kasa cigaba da karatun tayi, gaskiya ya Yusif yayi arayuwa, yana kokarin ganin yasakata nishadi akoda yaushe
Ahankali tatashi tafuto falon zuwa kitchen, mamy ma tashigo kitchen din tace "ai tunda naga yashiga dakinki nasan cewa saiya hanaki karatun sannan zai futo, gashi yanzu yataso ki"

Dariya tayi tace " a a mamy, nice nataso da kaina, inaso nahada masa abinci"

Mamy tayi Murmushi tanajin dadi aranta, tace "um to Allah ya temaka ni bari na fice" daga nan tafita daga kitchen din tsabar Nihla tana kokarin hadawa Yusif abinci


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Ahankali komai ke gudana, rayuwa natafiya yanda ya kamata awani wajan.
Tun Aslam da Ilham basu gane Dan qaramin cikin dake jikinta har suka dawo suka gane, sukaci gaba da bawa cikin ta kulawa, Wanda yatasa sosai yanzu

Zaune suke afalo shida ita ta dubeshi tace "ya Aslam yau ba zakaje wajan aiki bane?"

"Ok koratama kike ko?"

Tace "a a, inaso mu kasance tare ne, bansan kanayin nesa dani, shiyasa na tambayeka"

"yau banda aiki me yawa ne, zanyi agida kawai, wai in tambayeki mana Ilham"

Tace "inajin ka"

"idan kika haihu wanne suna kikeso a sakawa babyn?"

Ajiyar zuciya tayi tace "gaskiya idan mace ce Anty Aysha zamusa, idan kuma namiji ne... Muga, sunan wa yakamata musa masa.. Ina ganin sunan Babanku ko?"

Cikin farin ciki yace "Nikaina abinda nasa a raina kenan, inde na haifi mace, sunan tsohuwar budurwata zansa 🤣
But idan namiji ne, kidena ma tunanin Wanda zamu saka, Dan already abokina Zan yiwa takwara"

Kallansa tayi tace "wai ya Abba?"

Yace "yes, Abba zansa, because shine yabani shawarar yanda Zan shawo hankalin matata, kuma shawara tayi amfani ta kaini zuwa wata jihar, wadda bantaba tunanin akwai wata jiha Mai dadi kamarta ba"

Hannu tasa ta rufe fuskarta, wallahi maza kunyar su kadance, yanzu shi ya Abba dama shine yazuga ya Aslam ayi mata wannan abun kenan, kana ganinsa shiru-shiru Kamar bazai aikata ba🤣

Kallanta Aslam yayi yace "har yanzu de kunyar ce?haba qanwar budurwa ta, yakamata adena wannan kunyar haka"

Jikinsa ta fada tana murmushi, shikuma yadora hannunsa akan cikin ta yana shafa wa, tabbas yanzu ne yasan yayi aure.



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Yauma suna zaune shida ita afalo, gaba dayansu suna kan doguwar kujera, yau kuma littafin akdari ne a hannunsa yanayi mata bayanin sallah, da yanda zata gyara idan tayi rafkanuwa 🤣

Abin tun yana damun Diyana harya dena damunta, ace kullum karatu, karatu Yaqi ci Yaqi cinyewa Kamar cin qwan makauniya 🤣
Ganin idan tayi masa shiga ta daukan hankali ma saide yagani ya lumshe ido baya iya yimata komai yasa taci gaba yin shigar ta son ranta, tunda saide agani alumshe ido, batada damuwar komai, ita irin tsoron nanma da'ake tunanin ji a first night Diyana bata nuna komai, kanta tsaye take shigewa jikin mijinta ko'ajinta, kodan tasaba hulda da maza ne oho 🤔, kokuma Dan tasaba shiga cikin su suyi fira da Komai ne yasa hakan oho 🤔

Amma batasan cewa tana bala'in kunna ustazun nataba, kawai daure wa yake

Karatun yake mata amma tana kwance ajikinsa ta dora kanta agefen kafadarsa, tana ganin littafin, shikuma Adam yanayi mata bayani, shi yanaso maryam duk tasan wad'annan littattafan saboda yasan bata sansu ba abaya, shiyasa yadage yana koya mata, yanzu idan sun gama da littattafan ma, baqi zai fara koya mata na arabic, yanda zataji iya bude qur'ani da kanta ta karanta,🤣
Aishi yaji dadi sosai yanda maryam zata zauna tanaji ana karanta mata littafin addini tana koya, yaji dadin hakan sosai, kuma ansamu cigaba acikin Rayuwar ta

Littafin yana hannunsa na dama, ita kuma tana daga gefen hannunsa na hagu, ahankali takai hannunta ta sanya acikin masa hannun na hagu Wanda Babu littafin, idonta yana kan littafin amma tana wasa da tafin hannunsa acikin nata, wani irin abu yaji yana masa yawo ajinin jikinsa 😱
Hannun maryam yanada laushi sosai, yaso ya qwace hannun amma yakasa, haka yaci gaba yana karatun murya ashaqe, agefe guda kuma yana jin dadin yanda take wasa da hannun nasa, shiru yayi yadena karatun kawai yana saurarenta, Diyana taji yayi shiru tadago kanta ta kalleshi, sai ganinsa tayi idonsa a lumshe 🤣

Dariya yabata sosai, cikin ranta tace ya Adam kenan, sarkin lumshe idanuwa, taci gaba da abinda take

Ahankali yabude idonsa, duk sun qanqance, yadora su akan qirjinta, meyasa yake dagawa maryam qafa ne? Har yaushe zai tausaya mata bayan yasan cewa itama tasan komai,? Ai yayi hakuri, Tun ana jin tausayi kar adawo daukan haqqi kuma, ahankali Kamar me tsoron wani abu yadaga hannunsa ya dorashi akan qirjinta, Diyana da batasan abinda yakeba kanta na qasa kawai sai jin hannun ya Adam tayi akan qirjinta, wannan ne karon farko tunda take dashi dataji faduwar gaba, gabanta yafadi, cak ta tsaya da wasan datake da hannunsa

Kallanta yayi, yayi wurgi da littafin dake hannunsa akan daya kujerar, Diyana tabi littafin da kallo 🤣

Ahankali yafara shafa qirjinta yana jin wani irin dadi aransa, yau kam bazai iya hakuri ba, gara yafuto fili yafadawa matar sa yanda yake tsananin kaunarta, cikin sigar rada yanda ita kadai ce zata iya jin abinda yace, yace mata "Diyanaaaa!, please inaso nasha"

Mamaki yagama kashe Diyana azaune, anya ya Adam ne kuwa wannan? Kafin tayi wani yunquri yasaka hannunsa cikin rigarta yaciro guda daya tareda dora bakinsa akai, nan take ya lumshe idonsa yanasha Kamar jariri, Diyana tafara kokarin tashi saboda yanda takejin tsikar jikinta tana tashi, ga wani irin dadi da takeji, shikuwa Adam ganin zata tashi yasa yasake maida ta kan kujerar yaci gaba da abinda yake, yayinda yamaida hannunsa bayanta yazuge zip din rigarta gaba daya, nan take komai ya baiyana, Adam yana ganin haka ya haukace mata, wasa yaci gaba dayi dasu, cikin faduwar gaba Diyana tace nashiga ukuna, ya Adam Dan Allah kabari, nide wani iri nakeji, please kabari dan Allah "ta qarasa maganar muryarta na rawa 😢

Dago da kansa yayi ya kalleta cikin ido yace"i luv u Maryam...., i really luv you so much Diyanaaaaa.... Pls kibarni nayi yau Dan Allah..., kemafa kinsan Babu abinda zakiji"


Diyana kallansa take cikeda mamaki, amma kwata-kwata bata gane Inda maganar sa ta dosa ba dayace Babu abinda zataji, Wato yanaso yace mata ba zataji zafi bane danya samu abinda yakeso kome? 🤔

Miqewa tayi tsaye da qarfin ta, cikin sauri shima yatashi yafuzgota jikinsa tareda hade bakinsu waje daya, Kamar mahaukaci haka yake kissing dinta, tsoro yakama Diyana, dama ya Adam ya'iya wannan abubuwan amma yake fuska, Innalillah.... Wannan abun ai yayi yawa yawuce tunanin ta, batasan cewa zai'iya nata hakanba

Bakinsa yazare daga nata yadauketa cak sai cikin dakinta, yana zuwa dakin yadora ta akan gadon, ganin safiya ce yasa yasaki labulen dakin tareda kashe wutar dakin, yafara kokarin cire kayansa, Dasauri Diyana ta runtse idonta

Mamaki yakama Adam, wai meyasa maryam take masa haka ne? Saikace batasan komai ba shine zatake wani jin kunyar sa, ahankali yahau kan gadon, yashige jikinta, cikin sigar lallashi yace "Maryam kin amince nayi?"

Tace "ya Adam gaskiya a a, ni wallahi tsoro ma kake bani, Dan Allah kabari yaya Adam"

Kallanta yayi yaga jikinta sai rawa yake, me maryam take nufi? 🤔
Kansa yadora a kasan wuyanta yana kissing harya gangaro yadawo kirjinta, sannan yace "kiyi hakuri maryam, amma bazan iyaba"

Daga nan yaja blanket Yarufe su dashi yaci gaba da nuna mata tsantsar sosai, Tun Diyana tanajin Dan dadi dadi harta dawo tanajin azaba, kuka tafara tana cewa yabari, amma Adam yayi nisa, sai jinsa ma tayi yana karanto addu'ar saduwa da iyali

Batareda da Adam yasan ko Wacece matar tasaba, yashige ta zuciyarsa daya, kansa tsaye yatafi beje mata da wasaba kokadan, Diyana ta callara uban qara tana dukansa, amma Adam yayi shiru, Dan da alama ma Sam bayajin ta

Amatse yajita sosai, ga wani irin dadi dayakeji Kamar ya mutu, yanda yakeji Awannan lokacin kokadan bazai iya hakura ya qyaleta wai da sunan tausayi ba, ahankali hawaye suka tsiyayo masa daga idonsa, cikin wata irin murya yace "Diyanaaaa!" yaja sunan nata

Diyana kwa kuka take, idonta sunyi jajir, azaba take karba awajan sa kawai, Adam yace "Diyana kiyi hakuri...."


Yaci gaba da cewa "kiyi hakuri maryam... Amma bazan iya denawa ba, Maryam bazan iya rayuwa batare dakeba, Allah bazan rabu dakeba"


Diyana tana jinsa tayi banza da qyaleshi, kusan awarsa daya, sannan yadawo hayyacinta, a lokacin Diyana bata iya bude idonta, azaba takeji Kamar hauka, Inda tasan haka akeji wallahi da bazata sha duk magungunan da Mom dinta take dura mata ba lokacin bikin su, gashi tsabar mugun ta itama hajiya Na'ila tazo ta dirka mata wani rannan, batada bakin magana saide kaga hawaye yana silalowa daga idonta 🤣

Ahankali yake bude idonsa daya jiqe da hawaye shima, bargon daya rufa musu ya yaye Yakalleta, Dasauri yadauke idonsa saboda ganin irin barnar dayayi, kunyace ta kamashi yakasa hada ido da'ita

Yanzu dama maryam Virgin ce baisani ba shine yatafi Babu gargada? Innalillah...dole maryam tayi kuka, abinda yamata ko wacce ta dade da sanin abun zataji a jikinta, gaskiya ya dauki alhakin maryam dayake mata kallan yar'iska Tun tuni, bama shi kadai ba, duk family dinsu, but meyasa take yawo da maza ko'ina? "

Ganin Babu me bashi amsa yasa ya yunqura yatashi zaune, Kallanta yayi idonta arufe amma hawaye takeyi, Allah ya soshi baitaba fadawa maryam baqar magana akan yawon datake da maza ba, yauda yashiga ukunsa🤣

Cikin kuskurin kunya yace" Am, Diyana tah, kiyi hakuri dan Allah, ni wallahi bansaniba "

Cikin masifa tabude idonta tace" dama ai haka zakace, menene baka saniba ya Adam? Kasheni kaso kayi ko? To Allah bai baka damaba "

Shiru Adam yayi yakasa magana, ya'isa yace baisan ita Virgin cefa yatarowa kansa December? 🤔
Dan haka yayi shiru, yasa hannu yadauketa cak, yashige toilet din dakin nata da'ita, nan take yafara kokarin gasa mata jikinta sai masifa take masa amma kuma ta qanqameshi saboda yanda takejin zafin Ruwan



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Hajiya Na'ila tana zaune tana tunani aranta, ko yarannan suna zaune lafiya, tajisu shiru, Allah yasa de lafiya kawai, amma yakamata taje tagani da idonta, Dan tasan halin Adam da shegiyar kafiya

tashi tayi ta shirya tafuto tasa driver yakai ta gidan Adam, nan da nan kuwa driver yacika umarninta, ya ajiyeta tace yajirata yanzu zata futo, gidan tashiga sai kwala sallama take, amma taji shiru, falon Babu kowa sai littafi ayashe akan kujera 🤣
Tace to ina Diyanan tafita kuma? Yarinyar nan batajin magana tana gani de yanda sukai aka samu tadawo gidanta, ayi yara ace sune da zaman aure amma kaine daso su zauna lafiya? 😀
Tace ai shikkenan, sannan ta danna kanta cikin dakin Diyanan, a lokacin su kuma suka futo daga toilet shida ita, Allah yaso su sun dauro towel ajikinsa, hajiya Na'ila ta kallesu cikeda mamaki, tace "a a, ashe ku kuna ciki sai rafka sallama nake naji shiru"

Diyana tayi shiru ta qyaleta, 🤣
Hawaye suka silalo daga idonta, Adam kuwa kansa ya sosa, cikin kunya yace "Sannu da zuwa mama" daga nan yafuto daga dakin dagashi sai towel iya qugu

Hajiya takai kanta Kallanta kan Diyana tace "a a subhanallah, me aka miki kike kuka? Shiyasa fa hankali na Yaqi kwanciya nace sainazo naga halin dakuke ciki,"

Nanma Diyana shiru tayi ta qyale hajiya, cikin ranta ma haushinta takeji, ai duk itace taja mata, tabata magani tasha gashinan danta zai kasheta

Tafiya tafara da qyar, tana dingisa kafa, gashi sai bubbude kafa take tana runtse idonta, ko kayan sakawa bata nemaba takoma kan gadon nasu da Babu ko bedsheet saboda Adam ya cireshi, ta kwanta tana hawaye

Hajiya Na'ila tayi mutuwar tsaye, Innalillah kawai take maimaita wa acikin ranta, abinda idonta yagani kadai ya'isa ya tabbatar mata da cewa maryam takawo budurcinta dakin mijinta, gaskiya sun dauki alhakin Diyana, tatuna lokacin da'aka ce Adam zai aure ta sai fada take anhada danta da Diyana yarinyar datake yawo club club

Cikin tasauyawa ta kalleta tace "kiyi hakuri mana Diyana, kowa da kike gani da haka yafara, bari nayi masa magana yazo yakaiki Asbiti"

Fita tayi daga dakin tana magana cikin zuciyarta, wai meyake damun wannan yaran ne? Duk sai yanzu suke mu'amular aure, ita kuma Allah yake nuna mata wannan abun kunya 🙈, Allah sarki ashe shiyasa Adam Yaqi bin bayan matar sa, har take fada tana cewa Diyana batasan gyara ashe ita yarinyar batasan komai bama na aure bare aje ga maganar gyara, aikuwa ta dena zuwa gidansu kar gaba kuma taga abinda yafi haka 🤣, har gara Adam ma yaji kunyar ta yagudu dakinsa, amma shi Aslam kiranta yayi awaya ma taje gidan nasa


Bakin dakin nasa ta tsaya tayi nocking, sannan tadaga murya tace "ka futo ka dauki yar'mutane kuje asbiti"

Daga nan tafuto daga falon gaba daya ko dakin Diyana bata sake shiga ba, Mota tashige driver yaja suka tafi



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Tunda tagama school ta karbi result dinta second Class upper, taje tayi registration din Service, tana jira ayi posting dinsu ne kawai, da wannan damar tayi amfani tashiga Catering school tana koyar Birthday Cak, kullum zata shirya tayiwa mamy sallama tatafi, bazata dawoba sai yamma, wani lokacin kuma ya Yusif ne yake kaita da kansa, zuwa wannan lokacin kam ita kanta tasan cewa tagama mallaka masa zuciyarta, saboda yanda take samun kulawa sosai awajan sa, kuma har zuwa wannan lokacin Bata sake kiran Momy ba, dama wancen dinma dokar mahaifinta takarya takirata

Wayarta tace tayi qara tana dubawa taga Abokinta ne yake kira Wato Abdallah qanin Anty Nadiya, tanayin picking ya sanar da'ita cewa Posting dinsu fa yafuto, taje taduba nata, shi anduba masa nasa yaga sun turashi yola

Tace "toooo yola!, tabdi nikam ko'ina suka kaini? Sai Allah"

Yace "kije kiduba naki kema, sai munyi waya"

Bata jira komai ba, ta shirya tsaf, taje kafe aka duba mata, Wanda yaduba nata yaciro posting latter din yabata, tana dubawa taga anyi posting dinta kano, cikeda mamaki tace "kano kuma?"
Kudinsa tabashi tadawo gida, a compound taga su Baba da ya Yusif da Alhaji Isma'iel Abban ya Yusif, tana gaishe su ta miqa musu takardar, kowa yagani, duk sunyi mata murna da aka turata jihar musulmai, Alhaji Isma'iel ya kalli Yusif yace "to Yusif ai sai kuje tasiyo abubuwan dazata buqata gobe tabi jirgi tatafi ko?"

Yace "to Abba insha Allah"

Sannan ya kalleta yanayi mata wani kallan luv yace "kishirya anjima sai Muje shopping din"


Da yamma kuwa sukaje shopping, tasiyo komai na buqata, tagama shirya kayan ta tsaf, tunda aka ambaci service akano taji tanayin murna badan komaiba, tasan zataga Ilham da Momy

Da daddare baba yazo har dakinta, tayi mamakin ganinsa a dakin Dan ba shigowa yake ba, Kallanta yayi yace "Nihlan Diddi, gobe kuma sai kano ko?"

Murmushi tayi tace "hakane Baba"

Yace "to banda shirme de, ki tsaya kiyi abinda yakaiki, idan kun gama zaman camp din idan kinga zaki iya cigaba dayin service din Acan saiki zauna, idan kuma bakyaso saiki nemi relacation kidawo nan"

Tace "to Baba, amma Baba ai gara na dawo nan din yafi, saboda nanne gida"

Yace "a a, can dinma ai gida ne, ga yayun mahaifiyar ki duk suna can, sai kije can kiyi zaman ki"

Tace "to Baba kakira su awaya kafada musu zanzo"

Yace "saboda ga gwamna ko shugaban qasa ko? Sai an sanar dasu zuwan ki, 🤣kema ai iyayen ki ne, kikirasu da kanki kifada musu, ni bazan saka baki akan zaman ki agidanba, kawai de bazan dauki abinda za'aci zarafin 'yataba"

Murmushi tayi tace "to Baba insha Allah, zankirasu"

Kallanta yayi yaga tanata murna, yasan kuma bazai wuce ace murnar ganin Momy bace, Dan zuwa yanzu kam yasan ai ta cire Abba aranta, daga nan yatashi yayi mata sallama yatafi


Washe gari saida tayi sallar azahar sannan ta shirya cikin doguwar riga Mai adon stones ajiki, sannan tayi rollinga tasaka wani shegen glass a'idonta, sai zuba qamshi take, idan ka kalleta saika sake waigawa, tayi masifar yin kyau, farar fatarta yaqara futowa sosai sai shining jikinta yake

Ya Yusif ne yakai ta Airport sai firar soyaiya suke abinsu gwanin sha'awa, har lokacin tashinsu yayi, sukai sallama yace zai kawo mata ziyara idan yasamu dama, da haka tashige cikin jirgin akaro na farko atarihin Rayuwar ta, wayarta tadauko zata kira Momy, kawai saita fasa, gara tayi mata surprice kawai

Ko awa daya basuyi ba, jirginsu yayi landing, tana futowa daga Airport din mutane suke ta Kallanta, daga ita sai yar qaramar truly dinta tanaja, tayi mutuqar birge kowa, Mai taxi ta tare tashiga tafada masa Inda zai kaita, acikin motar ma kafa daya ta dora kan daya, tana daddana waya, har sukazo bakin get din family house din Mazawaje

Sallamarsa tayi, ta tsaya ta qarewa Babban get din gidan kallo, duk an sassauya abubuwa dayawa, yau gata a Mazawaje family akaro na biyu

Tura get din tayi tashiga, iliya Maigadi yana zaune yanajin radio, taga ya kalleta yayi shiru Kamar besanta ba, cikin mamaki tace "iliya d'anmai qarfi baka ganeni bane?"

Kallanta yasake yi, yaji sunansa radau abakinta yace "Wacece? Bangane kiba wallahi, baquwa mukayi ne?"

Murmushi tayi ta cire glass din idonta tace "iliya nice Nihla fa"

Cikin sauri yatashi tsaye yace "kai kai kai, wai Nihla kece? Aini jinake wata balarabiyar ce wallahi, a a a a, masha Allah, sannu da zuwa, sannu sannu, kice yau munada manyan baqi agidan namu, kawo jakar taki, kawo, kawo"

Nihla tayi Murmushi tace "iliya kenan,"

Sannan tabashi jakar, suka nufi part din Momy, saida yakai mata jakar har cikin falo sannan yajuyo yana qara yimata sannu da zuwa, Nihla ta zube akan sabun kujerun falon da aka sake tace "wash Allah nah, gajiya"

Sannan tadaga murya tace "Momy!!! To futo 'yarki tazo"🤣


Kamar almara Momy Tajuyo Kamar muryar Nihla, amma sai taqi gaskatawa, mezai kawo Nihla kano yanzu? Kawai de kunnanta ne

Nihla tasake cewa "Momy!, koba kowane agidan?"


Dasauri Momy tafuto falon, taga Nihla kwance akan kujera ga jakar tanan agefe, qaraso wa tayi cikeda tsananin mamaki, Nihla na ganinta tatashi ta gudu taje ta rungumeta cikeda murna

Momy tadagota daga jikinta tana Kallanta tace "  Nihla 'yata, yanzu Allah kece kika qara girma haka? Gaba daya kin sauya kamar ba Nihla ta tadaba"

Dariya tayi tace "Momy nice mana, wai meyasa kowa yake cewa na sauya ne? Momy girma naqara ne?"

"girman ma Nihla, kin qara kyau, Kamar balarabiya, mezakici adafa miki yanzu?"

Saida tayi farrrr da idonta sannan tace "Momy yanzu banajin yunwa, saide da daddare, but idan akwai cornflakes zansha kadan"

Momy ta lakace mata hanci, tace "Wato bakyason cin abinci Kamar da ko? Ni narasa ya'akayi ma kikai bul-bul dake masha Allah Babu wata rama Kamar da"

Dariya tayi, cikin ranta tace Anty Nadiya ce sirrin, afili kuwa sai tace "Momy bari nakai kayana daki"

Momy tace "a a Barshi, Adala zatazo takai miki, tashi Muje ki gaisa da sauran yan gidan"

Hannunta Nihla ta riqe Kamar wasu qawaye suka futo, kowanne part saida sukaje ta gaida kowa, kuma kowa sai nan-nan yake da'ita, kowa yayi murna da dawowar Nihla, saita zama wata abar sha'awa kowa Kallanta yake yanda ta sauya,Hajiya Farida maman su Diyana kuwa tana ganin Nihla taji tausayin Abba ya kamata 😢 🤣

Haka suka dawo part din Momy, Nihla ta dora kanta akan cinyar Momy tana bata labarin makaranta dakuma service din da aka turota

Suna wannan firar har la'asar tayi, Tatashi taje tayi wanka, tasaka riga da wando na jesy, (kayan ball) na mata, amma nata dogon wando ne Mai launin dark blue, Momy ce da kanta tahado mata cornflakes din, tace "to yata taso kisha, yauda kaina Zan baki"

Murmushi tayi tatashi, suka zauna a kafet din, Momy tafara bata, ita kuwa sai surutu take mata, Momy cikin ranta sai mamakin yanda Nihla ta sauya takeyi, kanta Babu dankwali hakan yasa dogon gashinta dayasha gyara kwanciya a bayanta

Adede lokacin yaturo falon nasu yashigo, yau kwanansa takwas baya qasar ma baki daya, saukarsa kenan

 da dogon gashinta yafara tozali, kasancewar tabashi baya baiga fuskar ko Wacece ba, mamakin hakan yasa yaqame a tsaye abakin kofa, Wacece wannan Kamar ba 'yar hausawa ba kuma Momy tana feeding dinta?

Momy ce ta lura dashi takalleshi cikin murmushi tace "a a Abba, shigo mana"

Jin an ambaci sunansa yasa bugun zuciyarta ya sauya, ahankali tajuya ta kalli bakin kofar itama, lokaci d'aya Idanunsu yahade dana juna, cikin abinda baifi second ashirin ba tagama qare masa kallo, yau ne karon farko daga taba ganinsa azahiri sanye cikin kakinsu na Pilot Mai launin fari da baqi  banda pic dinsa data gani awayar Anty Nadiya sanye da kayan , sosai kayan sukayi bala'in karbar jikinsa, yaqara girma, yaqara yin kyau Kamar ba shiba yasake zama babba tamkar wani cikakken magidanci, kawarda idonta tayi,ta karbi spoon din hannun Momy ta cigaba dashan cornflakes din ta, shikuwa kasa dauke idonsa yayi akanta, shin anya kuwa ita dince de agabansa? Inda ace baiyi mata kyakykyawan saniba Babu abinda zai hana yakasa ganeta, but ya'akai takoma haka? Dogon gashinta yasake kalla Kamar ba gashin bahaushiya ba, ahankali yaqaraso cikin falon cikin takun izza

Momy tace "Nihla ga yayanki yashigo fa, shima baya qasar yanzu yanzu yadawo, yaude ina cikin farin-ciki yarana duk sun dawo gabana"

Hankalin Nihla yana kan cup din gabanta, ko dago kanta batayi ba, bare yasaka ran zata kalleshi, kanta aqasa Kamar anyi mata dole tace "ina yini"

Ataqaice yace "lafiya"

Sannan yayi gaba, yajuyo yasake kallanta waiko zaiga ta kalleshi amma yaga gaba daya hankalinta ma baya kansa, shi wannan yarinyar zata gaisar asheqe Kamar ta samu sa'anta?

Momy kuwa tayi mamaki guda daya, mamakin daya kamata shine yanda Nihla taqi ambatar ko sunan Abba, da tasaba tanaji yarinyar tana ya Abba kaza, ya Abba kaza, duk da yana shareta bata fasa fadar sunansa ba, Kamar a bakinta aka rada mata sunan ya Abba, amma yau taga gaisuwar ma daqyar tayi 🤔


Dakinsa yashige yafada kan gado yana tunani, inaaa! Bazai iyuba, Sam bayason raini, Dan haka bazai dauki wannan ba, lumshe Idanunsa yayi, meyasa yake jin farin-ciki ne awani bangare na zuciyarsa?





(ko a film fad'an boss shine qarshe 🤪dafatan za'a min Comments 🙏🏻)










Amnah El Yaqoub ✍️
[7/3, 12:43 AM] El Yaqoub: ❣️DANGI DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub



Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493




33&34


Nihla ta kalli Momy "Momy kibani wayarki nakira su Ilham, banda number kowa acikinsu"

Momy tace "wayarki tada tana nan a dakin naki, ki kunna saiki dauka, ai Babu wadda ta sauya number acikinsu, nima Bari nakira Daddynku dasu Usman nafada musu zuwanki"

Tace "to Momy" sannan tashige dakinta


Da daddare kuwa su ya Usman sukazo dukansu, dama Momy tasa Adala ta shirya musu abinci Mai kyau

Alokacin Nihla tasake wanka tasaka riga da siket na atamfa Mai launin Jan duhu, dinkin yayi mutuqar yimata kyau, siket din kuwa hips dinta yacikashi dam, daurin dankwali nede tayishi simple amma gashinta awaje yake daga baya

Babu Wanda bai rude ba, lokacin dasuka ganta, gaba dayansu suna zaune acikin qayatattun kujerun dakin, Adala kuma tana dauko abinci daga kitchen zuwa kan dining, firarsu suke cikeda farin-ciki but Abba kam baya saka musu baki, baya cewa um bare um um, asali ma waya ce ahannun sa yana danne-danne, yayinda yadora kafa daya kan daya

Farouq yace "Momy, yarki fa tagama rikicewa, gaba daya ta sauya kamar ba ita ba, ni sai yanzu nema nakejin naqara matowa, inba itaba sai rijiya" 🤪

Ahankali yadago kansa ya kalli farouq, amma Bece masa komai ba

Murmushi Nihla tayi, har dimple dinta yana lotsawa, tace "ya farouq bakada dama, aina fadama dakai za'ayi, tunda kaji sharadin"

Wannan karon ma tana fara magana Abba yadauke idonsa daga kan farouq yadawo dashi kanta, har yanzu de wannan dimple din nata yana nan, yayi tunanin zata kalleshi amma kwata kwata saiyaga ko kujerar dayake kai bata kalla ba

Aliyu yace "ai farouq, bazan baka qanwata ba, mijinda Nihla zata aura ai sai Wanda duniya tasan dashi"

Usman yace "Kamar ni kenan" 🤣

Gaba dayansu sukasa daria, Momy tace "Dinner is ready kutashi Muje kowa yaci abinci"

Usman da farouq da Aliyu gaba dayansu ajere suka zauna, Momy ma tazauna akusa da Usman, kujeru biyun dasukai saura kuwa na Abba ne da Nihla, hankalin ta kwance taja kujerar tazauna sannan tafara cin Abincin ta, shima Abba daya qaraso wajan yaga saura kujera daya ta kusa da Nihla, haka yaja Yazauna, idonsa akan wayarta data ajiye a gabanta, yana zama wani irin sihirtaccen qamshi yabugeshi, baisan lokacin daya lumshe idonsa ba yabude, kowa shiru yayi yana cin abinci, wayar Nihla tafara qara, kowa yazuba mata ido yana Kallanta, Abba yakai dubansa kan screen din wayar yaga ansa
❤my Yusif❤ harda alamar hert ajikin sunan, Nihla tasa hannu tasaka wayar a silent, idonsa ne yasauka akan kyawawan yatsun hannunta, dogaye gwanin sha'awa, janye idonsa yayi, Nihla kuwa ko a jikinta taci gaba dacin Abincin ta, ana jimawa ya Yusif yasake kira, tasake sakata a silent, akaro na uku ma yasake kira, ahankali ta miqe tsaye tace "Excuse me, zan amsa waya"

Tana fadar haka ta nufi hanyar dakinta, Hips dinta Abba yabi da kallo, anya kuwa yarinyar nan itace bawani abu take sakawa a jikinta ba? gashi sai yawo take tana fitarda gashinta waje kowa yana kallo, amma Momy tana gani ko magana bata taba yiba


Har suka gama cin Abincin Nihla tanacan tana waya, da dade tana shan wayarta dashi sannan tafuto sukai sallama dasu ya Aliyu



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

"ku shikkenan idan akace anyi muku aure, ankai muku amarya daki saiku rasa control dinku gaba daya, tayaya za'ayi daren farko kace zaka shigi mace gaba daya, shiyasa mutanan da sukafi mazan yanzu iya zama da mata, da kanku kukesa matanku suna tsoron ku, yanzu saboda Allah wannan dame yayi kama? Kaja anyiwa yarinya dinki, tayaya kake tunanin zata sake yarda dakai akaro na biyu? "

Adam yayi shiru kansa aqasa, ko yayiwa doctor bayani bazata ganeba, gara yayi shiru tagama fadanta kawai, ahankali yadago kansa ya kalleta, matar kam babba ce zata iya haifansa, shiyasa Babu kunya baro baro take masa fada, yace" insha Allah Zan kiyaye gaba likita "

Fuska a cukune tace" to dade yafi muku, narubuta muku magunguna kasata agaba tadinga sha, sannan karka sake zuwa wajanta sai nanda yan kwanaki "

Kansa aqasa yace" to insha Allah "

Daga nan yafuto daga office din nata yaje wajan Diyana daya tarar tana bacci, baiyi kokarin tashinta ba, yabarta tagama baccinta sannan tatashi Dan kanta, yakamo hannunta da kafadarta suka futo daga asbitin, saida yasai magungunan da aka rubuta musu sannan suka wuce gida

Dakinta tashige ta kwanta tana tunani, dama haka daren farko yake? Ahakan wasu suke cewa sunason daren farko? Wannan aiba abin dadi bane abin wahala ne kawai, har akan wannan abun wasu matan suke fada? Har wasu sukai kansu ga aikata zina, tabdi, ita kam, itada ya Adam danba qara


Dakin yaturo yashigo yakalli fuskarta tayi fayau, zama yayi agefenta yace "maryam kiyi hakuri, insha Allah hakan bazata sake faruwa ba"

Shiru tayi masa batare datayi magana ba, ahankali ya miqe yafara cire kayan jikinsa, gaban Diyana yafadi, me kuma zai sake yi? 😳

Tsaf ya cire komai dagashi da boxer yahau kan gadon, cikin faduwa gaba tace "dan Allah kayi hakuri ya Adam,"hawaye ya silalo daga idonta

" ohhh Diyana, niba wani abu Zan miki ba, kawai inaso najiki ajikina ne "
Yana fadar haka yasa hannu yadaga mata hannayenta ya cire rigar jikinta, daga ita sai breziya ya janyo ta jikinsa ya rungumeta tsam, sannan cikin rarrashi yace "muyi bacci ko?"



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Tunda suka dawo normal shida ita yakasa yimata komai, yasan cewa Dida mace ce Mai matuqar kunya bazata taba kawo kanta gareshi ba, to shi kuma kunya yakeji da girman sa yaje gun yarinyar mutane da sunan neman haqqin sa, amma azahiri yana matuqar buqatar matar sa, saide zaici gaba da haquri kawai har Allah ya yaye masa abinda yakeji, saboda yakusa sati kullum da ciwon mara yake kwana, amma be nuna mata cewa yanayi bama bare ta daga hankalinta

Magun gunansa suna hannunta, kullum itace take bashi saboda tana tsoro karta je Yaqi sha, idan lokacin shan maganin yayi saiyaje tabashi yasha

Yauma da azahar yashigo gidan, kai tsaye dakinta yashiga, a lokacin tafuto daga wanka tana zaune gaban mirrow tana kwalliya daga ita sai Dan qaramin towel

Gabanta yaje ya tsaya yana Kallanta, duk kuma saita rikice tarasa mezataci gaba dayi, ta kalleshi tace "Sannu da zuwa ya Fawaz"

"yawwa sannu da kwalliya Baby Dida "

Murmushi tayi, ahankali tafara kokarin tashi zata nufi wajan kayan ta, Miqewar da zatayi towel din ya kunce yayi qasa 🙆🏻‍♀️
Ganinta haka Babu komai yasa cikin sauri Fawaz ya runtse idonsa, bugun zuciyarsa yafara sauyawa, ita kuwa Dida tsugunna wa tayi ta rarumi towel dinta ta daura 🤣

Tayi tunanin zata riskeshi yana kare mata kallo amma abun mamaki tana kallansa taga idonsa a runtse, mamaki ya kamata, to kode ya Fawaz baida lafiya ne?

Miqewa tayi tsaye tace "ya Fawaz Zan shirya, kaje Zan futo ma da maganin"

Babu musu yace "to" sannan yafuto, Dida tabishi da kallan mamaki, mum tace mata masu shaye-shaye basa kula mata, to amma ita ai matar sa ce, menene zaisa ya runtse idonsa Kamar yaga abinda ba halal din saba?

Haka ta shirya tafuto falon tabashi maganin yasha, anan falon suka zauna suna kallo, amma Babu fira, maganar sai de kadan kadan 🤣, ita Dida tana tunanin hali irinna Fawaz, shikuma idan ya kalleta saiya tuna dazu da towel yafadi, dama haka wannan abin na qirjinsu yake? Dama bata tsugunna ba, meyasa ma ya runtse idonsa ne?

Ahankali yatashi ya kalleta yace "zanje daki nadan huta, anjima Zan futo"


Cikin ladabi tace masa "to"

Dakinsa yashige yafada kan gado, ya janyo fillo ya rungume yana tunanin Dida, gara yazo daki ya kwanta yanda zaifi jin dadin tunanin nata, ahankali yaji yanayin sa yana sauyawa, Tun yana jin dadin tunanin harya dawo yana jin mararsa tana masa ciwo kadan kadan, sai qara matse fillo yake a qirjinsa

Shiru shiru har bayan sallar ishsha'i Dida bataga Fawaz yafuto ba,dakinsa tabishi anan taganshi akan gado yahada uban gumi, yatakure kansa waje daya, Dasauri ta qarasa wajansa "Innalillahi, ya Fawaz, menene yake damunka? Meyasa baka kirani ba?"

Kasa magana yayi, sai runtse idonsa yake, Dida tasa hannu ajikinsa tana jijjigashi, "ya Fawaz, kafadamin meyake damunka? Zaka iya tashi Muje asbiti?"

Girgiza mata kai yayi, ahankali yakamo hannunta yajashi jikinsa, batayi aune ba taji yadora hannunta akan mararsa, gabanta yafadi, Dasauri tafara kokarin dauke hannunta, amma Fawaz yariqe hannun yana qara tura matashi can qasan mararsa, cikin sauri ta fizge hannunta tana fadin "nashiga uku na, tsaya ya Fawaz ina zuwa"🤣

Falo tafuto takira wayar likitan daya dora Fawaz din akan magani, cikin tashin hankali tace "doctor, ya Fawaz baida lafiya, cikin sa yana ciwo, kuma bazai iya tashi mutaho hospital ba, Dan Allah ko zaka temaka kazo ka dubashi?"

Doctor yayi jimmm, yasan de ciwon cikin namiji baya wuce qarfin sha'awa ne kawai, Fawaz Yana buqatar matar sa ne, ajiyar zuciya yayi yace" keba matar sa bace? Kibashi haqqin sa"

"doctor kamarya? Mekake nufi?"


"ina nufin mijinki Fawaz Yana buqatar mace atare dashi, Inda baida aure sainazo na kawo masa maganin dazaisha, amma yanada iyali, menene amfanin ki? Kibashi haqqin sa kawai Tun kafin mijinki yaje yakai kansa wajan wata, Allah yakiyaye hakan"

Gaban Dida sai faduwa yake, kai tsaye tace "gaskiya Doc bazan iyaba"

Yace "to shikkenan, ai zaki iya biyawa mijinki buqata ta wata hanyar, amma de Karki Barshi haka,ke mace ce, kinsan hanyar dazakibi kisamawa mijinki nutsuwa basai nafada miki ba, sai anjima"
Doc. Ya kashe wayarsa yabar Dida da waya akunne, tunani takeyi tayaya zata iya cire kunya tayiwa yaya Fawaz wani abu? To amma kuma Doc yace zai iya kai kansa wajan wasu matan, yanzu yaya zatayi? Diyana ce tafado mata, Dan haka ta dannawa 'yar'uwar tata kira, a lokacin suna can suna bacci, Adam ya qwaqumeta ajikinsa, sama sama taji wayarta tana ringing, tameqa hannu ta dauka taga Dida ce me kiran, cikin sanyin murya tace "Dida ya' akayi?

"Diyana kinga ya Fawaz ne baida lafiya, cikin shi yana masa ciwo sosai, bakiga yanda yake hada gumi ba, tona kira Doc. Sai yacemin wai matar sa yake buqata, kokuma wai namasa wata dabarar, narasa ya zanmasa Diyana, Kibashi shawara Dan Allah ya zanyi? Abinda nauyi Diyana "

Diyana tayi shiru tana tuno irin azabar da tasha ahannun Adam, tace " karkiyi masa komai kirabu dashi yamutu "😳🙆🏻‍♀️

Cikin sauri Dida tace" narabu dashi yamutu fa kikace Diyana, haqqin sa yana kaina ya za'ayi nabarshi ya mutu? "

Diyana tace" to Dida Karki bari yamutu, ke saiki tsaya ya kasheki ai "
Qit takashe wayarta tana masifa, yarinya ana nuna miki annabi kina runtse ido, nace kirabu dashi zaki fara min wa'azi wani haqqi haqqi ai sai kije, lokacin dazakiban labari Babu wani haqqi dazaki tuna

Adam kuwa yana jinta yayi shiru Kamar bacci yake, sai dariya yake qasa-qasa 🤣

Haka Dida takoma cikin dakin nasa tazauna agefen gadon tayi tagumi, tarasa shawarar wazata dauka, Doc. Kokuma abokiyar shawararta Diyana, tajuya ta kalli Fawaz taga gaba daya ya rikice mata



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Tunda tadawo daga camp taci gaba da harkar gabanta agidan, kuma har zuwa wannan lokacin magana bata qara Hadata Da Abba ba, idan taganshi afalo ma bata futowa, idan tafuto kuwa ko gaida shi batayi take harkar gabanta, abin yana masa mugun ciwo, yarasa yaushe yarinyar nan takoyi rashin kunya

Yauda yamma taci kwalliya cikin riga irin readmade dinnan, Mai launin green, rigar tayi mata mugun kyau, kuma tayi daidai da jikinta shape din cikinta daya kwanta yafuto sosai, hakan yasa qirjinta Dagowa, daga qasan rigar kuma abaje take, sai farin mayafi data nad'a akanta, tafitar da gashinta waje
Falo tafuto hankalinta yana ka waya tana daddannawa,a lokacin Abba yana zaune da system agabansa yana serch wasu abubuwa, wando ne ajikinsa three quater, sai riga irin body hock dinnan, takama jikinsa rigar, hakan yasa muscle dinsa 💪🏻bayyana, sarai taganshi azaune amma ta dauke kanta, tazo tawuce ta gabansa ta zauna awata kujera ta gefensa, harda dora kafa daya kan daya, tadauki remote tana sauya tasha, wayarta ce tayi qara ta duba taga Ilham ce, cikin murmushi tadauka "meciki"

Ilham tace "mekikeci nabaka na zuba, abinda bai zoba bai wuce ba"

Wani irin dariya tayi me daukan hankali tace "um um aide baizo dinba, ke kuwa yazo, yakike yagida"

"lafiya Nihla, kinqi kizo, kewai karkizo ki takura mana kuma wallahi Babu wata takura, ya Aslam dinma baicika zama ba wallahi"

"kwantar da hankalinki insha Allah zansa rana dukanku nazo muku"

Ilham tace "to shikkenan, bari naje Zan aiki direba kasuwa, wani sabon direba ya Aslam yakawomin waiko Zan buqaci wani abu, wallahi yacika shirme dayawa"

Murmushi Nihla tayi tace "Toda ke waye yafada miki direbobi basuda shirme? Ai kowanne irin direba dakike gani duk haka suke" 🙆🏻‍♀️😳

System din gabansa ya janye yajuyo yana Kallanta, me yarinyar nan take nufi? Bade shi take fadawa magana ba, Wato kowanne direba mashirmaci ne, to Allah yasa tace harda Direban jirgi, wallahi dasai taga qarshen rashin kunya yau🤣

Momy ce tashigo falon, tayi Murmushi tayi matuqar jin dadin ganinsu atare , tayi tunanin masu zaman falon zaman arziqi suke, tace "a a, ashe duk kuna nan kuna kallo"

Abba Bece da ita komaiba yadauki computer dinsa da wayoyi yanaso yatashi daga wajan, Nihla ta kalli wani mujalla agefenta tabude taga pictures din kayan daki dasu kujeru masu mugun kyau, haka take bude shafi shafi tana gani, gaskiya kayan sunyi kyau sosai, sun birgeta, bangon farko takoma tagani, anan taga amsa A&A FURNITURES

Ta kalli Momy tace "Momy wannan kayan sunyi kyau sosai gaskiya, inane wannan A&A din?"

Momy tace "laaa campany yayunki nefa, Abba da Aslam ne suka bude, nayi tunanin ma kinsani ai"

Girgiza kanta tayi, tace "bansani ba"

Cikin ransa yace yawwa tunda batamin magana yanzu ai dole tatayani  murnar bude campany...

 Kafin ma yagama tunanin sa yaji tace "idan nasamu lokaci zanje nayiwa ya Aslam din murna" 🤣


Cikin ransa yace Aslam... It means banda Abba, cikin bacin rai yatashi fuuuuu yashige cikin dakinsa

Babu Wanda yalura da yanayin sa, saboda shi dama koda yaushe fuskarsa adaure take


Yana zuwa yafada kan gadon yana tunani cikin damuwa, tunda yarinyar nan tazo gidannan baitaba ji takira sunansa ko sau dayaba,yalura kallan arziki ma baya samu awajanta, to meyasa hakan? Meyasa?
Nan take ya tsinci kansa cikin damuwa a dalilin hakan





More Comments more typing, idan akai Comments dayawa nima inyi typing dayawa, idan akai Comments kadan nima inyi typing kadan, babu zafi 👌🏻






Amnah El Yaqoub ✍️
[7/4, 12:34 AM] El Yaqoub: ❣️DANGI DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub

Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493



Masu buqatar sa daga farko sunemi wannan number 09039066577, kokuma kai tsaye suje page dina suyi like saisu karanta


35&36


Furzar da iska yayi daga bakinsa tareda yin ajiyar zuciya, toshi menene ma zai dame shi?wata zuciyar tace saboda yar'uwar ka ce, sannan kaida ita DANGI DAYA ne, ba haka take wa su ya Usman, meyasa shi take rabuwa dashi?
Koda yake, yasan ba komai ne yake damunta ba sai yarinta 🤣
Wataran idan tayi hankali zata dena, danhaka shi zai dinga yimata magana kawai

Washe gari dasafe yana kwance akan doguwar kujera wayarsa na hannunsa yana danne-danne, Momy kuwa tana gefe tana waya da Daddy dayayi tafiya, Nihla ce tafuto daga dakinta kai tsaye wajan Momy tanufa ta dora kanta akan cinyar Momy, binta yayi da kallo, lokaci yayifa dazai fara yiwa yarinyar nan magana, to amma ta wacce hanya? Shi dama can bawata magana sukeba, mezece mata yanzun?

Hakanan ya tsinci kansa cikin faduwar gaba, tome hakan yake nufi? Tsoron ta yakeji kokuma kwarjini take masa? 🤔

Daqyar yayi gyaran murya yadaga kansa yana Kallan gashinta dako dankwali Babu yace " Am Zan samu coffee?"

Sarai tajishi amma saita shareshi, idan bazai kira sunanta ba yabari, babu wani coffee dazata hada

Momy ta kalleshi taga idonsa akan Nihla yake, da alamun da'ita yake kenan, kuma taga alama itama Nihlan taji tayi masa banza, kai wannan yara tarasa ya zatayi dasu, ta lura kowa jinkansa yake, yanzu shi bazai bude baki yace Nihla tashi kihadamin coffee ba, saide ya yi mata magana Kamar yana magana da wata daban ba qanwarsa ba

Ajiyar zuciya tayi tace "Nihla yayanki yana magana"

Cikin shagwaba tace "Momy Allah nina gaji"

Momy ta shafa gashin kanta tace "Nihla banason qiwa, maza tashi kije ki hada masa"

Daqyar tatashi tana bubbuga qafa tayi hanyar kitchen din tana gunguni "Allah ni nagaji..."

Yaja daga kwancen yagama qare mata kallo, ba qaramin birgeshi tayiba yanda take wannan shagwabar, shiyasa yace yarinta ce take damun yarinyar, kallan Momy yayi yace "Momy yanzu haka zakibar yarinyar nan tadinga yawo kanta Babu dankwali"

Momy tace "Abba kaima fa qanwar ka ce, kanada iko akanta, kayi mata magana mana"

Shiru yayi, besake magana ba, daga yin qorafi kuma sai ace shi yayi mata magana?

Nihla kuwa da niyya taqi futowa daga kitchen din dawuri, saida tagama Jan ajinta sannan tafuto da iya cup daya jal a hannunta, ko akan tire bata dora ba, takawo gabansa ta direshi batare datace komai ba, sannan takoma wajan Momy, Kallanta yayi yanda ta ajiye masa coffee din Babu ladabi aciki, aikuwa karaf idonsu yahadu dana juna, fuskar nan tasa ahade, lokaci daya kowa yadauke idonsa cikeda basarwa



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Yau juma'ah, su ya Usman sun saba ko wacce juma'ah da an'idar da sallah gidan suke zuwa susha firarsu da yamma can saisu tafi

Yauma zaune suke afalo suna kallo amma hankalinsu baya kan kallon ma, kawai firar duniya sukeyi, koda yaushe Momy ta kallesu wani irin dadi takeji yanda Allah ya hade mata kan yaranta waje daya.

Bakinsa dauke da sallama yashigo falon, yau manyan kaya yasaka harda Babbar riga, kayan sunyi masa kyau sosai Kamar bashiba, kallo daya Nihla tayi masa ta dauke kanta, bata taba ganinsa cikin manyan kayan dasuka karbi jikinsa Kamar yau ba, koda yaushe saide qananun kaya, farouq ya kalleshi yace "saurayi mijin yanmata, baka gankaba Kamar sabon Ango"

Murmushi yayi, Wanda ya qarawa fuskarsa kyau sosai, qaraso wa cikin falon yayi, duk kujerun dake falon bai zauna akowacce ba, sai wadda Nihla take zaune dayake a 2seater take zaune

Yanda ya zauna akujerar dab da ita saika dauka matar sa ce, gabanta ne yafara luguden faduwa amma sai tayi fuska ta basar Kamar yanda yayi

Aliyu yace "farouq bakada damuwa, shiyasa ko d'an yayan ne da qanne suke fadawa yayunsu Abba baya fada ma, kacika tsokana wallahi"

Usman yadauki wayarsa Kamar yana dannawa amma saiya shige cikin camera ya cire flash din camerar yadauke su photo batareda kowa ya lura ba, pic din ya kalla sosai anan yaga tsantsar dacewar dasukayi, murmushi yayi yasaka wayarsa cikin aljihu yace "gaskiya farouq yafada, munada manya manyan biki a gabanmu nan gaba, Gana Abba Gana Nihla"

Sai a lokacin Abba yayi magana, "ya Usman biki kuma?"

Usman yace "emana, to tsayawa zamuyi muyita kallan ku"

Murmushi kawai yayi, baisan dalili ba haka nan yakejin dadin zamansu a kujera daya, jiyake Kamar suci gaba da kasancewa ahaka

Ruwan dake ajiye a table din gabansu yadauka ya tsiyaya a glass cup yanasha, hakanne yabawa Nihla damar matsawa gefe can qarshan kujerar, domin kuwa ba qaramin takura ta yayi ba

Wayartace tayi qara, Kamar hadin baki dagashi har ita suka kai dubansu kan wayar, yau ma cin karo yayi da irin sunan da yagani kwanaki Wato ❤my Yusif ❤

Wani irin haushi ne ya kamashi, Wanda shi kansa yarasa dalilin jin hakan,daga farouq har Usman da Aliyu Abba suka zubawa ido suna kallan yanayin sa

Nihla kuwa hamdala tayi cikin ranta, ta miqe zata shige daki domin amsa wayar, saida taje tsakiyar falon ta tsinci maganarsa Kamar almara "please kid'an kawomin lemo a kitchen"

Cak taja ta tsaya, ita batayi gaba ba, ita batayi baya ba, wallahi ranta yabaci, Dan me dukda datake zaune baice taje tadauko masa ba, saida yaga zata shiga daki ta amsa waya, tayi tunanin su ya Usman zasuce tarabu dashi taje tayi wayarta, amma saitaji shiru, tome suke nufi? Ita zasu hadewa kai subi bayan dan'uwansu? 🤔

Cikin taqaici tayi hanyar kitchen din,takawo masa lemon ta ajiye, Usman sai kallan fuskarta yake ko zaiga yanayin ta amma sai yaga fuskarta Babu yabo Babu fallasa, shi kokadan baiji haushin abinda Abban yayi ba, domin kuwa yagama gane dan'uwan nasa kishi yafara batare daya saniba, shikuma gaskiya bazaiso ace mace Kamar Nihla tasake kubce musu ba, musanman ma yanzu dakomai yaji 🤣

Bayan ta ajiye lemon ko kallansu batayi ba, tashige cikin dakinta, wayar ta wullar akan gadon tareda dafe kanta 🤦🏻‍♀️, me wannan mutumin yake nufi da ita ne?



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Zaune suke suke afalon Diyana gaba dayansu, dukansu Kallanta suke tana basu labari, cikin damuwa taci gaba da cewa "idan na zauna afalo koda yaushe bashida wajan zama sai qarqashina, ga aiki, kullum saiya sakani aiki Dan masifa, narasa yaya zanyi, har gara wani lokacin Momy tana masa magana, amma wallahi rannan dasu ya Usman sukazo dukansu qyaleshi sukayi, kuma suna gani fa ankirani ne awaya "

Dida tace" to Nihla me kikeso suce miki?, lemo yanema ki kawo masa, kinga ai bazai iyu suce karkije ba, babu girmama wa aciki, Inda wani abu yace daban, dole zasubi bayanki "

Tace" to zaman dayake a wajena fa? Shikuma me zakice? "

Diyana tayi Murmushi tace" ai zama wannan kawai ni abinda na fahimta yana gyara kansa ne kawai, ada ma kowa yana cewa Nihla Nihla bare kuma yanzu daya ga abubuwa sun qara baiyana ai dole Yazauna a qarqashinki "🤣

Nihla tace" to aikuwa zandena zaman falon, bare yazo yananiqe min "

Ilham tayi Murmushi tace" keda abokinki "

Harararta Nihla tayi tace" kimin shiru kiji da abinda yake jikinki, wai Dan Allah idan kin haihu ma sunan wazaki sane? Dafatan nizaki saka "

Ilham tace" hum wallahi ingaya miki yace Ya Abba zaisa, in mace ne kuma Anty aysha "

Yatsina fuska tayi tace" Abba de Abba de, narasa meya musu duk suka daukakeshi haka"

Ilham tace "aikinfi kowa daukakarsa, keda kikace yana nan daram acikin ranki kina sonsa"

Wata irin dariya tayi tace "um da kenan, da kika sani yarinya, wallahi yanzu nafi qarfin sa"

Diyana tace"gaskiya kam, wallahi kija ajinki dakyau, yagane da da yanzu ba daya bane"

Dida tace "Allah sarki ya Abba, nikam wallahi tausayi yake bani, ko'ina yarinyar dayace yanaso din Dafarko?"

Ilham tace "nikam dukda abinda yamiki abaya, wallahi zanso ace kin aure shi, kin auri abokin mijina, muci gaba da zumuncinmu, Nihla ki auri ya Abba Dan Allah, shi ubangiji yanason bayinsa masu hakuri, duk danasan cewa abune Mai mutuqar wahala hakan"


Diyana tace "waiku cewa yayi yana sonta?, Nikaina nasan ya Abba yahadu babu qarya, yakai na mijin dakowacce mace zatayi Burin ace ta samu, to amma kutuna abinda yamata mana"
 ta kalli Nihla tace "wallahi koya dawo kinuna masa mata sunada daraja"

Nihla tace "yawwa Diyana, fada musu de"


Haka sukai ta firarsu cikin jin dadi, kasancewar haduwa tana musu wahala



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Ahankali kwanaki sukaci gaba da shudewa, Abangaren Dida, tunda tasamu ya Fawaz ciwon cikin sa yalafa tadena damuwa, sabgarta kawai takeyi, domin kuwa itade tana kunya bazata iya masa komai akan haka ba, cikin Ilham kuwa yaqara girma tana nan haihuwa yau ko gobe, babu wanda yakai Aslam murna saboda yasan cewa kwana kusa zai zama uba

Yau bataje makaranta ba Inda take service, ta dade tana bacci dasafe sai wajan goma da rabi tatashi, doguwar riga ce a jikinta ta bacci amma me kauri, rigar batada hannu, sai hula datasa akanta, tana hamma tafuto falon anan taga Momy itada wani da alama likitane sun futo daga dakin ya Abba, yanayin Momy ta kalla kawai tasan Babu lafiya saboda yanda jikinta yayi sanyi,kuma hakan baya rasa nasaba da abinda likitan yafada mata, sallama sukai da Doc din sannan tajuya zata koma dakin nasa, Nihla tace "Momy lafiya?"

"wallahi Abba ne baida lafiya Nihla"

Tace "subhanallah, Allah yabashi lafiya Momy" tafadi haka tana kokarin juyawa dakinta

Momy ta kalleta da mamaki tace "yayanki baida lafiya, amma kina kokarin juyawa daki? Ba zakizo ki ganshi ba?"

Turo baki tayi gaba alamar shagwaba, Sannan tabiyo bayan Momy suka shiga dakin nasa, yau ne karo na farko data shigo dakin Tun bayan barin ta gidan, gaba daya dakin saiya koma mata sabo saboda ansauya komai nasa

Yana kwance yana bacci, dagashi sai wando three quater, da vest fara qal ajikinsa,  kallonsa Nihla tayi, faffadan qirjinsa gashine kwance, sai Dan qaramin bakinsa daya fara bushewa, ko menene yake damunsa oho?

Kallan Momy tayi tace "Momy ai bacci ma yake, bari naje nayi wanka kafin yatashi" tafadi hakanne kawai danta gudu, saboda bata fatan ace yafarka yaganta a dakinsa

Abinda bata saniba kuwa shine idonsa biyu, kawai yana kunyar hada ido da Momy ne, tayaya zai iya Kallanta bayan fama dayayi da ciwon ciki Tun cikin dare kuma yau doc yazo yace yakamata ayi masa aure saboda sha'awa datake damunsa, tayaya zai iya hada ido da Momy?

Momy tace "a a, ai hakuri zakiyi da wannan wankan, nasa Adala tahada masa Tea, zanje na karbo, ki zauna karya farka shi kadai kozai nemi wani abu" 🤣

Wannan karan kam, ran Nihla baci yayi, harta kasa boye hakan akan fuskarta, Momy ma taga yanda yanayin ta ya sauya amma haka tayi shiru tafice daga dakin, taga alama Nihla har yanzu yarinya ce, yanda takejin ta aranta Kamar su Usman Babu yanda za'ai tadinga Hadata Da Abba Dan wata manufa, itace ta haifi Abba amma dole zata nuna masa kuskurensa akan abinda yayiwa Nihla abaya, amma hakan ba zaisa tazuba musu ido tana kallansu suna zaman doya da manja ba, koba komai dukansu yaranta ne, babu wanda zata nunawa banbanci acikinsu, tana wannan tunanin ta qarasa cikin kitchen din


Shiru Nihla tayi tana tana zaune akan bedside drower, ko Inda yakema bata kallo, shima yana jinta a gefensa amma bai bude idoba, asali ma jiyayi bugun zuciyarsa yana qara sauya wa, kuma yarasa dalilin hakan, yasan cewa a dole take zaune dashi, saboda yanda yake ganin tsanarsa qarara acikin idonta, yasan kozai mutu bazata kulashi ba

Ahankali wata dabara tafado masa, bari ya gwada, yasan idan yayi hakan dole zata ambaci sunansa, sannan tabashi kulawa

Ahankali yafara motsi tareda yatsina fuskarsa, cikin alamun ciwo yace "wayyo Allah nah.... Momy... Momy Zan mutu..."

Cikin sauri Nihla ta kalleshi, amma abin mamaki ko sunansa bata kamaba tace "subhanallahi, sannu" 🤣

Haushi yakama Abba, waime yarinyar nan take nufi ne? Murqususu yaci gaba dayi Kamar gaske, duk ya rikice Kamar bashi ba, handle din dakin da aka kama za'a bude yasa Nihla tayi tunanin Momy ce zata shigo, kuma tasan fada zata mata tace tana ganinsa ta qyaleshi, hakan yasa cikin sauri tatashi tadawo gefensa tazauna tana cewa "Sannu, sannu"

Jinta akusa dashi yasa yatashi Ahankali Yazauna, sannan yazuro qafafunsa qasan tiles din dakin yamiqe tsaye zai shige toilet, yana Miqewa kuwa mararsa ta murda agaske, cikin azaba yadawo Yazauna, baisan lokacin da yadora kansa akan kafadarta ba, hannunsa kuwa yana kan cinyarta, gaban Nihla yahau luguden faduwa, itafa tarasa gane Inda ya Abba yadosa, meyake nufi hakane?

Ahankali yaji maransa tadena ciwo yabude idonsa, amma me? Saiya kasa dauke kansa daga kan kafadarta, yanda ya kwantar da kan nasa hakan yabawa idonsa damar hango cikakkun nashanunta farare tas, cikin ransa yace wallahi natane Babu qari, but ya'akayi yarinyar nan takoma hakane cikin shekara hudu?

Turo dakin Momy tayi tashigo hannunta dauke da cup din Tea, ganinsu ahaka yasa ita kanta gabanta yafadi, anya Abba kuwa bason yarinyar nan yakeba? Me Abba yake shirin janyo musu? 🙆🏻‍♀️

Haka de takawar da tunanin aranta, takawo masa Tea din tace "gashi Abba, tashi kasha Tea"

Ahankali yadago kansa daga kafadarta, cikin dabara ta matsa can gefe dashi tana hamdala aranta, Tea din ya karba yafara shan ahankali, cikeda shawaga yace"Momy zafi "

Tace" nifa Abba dama ba rashin lafiyarka ba kadinga langabewa mutum kenan, kaiba qaramin yaro ba amma kadinga shagwaba, kuma wannan gashin na qirjinka ka zauna ka askeshi Dan Allah"🤣

Dukda yana jin jiki, saida ya danyi murmushi kadan, yasaci kallan Nihla, sai yaga kanta a sunkunye batama kallansu

Saida Momy tabashi magani yasha sai runtse ido yake alamun bayaso, sannan suka futo daga dakin itada Nihla


❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Yau Tun safe tatashi da matsananciyar naquda, daqyar ta'iya kiran Aslam dayake wajan aiki, yana jin yanayin muryarta yasan ba kalau ba, haka yadawo gida suka tafi asbiti
Tayi doguwar naquda sai cikin dare ta haihu lafiya, tahaifi danta namiji Mai kamada ita sak
Tun asuba labari ya'isa family house cewa Ilham ta haihu, dasassafe kuwa asbitin yacika sosai da yan'uwa, Nihla kam tafi kowa murna, gata da ihlam haka suke zaune a dakin, sai wajan la'asar sannan suka dawo gida, amma Nihla sai dare tadawo agajiye, hajiya Na'ila bataga ta zamaba, tunda akai haihuwar tayi kane-kane akan komai, ko kara bata yiwa hajiya Abida ba, Wato Maman Ilham 😃

Ita kuwa hajiya Abida abin ma bai wani dameta ba tunda ana kula da yarinyar ai shikkenan, ita dadi ma taji, tasan cewa hakan alama ce ta Ilham din tana zaune da sirikarta lafiya

Bayan kwana bakwai aka radawa yaro suna Abubakar Wato Abba, suna kiransa da lil Abba

Da yamma ta shirya tsaf cikin riga da siket na leshi, Mai launin dark blue da sirkin fari, qananun kalba ne akanta, da kanta ta tsara kwalliya taci daurin dankwali Mai kyau, ta tattare kalbar tata tadaureta abaya, wayarta ce take qara taqi dauka, su Dida ne suke kiranta Tun dazu, tasan kuma bazai wuce suce basu ganta ba

Saida ta shirya tsaf sannan tayafa mayafin ta Dan ma dedeci tafuto falo, hayaniyar su ya Usman take juyowa a dakin ya Abba, tace to wannan yaushe sukazo, gefenta ta kalla taga wata waya qirar iphone tayi Murmushi tadauka tace may be ta ya farouq ce, tana daukar wayar kai tsaye tatafi camera tadinga yin Selfie masu shegen kyau, sai Style take qarawa tana yin pictures din, saida tagama sannan ta ajiye wayar ta qwalawa Momy kira

Sai gata tafuto daga dakin ya Abba ita dasu ya Usman ashe ma tare suke, suna futowa farouq yace "kai kai kai, ina zakije haka Kamar Wanda zakije wajan gasar sarauniyar kyau?"

Murmushi tayi, tace "ya farouq gidan suna Zan tafi"

Ya Usman yace "gaskiya wannan wankan nawa ne"

Murmushi tayi batace komai ba, Aliyu kuwa baiyi mata magana ce kawai de yana murmushi cikin ransa yana yaba kyawun surar yarinyar

Shikuwa Gogan abakin kofar dakin nasa ya tsaya hannunsa zube cikin aljihun wandonsa, yana qare mata kallo Bece dasu komaiba, yatsani yaga tanayiwa mutane murmushi saboda yanda take yin mugun kyau, musanman ma yanda dimple dinta suke futowa
Fuskarsa adaure Babu alamun wasa yake kallanta, amma yakasa cewa uffan

Momy ta kalleta tace "masha Allah, yanmatan Momy kinyi kyau sosai, bari na gyara miki daurin dankwalin naki"

Nihla ta tsaya Momy kuwa ta qara gyara mata daurin, sannan tayi mata sallama tatafi



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Gidan suna yayi albarka sosai, Mazawaje family duk sunje, iyayenne mata kawai basujeba, saikuma 'yan'uwan mahaifiyar ta suma duk sunje sosai, maijego tana shiga cikin kayaiyaki na alfarma itada Baby

Har dare yayi anata hidima sannan mutane suka Dan rarragu, duk wannan abun da ake jikin Dida asanyaye yake, sai bayan mutane sun watse ne da daddare Nihla take cewa "Dida meyake damunki ne Tun yamma kinyi shiru"

Tace "tunanin ya Fawaz nake, ina tsoron karyaqi shan ma ganinsa"

Diyana tace "Dida kina shagwaba ya Fawaz wallahi, koda yake soyaiya ce, rannan ma munyi waya da mum take cemin tabawa driver yakawo miki jakar ki tunda kintafi Babu sallama" 🤣

Murmushi tayi kawai

Ilham tace "kice anaji da yayan nawa, toki sakarwa dan'uwana jiki de yamore ehe"

Diyana tace "um, nikam danba qara, Tunna farko bansake yarda ba"

Nihla tace "waiku Dan Allah miye hakan, kawai saiku dinga yin wannan firar agabana, salon ku lalatani"

Dida tace "kwana nawane kema Nihla, ai Kamar yaune"

Diyana tace "ke gwauruwa waye zaizo yadauke ki ne? Kingani ya Adam zaizo, kuma Dida ma nasan ya Fawaz zaizo"

Tace "nikam driver, dama shiya kawoni"

Itama Diyanan tace "wai kina nufin ya Abba ba zaizo yadauke ki ba?"

"ya Abba fa kikace, ashe kuwa saide na kwana anan, keni fa ko magana bamayi, kowa harkarsa yake agidan nan infada miki"

Ilham tace "haba Nihla, ya Abban kine fa, kudena Dan Allah"

Itade Nihla shiru tayi tanajin su suna zancen su ta qyalesu, taga alama Ilham ta Manta cin mutuncin dayayi mata



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️



Fira suke sunata kwasar daria amma shi yana zaune akujera shi kadai ya zubawa wayarsa ido, farouq Tun dazu ya lura kwata-kwata hankalin Abba yanakan wayarsa, ko kallansu Babu kawai ya qurawa waya ido

Ahankali yatashi yayi kitchen Kamar gaske 🤣
Soyake yaga menene yadauke hankalinsa haka, daya dauko Ruwan da niyya yazo wucewa ta bayan Abba,karaf idonsa yasauka akan screen din wayar Abba, pictures din Nihla ne, kuma da kayan data fita dashi dazu da yamma ne, toya akai Abba yasamu pictures din? Yaushe yayi mata? Dama sun fara shiri shida itane harya fara yimata photo awaya?
Ganin Babu me bashi amsa yasa ya tsaya yana kallan Abba dayake kallan pictures din daya baya daya, idan yashiga cikin guda daya saiya dade yana kalla sannan zai sake zubawa nagaba ido

Momy data lura shurun nasa yayi yawa tace "Abba na lafiya de ko?"

Kafin Abba yayi magana farouq dayake bayansa a tsaye yace "lafiya Momy, yana ganin abinda yake rayuwa tare dashi ne acikin gidan"

Cikin sauri ya juya ya kalli farouq, Dasauri yasaka wayar aduhu, sannan yasakata cikin aljihun wandon jeans dinsa, Innalillah... Baiso farouq ya kamashi yana kallan pictures din yarinyar nanba, kada yayi tunanin wani abu, ahankali yamiqe tsaye yace "Babu komai Momy"

Farouq ya kwashe da daria ganin yanda qanin nasa yayi fuska Kamar bashi ba, yace "idan tayi tsami maji"

Momy kam bata gane komai ba, danhaka tashare su, haka sukaci gaba da firarsu sannan sukai mata sallama kowa yatafi gidansa

Shima Abba compound din gidan yafuto, Momy kuwa daki tashige tana waya da Daddy akan matsalar Abba da likita yafada mata, yace ta bari idan yadawo gida saisu yi masa magana

Yadade a compound din yana kallan get din gidan, Agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa ya kalla kasancewar akwai yalwar hasken fitilu agidan yaga goma saura, zagaye yafarayi awajan hannunsa daya yana cikin aljihunsa, har zuwa wani lokaci kuma Yaqi komawa cikin part din nasu, Agogon yasake kalla afili yace

"why bata dawoba har yanzu?"








Gashinan anyi dayawa, dafatan zanga Comments, facebook readers ina godia sosai da sosai 🙏













Amnah El Yaqoub ✍️
[7/5, 12:37 AM] El Yaqoub: ❣️DANGI DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub


Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493



37&38



Babu me bashi amsa, haka yadinga zagaye wajan har saida ya hango maigadi yana bude get alamun itace suka dawo, sannan ya juya cikin sauri ya koma ciki

Ita kuwa Nihla bata lura dashi bama, ana sauke ta tashigo part din nasu, kai tsaye dakin Momy taje ta sanar da'ita dawowar ta sannan tatafi dakinta tayi wanka, tafara shirin bacci


Har shigowar ta falon yanajinta, sai a lokacin ya kashe wutar dakinsa shima ya kwanta



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


"Doctor magunguna na sun qare inaso kahada min wasu" cewar Fawaz

Doc yadubeshi yace "to Alhamdulillah gaskiya naga ana samun cigaba"

"hakane kam, but wani lokacin inajin raina yana baci haka kawai, kuma cikin raina inajin inason nasha qwayar ko kadanne"

Murmushi Doc yayi "hakane, dama dole zakaji haka, amma kaci gaba da hakuri, kana kai zuciyarka insha Allah zuwa nan gaba kadan zakaji tafita daga ranka ma gaba daya"

"ina fatan haka Doc, domin duk abinda mata ta bataso nima banaso, banason bacin ranta ko yayake"

"masha Allah, kanason matar nan taka Fawaz, dukanku kunason junanku,amma bansan wacce irin soyaiya ceba wannan, duk yanda kake sonta bazata iyama abinda kakeso ba, domin ta cetoka daga halaka"

"mekake nufi Doc?"

"matarka takirani rannan da alamun ma Kamar tana kuka, tace bakada lafiya inzo, nafada mata cewa maganin ai yana wajan ta, tabaka haqqin ka kawai, kai tsaye tacemin bazata iyaba"

Murmushi Fawaz yayi "ai tanada kunya Doc nima nasan bazata iyaba, kuma ni hakan datayi ya birgeni, inason mace Mai kunya, nikuma gaskiya kunyar tunkaranta nake da wannan abun, bansan ta Inda zan fara ba, please ko zaka bani wasu magungunan Wanda Zan dinga sha duk lokacin dana jini cikin wannan yanayin "

Dariya likitan yayi" lalle, ina Ruwan laila majnun, Wato ahakan batayi laifi awajan ka ba, kuma kai bazaka iya kai kanka wajantaba, lalle Fawaz irinku kadanne Awannan zamanin, to maganar gaskiya bazan baka kowanne irin magani ba, inzaku nemi haqqin junanku ku nema, idan bazaku nemaba shikkenan, amma kanada aure kanada mata bazan baka wani magani ba, wannan ai sai yarinyar ta rainaka ma tace baka iya mata komai "

Murmushi Fawaz yayi " tace komai ma Doc, amma ni bazan iyaba "

Likitan yayi shiru yana kallan Fawaz, ikon Allah kenan, Awannan zamanin? 🤔



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Tun bayan dasukai magana da Doc. Ya tattara maganarsa ya watsar yaci gaba da sabgarsa, har Tsawon sati daya, zaman su da Dida kuwa komai lafiya, yau Tun safe yakejin cikin sa yana murdawa, haka yatashi yafita, Dida na daki sai dirin motarsa taji, wajan wani abokinsa yaje, abokin na ganin Fawaz cikin damuwa ya tambayeshi meyake damunsa, nan take yafadawa abokin nasa, murmushi abokin yayi yace "dadina da gobe saurin zuwa"

Yatashi yaje daki yadauko masa wata kwalbar wine yace "abokina baka taba shan wannan ba, kasha ta, zakaji dadi, damuwar ka zata kau nan take"

Fawaz ya karbi kwalbar giyar nan yariqe, idan ya tuna cewa Dida bataso sai yaji jikinsa yayi sanyi, uwa uba shi duk shaye shayensa baitaba shan giya ba, to amma kuma idan ya tuna cewa damuwar sa zata kau saiyaji gara hakan "

Memakon yasha anan sai yatafi da ita gida, yana zuwa falo kuwa Dida tafuto daga daki zataje kitchen, kallan farko tayi masa ta hango rashin gaskiya awajan sa, taga sai boye hannu yake, bata zurfafa bincike ba tayi masa sannu da zuwa tawuce kitchen, shima cikin sauri yashige dakinsa, yadauko cup ya tsiyaya giyar aciki, Yazauna zai fara sha kenan taturo kofar dakin tashigo, abinda tagani agabansa ne yasa gabanta yayi mugun faduwa, giya? Dasauri taje tadauke gaba daya, ita dama tunda taga shigowarsa tasan cewa akwai abinda yake boye mata, cikin bacin rai tace "ya Fawaz miye hakan? Menene wannan?" idanunta suka cika da qwallah

Shiru yayi yakasa bata amsa, ita kuwa ta tsareshi da ido tana jiran amsa
Kallanta yayi sannan Dasauri yayi kasa da idonsa, cikin rashin gaskiya yafara yimata magana " Dida... kiyi hakuri, wallahi ba laifi na bane, wani abokina ne..."

Kafin ya qarasa ta tareshi tace "to laifin waye?ya Fawaz Dan Allah yaya kakeso nayi da raina ne eh? Kai yaro kullum zamu dinga magana akan abu daya shekara da shekaru?"

Hawaye yazubo mata, tasa hannu ta goge, sannan tadauke kwalbar giyar da wadda yazuba akofin, ta miqe zata futo daga dakin cikin fishi

Dasauri yatashi ya fusgota jikinsa, ya rungumeta tabaya, tsayawa tayi cak, hawaye yana zuba a'idonta, Tun tana na hawaye harta dawo yi abaiyane, shi kansa yasan cewa bai kyauta mataba, amma yaya zaiyi? Kansa yadora akan wuyanta yayi shiru kuma yariqe ta gam ajikinsa, Ruwan dataji yana Saukowa daga wuyanta yana shirin shiga cikin rigarta ne ya tabbatar mata da cewa kuka yake

Saikuma jikinta yayi sanyi, tadena nata kukan tanajan zuciya, cikin hawaye yace "kiyi hakuri, bazan qaraba, Allah abokinane yabani, bansan yaya zanyi ba Dida, ina cikin damuwa, cikina kullum ciwo yake min"

Nan take Dida tafara tunani, karfa garin kunya tasa mijinta ya koma ruwa, bayan tasamu daqyar yadena shan komai, yanzu inda yasha giyar nan tasan cewa alhaki yana kanta, kuma dalilin ta ne yasa mijinta bayan shan qwaya ya koma shan giya, dolen dole zatai kokarin raba ya Fawaz da wannan abokin nasa duk da batasan ko wayeba

Cikin kunnanta yake mata magana Kamar rad'a yace "kiyi hakuri kinji, Dan Allah Karki sake tafiya kibarni"

Ajiyar zuciya tayi tace "toka cikani natafi, abinci Zan dora mana"

Cikin shagwaba yace "um um kibarshi, nasan sake guduwa zakiyi kibarni"

Girgiza kanta tayi, taga alama Jan magana kawai yakeso, ita zataje tabarshi Awannan halin salon yasake fadawa cikin shaye shaye, kokarin janye jikinta tafara yi shikuma yariqe ta gam, hannunsa takama tadaga masa su sama zata fita daga dakin, shikuma yakai mata wani irin ruqo, sai jin hannunsa tayi akan kirjinta, zaro ido tayi tana ganin Inda hannunsa yake, shi kansa yayi mamaki, amma memakon ya janye hannun nasa saiyayi shiru, laushin dayaji ne yasa yakasa dauke hannunsa daga wajan, baisan lokacin daya fara shafawa ba, amma hannunsa gaba daya rawa yake 🤣

Wani irin yanayi ta tsinci kanta aciki Wanda bata taba tsintar kanta aciki ba, cikin sanyin murya tace "ya Fawaz kabari Dan Allah, ni wani iri nakeji"

Yace "um um, nima haka nakeji"

Jikinta tafara janyewa, cikin sauri yaqara riqota, yaci gaba da abinda yake, wannan karon kam shiru Dida tayi, harga Allah tanajin dadin abinda yake mata, Dan haka tayi shiru tabarshi, daqyar ya'iya dago kansa ya kalleta, abin mamaki sai yaga Dida ta lumshe idonta, murmushi yayi, gaskiya  in hakane yadade yana cutarsu gaba dayansu, cikin rad'a yace "akwai dadi?"

Ahankali ta daga masa kanta

Yasake cewa "kinaso in cigaba?"

Nanma Dida batayi magana ba kawai de tasake daga masa kanta, yana ji ta amince kuwa ya dauke ta cak, ya juya kan gadon sa da ita, kayan jikinta yafara cire mata, ahankali tabude idonta, mamaki ya kamata, tayi tunanin akan zaici gaba da kayan ta a jikinta, amma sai tayi shiru

Tana ganinsa yana kokarin cire nasa kayan tayi sauri ta rufe idonta, batasan lokacin daya gamaba sai jinsa tayi a jikinta, yasaka hannu ya balle mata breziyar jikinta, saida yagama kallan qirjinta tsaf yana ganin ikon Allah, sannan yadora bakinsa akai yafara sha, salon yanda yake mata ne yasa tarasa nutsuwarta, batasan lokacin data kai hannunta kansa ba, ta riqoshi sosai

Saida Fawaz yayiwa Dida charge sosai yanda bazata taba iya masa musu ba sannan yafara neman hanya, daga haka na futo nabar musu dakin



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


"maryam ga wannan kyautar danaso nabaki Tun ranar nan dakike min kuka, kuma Wanda nace yasiyo min bai kawomin da wuri ba"

Kallan hannunsa Diyana tayi cikeda mamaki, wata yar qaramar akwati ce da awarwaro aciki manya guda uku na gold, cikin murna ta karba tace "ya Adam duk nawane wannan?"

"yes naki ne, kawo hannunki nasaka miki"

Babu musu tabashi hannun, yazura mata awarwaron, sunyi mata kyau sosai

Tace "ya Adam nagode, nagode sosai"

"nine yakamata nayi miki godia maryam, saboda kyautar dakikamin, maganar gaskiya banyi tunanin haka Zan sameki ba, amma ina Mai qara baki hakuri akan hakan, kiyafemin"

Hararar wasa ta watsa masa tana shafa abin hannun nata

Murmushi yayi yace "yanzu ya za'ayi? Nayi hakuri fa maryam" ya qarasa maganar yana kashe mata ido daya

Cikin shagwaba tace "ya Adam Allah ni gaskiya bazan iyaba, duk wahalar daka bani haka bai isaba"

Daria yayi yace "a a, nide bai isaba, please maryam"

Shiru tayi masa, hakan yasa yafara aika mata da saqonni, amma yanda taji na farko wannan ma haka taji, banbancin kadanne, domin kuwa yauma taci wahala



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Zaune suke afalo shida Aslam, takardu ne ahannun su suna cikewa, sun baje a kafet din falon, yayinda sautin tv din falon yake tashi Ahankali

Cikin sauri tafuto daga dakinta tana saka wayarta acikin jaka, sanye take da riga da wando na kayan bautar qasa, kayan anyi masa shape sosai, wandon nan tacika abinta Dam, rigar ma tabi jikinta, sai jacket din kayan data dora asama, tasaka Dan qaramin hijabi daya tsaya mata iya qirji, idonta sanye da glass

Qamshin turaren dasukaji ya bigesu ne yasa dukansu suka daga kansu suka kalleta
Itama kallansu tayi tace "ya Aslam ina kwana"

Murmushi yayi yace "lafiya Nihla, ya service"

Tace "Alhamdulillah" sannan takama hanya zata fice

"ke koma kicire wannan kayan"
Ta tsinci muryar Abba yana mata magana

Cak ta tsaya awajan, Sanna Tajuyo ta kalleshi fuskarta Babu yabo Babu fallasa "makaranta fa zanje, kuma kowa da uniform dinsa yake zuwa"

"nace kikoma kicire wannan kayan bazaki fita dasu ki janyo mana magana ba"

Aslam daya ga za'ayi drama agabansa saiyayi gyaran murya yace "haba Abba"

Sannan yadubi Nihla yace "Nihla jeki"

Babu musu kuwa tajuya tafice daga falon

Aslam ya kalleshi yaga fuskar nan ahade tace "meyasa zakayi mata magana Abba? Bayan kasan waje dayawa doka ne coppers suje batare da uniform ba"

"kalli shigar ta mana Aslam, tayaya yarinya 'yar musulmai zata fita da wannan kayan ana ganin komai nata"

Murmushi Aslam yayi yadubi abokin nasa "Abba kana kishin Nihla, kode sonta kakeyi ne?"

Cikin sauri yace "Babu wani so"

Aslam yace "Abba banason rainin wayo, baka sonta tayaya zaka dinga wannan masifar akan zata fita da wannan kayan? Ni nayi mata magana ne? Malam ko kanaso ko bakaso, ina tabbatar ma kakamu dason Nihla"


Hannunsa yadaga masa "dakata Aslam, Dan Allah kadena min wannan maganar, meyasa bazaka fahimce niba ne?"

Haushi yakama Aslam yace "Ok fahimta ko? Nafahimceka"

Daga nan ya tattara takardun gabansa yafice daga part din, aikin da ba'a qarasaba kenan 🤣



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Cikin farin-ciki ya kalleta, yana goge jikinsa da dan qaramin towel, "Baby Dida Tun dazu kike wannan kukan, bayan kuma kece kikace nayi, cemin kikai kinajin dadi nayi"

Hawayen idonta ta goge tace "to aiba wannan nace kayi ba, kuma saida nacema kabari amma tsabar mugun ta ka qyaleni"

Murmushi yayi, yau Babu Wanda yakai shi murna ya angonce, gaskiya masu aure sunji dadinsu, yasan hakane ai da tuni an wuce wajan yace "toki hakuri, ai daga yau nadena, wajan yadena ciwo?"

Jan zuciya tayi tace "akwai zafi sosai, rad'ad'i nakeji sosai, kuma zazzabi ma nakeji"

Yace "subhanallah, bari nagani"

Batayi masa musu ba, haka tabarshi yabude kafarta yaga wajan, yasa bakinsa yahura mata iska kadan aciki, jiyayi Kamar ya qara, amma dole hakura zaiyi Tun kafin ya ballowa kansa ruwa, tasa shi agaba tana kuka

Rufewa yayi yace "shikkenan to kiyi hakuri, zai daina insha Allah"

Ahankali ta daga masa kanta, yasaka hannu yana shafa kanta



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Washe gari da yamma yana kwance a dakinsa, tunanin maganar Aslam yakeyi, yanzu idan maganar Aslam ta tabbata gaskiya yaya zaiyi? Gabansa yafara faduwa, idan hakane kuwa ai yashiga ukunsa, tayaya zai iya fuskantar yarinyar dayace bayaso cikin bainar jama'ah yace yana sonta yanzu? Anya kuwa su Momy zasu bashi goyon baya akan hakan? Innalillah...

Sumar kansa ya hargitsa, yana tuno lokacin da Momy take ce masa tana gujemasa ranar dazaiyi DANA SANI (my first novel)

Kai, bazai iyu bama, tayaya zai fara son Nihla? To amma meyasa yakejin kishinta aransa? Meyasa ranar sunan takwaransa yakasa kwantar da hankalin sa akan dadewa datayi bata dawo gida ba? Meyasa yakejin haushi idon yaga tana wa yan'uwansa Fara'ah bashi ba? Meyasa? Meyasa duk yakejin hakan?

Wannan alamomin duk sun nuna cewa tabbas yanason Nihla, Innalillahi wa inna ilaihir raju'un..., Idanunsa ne suka cika da qwallah, yasan cewa Babu me fuskantarsa

To amma yasan Nihla, yasan cewa Nihla tana sonsa, yasan cewa koda kowa zai juya masa baya banda ita, amma yanda yake ganin tsanarsa a'idonta yasan cewa abinda wahala, amma tayaya zai gane cewa tana sonsa? Ta wacce hanya?

Wata dabara ce tafado masa, lokaci daya yadanji sanyi aransa, haka yatashi yashiga toilet yayi wanka, wata shadda yadauko yasaka Mai launin Ash, yasaka hula tareda Agogon sa qirar gucci, yayi masifar yin kyau, idan ka kalleshi Babu qarya saiya birgeka

Falon yafuto yanata zuba qamshi, Nihla tana kwance da waya a hannunta tana chatting, Momy tana zaune agefe, gaba dayansu kallansa sukayi, yayi mutuqar kyau Kamar bashi ba

Momy takasa yin shiru tace "Masha Allah, Abba wannan wankan sai ina?"

Murmushi yayi Wanda yaqara wa fuskarsa kyau, yasaci kallan Nihla, Sanna yace "Momy zanje wajan zance"

Momy tayi dariya tace "Alhamdulillah, gara da kayiwa kanka fada ai"


Haushi yakama Nihla, tayi shiru batace komai ba, Abba kuwa ya juya zai fita daga falon

yaje dede kofar falon ya tsinci maganarta tace "ya Abba"

Cak yaja ya tsaya awajan, shi yasan cewa Nihla tana sonsa, wani farin-ciki ya kamashi, finally yau de takira sunansa, cikin murmushin da yaqara masa kyau ya juya yana Kallanta yace "na'am"

Budar bakinta saitace "idan kaje ka gaishe ta" 🤣


Be'iya cemata komai ba saide Jinjina kansa dayayi kawai tareda ficewa daga falon

Yana fita itama tatashi tashige cikin dakinta, Momy tabita da kallo amma bataga komai akan fuskarta ba
Tana zuwa dakin tafada kan gadon ta tasaki wani irin kuka Mai cin rai, ita kanta tarasa dalilin yin kukan, haushin ta daya, yanda tadage ta gyara kanta, take Jan ajinta, duk Dan yaso ta tayi amfani da wannan damar wajan nuna masa kuskuren daya aikata abaya, yanzu komai yatashi abanza kenan, ashe duk wannan dauke kan datake abanza, ashe hankalinsa yanacan kan wata daban, Wato harda yimata Fara'ah yana amsawa Dan zaije wajan wata, to tunda hankalinsa yana kan wata, tayaya zata iya rama abinda yamata?

Haka tasha kukanta sannan tashige toilet ta wanke fuskarta tadawo falon tazauna



Yana futowa daga falon nasu yake ganin duhu-duhu a'idonsa, duk hasken dayake wajan Abba baya gani, duhu kawai yake gani, baisan Inda yake saka qafarsa ba,lokaci daya Idanunsa Yarufe ruf yadena ganin komai sai jinsa yayi yafada jikin mutum Wanda baisan ko waye ba

Daqyar Aslam da Allah yakawo shi gidan yanzu, yakawo Abba cikin falon

Momy da Nihla cikin tashin hankali sukai kansu, Momy tana cewa "subhanallah, Aslam lafiya? Menene ya sameshi? Yanzu yanzu fa yafita"

"Momy wallahi shigowa ta kenan nima naci karo dashi"

Momy ta kamashi suka qarasa cikin dakin Abban, akan gado suka kwantar dashi, Nihla tabude fridge din dakin tabawa Momy ruwa tace "Momy ga ruwa" jikinta sai rawa yake

Momy ta kalleta taga yanda duk ta rude, ta karbi Ruwan aka shafa masa a fuska, Allah ya temakesu yafarka, yana bude idonsa yasauke su akanta, kallo daya tayi masa tace "Sannu"

Yadaga mata kai, daga nan tafice daga dakin

Momy tace "meyake damun kane Abba na, naga lafiya kafita"

Ahankali yace "Momy kaina ke ciwo"

Tace "to Allah yasawaqe, bari ajima idan bakaji sauqi ba sai akira Doc"
Bece da ita komai, domin kuwa abinda yakeji yafi ciwon kan yawa, Inda ace ciwon kai ne Toda sauqi 🤣


Momy na fita Aslam yace "Abokina meyake faruwa ne? Meke damunka?"


Cikin damuwa yace "Aslam kayi Gaskiya, kafini gaskiya Aslam, ina sonta, Nikaina yanzu na tabbatar ina sonta" ya qarasa maganar tareda fashewa da kuka

Gaban Aslam yafadi, bade maganar datake ransa hakace take shirin kasancewa ba, kallan Abba yayi yace "Wacece?"


Kai tsaye yace "Nihla"


Aslam yayi shiru Tsawon second talatin,zaka dade kafin kaga Abba yana kuka Kamar haka, yasan cewa tabbas tunda haka ta faru toba qaramin so yakewa yarinyar ba, haka yasa hannu yayi tagumi hannu bibbiyu,
gaskiya Abba yadauko musu Babban aiki, kallansa yayi yace

 "Gaskiya Abba akwai damuwa,ka janyo mana Babban aiki a gabanmu, maganar gaskiya itace kana ruwa tsundum kusada kada"


Cikin masifa Kamar bame kukaba yace "Dan Allah Aslam idan bazaka bani goyon bayaba to kamin shiru kawai, meyasa bazaka fahimci abinda nakeji bane?"


Cikin damuwa shima Aslam din yace "Abba aini nafi kowa fahimtar ka" 🤣

"dan Allah Aslam tashi kafita kabarni da abinda nakeji"  yasa hannu ya goge hawayen idonsa




Sharhi please












Amnah El Yaqoub ✍️
[7/5, 10:18 PM] El Yaqoub: ❣️DANGI DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub


Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493



39&40



Aslam yatashi yafuto daga dakin jikinsa a sanyaye, domin kuwa yasan abokin nasa yana cikin damuwa yanzu, maganar aikin data kawoshi ma baiyi ba.

Fitar Aslam keda wuya Abba ya danna kansa cikin fillo yana hawaye, to Aslam ma dayake makusancin abokinsa yakasa fahimtarsa inaga sauran jama'ar gida? 🤔

Har dare yayi sosai Abba bai sake futowa daga dakinsa ba, saide Momy tana zuwa tana dubashi akai akai



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Karfe goma na safe ma agida tayi mata, babu part din da batajeba cikin family house din nasu, tana zuwa part dinsu Nihla taji shiru Kamar Babu kowa, kai tsaye dakin Nihla tashiga taganta kwance tana bacci fillo rungume a qirjinta

Batare data tasheta ba, ta'ajiye mata lil Abba agefenta, yaron kuwa idonsa akan fan din dakin dake juyawa Ahankali

Fita tayi daga dakin tashiga kitchen din tanaso ta hadawa kanta Tea Dan taga Momy da Nihla harkar gayu suke ji ita kuwa tana goyon yaro bazata iya wannan zaman ba

Cikin baccinta taji yaron yana wasa, bude idonta tayi ta kalleshi, shi kadai, sai tsotsar hannu yake, murmushi tayi tatashi zaune tareda daukar sa tace "Wato mamanka tazo shine ta ajiye min kai tagudu danka tashen a bacci"

Kissing dinsa tayi, suka futo falo, anan taga taga Ilham zaune tana shan Tea da uban Bread a gabanta, Momy tana zaune da alama itama yanzu tatashi

Qarasowa tayi ta ajiye yaron tace "ashe kinzo, yau kece agida kenan"

Kafin Ilham tace wani abu momy tace "nima yanzu na futo naganta"

Ilham tace "Momy Tun dazu ya Aslam ya kawomu yawuce wajan aiki, ina zuwa wajan umma nace ko Abincin ta ba zanci ba wajan Nihla Zan tafi, shine na tarar da ita tana bacci, nabar mata Yayanta a dakin na futo"

Momy tace "Ah kin kyauta wallahi, gashinan ya warware,"

Daukansa Momy tayi tace "Abba nah, mekakeci ne?"

Daga nan tayi cikin dakinta dashi tabarsu anan suna fira

Har yamma Ilham tana wajan Nihla suna ta firarsu, yaron ta kuwa yana hannun Momy saide idan yayi kuka takawo mata shi, yanzu ma nono tagama bashi Nihla ta karbe shi tana masa wasa, sai dariya yake

Tace "Ilham wannan yaron Kamar ku sai sake futowa yake"
Miqewa tsaye tayi tadauki towel dinsa ta goyashi taci gaba da magana "gashi sai dariya yake gwanin sha'awa wallahi ba Kamar me sunansa ba, kullum fuska adaure ko murmushi Babu" 🤣

Karaf maganar ta sauka a Kunnan Abba daya shigo cikin falon yanzu, Tun safe yaje company sai yanzu yadawo, Wato shine kullum fuska adaure, Ilham de taga shigowarsa, danhaka sai tayi shiru 🤣
Ita kuwa Nihla data bawa kofa baya ko'ajikinta, taga de Ilham din tayi mata shiru kawai kuma sai qifta mata ido take 😃, amma bata gane komai ba, yaron taci gaba da jijjigawa a bayanta ko zaiyi bacci, amma memakon bacci ma saiya fara kuka

Ahankali ya qaraso cikin falon, cikin ladabi Ilham tace "ya Abba sannu da zuwa"

Saida yadan saki fuskarsa sannan yace "yawwa, ya Baby"

Tace "gashinan Alhamdulillah"

Shiru Nihla tayi, kode yaji maganar data fada ne, shiyasa Ilham take qifta mata idanu? 🤔

Abba kuwa bai sake cewa komai ba yanufi Nihla fuskarsa adaure ko alamun wasa Babu, muryar sa yarage cikin fada yace "bani yaron nan, saboda rashin hankali kina goyo"

Mamaki yakama Nihla, menene abin rashin hankali a goyo? Batare data ce masa komai ba tafara kokarin kunce yaron, saura kadan yaron ya qwace daga hannunta garin sauko dashi, aikuwa yakama gaban rigarta ya riqe, karon farko da kunya takama Nihla ganin ga ya Abba a tsaye, Sannan wannan yaro yakama riga yariqe har hakan yasa ana hango albarkatun qirjinta

Batayi auneba taji ya Abba yasaka hannunsa awajan ya cire hannun yaron, sannan ya juya zai tafi dashi

Ilham tana zaune tazama yar kallo, duk abinda ake akan idonta, saide bataji abinda ya Abba ya cewa Nihla ba, tayi Murmushi tace "lalle Nihla kin iya goyo, kema da yanzu danaki Babyn"

Abba yana kokarin shiga dakinsa yaji wannan maganar ta Ilham, Wato da ace anyi musu aure a wancan lokacin da yanzu itama da nata yaron, ko juyowa beyiba yashige cikin dakinsa

Nihla kuwa tana qame a tsaye, Ilham tace "kitaho ki zauna mana, kin daskare a tsaye, shiyasa nake ta qyafta miki ido, amma inaaaa gulma ta rufe miki ido bakisan yashigo ba sai zuba kike" 🤣

Nihla ta kalleta "niba wannan ne yasa na tsaya ba, bakiga abinda d'anki yamin bane?" tayi qwafa tadawo tazauna akujerar tana kumburi

Ilham tayi dariya tace "nagani mana, jiyake rigar mamansa yariqe, besan takwaransa ya budewa abubuwa yana ganiba" 🤣


"kuma basai ya tsaya nacire yaron nabashi ba, amma haka kawai saiya wani sakamin hannu a qirji"

Dariya Ilham tayi "kiyi hakuri, ganide ba tabawa bane, kuma gani yayi zaki yarda takwaransa, shiyasa yakawo muku temakon gaggawa" 🤣

Nihla tayi shiru batace komai ba, al'amarin Abba kullum qara tsamari yake, da yana zama agefenta yanzu kuma yafara kawo mata hannu, nan gaba kuma ai batasan mezai faruba

Ilham tace "wai Dan Allah meyake cemiki ne naji yayi qasa da murya yana magana"

"cemin yayi nabashi yaron, saboda rashin hankali ina goyo, menene abin rashin hankali agoyo"

Ilham tace "eto da gaskiyarsa, may be bayaso abubuwan sa suzube ne"

"mekike nufi Ilham?"


"Nihla kinsan goyo yanasa nonon wasu matan yazube, inaga shiyasa, inba hakaba ai bazai ce kina goyo ba"

Nihla tadafe kanta 🤦‍♀️ tace "Innalillahi.... Wallahi gayen nan yagama dani gaba daya"

Ilham tace "kema ai kinga ma dashi, Dan wallahi nide abinda na fahimta ko, ya Abba sonki yake, kigafa yanda yawani matsa gab dake Kamar zaisaku ajikinsa keda Babyn kawai saboda zai karbe shi, Nihla kiyi tunani mana"

"Ilham kenan, babu wata soyaiya, rannan ma sallama ya mana nida Momy yace yatafi zance"

Ilham tace "to nide abinda idona yagani aishi Zan fada"

Haka sukaci gaba da firarsu har hudu da rabi tayi, hajiya Na'ila takira wayar Ilham din tace tazo kafin tatafi gida, tashi tayi tafara shirya wa, Momy takawo mata wani turaren wuta Dan Sudan Mai qamshi, ta karba tana godia

Momy ta kalleta tace "Nihla karbo mata yaronta awajan Abba, zasu tafi"

Tashi tayi ta nufi dakin nasa, Ilham tanayi mata dariya qasa-qasa, ahankali ta tura dakin tashiga, taganshi yana kwance yadora yaron akansa yana masa wasa

Cikin ranta tace ashe yana yiwa yara wasa, sallama tayi ta qaraso, tunda tashigo idonsa akanta Ahankali shima ya amsa sallamar tata

Gabansa ta qarasa, ganinsa dagashi sai ita yasa taji duk yayi mata kwarjini, tana jan yatsun hannunta tace "Momy tace akawo shi zasu tafi"

Da idonsa ya nuna mata yaron yace "gashi nan daukeshi mana"

Wai yaro akan qirjinsa bazai bata shiba saide tasa hannu tadauka, zuciyarta daya kuwa tasaka hannu tadauki yaron
Jin hannunta yadan taba Kirjinsa hakan yasa ya lumshe idonsa, gaskiya yanzu kam yaqara tabbatar wa kansa cewa soyaiyar yarinyar tayi masa mugun kamu

Nihla bata lura da yanayin sa ba tafuto daga dakin, bayansu yabi da kallo itada Babyn, sai yaji dama basu tafiba, dama tazauna yasaka su agaba yana kallansu itada babyn


Bayan sun futo daga part din Momy Nihla tawuce part din umman Ilham itada Yaron, ita kuma Ilham tawuce part din hajiya Na'ila

Ta dade a part din hajiya Na'ila kome take bata oho 🤔 sannan tataho part din ummanta wajan Nihla, takira ya Aslam yazo yadauketa suka tafi, Nihla taji dadin ziyarar da Ilham takawo musu, Ilham tana sonta sosai, tazo gida amma bata wuni awajan sirikarta da ummanta ba, sai awajanta tawuni



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Wanka yashiga ita kuma tana gyara masa dakin nasa, wayarsa ce tafara qara, tanufi wayar taduba taga number ce take kira

Zuciyarta daya tadaga wayar, sai taji muryar mace tace "Malam Adam yau zaka shigo makaranta kuwa?"

Gaban Diyana yafadi, cikin masifa tace "Wacece ke? Menene hadin ki da mijina?"

Alokacin yafuto daga wanka yayi gaban mirrow zai shirya, yana ganin wayarsa ahannun Diyana sai masifa take amma ko Kallanta beyiba, shide yasan yanada gaskiya, kuma Babu wata mace daza dauke hankalinsa daga kan Diyana a yanzu,yanda yakeji da amarcin nan ai Babu me rabashi da maryam

Diyana kuwa sai masifa take, amma wadda takira wayar bata qara cewa komai ba Tun maganar ta ta farko, daga qarshe ma saita yanke wayar

Diyana Tajuyo ta kalleshi tace "ashe yanmatan university har kiranka suke kuna waya bansani ba"

Kayansa yake sakawa cikin sauri saboda yayi latti dayawa, yace "to menene abin damuwa maryam, tunda kece Mai ni"


"wata yar'iska takira ka awaya da wannan safiyar kacemin menene abin damuwa? Amma yanzu idan nice wani yakirani da yanzu kafara fada ko"

Hularsa yasaka yajuyo yana Kallanta, kishi qarara yagani akan fuskarta, Bece da ita komai ba yadauki key din motarsa yana kokarin fita

Itama cikin haushi tafice daga dakin, da wayar tasa a hannunta



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Wayar Dida ce a hannunsa yana sending pictures dinta zuwa tashi wayar, gyaran falo take, yana ganinta tagama ta goge sauran kayan kallo, sai aikin take da jikinta Kamar batasan ciwon jikinta ba

Kitchen ta wuce yatashi yabi bayanta, yana mata wani irin mayen kallo, "wai har yanzu aikin bai qare bane?"

Kallansa tayi "bai qareba, abinci ma zanyi mana"

"kibar Abincin nan Dan Allah, basai naje nasiyo mana ba, ke kullum bakya hutawa"

Wani irin kallan soyaiya tayi masa "menene abin gajiya acikin girkin mutum biyu"

Ajiyar zuciya yayi yatako yazo bayanta ya rungumeta, yayi qasa da muryar sa yace "please kibarshi"

"ya Fawaz Dan Allah kabarni nayi aikina, sokake kahanani kai kuma ka bata kudin ka, menene amfani na da zakaje siyo mana abinci"

Kissing din wuyanta yayi, yasake qasa da muryar sa yace "wai wajan nan har yanzu bai warke bane?"

Zaro ido tayi, takwace jikinta Dasauri "wallahi be warke ba, bari naje daki akwai abinda zanyi" cikin sauri tafice daga kitchen din tabarshi anan

Murmushi yayi ya shafa kansa sannan yadawo falo Yazauna, yana ganinta takoma kitchen din tana aikinta, harta gama tazo tazuba musu cikin flet daya, cikin nutsuwa suka gama cin Abincin, sannan ta maida komai kitchen, kafin tafuto daga kitchen ya kwanta atsakiyar kafet din falon yafara murqususun qarya Kamar gaske, Dasauri Dida ta qaraso wajansa "ya Fawaz menene? Lafiya kake kuwa?"

Idanunsa a runtse yace "Dida cikina ciwo yake min, bayan kinsan meyake damuna, kuma gashi kince wajan bai warke ba"

Gabanta yafadi, cikin in-ina tace "emana, be warke bafa da gaske dane, sannu insha Allah zai daina"

Yace "shikkenan Babu komai idan na mutu ma shikkenan"

Dasauri tace "mutuwa! A a ba yanzu ba insha Allah,"

Yace "yanda nakeji Kamar mutuwa zanyi Dida"

Cikin shagwaba tace "to shikkenan kazo kayi amma Dan kadan gaskiya, kuma idan nace ya'isa to katsaya ahaka"

Dadi yakama Fawaz, sai yau yaqara tabbatar wa Dida yarinya ce, yace "eh nayarda"

Lokaci daya yatashi ya janyo ta jikinsa, dayake yarinya ce kwata kwata bata ganoshi ba, yanda yamiqe lokaci daya Babu wani alamar ciwo, anan falo yafara nuna mata yanda yayi missing dinta, daga baya sukai ciki



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Zaune take akan kujera har yanzu dube dube take cikin wayar tasa, amma bataci karo da number mace ko dayaba, koda yake tayaya zaiyi saving numbers din yanmatansa a wayarsa, haka nan ranta yake mata zafi Tun safe

Shigowa yayi da sallama ta amsa masa batare data kalleshi ba, yayi Murmushi yana zama agefenta, yace "wash Allah, nagaji wallahi"

Tanaci tayi banza dashi

Hannu yamiqa mata yace "bani wayata, dazu na Manta ban dauka ba"

Asheqe tamiqo masa wayar, ya karba yace "Maryam ina abinci"

"Dining"

Abida tace masa kenan, yatashi tsaye yace "wai saboda wata takira wayata shine kike wannan fishin? Ni nayi tunanin ma kin huce, ai shikkenan, yau bazan samu damar da za'a kaini inci Abincin bama, to zanje na Auro wadda takirani awayar, saitazo tadinga bani, tunda naga alama nema kike ki rainani"

Nanma banza tayi dashi, shima yaje yaci Abincin sa hankali kwance, yana gamawa yakara wayarsa akunne Kamar yayi kira yafara cewa "hello hajiya ta, kiyi hakuri dazun wata qanwata ce tadauki wayar wallahi, kinaji na.. Kinsan me za'ayi yanzu....?

Diyana bataji qarshan wayar ba saboda shigewa dakinsa dayayi yarufo kofa, Baqin ciki yakamata, dama ai tasan matar cushe bata daraja, wani kukane yazomata Mai cin rai, tatashi cikin kuka ta nufi dakinsa, duk kayan ta dasuke dakin tafara hadawa tana hawaye


Dariya takama Adam, yayi fuska, sannan yatashi yazo bayanta ya tsaya yace "mekike shirin yi haka maryam? Ina zakije kike daukan kaya haka"

"gidanmu Zan tafi, bazan zauna bakin cikin wata yadameni ba"

"saboda nace Zan qara aure kike kuka? To aikuwa ki shirya, Dan uku suna nan zuwa, Allah yabani damar dazan ajiye mata har hudu acikin gidannan, kuma ni banyi miki alqawarin cewa Zan zauna dake kekadai ba, garama kisa aranki kishiya tana nan zuwa"

Hannunta ta dora akanta tafashe da kuka, ta tsugunna awajan tana kuka bilhaqqi

Adam baisan lokacin da dariya ta kwace masaba, Yazauna agefen gadon yanata dariya yace "maryam, yanzu saboda kishiya kike wannnna kukan?ashe kina sona haka? To kinga ni wasa nake miki"

Kallansa tayi cikin harara, tatashi zata fice daga dakin

Cikin sauri yatashi yariqota, tafara fizge-fizge "nika cikani natafi gidanmu tunda dama baka kaunar ganina"

Yace "maryam nifa wasa nake miki"

"Babu wani wasa, bayan gashinan kashigo daki kana waya da'ita, kacika...... Bata qarasa maganar tataba yahade bakinsu waje daya, diff kakeji Diyana tayi shiru



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Itada Momy ne a kitchen sunata aiki kayaiyakin yin kek ne agabansu Nihla tana hadawa

Adede lokacin yafuto daga dakinsa yana daura agogo a hannunsa, yana sanye cikin suit,sunyi mutuqar yimasa kyau, amma baisaka jacket dinba, a hannunsa ya riqeta, ko wajan Momy bai nufa ba yafita Dasauri, zai qarasa campany wajan Aslam


A kitchen din kuwa Momy ta kalleta "Nihla idan kinsan bazaki iya yin kek dinnan ba Tun wuri nasa ayi muku oder"

Murmushi tayi "Momy kenan, kede zuba ido kisha kallo, da kaina zanyi kek din"

Momy tace "shikam Abba da alama ma ya Manta cewa yau yake birthday, ke kuwa gashi baki Manta nakiba Tun safe kin hana kanki sukuni, nima kin hanani zama saboda wannan bikin birthday ganaki Gana Abba"

Murmushi tayi tace "Momy ai abune na rana daya, idan tawuce shikken"

"hakane, to Allah yabada sa'ah, guda daya zakiyi muku ne ke dashi kokuma daban daban zakiyi?"

Kai tsaye tace "Momy da nawa Zan farayi, idan yanaso shima sai ayi masa"

"wacce irin magana ce wannan Nihla? Nafada miki Abba ya Manta yau yake birthday, ya za'ai kuna gida daya keda yayanki kuma ranar birthday dinku daya aje ana rabe raben wani kek, kiyi muku babba guda daya keda shi, sannan idan masu kayan Decoration din sun kawo kishirya muku komai tare "

Jikinta ne yayi sanyi tace" to Momy "

Momy tafita daga kitchen din, ita kuma tayi shiru tana tunani, Allah yasa ta dinga control din kanta agaban Momy karta ga tana tsanar danta qiri-qiri



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️



Cikin motarsa qirar Rang rover yafuto daga gidan, adede lokacin wani matashi yafaka motarsa, yafuto hannunsa dauke da Wata leda anyi rapping dinta, cikin sauri ya Dakatar dashi yace "yallabai Dan Allah nanne family house na Mazawaje ko?"

Yace "lafiya?"

Matashin saurayin yace "a a babu komai dama maigida nane ya aikoni daga Abuja wajan hajiya Nihla, gift din birthday dinta ne yace ayyuka sunyi masa yawa bazai samu damar zuwaba, amma very soon yana hanya"

Cikin mamaki yafara magana aransa Birthday? dama yau take yin birthday?to ai shima yaune nasa, Waye wannan  daya aiko mata da gift daga Abuja? Haushi ne ya kamashi, yaji wani irin kishi aransa

Kallan matashin yayi yace "i don't no, ka tambayi wasu"

Daga nan yaja motarsa yayi gaba, matashin yayi sa qare yana kallan motar Abba, ikon Allah, shikuma wannan daga tambaya? 🤣
Cikin gidan yanufa yaga maigadi anan yafara tambayarsa



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️



"kaga Abba idan muka saka hannun jarinmu Awannan campany zamu samu riba sosai, saboda shima Babban campany ne ansan shi sosai"

Yana jiran yaji Abba yabashi amsa sai yaji shiru, cikin mamaki ya kalleshi "Abokina mekake tunani ne?"

Nanma yaji shiru, ta'bashi yayi yace "Abba!!"

Cikin sauri yadawo daga duniyar tunanin daya lula, ya kalleshi "Aslam ya akayi?"

Dan qaramin murmushi Aslam yayi "kana nufin kacemin duk wannan maganganun danayi baka jina?"

Kallansa yayi yadaga masa kai alamar hakane

Wani murmushin Aslam yasake yi "meyake damunka haka Abba? Tunanin me kake? Yanzu fadamin menene matsalar?"

Ajiyar zuciya yayi "yanzu Aslam misali idan mace tana Birthday me kake ganin za'a bata amatsayin gift?"

Aslam yayi Murmushi, sai yanzu yagano Inda tunanin Abba yadosa
Yakalleshi yace "um nide aganina za'a iya bata kyautar sarqa idan ranar birthday din tazo saika saka mata, kokuma zobe kakama hannunta kasaka mata, kokuma ka tambayeta abinda takeso, shine ma yafi"

Cikin damuwa Abba yace "zobe, sarqa, kokuma kayan ciye-ciye ai duk sun zama gama gari Aslam"

Aslam ya kalleshi cikin mamaki, lalle Abba yashiga dayawa 🤣

Yace "tome kake gani za'a bata?"

"why not asiya mata Mota? Kamar zatayi murna da'ita"

Aslam yayi dariya yace "gaskiya Abokina Nihla tayima Babban kamu, irin wannan soyaiya haka aiko Nadiya ba'a nunawa itaba"

Memakon yabawa Aslam amsa sai yace "please ka bincika min yanzu, inaso akawota yanzun nan"

Aslam yace "okey" sannan yadauki wayarsa yafara dube-dube, yadago yadubi Abba yace "wacce irin qira kake buqata?"

Kai tsaye yace "Camry"


Aslam yace "angama"



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Suna tsaka da aiki iliya maigadi yashigo yace tanada baqo, cikin mamaki tafuto anan taga Baqon fuska, suka gaisa dashi faram faram, gift din hannunsa yabata yace "gashi daga Abuja, inji ogana, yace kiyi hakuri shima yakusa zuwa"

Murmushi tayi jin daga Inda saqon yake, tasan ya Yusif ne, tace "a a babu komai wallahi, zamuyi waya dashi, qaraso mana ciki kasha ruwa"

Yace "a a Hajiya, inakan hanya ne wallahi, babu damuwa"

Nihla tace "to shikkenan nagode" daga nan takoma ciki

Tana zuwa tabawa Momy gift din nata tace "Momy, ya Yusif ne ya aikomin da birthday gift"

Jikin Momy yayi sanyi, amma dukda haka saida ta nuna murnar ta afili, tace "masha Allah, Allah yasaka da alkhaairi, da alama ko menene aciki zaiyi kyau Kamar kyakykyawar 'yata"

Murmushi tayi tafara kokarin budewa tace "Momy bari mu bude mugani"

Cikin sauri Momy ta riqe hannunta "a a, kibari idan mungama aiki, kinyi wanka, me makeup tazo tazo tayi miki kungama bikin birthday dinku lafiya saiki bude abinki atsinake"

Tace "to Momy,"

Sannan tayi hanyar dakinta da kyautar tata


Dawowa tayi sukaci gaba da aiki, Momy tana ganin tsantsar baiwar da Allah yabawa Nihla, kek din ta cire daga cikin oven tafara yaiyenke gefensa,sannan tadauko wifed cream na ruwa, ta ajiye, tafara neman sauran kayaiyakin buqata

Kallan Momy tayi tace "Momy, wai yaushe Daddy zai dawo ne?"

"kinyi missing dinsa kenan, gobe zai dawo insha Allah,"

Cikin murna tace "to Allah yakaimu"

Momy taga yanda Nihla take murna saitaji dadi, amma itama kanta tana murna da dawowar da Daddy zaiyi saboda tanaso tayi masa maganar matsalar Abba, gara su zauna dashi suyi masa magana akan Budurwar sa Nadiya, yaushe zasuje anema masa auren nata, bazai iyu suci gaba da zama dashi hakaba


Iliyane yasake shigowa cikin part din, fuskarsa dauke da murna, yafara kiranta

Dasauri ta kashe oven din suka futo daga kitchen itada Momy, Momy ta zauna akujera tace "dama ni duk kin gajiyar dani, bari nadan huta"

Nihla ta kalli iliya tace "iliya danme qarfi lafiya kuwa?"

Yace "hajiya kinada wani Baqon ne, gashinan yashigo har ciki, yana compound"

Cikin mamaki tafuto harabar gidan, da wata hadaddiyar mota tayi tozali Ash color, qirar CAMRY, na cikin motar da yaga tafuto yabude shima yafuto, yagaidata tareda miqa mata wats takarda da key din motar yace "gashi inji yallabai"

Jikin Nihla yayi sanyi, yallabai kuma? Waye hakan? Cikin mamaki ta kalleshi tace "please waye ya aikoka?"

Yace "daga campany ne"

Daga nan ya juya yatafi, batare daya sake cemata komai ba

Motar ta qarewa kallo, tayi masifar yin kyau na qarshe, amma waye wannan dazai aiko mata da Mota?

Cikin sanyin jiki tajuya cikin falon su, Momy tace"yanaganki haka jiki a sanyaye, menene? "


Zama tayi kusa da Momy ta miqa mata car key din tace
"Momy Mota aka aikomin dashi"

Momy tace "Mota kuma?"

Daga kai Nihla tayi, Momy cikin sauri tatashi ta leqa taga motar Sabuwa ce dal sai daukan ido take, dole nema ta birge Wanda aka mallaka wa ita

Tadawo wajan Nihla tace "waye ya aiko miki?"

"nima bansaniba Momy, amma gashi harda takarda bari nagani"

Momy tace "duba kam" 🤣

Nihla tabude 'yar qaramar takardar da aka hado da'ita tafara karantawa :

{ _Ina tunanin Babu Wanda_ _ya taba sanar da ke cewa__ _murmushin ki abin so ne ga_ _kowa,duk lokacin da kike yin_ _murmushi yana mayar da fuskar ki tamkar wata_ _fitila mai hasken gaske, You're Beautiful, shiyasa_ _akoda yaushe qwaqwalwata take_ _zana mini kyakkyawar_ _fuskar ki a cikin zuciyata, wadda ta zamo_ _abar kallo a gare ni a_ _duk lokacin da nake_ _zaune ni daya cikin kadaici_ , _murnar qarin shekara._
 *ABBA*  }


Gabanta ne yahau luguden faduwa bayan tagama karantawa, cikin ranta tace ya Abba!

Momy dake zaune ta kalleta cikin matsuwa tace "waye ya aiko miki"?


















Gaskiya banda bakin godewa masu yimin sharhi akan wannan littafin, saide nace Allah yabarmu tare yabar zumunci, inajin dadin yanda kuke sharhi akan DANGI DAYA nagode 🙏🏻










Amnah El Yaqoub ✍️[7/7, 2:00 AM] El Yaqoub: ❣️ DANGI DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub


Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493



41&42


Gabanta sai faduwa yake, yayinda jikinta yayi mugun sanyi tadubi Momy tace "Ya Abba ne"

Ita kanta Momy saida tayi mugun mamaki, Abba kuma? Wannan yaron kuwa yasan meyake shirin janyo musu? Aqasan ranta tabbas tayi murna sosai yar'uwa da siyan motar, koba komai Kamar kansu yafara haduwa ne, amma ganin yanda Nihla tayi tsaye jikinta asanyaye yasa tayi Murmushi tace "Ah masha Allah, gaskiya Abba na ya kyauta, to menene kuma kikai shiru banga kina murna ba?"

Murmushin yaqe tayi  "Momy ya Abba fa nace miki "

" aina jiki Nihla, naji abinda kika fada, to menene kuma Dan yayanki yasai miki Mota? Dama ai acikinsu shine baiyi miki Babbar kyauta ba tunda kika zo gidannan, kisaki ranki kije kici Gaba da aikin ki, idan yazo sai kiyi masa godiya"

Sai yanzu tayi wata irin ajiyar zuciya tace "to Momy"

"kin fadawa su Ilham kuwa?"

"eh Momy nafada musu, harsu ya Usman ma"

"to shikkenan, kije kici Gaba da aikin ki kiyi sauri Dan Allah"

Nihla na wucewa Momy ta kalli key din motar dake hannunta, Innalillahi wa inna ilaihir raju'un... ta dade tana zargin Abba nason Nihla, gashi yau ta qara gani da idonta, kome ya rubuta mata ajikin takardar? 🤔 Su suka sani, abinda tasani de shine itace mace ta farko dazata ziga Nihla akan karta kuskura ta amince wa Abba dukda shine danta mafi soyuwa acikin zuciyarta, Alhamdulillah da Daddy zai dawo gobe.


Tana aiki a kitchen amma zuciyarta tana wajan wannan kyauta

 (ina tunanin Babu Wanda ya taba sanar da ke cewa murmushin ki abin so ne ga kowa...)

Kalamansa suka fado mata arai, ta tsaya da aikin tayi shiru, yanzu shi ya Abbanne yaturo mata da wannan kalaman?To idan kyautar Mota Momy tace bawani abu bane, shikuma wannan kalaman fa? Amatsayin me zata daukesu?

Kanta datafe tace "kaiii ya Allah!" sannan taci gaba da aikin, tsaf ta shirya kek din yayi mutuqar kyau, Babban kek ne sosai data hada wiped cream fari da ja, tayi adon dasu, ta yankashi daga tsakiya tasaka cream din Wanda tadan disa jar color aciki, Sannan tasake rabashi tasaka farin kawai batare datasa komai ba, yanda idan ka yankashi zakaga cikin kek din yayi kaloli hawa biyu, sama fari, qasa ja

Momy tashigo kitchen din tana yin tozali da kek din tace "kai kai kai, masha Allah, amma gaskiya wannan kek din yayi kyau sosai yata, babu wanda zaigani yace kece kika yi"

Nihla tayi Murmushi kawai

Momy tace "yabaki rubuta sunaba? Ki rubuta sunanku ajiki, amma kifara saka naki sunan, sannan na Abba"

"to Momy"

Sauran cream din ta dauka ta rubuta Happy birthday Nihla & Abba

Momy tace "yawwa kinga saiya qarayin kyau sosai, kije kiyi wanka wadda zata miki kwalliya tana hanya"

Hannunta ta wanke tace "to Momy,"
sannan tafice daga kitchen din, Momy kuma ta kira Adala akan shirya abincin dazasuci anjima



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Wanka tashiga tayi, tafuto daure da towel tana goge jiqaqqen gashin kanta Momy tashigo ta leda a hanunta tace "to gashi inji farouq yace ga tasa kyautar nan"

Cikin murna ta karba tabude ledar wani kwali ne Mai kyau babba, tabude  taga riga me bala'in kyau ta bayyana, me launin pink,rigar daga qasan ta abaje take sosai gawani uban stone da taji , cikin murna ta rungume Momy, tace "Momy kiga rigar wallahi tayi kyau"

Momy tayi daria "yau kam aini ina ganin ikon Allah awajan wannan yan'uwan naki, kingani ko, wannan ne abinda nake fada miki dangane da kyautar da Abba yayi miki, shiyasa nace ki saki ranki"

Nihla cikin ranta tace Momy kenan Dan baki karanta abinda yake cikin takardar bane

Cikin sauri tashafa Mai da turere sannan tazura rigar, tajuya bayanta tace "Momy zugemin zip din"


Momy tarufe mata,rigar ta karbi jikinta sosai, breast dinnan sun futo sosai masha Allah

Momy tace "rigar kuwa tayi miki daidai Kamar danke akayi"

Zama tayi tafara gyara gashin kanta tace "wallahi Momy tayi kyau sosai"

Momy tafuto daga dakin, itama tana gama gyara kanta tafuto tasamu wata Babbar Cardboard paper ta yanki dede yanda takeso sannan ta rubuta Happy Birthday Nihla da biro sannan tadinga bin wajan biro din tana liqa stone's ajiki fari da baqi, dakuma ja, sai rubutun biro din yabuya sai stone din kawai kake gani

Tafuto farkon kofar dazata kawoka cikin falon ta manna anan, Momy de tazama yar kallo sai bin Nihla take da kallo

Mai kwalliya ce tashigo tareda temakon iliya, nan suka baje afalo tafara yimata kwalliyar tagani tafada, tunma kafin agama Momy tayaba, da aka gama kuwa ita kanta maiyin makeup din saida tayi mata picture, gawani irin Style datayi mata na gyaran gashi, Momy kawai masha Allah take fada aranta, tabbas Abba ya cucesu, Inda ya aure ta ko banza wata rana zata haifa musu yara kamarta

Momy ta biya Mai kwalliyar kudi masu yawa sannan tasa driver yamaidata, ita kanta tasan yau tayiwa yar gata kwalliya



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Da yamma su yaya Usman sukazo,gaba dayansu zaune suke afalo, ankawo musu abinci kowa yanaci
Futowa tayi suka gaisa gaba dayansu kuwa Babu Wanda bai yababa, Usman yana murmushi cikin ransa yana yiwa qaninsa fatan samun Nihla

Momy tasa Adala ta shirya falon da kek din dakomai, sannan ta shirya lemuka agefe, falon yaqara tsaruwa yayi kyau sosai

Direban Ilham ne yakai ta gidan Dida da Diyana suka daukosu suka Taho gidan gaba dayansu, zuwansu ne yasa Nihla tatashi sukai cikin dakinta dasu

Aliyu yace "Momy karfe biyar saurafa, me take jirane?ta yanka kek din mana muwuce ko"

Momy tace "lalle Aliyu yazama dole acika tara, kamanta da birthday din Abba kenan"

Aliyu yace "yasalam!, wallahi Momy namanta, yanzu kam nasan Wanda muke jira"

Usman yace "ni dama ban Manta ba, nasan yau Abba yake birthday, saikuma da Nihla takirani ta sanar Dani cewa itama tana birthday"

Farouq yace "um yau zamu ga yanda d'an miskilin Momy zai yanka kek, ko zai bawa Nihla,? Momy kina ganin bata kiwa?"

Tace "kaifa farouq haka kake dajan magana, saikace abokinka?"

Dariya yayi yace "Momy kinsan me, wallahi rannan nakama Abba yanata kallan pictures din Nihla, Kamar fa yana ciki"

Usman yace "nifa na dade da ganewa, kune de baku fahimta ba amma yanda yake kallanta ma ai ya'isa mutum yagane akwai wani abu"

Ajiyar zuciya tayi "Usman Nikaina nasan Abba yanason Nihla, amma bazan yi masa magana ba, zan zuba masa ido naga gudun ruwansa, ban qara tabbatar wa yana sonta sosai ba, sai yau daya aiko mata da Mota wai shine gift dinsa"

Gaba dayansu suka kwashe da dariya, Aliyu yace "lalle Abba, ko'itace wannan Sabuwar motar damuka gani a compound?"

Momy tace "itace Aliyu, kuma shi kansa yasan cewa abinda yake shirin yi bazai taba iyuba"

Usman yace "Momy saboda me? Meyasa zakice haka? Abba yanason ta"

"Usman ka Manta abinda Abba yayiwa Nihla ne?"


Yace "nasani Momy, abinda yafaru abaya yariga yafaru Momy, Abba da Nihla duka yaranki ne, Kibashi dama yanemi yafiyarta suyi aurensu"

"aure fa kace Usman, Hmm to ai ko Nihla ta amince saina zigata tarabu dashi, waye yayi wasa da damar sa?"

Farouq yace "Amma Momy munason kasancewar ta acikin mu ne shiyasa"

Shima Aliyu yace "Momy ni ina ganin abarshi da yarinyar yanemi yafiyarta yafi, ubangijin daya haliccemu ma muna masa laifi yayafe mana, ke kanki zakiji dadi ace Nihla ce matar Abba, akan yadauko wata yakawo miki, haba Momy kiduba mana"


Cikin fishi Momy tace "toku hademin kai saboda qaninku, yayi mata laifi kuma saiya gane kuskuren abinda ya aikata mata"

Usman baice da'ita komai ba yatashi yafuto daga falon yana kiran wayar Abba, ya sanar dashi cewa sutaho gida yana nemansa, bai fada masa cewa shi suke jira yazo a yanka kek ba



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Diyana ta kalleta "Nihla gaskiya kinyi kyau sosai masha Allah, Kamar amarya"

Cikin sauri tace "agidan ya Yusif ba, bari na kawo muku lemo, babu komai a fridge dina"

 fita tayi tabarsu

Ilham ta kalli Dida da Diyana tace "wallahi akwai abinda nake zargi, kunsan Allah ya Abba naga alama yanason Nihla, bakuga abinda yamata ba rannan"
Nan take ta basu labarin komai

Adede lokacin Nihla takawo musu lemuka ta ajiye sannan tazauna

Diyana tace "aini Ilham haka nakeso, ya Abba ya haukace akan Nihla, yanda zataji dadin juya shi son ranta"

Ta kalli Nihla tace "wallahi idan nice ke ko, riga da wando zanyi ta sakawa a gidannan tunda momy ba magana zata mikiba, kidinga daukan hankalinsa"

Girgiza kanta tayi "bazan iyaba Diyana, dane da kaina yake rawa nake iya yimasa komai, amma yanzu ni, bazan iyaba, ina fata de yasoni,shima ya dandana abinda naji a raina, yaji irin quncin danaji a lokacin daya qini, nikuma daga baya sainayi aure na"

Dida tace " gaskiya Nihla Kamar be kamata ba, tunda kowa yafara fahimtar yana sonka kibarshi da wannan ma ya'isa, meyasa zakike masa fatan yaqara sonki duk dan yaji abinda kikaji kuma daga qarshe ki auri wani bashi ba?

Nihla tace "Dida kenan, bakisan abinda naji bane, bakisan wahalar da zuciyata ta fuskanta ba, to wallahi rannan har kuka nayi, saboda taqaici na daya zaije wajan wata zance, hakan yana nufin bayasona kenan, nikuma nafiso yasoni ta yanda Zan nuna masa kuskurensa, sannan daga qarshe na auri ya Yusif, Kamar yanda shima yaqini yace zai Auro wata,da kam naso ya Abba Kamar hauka,kuma naji dadin yanda kukace yafara sona saboda lokaci yayi da zanqi shi na auri bare, Kamar yanda yaqini abaya yaso bare, amma a yanzu soyaiya ta kacokam takoma kan ya Yusif, shi nakeso, kuma shi Zan aura insha Allah"

Ajiyar zuciya Ilham tayi "to munji, komai de Yusif Yusif, to munji, saura kuma anjima kikasa bashi kek din" 😏

Diyana tace "shikkenan Nihla, ni dama bazan miki dole akan ya Abba ba, saboda naji ciwon abinda yamiki nima, amma yanzu de tunda taro ne yahadamu anan, Dan Allah kiyi hakuri Karki bamu kunya, kiyi hakuri farin ciki ne yahadamu, kuma shi muke fata yarabamu, Kibashi kek dinnan a baki please "

"abakifa kikace Diyana, saikace wani ya Yusif"

Dida tace "ai roqonki mukayi, please"

Shiru tayi musu kawai, domin kuwa bata tunanin zata iya abinda suka nema

Ilham tace "zamu ga kyautar da ya Abba zai miki"


Nihla tace "Hmm gatacan kun ganta awaje"

Gaba dayansu sukace "Kamar ya"

Tace "Sabuwar motar datake compound shine ya aikomin  dazu"

Gaba dayansu suka hada baki wajan fadin "Mota!"

Dida tace "um Ilham nayarda da maganar ki"

Diyana ma tayi daria tace "gaskiya nima nayarda yanzu, tab Mota! saikace Wanda kika kai masa budurci lafiya" 🤣

Nihla tace "Diyana banason Wulaqanci, ni wallahi da niyata nabashi key dinsa, amma wai sai Momy tace idan yazo namasa godia, ni kuwa ya Abba mezai fadamin"

Ahankali Momy taturo kofar dakin tashigo tace "toku kowa yazo ku ake jira"

Fita sukai gaba dayansu zuwa falon, sai fira suke cikin farin ciki

Da niyya Diyana ta kalli su ya Usman tace "ya Usman ba yanzu zata yanka bane?"

Kafin Usman din yabata amsa farouq yace "sai Abba yazo, suna hanya, yana zuwa zasu yanka tare"

Dariya ta kamata, Wato ta lura yaran Momy ma gaba dayansu jona Nihla da Abba sukeyi, tatashi tsaye tace "to mufara yin picture kafin yazo"





❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Daga cikin motar suka futo shida Aslam, suna tafiya ahankali cikin aji, hannunsa daya yana cikin aljihun wandon suit dinsa,dayan hannun kuma yana riqeda wayarsa da kuma jacket dinsa

Ya kalli Aslam yace "kana ganin wannan kyautar kuwa zata birgeta?"

Aslam yace "sosai ma kuwa, kasan mata da Mota, sannan motar tayi kyau sosai, dole zatayi mata kyau Idan tahau"

Jinjina kansa yay"to amma wannan kalaman fa?"

Murmushi Aslam yayi" haba Abba, ai wannan ma nasan zasufi birgeta fiyeda motar, zasu tsaya aranta nake fadama, haba paper nawa muka 'bata akan tsara kalaman? "🤣


Murmushi yayi shima Bece komai ba, cikin ransa yana fatan hakan, qarasowarsu part din keda wuya sukaci karo da rubutun da Nihla ta liqa awajan

Aslam yace" wow wow, Abba waye yayi mata wannan abun? "

Murmushi yayi"bansan waye yayi ba, batare nake dakai ba"

Aslam yace "a a, Abba kenan, Abba na Nihla"

Dariya sukayi suka qaraso cikin falon, ba sukai ga shigowa ba kuwa ya farouq ya kashe wutar falon baki daya

Ahankali Abba yace "subhanallah"

Kunnawa yayi haske ya gauraye falon, da'ita yafara yin tozali, cikin ransa yace " Beautiful"

Itama ana kunna wutar falon idonta yasauka akansa, kalamansa suka fara dawo mata, nan take tayi gaggawar janye nata idon, tayi watsi da kalamansa daga qwaqwalwarta

gaba dayansu suka hada baki suna fadin " Happy birthday to you, happy birthday to you, happy birthday happy birthday happy birthday to you... Suna qarasawa suka fara tafi kowa yana daria

Qamewa Abba yayi awajan yakasa motsi, ashe shirin da ake musu kenan shiyasa ya Usman yace yataho gida?


Ya Aliyu yace "to bamuda lokaci, azo ayanka kek, wannan yaron duk ya bata mana lokaci"

Dariya sukai gaba dayansu, Nihla de kanta yana qasa bata cewa komai

Ya Usman ya kalleshi yace "to Abba a qarasa mana, Aslam farouq Muje da Allah"

Cikin aji ya qaraso gaban kek din, mamaki duk yagama kamashi, Diyana ta janyo Nihla ta kawota kusa dashi, ita kuma ta tsaya daga hannun hagun ta

Sunkuyawa tayi zata yanka kek dinta, ya Usman yace "Nihla ya haka,? tsaya ayi pictures tukun"

Ya kalli farouq yace "farouq ayi musu pictures"

Ya farouq yafara daukan su pictures, gaba dayansu sunyi bala'in birge kowa, danma Babu wani Fara'ah da Nihlan take

Nihla kuwa jinta akusa dashi yasa duk ta takura, gashi sai binta yake dawani mayan kallo

Aliyu yace "Nihla ku yanka kek din mana, me ake jira"

Ahankali ta sunkuya zata dauki wuqar yanka kek din, adede lokacin shima ya sunkuya, yakai hannu takai hannu saijin Saukar hannunsa tayi akan nata hannun, gashi duk sun sunkuya hakan yasa dogon gashinta zubowa ta dede fuskarta, kallan hannunsu yayi, sannan ya juya ya kalleta, itama kallansa tayi tana masa nuni da idonta akan yadauke hannunsa amma saiya shareta Kamar bai ganeba

Hasken camera kuwa sai aiki yake awajan, saboda Babu Wanda basu birgeba, kowa zaiyi tunanin wasu shahararrun masoya ne

Ahankali ta motsa hannunta suka yanka kek din tare, sannan ta dago, shima yamiqe tsaye Ahankali

Bakinta zatakai kek din, Diyana tataka kafarta alamun tabashi amma sai tayi mursisi da'ita, takai kek din cikin bakinta

Aslam daya harde hannu aqirji yana Kallansu cikeda birgewa sai lokacin yayi magana yace "no!, Nihla Kibashi mana"

Cak ta tsaya da hannunta, ita bataci ba, ita bata bashi ba, ahankali ta juya tana fuskantar sa, tadaga kanta ta kalleshi saboda yamata tsawo, gani tayi idonsa akanta ko kunyar jama'ar wajan bayaji

Ahankali tadaga hannun Kamar bataso ta nufi bakinsa dashi, shikuma ganin Kamar zata bashi kunya agaban qannansa su Diyana yasa cikin aji yadora duka hannunsa biyu akan nata, wani irin zirrrr yaji ajikinsa sakamakon laushin dayaji hannunta yana dashi

Ahankali yakai hannunta bakinsa yakaryi kek din Dan kadan yaci, sannan yasake kai hannunta bakinsa yayi kissing bayan hannun nata,sannan yasaki hannun

Farouq  dayaga pictures bazai yi ba saiya koma yimusu vedio kawai 🤣

Diyana datake ziga Nihla akan tabawa ya Abba kek abaki sai tayi shiru tana ganin ikon Allah, tana ganin yanda ake bawa masoyi kek, ita tana ganin idan an bashi abakin ma yayi, ashe shi nasa salon ya dame nasu

Shikuwa bejira komai ba ya yanko wani kek din Dan qarami yanufi bakinta dashi, qin bude bakin tayi, yazuba mata ido yana kallan Dan qaramin bakinta yace "Open your mouth"

Ahankali tabude bakinta yasaka mata kek din, gaba daya jikinta yayi sanyi,maganar su Ilham de tazama gaskiya


Yana saka mata duk falon aka hau tafi, sannan kowa yazo yayanki yanda yakeso, jiki a sanyaye Nihla ta zauna akujera, ta kalli ya farooq tace "ya farouq katuramin pic din ta WhatsApp  gaba dayansu, harda Wanda nayi rannan a wayarka"

Cikin mamaki yace "wayata? No awayar Abba kikayi, yaturo miki"

Shiru tayi bata sake cewa komai ba

Momy tafuto daga daki tace "a a, har angama kenan naga kowa ya yanka yanaci"

Dariya sukai dukansu, cikin shagwaba Nihla tace "Momy shine kikaqi zuwa"

"in banda abinki Nihla abinku na yara mezai kawoni, fatana nide Allah yarayamin ku"

Gaba dayansu sukace amin

Abba ya kalleta,"Momy thank you, kek din yayi dadi sosai"

Murmushi Momy tayi tace "ai Nihla ce tayi da kanta, ita zakayi wa godia"

Wani irin dadi yaji acikin ransa, ya juya Yakalleta Bece da'ita komai ba, Sannan yatashi yace "nagaji"  yakalli Aslam yayi cikin dakinsa, shima Aslam din yagane nufin sa danhaka yabi bayansa cikin dakin hannunsa dauke da Lil Abba


Saida su Dida sukaci sukasha sannan sukai shirin tafiya, amma ko waccensu da magana a bakinta, sai dariya sukewa Nihla ita kuwa ta sharesu

Saida sukai sallah sannan suka tafi, suma su ya Aliyu kowa yatafi, Momy tasa Adala tafara gyara wajan, ita kuwa Nihla dakinta tashige tazauna agefen gadon ta tana tuna abinda ya Abba yayi mata, idan tatuno yanda yayi kissing hannunta saitaji gaba daya tsikar jikinta tatashi

Haka tashiga wanka tafuto tayi sallah, tasaka kayan bacci masu kauri, sannan tazauna atsakiyar gadon tatafi duniyar tunani, yakamata ace ya Yusif yazo ko yaya ne taganshi, zamanta agidan nan tana hango yar qaramar qura, kowa cewa yake ya Abba yana sonta, Shin idan Momy da Daddy sukaji wannan batun yaya zasu dauki maganar? Su Ilham ma dasuke DANGI DAYA dashi suna bashi goyon baya to inaga iyauensa? Tasan cewa suma sai sunfi kowa murna, kuma da kunya tana zaune acikin gidansu taqi dansu na cikin su,abinda kunya, saide kuma yanda takeji aranta ko duniya da abinda yake cikinta ya Abba zai bata bazata iya auren saba kwata kwata, baba kansa yasan cewa ya Abba baya sonta, amma ya Yusif yayi mata komai, yaso ta a lokacin da Abba yagujeta

Saboda haka Tun ana yad'a jita jita a family gara tayi maganin abun Tun kafin ya furta mata kalmar soyaiya

Hannunta tadaga sama tayiwa Allah godia daya saka soyaiyar ta acikin zuciyar Abba, ko banza zaiji abinda taji abaya

Gift din ya Yusif tafara budewa

Bude ledar keda wuya  kwalin Sabuwar waya qirar iphone ya baiyana
Murmushi tayi tace "Allah sarki ya Yusif"
Lokacin dazai siya mata waya tatuna, ya tambyeta wacce takeso tace iphone amma a lokacin kishi ya hanashi siya mata, shine sai yanzu kenan yasiyo mata

Kwalin wayar ta dauke anan taga wani kati Dan qarami Mai kyau sai sheqi yake, saikuma rafar kudi yan dari biyar guda daya, Wanda ta tattabar da cewa rafar dubu hamsin ne

Katin tabude taga rubutu aciki Mai kyau, nan take tafara karantawa :

_Alkawari ne na dauka, ba zan taba barin damuwa ta wanzu_ _a cikin zuciyar ki ba matukar muna a tare da_ _juna, ina fatan nan da dan wani lokaci kadan zaki_ _tabbatar da hakan bayan kin zamo  mallakina kuma mata_ _a gare ni, ke kadai zuciyata ta amincewa Nihla,naso_ _nazo naciyar da mata ta kek da kaina amma aiki yamin_ _yawa, dafatan zakimin uzuri, Happy birthday_


Tana gama karantawa tayi kissing katin, tace "i luv u ya Yusif"


Wayarta tadauka ta kirashi, ringing din farko yadaga, cikin farin-ciki tace "ya Yusif, irin wannan gift haka, gaskiya naji dadi nagode sosai, i luv u so much dear"

Murmushi yayi tareda lumshe idonsa "saqona ya'iso gareki kenan"

"yes, yazo, kuma wayar tamin kyau sosai, naji dadi"

"da gaske kinji dadi?"

"emana ya Yusif, naji dadi sosai"

Yace "to tayaya Zan gane hakan?"

"mekakeso nayima Wanda zaka gane?"

Yace "um think about it"

Fari tayi da idonta Kamar yana ganinta tace "to idan kasamu time kasamu baba kayi masa magana akan soyaiyar mu, kaga shikkenan dana gama service sai bikinmu "

Sosai Yusif yayi mamakin kalaman ta, Murmushi yayi yace "Really?"

Tace "yeah"

Murmushi yasaki har tana jiyoshi sannan yace "gaskiya naji dadi, nagode sweethrt,kuma zan sameshi a gobe muyi maganar, zan fadawa Abbana ma, but yanzu yaya taron?"

"Alhamdulillah ya Yusif, komai yayi daidai, rashin daidai dinsa shine baka nan"

"to kiyi hakuri, tuba nake, idan nasamu time zaki ganni verry soon"

"to shikkenan ya Yusif thnks"

Yace "yr wlcm"

Daga nan sukai sallama.


Momy ce taturo dakin tashigo, cikin murna Nihla tanuna mata abinda Yusif din ya aiko mata dashi

Murmushi Momy tayi, tazauna abakin gadon, saide wannan ne karon farko da taji tausayin Abba aranta, saboda yanda taga Nihla tana farin-ciki akan kyautar da saurayinta yayi mata, saide Babu yanda zatayi, dole sai Abba yagane laifin dayayi abaya, bazata biyewa son zuciya dason datake wa danta ba

cikin nutsuwa tace "nagani Nihla, Yusif yayi kokari sosai, amma dafatan de dashi za'ayi ko 'yar Momy?"

Ahankali tadagawa Momy kai cikin kunya

Momy tayi Murmushi "to shikkenan, idan kunyi waya dashi kifada masa momynki tana gaishe shi, sannan kifuto muci abinci, goma saura yanzu"

Ahankali tace "to Momy"

Falon suka futo itada Momy, yana zaune shi kadai a dining yana daddanna waya, tunani yake aransa meyasa har yanzu Nihla bata sakewa dashi tayi masa magana Kamar da? Bayan kuma tasan cewa shi bawata magana yakeba dama can

Yayi tunanin dazu da farouq yace pictures dinta suna wayarsa zatace yatura mata, amma sai yaji tayi shiru, yarasa me zaiyi mata tadinga sakewa dashi suna magana Kamar da

Zuwansu wajan ne yakatse masa tunanin dayake, Nihla ta kalleshi yana sanye da jallabiya fara qal wadda ta karbi jikinsa, sumar kansa ta kwanta luf tana sheqi gwanin sha'awa, hankalin sa yanakan waya

Zama sukai, Momy tace "Nihla zuba mana Abincin"

Tashi tayi tafara zuba musu, ahankali ya ajiye wayarsa yazuba mata ido yana Kallanta, rigar jikinnata tayi mata kyau,wadda ta kasance marar hannu,kyakykyawar fatarta ya kalla tayi luwai luwai da'alama zatayi laushi

Momy ta kalleshi taga ya zubawa Nihla ido, duk abinda take akan idonsa, tunani tafara to kode Abba ya Manta tana wajan ne yakebin 'yarta da wannan mayen kallon? 🤔
ahankali ta dauke kanta

Nihla tazuba wa kowa sannan tazauna kowa yafara cin Abincin
Suna tsaka dacin Abincin yadubeta yace "please inason Tea"

Dago daradaran idanunta tayi ta kalleshi batare da tace komai ba tatashi ta janyo flaks din dake gabansa tadauki cup tazuba suger kadan sannan tasaka madara

Momy ta kalleta, gaskiya ne Nihla ta karanci Abba tas, Inda wanine zai hada masa Tea dinnan da tuni yayi magana yace kar asaka suger dayawa, amma ita ko magana baiyi mata ba saboda yasan tasani

Ruwan zafin tafara tsiyayowa by mistek hannunta yazame Ruwan zafin yazubo ahannunta

Flask din ta ajiye dasauri tace "auch..." tafara yarfe hannunta tana runtse idonta

Spoon din hannunsa yasaki yatashi dasauri ya nufeta, yanda take girgiza hannun ne yasa qirjinta suke rawa Wanda batasaka musu ko 'yar breziya ba, numfashin sane yafara kokarin daukewa, badan tana cikin jin azabar zafi ba da Babu abinda zai hanata ganoshi, jiyake Kamar ya fuzgota jikinsa
Ahankali yadora hannunsa akan nata yariqe hannun data qone din, gaba daya damuwa ta baiyana a fuskarsa, hannun yakai bakinsa yafara hura mata iska awajan,runtse idonta tayi yace "wayyo Momy hannu na"

Kallanta yayi yaga idonta yacika da qwallah, yace "Sannu, kidena kuka"

Hannun yakalla dogayen yatsunta masu kyau sunyi jajir, yasake hura mata iska awajan

Cikin shagwaba tace "wash!"

Dago kansa yayi yazuba mata manyan idonsa, rakinta yana birgeshi, haka yatsira mata ido yana Kallanta ga hannunta yariqe cikin nasa

Momy tadena cin Abincin ta tsaya tana kallan ikon Allah 😱, kode sun Manta tana wajan ne? Lalle wannan Inda ace Nihla tana sonsa Kamar yanda yake sonta a yanzu, Toda Babu abinda zai hana su hanata zaman gidan mijinta, irin wannan rashin kunya a gabanta har ina!🤦🏻‍♀️Ita Nihla yanda take shagwabar saika rantse da Allah da niyya takeyi, shikuma gaba daya ya susuce akanta yasakata agaba Kamar zai maida ta cikin jikinsa

Gyaran murya tayi, Abba yajuyo ya kalleta batare daya cika hannun Nihlan ba, itama sai a lokacin tabude idonta ta kalli Momy

Momy tace "jeki saka qanqara akan hannun, zakiji yadena zafi, Allah yasawaqe"

Cikin sauri yace "bari a dauko"

Yasake kallan Nihla yace "Sannu" sannan yasaki hannun nata yawuce kitchen batare daya jira ta amsa masaba
Tausayinsa yad'an kama Momy yanda taga gaba daya ya rikice, to idan yaji akwai wanda Nihla take tare dashi yaya zaiyi kenan?

Tana  tsaye sai turo baki take gaba yadauko qanqarar yadora mata ahannun sannan ta danji dama dama

Suka zauna kowa yayi shiru, Momy tadubeshi, taga ko kallan Tea din beyiba, magana tafara aranta, yasa yarinya tahada masa abu, a dalilin haka ta qone amma baima kula Tea dinba, tace "Abba kasha Tea din mana"

Bece da'ita komai ba, kawai de ya girgiza kansa 🤣

Ajiyar zuciya tayi tace "nikam na qoshi, saida safen ku,"

Ta kalli Nihla tace "idan hannun be daina zafi ba koda cikin dare ne kizo ki fadamin saina tasoshi yakaiki asibiti"

Abba yayi Dan qaramin murmushi saboda yasan sarai dashi take

Wajan yarage saisu biyu kawai,kowa yayi shiru Babu me magana, ta dago ta kalleshi ta kawar da kanta, shikam, zuba mata idanu yayi, wani irin dadi yakeji cikin ransa, besan cewa ya takura taba, dazai matsa da tafi cin Abincin yanda ya kamata, tunda shi baci zaiyi ba

Bata tsammata ba taji yace "kek yayi dadi"

Ahankali batare data kalleshi ba tace "thank you"

Daga nan tayi shiru, tana tunanin maganar Momy da tace idan yadawo tayi masa godia akan motar daya bata, tarasa tayaya zata gode masa, kwata kwata ma batasan tuno da maganar motar, saboda wannan takardar daya hado mata da'ita tarasa gane Inda yadosa, shi ya Yusif dasuke soyaiya tayi masa godia yanda ya kamata amma shifa ya Abba?

Ahankali tadago kanta ta kalleshi, karaf idonsu yahadu, tayi saurin janye nata idon tace "nima... Nagode sosai"

Murmushin  yayi, zaiso ace taci gaba da magana saboda yana jin dadin yanda Dan qaramin lips dinta suke motsawa dan haka yace "for what?"

Kai tsaye tace "motar daka turomin"

Memakon yayi mata maganar motar saiya jefo mata tambaya "Can you drive?"

Tace " i can't, but yaya farouq saiya koyamin"

Shiru yayi na Tsawon mintuna, farouq, farouq, karfa tasa yafara kishi da yan'uwansa, ya kalleta yace"dole sai shi?"














Amnah El Yaqoub ✍️
[7/7, 11:07 PM] El Yaqoub: ❣️DANGI DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub


Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493



43&44




Kanta tsaye tace "ehmana"

Fuskarsa ta nuna alamun damuwa yace "no, kibarshi, zan koya miki"

Kallansa tayi, lalle ya Abba yasakko, ahankali tace "nagode, amma kabarshi"

Tsam ta miqe daga wajan, Dan taga alamun zancen yakeso, kawai yazo yasa ta agaba, hanyar dakinta tanufa batare data qara masa magana ba, shima binta yayi da kallo, saida yaga tashige dakinta sannan yasaki ajiyar zuciya

Shima dakinsa yatafi ya kwanta, tunani yafara akan tayaya zai shawo kanta? Har tausayin kansa yakeji wani lokacin, tana bashi irin wannan amsar tayaya zaiji qwarin gwiwar fada mata abinda yake ransa?

Har qarfe biyu da rabi yakasa bacci yana tunanin ta, yaji haushin kansa yafi a qirga, Inda ya amince da'ita Tun farko daduk haka bata faruba, ganin tunanin Babu Inda zai kaishi yasa yatashi yanufi toilet yadauro alwala yazo yafara fadawa Allah kukansa

Bayan ya idar ya kashe wutar dakin ya kwanta, bai taba barin wayarsa akunne ba idan zaiyi bacci, koda yaushe kashe ta yake idan zai kwanta, amma yau akunne yabarta, rigar jikinsa yazare dagashi sai boxer yaja fillo ya rungume a qirjinsa sannan yadau wayarsa yana kallan pictures dinta, ahaka bacci ya daukeshi.

Dadewar dayayi beyi bacci bane yasa daya koma bacci bayan sallar asuba, yajima yanayi, bai tashi ba sai wajan shadaya

Wanka yayi yafuto domin ya gaida Momy,ganin su yayi gaba dayansu zaune afalo,ga Daddy ga Momy ga kuma Nihla agefen Daddy tana sanye da Jan leshi Wanda akayi mata dinkin riga da siket amma wuyan rigar irin budaddan nan ne da'ake yi yanzu

Cikin murna ya qaraso Yazauna ya gaida Daddy da Momy

Itama Nihla fuskarta Babu yabo Babu fallasa ta gaida shi ya amsa cikeda kulawa

Daddy yace "Tun karfe takwas nadawo momyn ku tace baka tashiba"

"eh Daddy, ban kwanta da wuri bane shiyasa"

"to Alhmdlh, kuma bana nan sai qanwar ka tazo service harma kasiya mata Mota"

Shiru yayi Bece komai ba
Daddy yace "to Allah yasaka da alkhaairi, Allah yabar zumunci" 🤣

Ahankali yace "Amin"

Tashi Daddy yayi yakalli Momy yace "idan yagama break fast ki turomin shi"

Momy tace "to Alhaji"


Bayan yagama cin Abincin kuwa Momy ta turashi dakin Daddy, sannan itama tabi bayansa, Nihla kuwa kwanciya tayi tana daukan remote

Zaune yake agabansu kansa aqasa, yarasa dalilin wannan kira, Daddy yadubeshi yace "Abubakar Momynka ta sanar Dani rashin lafiyar dakayi kwanaki harma da abinda likita yace"

Abba najin haka cikin ransa yace Innalillah.., yayi shiru Kamar ruwa ya cinye shi

Daddy yaci gaba da fadin "nadade inama kallan marar lafiya ashe ba haka bane kalau kake tunda gashi har kana rashin lafiya akan haka, ina ita yarinyar dakace kanaso din take, inane gidansu sai Muje ayi magana guda daya, ka dade da sanar damu cewa kana sonta, amma maganar aure kayi shiru"

Shiru Abba yayi, idonsa yayi jajir, ga kunyar iyayen nasa dayakeji Ahankali yace "Daddy tayi aure"

Cikin sauri iyayen suka kalleshi, Daddy "to shikkenan Allah yakiyaye gaba, sai kayi kokari kasamo wata ka aura, bazai iyu kaci gaba da zama da rashin lafiya ba"

Jinjina kansa yayi yace "insha Allah Daddy"

"zaka iya tafiya"

Ahankali yatashi yafuto daga dakin, ta gabanta yazo yawuce yashige dakinsa, itade Nihla taga shigar sa daki Kamar yana cikin damuwa, tabe baki tayi taci gaba da kallonta



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️



Bayan sati daya tana kwance tana bacci da weekend kasancewar bazata ko'inaba
Wayarta ce tahau ruri cikin magagin bacci takai hannu tadauki wayar cikin sexy voice tace "Hello"

"Baby na kina bacci kenan"

Tace "Um"

Murmushi yayi "to albishirinki"

"goro ya Yusif"

"yau ina kan hanyar zuwa naganki, aide adress din dakika taba turomin kina nan ko?"

Bude idonta tayi "ya Yusif da gaske kake zakazo?"

"Yes, yau zanzo insha Allah, yanzu hakama wanka zanyi nabiyo jirgin dazai tashi 12"

"wayyo ya yusif, mekakeso na shirya ma?"

"Karki wahalar min da kanki, kiyi zaman ki kawai"

Murmushi tayi, amma Babu yanda za'ai zaizo takasa shirya masa wani abu

Daga nasa bangaren yace "me kikeso nataho miki dashi?"

"mamy ya Yusif, ita nakeso, nayi missing dinta"

Murmushi yayi yace "tunda zaki ganni ai Kamar zaki ganta ne"

"to shikkenan ya Yusif sai kazo"

Tashi tayi taje ta sanar da Momy, nan da nan kuwa Momy ta aiki Adala kasuwa tasiyo musu abubuwan buqata, Adala tana dawowa suka hau aiki itada Nihla,ko sau daya bataga Abba yafuto ba, may be baya gidan ne, aikin sukaci gaba dayi lokaci daya gida yadauki qamshin hadadden girki

Saida Nihla taga komai yayi normal sannan taje tashiga wanka

Karfe biyu saura yakirata yace yana bakin get
Kwalliyar datayi ta doguwar riga ta atamfa ya karbi jikinta, tayi mutuqar kyau sosai
Da kanta tafuto taje ta taryoshi daga bakin get,ta karbi key din motarsa tabawa Direban gidan tace yashigo masa da ita

Yusif sai Kallanta yake, kwalliyar tata tayi bala'in tafiya da imaninsa, ahankali suke ta kowa gwanin sha'awa har suka qaraso part din Momy, Nihla sai Fara'ah take, a falon suka zauna Momy tafuto suka gaisa, tayaba da Yusif din Babu laifi, cikin sakin fuska tace "yaka baro mutanan Abuja" yace "Alhamdulillah, suna lafiya wallahi"

"aaa masha Allah, ai kullum muna jin labarinka awajan Nihla"

Yusif yayi Murmushi cikin ransa yana yabon matar

Tashi tayi tace "bari akawo maka Dan ruwa, Alhaji yafita aida kun gaisa dashi "

tatafi tasa Adala takawo masa kayan motsa baki dakuma Abincin da aka shirya masa

Kallanta yayi yace "wannan ce Momy ko?"

"itace ya Yusif"

"tanada kirki gaskiya, idan naje gida saina fadawa baba cewa kina nan kalau wani kyau ma kike qarawa"

Murmushi tayi masa, tatashi tazuba masa Abincin, yafaraci, Dan kadan yaci yace ya'isa

Yakalleta yace "Nihla gaskiya bazan boye miki ba ina qaunar ki, kuma naji dadin yanda naganki hankalin ki kwance, fatana mu kasance inuwa daya amatsayin Ma'aurata nanda Dan wani lokaci qanqani"

Kallansa tayi "ina fatan hakan ya Yusif"

Fira sukaci gaba dayi har yamma tayi, yatashi yayi sallah suka dawo falon suka zauna, wayarta ce tayi ringing, cikin zolaya tace "bakada kirki yaron nan"

Daga daya bangaren akace "ninema yaron, gaskiya kin cuceni, koke aka kawomin yanzu tsaf Zan riqeki"

Dariya tayi "lalle ma Abdallah, aikuwa baza'a kawo makaba, yakake yagida, ya service"

"gida lafiya Nihla, dama nashigo kano ne shine zanzo mugaisa saina wuce"

"Ok to shikkenan abdallah saikazo, zan turoma adress din gidan yanzu"

Wayar ta katse ta kalli Yusif "ya Yusif abdallah ne yakirani, wai zaizo mugaisa"

Yace "Ok Abdallah qanin Nadiya qawarki"

"eh shi"

Yace "to saiyazo, ina pictures din birthday din naki baki turomin ba, nunamin nagani" 🙆🏻‍♀️

Hankalinta kwance tabashi wayarta tace "gashinan suna cika duba kagani"

Bude wayar yayi yashiga gallery anan yaga pictures din, lokaci daya yanayin fuskarsa ya sauya yace "ashe bake kadai kikai ba"

Jikinta ne yayi sanyi "eh nida ya Abba ne"

Tabe baki yayi yabata wayarta, sannan yatashi yace "toni Zan tafi"


Shagwaba tafara masa "haba ya Yusif, ya za'ai katafi Tun yanzu, karfe hudu nefa"

Jiyayi ta birgeshi, yace "karfe hudu nakeso nabi jirgi nakoma, bakina tareda wani masoyin nakiba, menene zaki damu?"

"saboda ina sonka, kuma kai zuciyata ta'aminda dashi shiyasa nabaka dama ka gabatar da soyaiyar mu awajan mahaifina"

Yaji dadin maganar ta, kuma ya gamsu sosai, danhaka shima ya lallabata yace bayason yayi missing flight ne, daqyar ta yarda, takira masa Momy sukai sallama sannan suka futo harabar gidan tare domin tayi masa rakiya

Awajan motarsa suka tsaya suka jingina da motar, sai kallan soyaiya suke sakarwa junansu, yabude bayan motar yabata wata leda cikeda coculate, ta karba tayi masa godia, yace "to Zan tafi, mezaki fadamin Wanda Zan dinga tunawa ina jin dadi"

Murmushi tasakar masa har dimple dinta suka futowa sosai, adede lokacin maigadi yabude wa Abba get yashigo ciki

Dasu yafara tozali, lokaci daya gabansa yayi mugun faduwa, jikinsa har rawa yake yana neman yakasa driving din, hakan yasa yafaka motar tasa a'inda bai kamata ba, waye wannan yake tareda Nihla? Wanne dan'iskanne yazo yasakata agaba ita kuma sai wani murmushi take masa?

Cikin sauri yabude motar yafuto, fuskarsa adaure, Dafarko yayi niyyar zuwa wajansu, amma saiyayi hakuri yarabu dasu yazo yawuce su ko kallan Yusif din baiyi ba


Yusif ya kalleta da mamaki "waye wannan?"

Tabe baki tayi sannan tace "ya Abba"

Nan take shima bacin rai ya wanzu a fuskarsa 🙆🏻‍♀️


Falon yashigo anan yaga kayaiyakin da'aka ajiye da alama wannan gayen aka sauka dasu, zama yayi akan kujera yadafe kansa🤦🏻‍♂️, lokaci daya idonsa yayi jajir, to zaman mema zaiyi anan? Meyasa zai zauna yanacin Baqin ciki ita kuma tanacan tareda wani? Lokaci daya wani irin kishi ya rufe masa ido, glass cup din da'aka kawowa Yusif domin shan lemo yasa qafa yayi ball dashi, lokaci daya cup din yahadu da bangon falon ya tarwatse awajan, cikin bacin rai yafuto daga falon yanufi wajan Nihla da Yusif



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Cikin kuka tace "mum wallahi Tun safe nakejin qaiqayin, Tun yanayi Dan kadan yadawo yanayi dayawa, idan nasosa ma sakeji nake"

Hajiya Farida tace "Dida, to kiyi shiru kidena kuka mana, ba komai gane sanyi ne yake damunki, kuma muddin kina dashi to shima Fawaz din zai iya samu, kina amfani da Ruwan zanyi ne?"

Tace "eh mum inayi"

Hajiya Farida tace"to ai kinji, Dida Tun kuna gida nake muku magana akan Ruwan sanyin nan, kidena tsarki da Ruwan sanyi, sannan idan kina period kwata kwata kidena shan Ruwan sanyin ma bare kiyi tsarki dashi ko wanka, kiyi shiru zansa akawo miki magani yanzu, shima Fawaz din saiki bashi yadinga sha "

Tashare hawayen ta tace" to mum, mungode "

Yana zaune agefenta yayi tagumi, yace" to yanzu kinsa itama hankalinta zai tashi, bayan nace Karki fada mata kinqi ji, tunda safe fa nakira ummah nima nafada mata, kuma tacemin zata kawo miki magani da kanta "

Zaro ido Dida tayi," nashiga uku ya Fawaz meyasa zaka fada mata, aida kunya "

Yace" keni bawata kunya, meyasa Dan muna cikin damuwa zamu kasa sanar da iyayen mu, sunefa suka haifemu Dida "

Shiru tayi masa tafara matse cinyoyinta, ya kalleta yace" qaiqayin kikeji ne? "

Ta daga masa kanta, ahankali yatashi yadawo gabanta ya tsugunna sannan yasaka hannu yadaga yar qaramar rigar dake jikinta bejira komai ba yatura hannunsa ciki 🙈

Cikin nutsuwa yafara sosa nata wajan yana Kallanta, yanayin sa ne yafara sauyawa cikin shaqaqqiyar murya yace "yana raguwa qaiqayin?"

Idanunta a lumshe tadaga masa kai, yasaka hannu yasake bude kafarta yaci gaba da sosa mata,daga susa sai aka zarce abinda yafi yafi susa, gaba dayansu sunyi shiru kowa da abinda yakeji

Sallamar da sukaji ana doka wa ne yasa suka dawo hayyacinsu, ahankali yatashi duk hankalinsa yatashi, yace "ga ummah nan," sannan yashige cikin daki

Hajiya Abida Maman Fawaz tashigo falon tace "Sannu Dida, ke kadai ce agidan ne?"

Cikin kunya tace "a a umma ya Fawaz din yana daki"

Zama tayi akan kujera ta cire mayafin ta tashiga kitchen din didan da kanta, tafuto da wani itace daga leda ta wanke shi sannan tasaka tafarnuwa aciki tazuba a tukunya tadafa mata shi

Saida ya dahu ta debo a cup takawo mata tace "karbi wannan kisha"

Adede lokacin Fawaz yafuto daga daki bayan yagama dedeta kansa 🤣

Hajiya Abida tace "Sassaqen Zogale ne wannan, shi zaku dinga sha dagake har shi, ga sauran can a kitchen nabar muku, kudinga sha kuna tsarki dashi, ina tabbatar miki koda sanyi Hajiya Farida ta haifeki to insha Allah saiya barki" 🤣

Dida da Fawaz sukai murmushi gaba dayansu, sannan hajiya Abida tayi musu sallama tatafi

(Yar'uwa kisamu Sassaqen Zogale, ina nufin jijiyar Zogale, za'a saro miki shi daga jikin bishiyar Zogalen, saiki qara daddatsa shi yayi Dan dede misali kisa shi a tukunya kidafa da tafarnuwa, kokuma kidafa da jar kanwa, idan ya dahu saiki dinga sha safe, rana, dare, daga lokacin zakiyi hannun riga keda cutar sanyi, Allah yasa anfahimta 🙏🏻)



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Hannunsa zube cikin aljihun wandonsa jeans Mai launin fari yaqaraso wajansu fuska daure, kana kallansa zaka hango tsananin kishi afuskar sa
Kallan Yusif yayi yace "Sannu ko"

Ya Yusif shima da kishi Yarufe masa ido yace "Sannu fa"

Kallan Nihla yayi "ina jiranki kizo Muje ki hada min abinci"

Kallan mamaki tabishi dashi, da'ita ce take hada masa abinci? Tace "abinci kuma?"

"eh abinci, kokuma da kaina zanje nahada? Bayan kinsan ban'iyaba?"

Tace "Abincin...." cikin sauri ya Yusif ya tare ta, ta hanyar daga mata hannu
Ya kalleshi yace "Abba ko?"

Fuskarsa Babu alamun wasa yace "Yeah"

Ya Yusif yace "kanata kishi kana bacin rai saboda kawai muna tare, to bakaga tana tareda mijin da zata aura bane?"

Haushi yaqara kama Abba, baice masa komai ba yakalli Nihla yace "banda lokacin batawa anan, zaki wuce mutafi kokuma saina daukeki nashiga dake?" 🙆🏻‍♀️

Cikin fishi Yusif yace "karka kuskura kafara tabamin mata, idan tana yarinya ka tureta narabu dakai to yanzu ko Dan yatsanta ka taba ranmu ne zai baci gaba daya"


(Lol dama kunsa ba 🤪)


Abba ya kalleshi, sai yanzu yagane komai, sai yanzu yagane shine meyi masa shishshigi akan qanwarsa Tun tana qarama, kuma shine silar dayasa yayi fishi da'ita kafin subaro qauyen na jigawa, meyasa har zuwa yanzu yake masa katsalandan acikin rayuwarsa ne? 🤦🏻‍♂️

Cikin fishi yakai Hannu zai fuzgota shima Yusif cikin sauri yasa hannu zai tareta, Nihla tana ganin ikon Allah tace "nashiga uku, ya Yusif Dan Allah kayi hakuri karabu dashi banaso kokadan ranka yabaci akansa, Muje kada kayi missing fligh"


Yusif yace "shikkenan my dear, idan nasauka Zan gaida su baba"

Abba jin tace Yusif yasake kallan gayen, ashe shi nede yake kiranta awaya, kuma shine Wanda ya aiko mata da gift daga Abuja, damuwa tataru tayi masa yawa

Adede wannan lokacin shima yaqaraso wajansu, Tun daga nesa ya gansu a tsaye cirko cirko da alama ba kalau ba, yana zuwa kuwa yayi musu sallama, Nihla da Yusif suka saki ransu, shikuwa Abba mamaki yake meya kawo Abdallah gidansu? "

Fuskantarsa yayi yace" kai meya kawoka gidannan? Mekazoyi? Mayaudaran banza Mayaudaran wofi, kafice kabar gidannan yanzu yanzu "

Nihla tarasa yanda zatayi, tace" Abdallah Dan Allah kayi hakuri "

Abdallah yace " Babu komai Nihla, sai munyi waya "

Yayiwa Yusif sallama ya juya yatafi ransa fal da tunani me yakawo Nihla gidansu ya Abba saurayin Anty Nadiya? Dama Ta sanshi ne?

Shima Yusif yayi mata sallama yatafi, Abba kuwa Be qara cemasa komai ba saima hanya daya nuna masa

Nihla ta kalleshi," haba ya Abba, meyasa kake min hakane? Sainayi baqi zakazo ka tozartani agabansu, me kake nufi danine? "

bata jira amsarsa ba tawuce tayi part dinsu cikin fishi

Wato duk abinda yake Tsawon wannan lokacin batasan ma meyake nufi ba, tunda gashi tana tambaya meyake nufi da'ita, bin bayanta yayi yace "dakata"

Tayi banza ta qyaleshi taci gaba da tafiya

"ki dakata nace"

Nanma tayi shiru ta qyaleshi harta qarasa cikin falon, sannan Tajuyo ta kalleshi cikin fishi, bacin raine yasa batasan lokacin data daga muryarta ba, takalleshi tace " inajin ka"

Momy tana daki Tun dazu tana sallah taji Kamar qaran fashewar kwalba, kuma data idar ma bata futo ba, tazauna tana lazimi, yanzu kuma tafara jiyo murya sama sama Kamar ana fada, ahankali tatashi tace "toba lafiya ba duk yanda akayi"
Hijabin jikinta ta cire tafuto daga dakin, turus tayi ta tsaya abakin kofar dakinta ganin Abba da Nihla a tsakiyar falon kowa ransa abace, gaba dayansu Babu Wanda ya lura da ita bacin rai Yarufe musu ido, itama kuma ta zuba musu ido tana kallansu daga nan kofar dakin nata, me wannan yaran sukeso su zama ne? Karfa wannan halin nasu yaci gaba da tafiya harkan yaransu, yanzun menene yake faruwa me yahada su?

Cikina fishi yakama hannun ta yariqe yace "dan me zaki dinga kawo maza barkatai kina saurarensu, kinje kin tsaya musu agaba kina bude baki kina musu dariya, sannan ina kiranki kinyi banza kin share ni kintafi kinbarni"

Hannunta ta fizge tace "dan Allah dakata ya Abba, dan me zaka shiga cikin rayuwa ta kanemi katakuramin, meyasa kai akoda yau...." maganar tace ta tsaya cak, sakamakon hade bakinsu dayayi waje daya 🙆🏻‍♀️

Momy dake kofar dakinta a tsaye tayi sauri ta runtse idonta

Lips dinta na qasa yakama yanasha Kamar yasamu sweet, laushin da lips dinnata yake da shine yasa ya lumshe idonsa

Gabanta yayanke yafadi, dukansa tafarayi tana kokarin fizge bakinta, amma saiyasa duka hannunsa biyu ya tallafe kanta dasu, gaba daya yanayin sa ya sauya jinsa awani irin yanayi dabai taba tsintar kansa aciki ba

Zuwa wannan lokacin hawaye yagama wankewa Nihla fuska

Saida yayi kissing dinta sosai sannan yazare bakinsa daga cikin nata, yakama hannayenta yariqe cikin nasa sannan yazuba gwiwar sa aqasa, yadaga kansa yana Kallanta yace "i love you NIHLA, ina qaunar ki sosai, please kiyafemin abinda na aikata miki abaya, Dan Allah na roqeki kiyafemin, kidena kula wasu mazan Dan Allah, sosai zuciyata tanamin zafi akan hakan, bazan juri ganinki tareda kowa ba, da gaske zuciyata zata iya samun matsala" yayi shiru yana Kallanta, hawaye kuwa wani nabin wani akan fuskarta

Fuskarsa yadora akan hannayenta dayake cikin nasa hannun yayi shiru, lokaci daya Nihla taji ruwa yana sauka akan hannunta, hakan ya tabbatar mata da cewa kuka yake

Momy dake kallansu lokaci daya taji qwallah tacika idonta ganin yanda Nihla take kuka shima ya tsugunna a gabanta yana mata kuka



Dago kansa yayi ya kalleta idonsa yayi jajir, ganin taqiyin magana yasa Ahankali yatashi tsaye, har lokacin kuma hannunta yana cikin nasa

Dora hannun nata yayi akan qirjinsa yace "zaki iya Rayuwar aure dawani batare daniba?"


Hannunta ta qwace daga kan qirjinsa, ta kalli idonsa tace "ya Abba, wacce irin magana kake min haka? Kasan abinda kake fada kuwa? Saboda banda gata ne yasa zaka nemi kayi wasa da rayuwa ta? Alokacin dana soka nunamin kayi baka qaunata, baka duba maraicin mahaifiyata danake tare dashiba Alokacin haka kace baka qaunata cikin bainar jama'ah, mutanan dakake cewa narabu dasu sune suka soni, suka qaunaceni Alokacin da dan'uwana ya nuna baya qaunata"

Hawaye yacika idonta, bata damu data goge ba taci gaba da cewa "Inda ace mahaifiyata tana raye, bazata taba bari hakan tafaru daniba, Tun banda wayo nasan cewa Diddi tasoka ya Abba, amma kai kaqi abinda tahaifa kaso Nadiya, to idan baka saniba Anty Nadiya itace tanusar dani nasan menene rayuwa, ta nunamin maisona da maqiyina, amma yau dan'uwanta yazo wajena kaci masa mutunci, da kaqini, sai yanzu da hankalina ya karkata wajan wani sannan zakace kana sona? ta yaya? Impossible! "

Tasa hannu tashare hawayen idonta sannan tawuce tabarshi awajan

Zuwa wannan lokacin kam Momy ma sun sata kuka, hawaye yacika fuskarta

Shikuwa Abba kansa ne yayi mugun sarawa, yazube awajan yana fadin" Innalillahi wa inna ilaihir raju'un... "










🤔Um jama'ah rikicin Mazawaje family naga alama ba qarewa zaiyi ba saide mu taqaita, nagaji wallahi, yakamata mu huta haka, kuma zaku Dan huta da Comments, Mutara zuwa jibi ko gata insha Allah, nagode 🙏🏻









Amnah El Yaqoub ✍️
[7/10, 1:36 AM] El Yaqoub: ❣️DANGI DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub

Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-10548777110149


45&46



'Da uwa sai Allah, tausayin Abba yakama Momy, ta kowa tafarayi Ahankali zataje wajansa, saikuma ta fasa tajuya cikin dakinta itama saboda bataso yaran su fahimci cewa tasan abinda yafaru atsakaninsu

Agefen gadon ta tazauna tafada duniyar tunani, ada kam abinda tasa aranta shine koda Nihla ta amincewa Abba itada kanta zatasa karta amince, to ashe awajan Nihla itama hakanne, ashe bata son Abban a yanzu, ashe tunanin ta qarya yake bata,da gaske yarinyar bata qaunar Abba, amma yaya zatayi? Tanajin Nihla acikin ranta Tun tana qarama, tanajin ta Kamar yarta ta cikinta, ba zatayi mata dole akan Abba ba, dole zasu bata haqqinta, tazabi Wanda ranta yakeso, hakan shine adalci, amma Abba Babu kunya yakama yarinya yana mata kiss? 🤔
Baya tsoron tazo wajan ko Daddy


Nihla nashiga daki tashare hawayen idonta, tafara cire kayan jikinta domin ta watsa ruwa,akan gado tazubar da kayan nata, daga ita sai towel tashige wankan, kokadan bataji tausayin ya Abba ba, koma menene shine yajawa kansa acewarta


Abangaren Abba kuwa awajan Yazauna yadafe kansa, idonsa sunyi jajir tsabar kuka, bai taba tunanin cewa watan watarana zaiyi kuka akan soyaiya ba, amma gashi na farko yayi kukan Baqin ciki akan Nadiya, yanzu gashi yana kuka na biyu shikuma kukan nadama akan Nihla, ahankali yatashi tsaye jiri yana dibansa, yashige cikin dakinsa, akan gado yafada yadauki wayarsa yakira Aslam, bugun farko Aslam yadaga yace "Abba yane"

Cikin muryar kuka yace "komai yaqare Aslam..., komai yazo qarshe, tace bata sona"

Aslam yayi shiru Kamar an doka masa sanda
Yasaki ajiyar zuciya yace "Abba wannan shine abinda nake gujema Tun farko, meyasa zakayi magana Awannan lokacin? Yanke hukunci cikin fishi banaka bane, a lokacin Abba Kowama yana jin abinda kake ji, duk cikin mu Babu Wanda yake son wannan hadin da akayi mana, amma haka mukai shiru, amma yanzu de kayi hakuri, nasan cewa Nihla zata soka"

"bazata soniba Aslam, yarinyar nan har tsugunna mata nayi nabata hakuri, amma taqi yafemin, saima laifukan dana aikata mata abaya tasake maimaita min, Aslam tayaya zata yafemin idan tana tuna abinda nayi mata? Yanzu shikkenan mutum bazai iyayin kuskure ba a rayuwa kuma yadawo ya gyara? "

" Abba!!, kaima fa abinda kayiwa yarinyar nan bashida dadi, dole zata tuna, saide Ahankali ta Manta "


Cikin hawaye yace" kuma sai tace bazai iyu tasoni ba "

" kayi hakuri Abba, amma ka denayin kukan nan, insha Allah nima Zan tayaka addu'ah zata soka, mu miqa lamuranmu ga Allah, shine kawai mafita "

" Aslam bazata soni ba, tsanata nake gani qarara akan idonta, wallahi idan taqi aure na Allah saina saceta "🙆🏻‍♀️

😳Zaro ido Aslam yayi" a a Abba ba za'ayi hakaba, babu maganar sata, mubi komai Ahankali "

" wani fa takawo gidan Aslam, agabana take masa murmushi, Allah idan yasake zuwa wajan ta saide ayi biyu Babu, zan kasheshi nima nakashe kaina tunda haka takeso "


Aslam yayi Murmushi, Abba da kishi sai Allah, afili yace" Abba, kayi hakuri, kaci gaba da bata haquri, amma kasan abinda zamuyi yanzu? Mufara gyara sama tukunna, Abuja zaka shirya Muje munemi mahaifin ta mufara bashi hakuri, sai aci gaba daga inda aka tsaya "🤣

Jan zuciya yayi yace" shikkenan "  qit ya kashe wayar

Ilham ta dafa Aslam tace" meyake faruwa ne? "

" nida Abokina ne, yanason qawarki sosai amma tana bashi wahala, yayi laifi yanaso ya gyara laifukan dayayi mata amma taqi bashi damar hakan, yanzu abnda yake fadamin har tsugunna wa yayi a gabanta yabata hakuri amma taqi yarda "

Ilham ta zaro idonta cikeda mamaki tace" ya Abban? "

" shikuwa, ai soyaiyar Nihla nema take tahaukatashi Kamar yanda taki ta haukatani, kika hanani kallan ko wacce mace "

Murmushi tayi tace " ya Aslam kenan, amma ina tausayin ya Abba gaskiya, Dan Nihla koda yaushe muka hadu sai munyi mata maganar sa, amma sai takawo maganar saurayinta "

Cikin damuwa Aslam yace" akwai damuwa de gaskiya, Allah yashiga cikin lamarin kawai"

"amin" cewar Ilham



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

After one week

Kwance suke akan gado, ta dora kanta akan qirjinsa, yayinda hannunsa yake kanta yana shafa mata, yace "Baby Dida kinga maganin nan na ummah wallahi yayi kyau sosai, gashi yanxu shiru kake ji Babu kowacce damuwa"

Idanunta a lumshe tace "Um, Allah yakiyaye gaba, amma ai zamuci gaba da sha"

Yace "to, duk yanda kikace haka za'ayi"

Kanta ya daina shafawa yatura hannunsa cikin blanket din dasuke ciki yana shafa qirjinta, rabuwa tayi dashi yana abnda yakeso, amma da aka jima taga abinnasa bana qare bane, kawai saita fara masa kukan shagwaba "ya Fawaz yanzu fa kagama, nide Dan Allah muhuta..."

"Baby Dida kadanfa Zan qara, bazan dadeba kinji"

"naji, amma gaskiya daga wannan shikkenan ko"

Murmushi yayi yace "um inajin"

Itama Murmushin tayi masa daganan suka lula duniyar Ma'aurata



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Zaune suke afalo itada Momy, wayarta tayi qara, tana dubawa taga baba ne, cikin girmama wa tadaga suka gaisa yace "Yusif yazomin da wata magana yace kece kika bashi dama yazo muyi magana ko?"

"eh baba nice nace yayima magana"

"to yamin magana, amma kuma yace kinfada masa wai saikin kammala service tukunna, menene abin jira Nihla, tunda Allah yakawo miji kawai ayi aure, auren ki na farko matsala ce tasa ba'aiba, amma yanzu tunda gashi kinsamu ilmi ai Babu abinda zamu jira, amma mahaifin Yusif din baya nan, idan yadawo daga tafiyar dayayi zamuyi magana akan hakan insha Allah, idan ma aurenne sai ayi, inyaso saiki qarasa service din agidan mijinki "

" to shikkenan baba, Allah yasa hakane yafi alkhaairi, "

" amin, Allah yayi miki albarka ki gaida su hajiyan "

" to baba zasuji "

Tana kashewa ta kalli Momy tace" Momy nida baba ne, yana gaishe ki, maganar Auren ya yusif yayi min, Momy nida nafiso saina gama service dina, amma shi baba yace wai basai nagama ba kawai zasuyi magana da babansa, su tsaida magana daya "

Tun lokacin da al'amarin Nihla da Abba yafara wakana, Momy bata taba Jin faduwar gaba irinna yauba, jikinta yayi sanyi, Nihla de da gaske take tarabu da Abba Yusif din takeso
Murmushi ta qaqaro tace" Alhamdulillah, to Nihla ai hakan yafi, menene amfanin jira yata, abinda Mai hakuri yafada gaskya ne, aide kina sonsa ko? "

Momy tayi Tambayar tana zubawa Nihla ido ko zataga yanayin ta ya sauya amma saitaga Babu damuwar komai akan fuskarta
Saima kanta data daga alamar eh tanaso

Murmushi tasakeyi, kafin tayi magana yaturo kofar dakinsa yafuto yayi mutuqar cikin suit kalar ash, qaraso wa yayi Yazauna akan hannun kujerar da Nihla take zaune 🤣
Yasa hannu yadauki Ruwan da yagani ansha, yazuba a cup yafara sha Ahankali, Nihla sai matsawa take gefe, tarasa wannan abu na ya Abba, duk kujerun falon sai akusa da'ita zai zauna, wayarta tabude tashiga chatting tanayi

Shikuwa yana shan ruwa hankalinsa yana kan wayar tata, jikinta ne yabata ana kallonta, danhaka tashiga cikin chat dinta itada ya Yusif tayi sallama daganan bata jira komai ba tafara tura masa da kiss💋💋💋

Wani irin qullutun Baqin ciki ya tokarewa Abba wuya, ahankali yaji Ruwan dayake sha yafita daga ransa

Yusif kuwa baya rufe datar sa, yana ganin saqon Nihla yadoko mata kira

Nanma akan idon Abba kiran yasake shigowa, murmushi tasaki sannan tayi cikin dakinta tana amsawa wayar

Abba yabita da kallo ransa abace, Momy ta kalli yanayin sa, tace "Abba na sai ina?"

"Momy zamuje Abuja ne nida Aslam"

"Abuja kuma? Wajan wa? Me akeyi?"

"Momy wajan baba Ibrahim zamuje mugaidashi"

Tausayinsa yakama Momy, tasan duk saboda Nihla zaiyi hakan, taji dadi aranta tunda yau Abba zai gyara kuskuren daya aikata, tace "to sai kundawo"

Daga nan tatashi, tsaye tayi hanyar dakinta, Abba ya kalleta dakyau yaga jikinta yayi sanyi, Kamar akwai abinda yake damunta yace "Momy bakyajin dadi ne?"

Juyowa tayi "lafiya ta kalau Abba, kaina ne yake ciwo kadan"

"Momy ko mutafi asbiti?"

"A a Abba na, karka damu ai Nihla tana nan"

Yace"To shikkenan Momy, Allah yasawaqe "
Momy tashige dakinta tafada duniyar tunani, tunda Nihla tayi mata magana akan sunyi maganar Yusif da babanta shikkenan ta saddaqar Nihla bazata auri Abba ba, bazata auri danta ba, ahankali tatashi tasha magani, sannan ta kwanta


Abba kuwa dakinsa ya koma yadauko wayoyinsa, yana futowa daga dakin yaga wayar Nihla akan kujera, mamaki ya kamashi, yaushe tadawo falon?

Hanyar kitchen yanufa yaleqa kansa yaganta a kitchen tana kokarin kunna gas
Bece da'ita komaiba, ya koma falon yadauki wayar tata batare da tunanin komai ba yahadata da bangon falon ya doka, nan take wayar tafashe tayi raga-raga🙆🏻‍♀️

Yajuya yafice daga falon, yahau Mota yanufi gidan Aslam



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


"congratulation Adam, matarka tana dauke da juna biyu Tsawon wata uku"

Adam yasaki murmushi yace "Doc da gaske kake?"

"qwarai kuwa, haka bincikenmu ya nuna, sannan wannan zazzabin datake fama dashi da amai, insha Allah zata denaji, karkuma kuyi wasa da bata magungunan da aka rubuta muku"

"insha Allah Doc. Nagode sosai"

Kallan Diyana yayi da aka yiwa qarin ruwa, tana bacci, saida Ruwan yaqare sannan yakira Doc aka cire mata, sukayi shirin tafiya gida

Kamota yayi ya rirriqe yana ta mata sannu, ta kalleshi tace "ya Adam sai farin-ciki kake, bayan kuma kasan banda lafiya"

"aidole nayi farin ciki maryam, kinsan me Doc yace kuwa?"

Shiru tayi masa, Dan a tunanin ta baidamu da rashin lafiyar tata bane, Motar tabude tashiga, shima yashiga sannan tace "ina Zan sani saika fada"

Cikin murna yace "to cemin yayi matata maryam tana dauke da Baby na acikinta na wata uku"

Cikin sauri ta kalleshi tace "da gaske?"

"sosai ma kuwa, bari mu koma gida nakira su Aslam da mama nafada musu"

"yanzu ni ahakan ciki ne dani?"🤔

"maryam kenan kina mamaki kenan, aike yanzu kin zama sarauniya maryama sai abinda kikace"

Shiru tayi masa tazuba masa ido tana kallan yanda yake farin ciki, Allah sarki ya Adam, rayuwa kenan



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Kasancewar jirgi suka biyo ko awa daya basu yiba suka sauka,baba yayi mamakin zuwan su Tun lokacin dasuka kirashi awaya

Afalon gidan aka saukesu, mamy takawo musu abin motsa baki suka gaisa dasu, sannan ta basu waje

Sosai suka gaisa da baba, Inda suka sake bashi hakuri akan abinda yafaru abaya, baba ya nuna musu Babu komai dama basune sukai masa laifin ba, amma komai yawuce insha Allah

Yusif ne yashigo falon yayi kyau cikin qananun kaya Baqin wando da farar riga an rubuta handsome agaban rigar
Ido biyu sukai shida Abba, kowa ya kawar da kansa


Tunani Abba yafara, kenan gida daya take rayuwa da wannan gayen, shima Yusif din anasa bangaren tunani yake menene yakawo wadannan gidansu


Ahankali yaqaraso wajansu yamiqa wa Aslam hannu suka gaisa
Sannan yabawa Abba hannu yana kawarda kansa gefe

Shima Abban kansa ya kawar gefe sukai musabaha ahaka 🤣

Baba yayi shiru yana kallon su, gaisawa suke amma kowa fuska adaure, kuma kowa ya kawar da kansa basa kallan junansu

To tabbas da wani abu aqasa, duk yanda akai yarannan sunsan juna, sannan shi Yusif yayi masa maganar Nihla, ga kuma Abba shima yazo domin gyara laifin dayayi abaya, da alama shima da wani abu a tsakaninsa da yarinyar, to daga nanfa baba yafara tunanin akwai matsala

Suna gaisawa dasu yawuce dakinsa, suma su Abba basu jimaba suka dauki hanyar Airport domin komawa kano



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Azaune take aqasan kafet din dake malale acikin qayataccecn falon na Momy datafe kanta da hannunta guda daya tana kuka, dayan hannun kuma ta riqe fashshiyar wayarta dashi, ba fashewar wayar ce tasa ta kukaba, Information dinta dayake ciki takewa kuka, saboda idan waya ce akwai Sabuwar da ya Yusif yakawo mata, kuma akwai tsohuwar wayarta ta farko duk suna nan

Allah ne yakawo su Usman gidan gaba dayansu

Ya Aliyu ya kalleta yace "Momy me aka yiwa wannan yarinyar ne take kuka?"

"wallahi Aliyu futowa mukai falon nida ita shine mugaka wayarta afashe, shine take kuka"

Ya Usman yace "subhanallah... To garin yaya ta fashe Momy?"


"yaya ma za'ai kayimin wannan Tambayar Usman, Abba zai fasa mata wayar nina sani"

Farouq yace "haba Momy, ya za'ai yafasa mata waya, Abba bazai yi hakaba, da hankalin sa dakomai yazaiyi yafasa mata waya"

Momy tace "a a Farouq rabu da shiru-shiru, rabu da shiru-shiru farouq, dukanku nice na haifeku Babu Wanda bansan halinsa ba acikinku, nafada muku Abba ne yafasa wannan wayar"

Suna wannan zancen yashigo cikin falon, yayun nasa yagaisar sannan yace "Momy nadawo"

Momy tace "naganka ai Abba" 🤣

Ya Usman yace "Abba meyasa kafasa wa yarinyar nan wayarta, saboda me haka kawai zaka fasa waya?"

Juyawa yayi ya kalli Nihla datake goge hawayen idonta, haushi ya kamashi, saboda yafasa wayar da saurayinta yake kira shine take wannan uban kukan

Yamaida kallansa ga Usman yace "ya Usman ni ban fasa mata waya ba" yanemi waje Yazauna yana cire jacket din saman suit din jikinsa

Momy tace "Abba, nasan halin ka sarai, idan bakaine ka fasa mata wayaba waye zai fasa? Adala bata nan, dagani saikai sai ita dakuma Daddynku, mune zamu fasa wayar kenan?"

Cikin kishi dakuma wata irin murya Kamar zaiyi kuka yace "to Momy meyasa zata dinga waya dawani can, bana fada mata banaso ba"


Hawaye suka zubowa Nihla ta kalli Momy tace "Momy ai kinji shi ko? Allah saiya biyamin wayata"

Tashi yayi tsaye ya kalleta, ya girgiza kansa, sannan ya sunkuya yadauki wayarsa da jacket dinsa daya cire yayi hanyar dakinsa











To,ko  Alhaji Abubakar zaibawa Ibrahim hakuri akan abinda yafaru abaya?

Yaya labarin abdallah qanin Nadiya ne? Anya kuwa zai iyayin shiru akan abinda yagani dangane da Abba da Nihla?






More Comments more typing....👌🏻









Mrs Usman ce ✍️
[7/11, 12:19 AM] El Yaqoub: ❣️DANGI 'DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub

Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493



47&48


Momy tayi zuru da ido tana Kallonsa, gaskiya ne karabu da miskilin mutum, ka kalleshi kawai, kagama yiwa yarinya kuka ka matseta kayi kissing dinta amma kaduba kaga Kamar bashi ba, kome yataka oho?

Usman yace "Nihla kiyi hakuri kidena kuka kinji, zanyi masa magana saiya nemo miki waya wayar, kiyi shiru"

Ahankali yatashi yabi bayan Abba, zaune ya sameshi yayi tagumi hannu bibbiyu, zama yayi a gefensa
"Abba!, meyasa zaka fasa mata waya, tayaya zata soka ahaka Abba?"

Kallan yayan nasa yayi, qwallah tacika idonsa, bai iya boye waba danhaka yabasu damar zubowa, jikin ya Usman yafada, cikin hawaye yace "yaya ashe kowa yagane halinda nake ciki? Yaya zanyi da soyaiyar ta yaya?"

Usman ya shafa kansa "kadena kuka mana"

"dama wannan shine abinda muke gujema tunda farko" Aliyu daya shigo dakin yafada

Gaba dayansu suka daga kansu suka kalleshi, farouq ma yashigo dakin sannan Yarufe

Zama sukai duk su hudun, Aliyu ya cigaba da cewa "yanzu wa gari ya waya? Kai taurin kai gareka Abba, yarinyar nan kowa yasan tasoka, amma ka Qita, tayaya zata soka yanzu?"

Hawaye suka zubo daga idanun Abba, Usman yace "Abba na hanaka kukan nan, kuka bazai kawo mafita ba"

Cikin hawaye yace "ya Usman kabarni nayi kukana, cewafa tayi batasona, kuma bata barni hakaba saita dinga kula wasu"

Dariya takama farouq, bai boye ba yasaki dariyarsa 😃

Wani irin haushi yakama Abba, yazuba masa ido yana kallansa batare dayayi magana ba
Saida farouq yagama dariyarsa yace "wallahi banga laifin Nihla ba, gara ta gwaraka ka gwaru"

Cikin haushi yace "Aidama nadade da sanin sonta kakeyi, ai shikkenan"

Farouq yayi Murmushi yace "ahhh ina son Nihla,wayace ka Qita? Lokacin dakace baka sonta nace Zan aure ta kaji haushi nane? Sai yanzu dakake sonta ne zakace ai dama kasan ina sonta, a a ina auren ta"


"dan Allah kuyi mana shiru munemo kanmu mafita" cewar Aliyu

Gaba dayansu kuwa sukai shiru, ya Usman ya kalli Abba yace "Abba kishi banaka bane, ka lallabata kagane? Kabata kulawa, kuma ka sameta kasake bata hakuri, kai Abba inta kama ma saika tsugunna a gabanta ne, to kayi inde hakan zaisa tahuce"

"ya Usman har hakan fa nayi mata taqi yarda"

Aliyu da farouq suka saki murmushi, lalle Abba da gaske yake

Shima ya Usman din murmushin yayi yace "naji, kaci gaba da bata hakuri, insha Allah wani lokacin zata hakura"

Aliyu ma yace "yawwa kuma naga Kamar Momy ma tanabin bayanta, yakamata kasamesu itada Daddy kuyi magana, amma wannan fishin naka akan ankirata awaya Babu Inda zai kaika"

Haka yan'uwan nasa suka sakashi agaba sunayi masa huduba, dakuma shawara akan abinda zai kawo musu mafita



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Zaune yake agaban iyayen sa,acikin dakin Daddy, kansa aqasa, Momy tana zaune agefen Daddy, yayinda hankalin Daddy yake kan news din da akeyi

Saida aka gama sannan ya kashe, yajuyo ya kalli Abba yace "Abubakar muna jinka, kazo kace akwai maganar dakake so muyi, amma kayi shiru"

Gabansa ne yafara faduwa, yarasa ta Inda zaiyi wa iyayen nasa bayani

Momy tace "kayi shiru Abba"

Ahankali yadago kansa ya kallesu sannan yasauke idonsa cikin sauri,"Am.. Daddy dama.... dama inaso ne infada muku inason yin aure"


Murmushi ya baiyana a fuskar Daddy, amma Momy kuwa Kallonsa tace, tanaso taji yafadi abinda ta dade dasani

Daddy yace "wacce Abba? Alhmdllh ashe de kaji fadan damukai ma"


Ahankali yadaga kansa alamar yaji

Momy tace "to Wacece? Ko wata yar Abujan kasamu?"


Kallanta yayi ya girgiza kansa alamun a a

Daddy yakalli Momy yace "ikon Allah,  kinga yau Abba kunyar mu yakeji"

Momy tayi Murmushi batace komai ba

Daddy yace "to a wanne garin take? Saina tura su Alhaji Baqir suje su nema ma auren ta, Wacece?"

Karon farko da Abba yaji tsoron mahaifin sa, gabansa sai faduwa yake, jikinsa yayi mugun sanyi, har wata irin karkarwa yakeyi
Ahankali yadago kansa ya kalli Daddy yace "Nihla ce Daddy"

Lokaci daya, annurin fuskar Daddy ya dauke
Yamiqe tsaye yace "zancen banza, zancen wofi, Abubakar ashe bakada hankali bansani ba?"

Yasake maida kallansa wajan Momy yace "toke Rahma idan kin gama sauraren abinda yake fada, saiku tattara kufita, nima zanje daki nahuta" yana fadar haka yafara takawa zai tafi dakinsa
Caraf yasa hannu yariqe kafar mahaifin nasa, kansa aqasa, amma yakasa Dagowa, Daddy jin anriqe masa kafa yasa ya tsaya cak, hawaye ne yake disowa daga Idanunsa, numfashin sa yafara sama sama Kamar Mai Asma, yasaka hannunsa daya ya goge, yayinda dayan hannun yake riqe da qafar Daddy
Ahankali yadago kansa ya kalli Daddy yace "Daddy please, Dan girman Allah Daddy kayi hakuri kuyafemin irin laifin danayi abaya, Daddy ka tausayamin wallahi ina sonta...." ya qarasa maganar yana sakin wani irin kuka Mai cin rai

Daddy yajuyo ya kalleshi yace "Abba!, kalleni nan, niba mutumin banza bane, kuma niba qaramin yaro bane dazaka raina wa hankali, saida kasa natara mutane agabansu ka nunamin ban isa dakai ba, yarinyar nan akan ka aure ta kazabi karbar Mazawaje family, sai yanzu zakazo min da wata irin magana, kaga da Allah, tashi kafice kabarmin dakin nan indena ganinka "

Ahankali yamiqe yadafe kansa dayake masa muguwar sarawa, yakalli Momy da jikinta yayi sanyi yace" Momy, Dan Allah Kibashi hakuri, kuyi hakuri Momy wallahi zuciyata zafi takemin, Momy inason Nihla "

Momy tace" Abba ai lokaci yaqure ma, Nihla akwai wanda takeso, sannan mahaifin ta yayi magana da ita akan hakan, kaine ka janyo koma menene, katashi kafice kawai, banason maganar banza "

Hawaye yasake zubowa Abba, shikkenan Babu wani Mai goyon bayansa kuma, tunda Momy ma tace haka to Babu Wanda bazai iya juya masa baya ba

Duhu duhu yafara gani, ahankali yafara takawa sai jiri ne yake dibansa, hannunsa yana dafe da kansa, haka yatafi yabar falon na Daddy yana tafiya yana hada hanya

Hawaye ya zubowa Momy, tana tausayin Abba sosai amma dole zataso yagane dai dai da abinda ba dai dai ba
Cikin sauri tatashi zatabi bayansa Daddy yace "Karki kuskura kije Inda yake, kinji nafada miki"
Yana fadar haka ya juya yashige dakinsa ransa duk abace

Momy ta zube akan kujera tana sakin wani irin kuka Mai ciwo



Jikin bango yakebi yana tafiya Kamar Mai koyon tafiya, sakamakon duhun dayake gani acikin idonsa, da haka ya qarasa dakinsa yazube akan gado yana sakin kuka sosai abaiyane, nan take wani irin zazzabi Mai zafi ya rufeshi



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

"Abdallah yakirani awaya yafadamin komai, meyasa kika boyemin gaskiyar ke Wacece Nihla?"

"Anty Nadiya... Dan Allah kiyi hakuri, wallahi bansan ta yanda za'ai nayi miki bayani ba, Anty Nadiya ya Abba ke yakeso, kuma a lokacin dana hadu dake kuna tare da juna, yana sonki kina sonsa, meyasa Zan rusa muku soyaiyar ku, bazan iyaba, shiyasa nayi shiru ban fada miki alaqa ta dashi ba, duk family dinmu kowa Abba yake cemasa, nahadu dake naji kince sadiq Mazawaje, banyi tunanin shi bane saida kika nunamin pic dinsa, kuma daga lokacin nake sporting dinsa awajan ki, harga Allah banso kikaqi auren saba, saboda banji dadi ba kokadan Anty Nadiya, koma meyayi min shidin dan'uwana ne,nida shi munkance cikin DANGI DAYA, duk da yayi min laifi wallahi banso kika Barshi ba, amma kiyi hakuri Anty Nadiya akan rashin sanar dake dabanyi ba "

Ajiyar zuciya Nadiya tayi" nafahimceki Nihla, sai da abdallah yafadamin komai nasan cewa bakida laifi, Sadiq yahadu Nihla Nikaina nasan da haka,ashe ba banza ba kika rikice, Nikaina rashin kulawar sa ce tasa narabu dashi, amma Abdallah yacemin yaga soyaiyar ki sosai acikin idonsa, hakane? "

" hakane Anty Nadiya, yafadamin ma, kawai de bazan iya sauraron sa bane, kuma nafada masa "

" eto yakamata de yasan darajar ki gaskiya, sai kiyi addu'ah Allah yazaba miki mafi alkhaairi, idan ansa ranar bikin saiki sanar Dani "

" munyi maganar ya Yusif da baba ma Anty Nadiya, insha Allah idan ansa Zan sanar dake "

" to shikkenan qanwata Mai yan samari, sai munyi waya, kicewa sadiq Nadiya tana gaishe shi "🤣

Murmushi Nihla tayi tace" Babu ruwana Anty Nadiya, kunfi kusa kedashi "

Da haka sukai sallama



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Sanye take da atamfa Mai launin pink da brown, dinkin riga da siket ne amma Yazauna a jikinta sosai, mayafi tayafa dan qarami iya gefen kafadarta daya, yayinda data riqe hand bag dinta tafuto daga cikin dakinta, da alama unguwa zataje, adede lokacin shima yafuto idonsa yasauka akanta, tayi mutuqar yimasa kyau sosai, kasa dauke idonsa yayi akanta harta qaraso ta gabansa zata wuce shi batare data kalli Inda yakeba, hannu yasa ya fuzgota, lokaci daya tafada jikinsa, bai jira komai ba yasaka ta cikin qirjinsa ya rungumeta sosai

Tudun nashanunta dayakejinsu akan qirjinsa ne yasa ya lumshe idonsa, sannan yaqara matseta tsam ajikinsa, jijiyoyin jikinsa suka fara karbar wani irin saqo, wani irin zirrr yakeji tundaga tafin qafarsa har zuwa kansa, kansa yasake turawa cikin wuyanta yana shaqar wani sihirtaccen qamshi dake tashi a jikinta, bayaso yadena jin abinda yakeji ajikinsa, baiqi ace su dauwama ahaka ba, ahankali yadago bakinsa, yadora Dan qaramin lips dinsa akan kunnanta yana gatsawa Ahankali

Wani irin numfashi Nihla tasaki, gabobin jikinta suka saki lokaci daya

Motsi tafara tanaso taraba jikinta danasa, cikin shagwaba tace "ya Abba please kasake ni mana, Momy fa zata iya zuwa"

Wata irin murya yayi magana da'ita, wadda tunda take dashi bata taba Jin muryar sa hakaba, cikin shagwaba yace "to kice kin yafemin mana please "

Ahankali ta zare jikinta daga nasa ta kalleshi tace "ya Abba kenan, kada kadamu, nayafe maka, komai yawuce kaji ya Abba na, duba kaga yanda ka rame, Pls kasaki ranka kaji?"

Yace "da gaske kike kin yafemin?"

Tace "ya Abba, nace nayafe ma, komai yawuce fa, Muje ka rakani unguwa...."

Cikin sauri yafarka daga mafarkin dayake 🤣🤪
Sakamakon qaran wayarsa data tashe shi, a dalilin wani abokin aikinsa dayake kira


Kansa yadafe da hannunsa duka biyu ya furta kalmar "Innalillahi wa inna ilaihir raju'un..." 🤦🏻‍♂️

Jikinsa yataba yaji zafi sosai, ga kansa dake sara masa, zuciyarsa ce yaji tana tashi, cikin sauri yasauko daga gadon yanufi toilet yafara kwara amai, babu komai acikinsa sai riqe cikin sa yake ga ciwon kai, ga zazzabi, haka yadawo ya kwanta agadon, yanzu duk abinda yafaru dama mafarki yake? Ya Allah!

Saida yaji dama dama sannan ya koma toilet din yayi wanka, yadauro alwala yafuto, jallabiyar sa yasaka fara qal da ita, sannan yatada kabbarar sallah, yadade yana sallah sannan yadaga kansa ya kalli agogo yaga sha biyu da kwata

Ahankali yamiqe, yafuto daga dakin nasa, kai tsaye dakin Nihla yanufa, wannan shine karon farko daya fara shiga dakinta

Ahankali yatura kansa cikin dakin, tana kwance agado wayarta da ya yusif ya aiko mata take gani, tana sanye da riga da wando na bacci, wandon ko gwiwar ta baizoba, rigar ma batada tsawo hakan yasa fararen cinyoyinta suka fara futowa

Ganin mutum kawai tayi akanta, cikin sauri tatashi zaune tace "subhanallah... Ya Abba lafiya?"


Ahankali yake ta kowa har yazo gabanta, ganin yana nufota yasa taja blanket din kan gadon tadora a jikinta

Bai tsaya a ko'inaba saida yazo saitin qafafunta, yazuba gwiwar sa aqasa har kafarta tana gogar gwiwar tasa

Shiru yayi yazuba mata ido yana Kallanta, Bece da ita komai ba

Nihla sai kallan mamaki take masa tace "lafiya ne?"


Ahankali, cikin sigar rada yace "kiyi hakuri"

banda dare ne kuma su kadai ne a dakin Babu abinda zai hana takasa jin Mai yace

Tace "for what"

"for Everything, please kiyafemin, nakasa bacci, hankali na yakasa kwanciya, meyasa bazaki yafe minba Nihlaaaa" ya qarasa maganar yanajan sunanta

Shiru tayi masa batace komai ba, Yakalleta yaci gaba da cewa "nasa ranki yabaci saboda nafasa miki wayarki, kiyi hakuri, insha Allah bazan sakeba, but kidena waya agabana, raina yana zafi, idan kikaci gaba dayi zan'iya fasa gaba dayan wayoyin hannunki, Allah ne yasakamin kishin ki acikin zuciyata, bazan dena ba kuma saboda ina qaunar ki, Nihlaaa! kidubi girman Allah kiyafemin, kisoni"

Kallansa tayi, mamaki ya kamata, lalle ya Abba

Ahankali tace "idan kagama inaso Zan kwanta, a tunani na mun dade da gama wannan maganar, babu abinda yayi saura bayan wannan"

Tana fadar haka takwanta, tajuya masa baya sannan taja blanket dinta tarufe jikinta dashi gaba daya

Bayanta ya kalla, yau shi Nihla take juyawa baya, shine yasa kafarsa aqasa yana neman yafiyarta amma taqi, yau shida Nihla takeso shine takasa bashi soyaiyar ta akaro na biyu

Dumin dayaji akan kumatunsa ne yasa yagane hawaye ne suka zubo masa, ahankali yasa hannu ya share, yamiqe yafuto daga dakin tareda ja mata kofar dakin

Yadade awajan ya tsaye idonsa arufe, tsayuwa ma neman gagararsa take, cikin damuwa ya juya yana tafiya ahankali Kamar zai fadi, yayi hanyar dakinsa

Momy ta duba gefenta taga Alhaji yayi bacci, ahankali ta sauko daga kan gadon tafuto daga dakin nasa, Allah nagani bazata iya runtsawa batare dataga halinda yaranta suke ciki ba, dakin Nihla tafara zuwa taganta tana bacci amma wutar dakin akunne, tasa hannu ta kashe mata wutar sannan tajuya, Nihla tana jinta, saboda ba bacci takeba

Dakin Abba tanufa, tana budewa taganshi azaune atsakiyar gadonsa yana kuka wiwi

Gaban Momy yafadi, cikin sauri ta qarasa wajansa tana fadin "Innalillahi wa inna ilaihir raju'un... Abba!!"

Tana qaraso wa wajansa yafada jikinta, kansa tashafa tace "me yafaru?"

Ahankali yazame yadora kansa akan cinyarta, cikin kuka yace "Momy bata sona, naje wajanta yanzu taqi kulani, Momy zuciyata zafi take min, rannan ma nabata hakuri taqi kulani Momy, yanzu ma haka,Momy ya zanyi? Wallahi ina sonta, kowa Yaqi bani goyon baya, shikkenan ni Kowama ya tsaneni..." hannu tasa tarufe masa baki

Ahankali tace" kayi hakuri Abba, kadinga maimaita kalmar Innalillahi wa inna ilaihir raju'un, insha Allah zakaji sanyi aranka "

Beyi musu ba haka yafara fada cikin ransa, Momy tana shafa kansa, tunani fal ranta, ahaka sukai bacci, Momy de baccinta ragagge ne, amma shi ya danyi kadan

Kiran sallar farko ne yatashe su, taji jikinsa da zafi, tabashi magani yasha sannan yatafi masallacin gidan, ita kuma ta nufi dakin Daddy



Bayan an idar da sallar asuba Momy bata koma bacci ba, addu'ah taci gaba dayi har gari yawaye tashiga kitchen da kanta tafara hada musu break fast

Karfe tara da minti uku tagama komai, takai musu kan dining, har lokacin Nihla bata futoba da alama bata tashi ba, Abba ma haka

Hanyar dakinta tanufa zataje ta watsa ruwa wayarta tayi qara, duba me kiran tayi mamaki ya kamata, afili tace "Mai hakuri!"

Sannan tadaga wayar, bayan sun gama gaisawa baba yace "hajiya dama maganar yar taki ne"

Tace "to Allah yasa de bamuyi laifi ba,"

"A a bakuyi laifin komai ba, jiya de munzauna da mahaifin Yusif dakuma yan'uwana dasuke yalleman, anyanke ranar bikin yartaki nanda wata biyu masu zuwa insha Allah, saiki fada mata, sannan kuma idan ansamu lokaci Zan turo muku da naku goron saka ranar saiki rabawa mutanan gidan "

Jikin Momy yayi sanyi sosai, cikin sanyin jiki tace" to shikkenan Ibrahim, mungode sosai, Allah yasa ayi damu, insha Allah zan sanar mata itama idan tatashi, yanzu tana bacci "

Yace" to shikkenan hajiya, ki gaida mutanan gidan "

Daga nan sukai sallama, Momy ta zubawa wayar ido tana kallo, wannan al'amari yafara bata tsoro fa, qamshin turaren daya saka ne yasa tadago kanta da sauri ta kalleshi, sanye yake cikin qananun kaya dasuka karbi jikinsa, ta kalli fuskarsa tayi fayau, kana ganinsa zaka hango tsananin damuwa a tattare dashi, tace "Abba na katashi?"

"yes natashi Momy, good morning"

Bata kula da gaisuwar dayake mata ba tajashi har dining tace "zoka zauna nabaka abinci, duk idonka yafada, kacire damuwa aranka fa"

"A a, Momy, bazan iyacin komai ba, kibarshi kawai, inaso zanje saudia, may be nadawo after 3 day's, Momy nasan Daddy yana fishi dani, Kibashi hakuri, kifada masa naje saudia"

Tausayinsa ya kamata, duba yanda yashiga damuwa ahaka ma baida labarin saka mata rana, ahankali tace "saika dawo, zan sanar dashi, amma kayimin alqawarin zaka kula da kanka"

Badan yaso ba ya qaqaro Murmushi   yace "insha Allah Momy"

Ahankali yatashi yafita daga falon Momy tabishi da kallo jiki a sanyaye





Sharhi please 🙏











Amnah El Yaqoub ✍️
[7/11, 11:52 PM] El Yaqoub: ❣️DANGI 'DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}


Writing by Amnah El Yaqoub

Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493


49&50


Tasan cewa ba komai ne zai kaishi saudia ba saidon saboda damuwar dayake ciki
Kuma hakan ma tunani ne Mai kyau, domin kuwa addu'ah ita kadai ce mafita Awannan halin da yake ciki, ta Inda yake birgeta kenan, kokadan baya Manta Allah acikin dukkanin al'amuransa

Dakin Daddy tawuce domin sanar dashi yanda sukai damai hakuri

Tana shiga taganshi yafuto daga wanka yana shirya wa

Waje tasamu tazauna agefen gadon tace "Alhaji barka da tashi"

"yawwa Rahma"

Tasake dubansa tace "Alhaji kana nunawa al'amarin yaron nan Kamar bai dameka ba, kuma yana cikin matsala sosai fa, jiya kasa bacci yayi, ita Nihla taqi amince wa dashi, kai yazo da maganar ka koreshi, yanzu haka jikinsa Babu dadi yatafi saudia nasan kuma saboda hakan yatafi, dazu Mai hakuri yakirani yace ansawa Nihla rana nanda wata biyu bikin "

" daidai kenan "

Cikin sauri ta kalleshi tace" Alhaji,yakamata aduba wannan al'amarin, bazai iyu nasamu yarinyar nan da batun taso danaba, Kamar na tursasata ne, tunda batayi niyya ba"

"kinsan da hakan kikazo kikemin magana, ni mezan iyayi akai?"

"Alhaji kaine kuwa zaka iyayin komai, tunda idan kafada tazauna"

"ba kuma zan fada dinba bare tazauna, angama break fast ne?"

Momy ta kalleshi cikin mamaki, Annabi yayi gaskiya dayace abu uwa har sau uku, sannan yace uba 🤣

Tace "angama"

Sannan tashige toilet domin yin wanka


Zaune suke a dining Sunayin break su uku, Momy ta kalli Nihla cikeda kulawa tace "Dazu munyi waya da Mai hakuri yace zai aiko mana namu goron"

Dago kanta tayi "Momy goron me?"

Cikin farin-ciki Momy tace "nasaka ranar yata nanda wata biyu"

Cikin kunya tasa hannu ta rufe idonta

Daddy yayi Murmushi ya kalleta yace "saiki Rubutamin list din abinda kike buqata kije daki ki dauki atm dina kuje keda yayanki kusiyo, abinda Babu kuma saiki shirya kuje Dubai keda momynki kusiyo Acan"

Kanta aqasa cikeda kunya tace "nagode Daddy"

Momy ma tayi Murmushi cikin ranta tana Jinjina irin yanda Allah yasaka musu qaunar yarinyar aransu baki daya



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Tunda yaje saudia baije ko'inaba, yana zaune cikin harami yana addu'ah, ya kashe wayoyin hannunsa, bai nemi kowaba, kuma bayason a nemeshi adede wannan ranakun
Addu'ah yake Allah yakawo masa mafita akan wannan al'amari, idan har Nihla matarsace to Allah yahuci zuciyarta ta soshi, idan kuma ba matar sa bace Allah yabashi hakuri da juriya akan rashin ta, Allah kuma yasa hakane yafi alkhaairi a gareshi

Sosai yaduqufa wajan neman zabin Allah, yana kaiwa Allah kukansa saboda shine Mai kowa Mai komai,kowa ya juya masa baya, banda 'yan'uwansa da Aslam Babu Wanda yake sonsa da Nihla, sai kuma Momy datake tausaya masa, abinci ma ba sosai yake cinsa ba, gaba daya ya rame cikin kwana kin, ya lalace, ga qirjinsa dayake masa zafi sosai idan yatuno da cewa Nihla tayiwa baban ta maganar Yusif, jiyake Kamar ana zuba masa barkono acikin qirjinsa

Allah shine gatansa a yanzu, bashida wani gata daya wuce yakai kukansa wajan mahaliccinmu

Daren juma'ah kuwa yayi addu'ah sosai, yayi kuka yayi kuka harya gaji, sannan cikin dare yabiyo jirgi yadawo gida, su kansu su Momy basusan yadawo ba, saboda Saukar cikin dare yayi



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Zaune yake afalon shi kadai, yana sanye da three quater, da wata riga marar hannu, computer ce agabansa yana ta typing cikin sauri, gaba daya hankalinsa ya tattara shi akan abinda yakeyi

Momy ce tafuto falon sai ganinsa tayi, ta tsaya tayi turus, tace "Abba na yaushe kadawo Babu sanarwa?"

Dagowa yayi daga typing din dayake yadubeta "Momy cikin dare nasauka, bansan na tasheku ne shiyasa banje dakin ki ba"

"to sannu da zuwa, duk wayoyinka akashe, ina kabarsu ne?"

"Momy kashe su nayi wallahi, ina Daddy?"

Zama tayi a gefensa tace "yana dakinsa, yanzu zai futo shima"

Yace "Ok" sannan yaci gaba da abinda yake

Futowa tayi daga dakinta tayi kyau sosai cikin wani Material,qamshin ta dayaji ne yasa Ahankali yadago kansa ya kalleta, karaf idonsu yahadu, itace tafara janye nata idon, shikuwa Kallanta yayi yana mamakin canjawar datayi cikin kwanaki hudu, jikinta yayi lumai, sai wani qara cika takeyi, hankalin ta kwance
, sauke kansa yayi yaci gaba da abinda yake

Momy ta kalleta tace "wannan gyaran jikin nasu gaskiya sun iya sosai, idan aka miki na 3week ma ya'isa, saiki zauna agida kidena fita ko'ina, saiki sanar awajan service din naku ma"

Tace "to Momy"

Ta kalli Abba dake zaune yana typing amma tunani ne da tambaya fal ransa, gyaran jikin me ake mata? Ko bikin qawarta za'ayi? 🤔

Bai samu amsar Tambayar tasaba yaji tace "Ya Abba ina kwana"

Wani irin sanyi yaji aransa, koba komai yana jin dadin yanda take kiran sunansa, gaba daya jiyake Kamar tafi kowa iya fada
Idanunsa har wani lumshe wa suke yadago yazuba mata wani irin kallo Mai karya garkuwar jikin yanmata 🤣
Cikin kulawa yace "lafiya"

Daga haka bata sake cemasa komai ba, Momy ma taji dadin yanda Nihla koda wasa bata raina yayun nataba, gashi de Abba bawani shiri sukeba, ba qaunar sa takeba, amma tana bashi girman sa yanda yadace

Momy tace "Nihla jeki kitchen kidaukomin wannan garon, saiki kaiwa maqota"

Ahankali tatashi, yana jin tashin ta yadaga kansa yabita da kallo, ba komai ne yafi daukar hankalinsa ba irin hips dinta, Momy ta kalli Abba taga inda hankalinsa yake ta girgiza kai 🤣

Saida yaga tashige sannan yasaki wata ajiyar zuciya Mai nauyi, yamaida hankalinsa ga abinda yake

Murmushi Momy tayi cikin ranta tace oh Abba, babu ta ido, inaga mantawa yake da kowa idan Nihla tana waje, agefe daya kuma tausayin dannata yana damunta

Goron takawo da alawa Momy tafara yimata bayani "kikai duka gidajen Dan Allah, idan an tambayeki na menene kifada musu, idan kuma bazaki iyaba kice su kirani awaya"

Tace "to Momy"

Kasancewar unguwar Babu mutane sosai yasa tasaka hannu ta kunce Babban dankwalin kanta, gashin kanta yazubo gafen fuskarta, tasa hannu ta maida shi baya sannan tayafa dankwalin a jikinta kasancewar da girman sa, tadauki goron tanufi hanyar fita

Cikin sauri yatashi yasha gabanta yaje bakin kofar falon ya tsaya, daga Momy har Nihla mamakin yanda yayi tsalle yaje bakin kofar dakin ya tsaya suke 🤣

Shikuwa ko ajikinsa yace "haba Momy Dan Allah, ya za'ayi kibarta tafita ahaka, haka kawai taje tadauko mana magana"

Momy ta girgiza kanta "Abba kabata hanya tawuce mana, menene haka"

Cikin shagwaba yace "gaskiya Momy a a"

Momy ta dubi Nihla tace "dawo ki zauna Nihla, bani goron"

Babu musu tadawo tazauna tareda bata goron

Momy ta kalleshi tace "to tunda ka hanata kaiwa, gashi saikazo kakai"

Yace "wai goron menene ma Momy, saikace masu shirin taro"🙆🏻‍♀️

Momy kanta tsaye tace "goron saka ranar qanwar ka ne, na saka ranar auren Nihla ne"

Wani dummm! Yafara ji akansa, gabansa yafara faduwa, numfashinsa yafara yin sama, daqyar ya'iya cewa "Momy saka rana kuma?"

Momy data fara tsorata da yanayin sa yace "emana, menene?"

Hannu yasa yadafe kansa dake masa mugun ciwo, qirjinsa ya riqe numfashi yana neman gagararsa, ahankali yadora dayan hannunsa akan qirjinsa, Idanunsa suka fara rufewa, yafara ganin duhu-duhu har suka rufe gaba daya yadena gani dajin komai, nan take ya sulale awajan yafadi

Cikin sauri Momy tayi kansa tana fadin "Innalillahi wa inna ilaihir raju'un.... Abba!"

Girgiza shi tafara yi amma Babu alamar numfashi awajan Abba, gaba daya Momy ta rikice sai jijjigashi take, hasbunallah wani'imal wakil... Abinda take guje musu kenan dama, nan take hawaye ya balle mata

Ta kalli Nihla cikin kuka tace" yi sauri ki kira Daddynku mutafi asbiti"

Da gudu tajuya zuwa dakin Daddy yana zaune yana duba jarida, ganin yanda tashigo dakin hankali tashe yasa yatashi tsaye da sauri yace "lafiya?"

"Daddy kazo inji Momy"

Cikin sauri yafuto itama Nihla ta biyo bayansa, yana qarasa wa wajanda Abba ke kwance ya tsugunna yana taba fuskarsa yace "meyasa meshi ne Rahma?"

Cikin kuka tace "Alhaji kaga abinda nake fadama ko? Kaga irinta ko? Babu abinda aka masa, kawai dagajin ansa ranar Nihla shine yayanke jiki yafadi"

Daddy yace "subhanallah... Kamamin shi Muje asbiti"

Daqyar suka dagashi, suka tafi asbiti baki dayansu, sai adala kawai aka bari agidan

Zuwan su asbiti keda wuya likitoci suka karbe shi cikin gaggawa, suka shiga bashi temakon gaggawa, Daddy da Momy kam kasa zama sukai, sai Nihla ce take bawa Momy hakuri akan tadena kukan datake amma ina! Hawaye Yaqi tsayawa a idanun Momy

Sun kusa awa daya da zuwa asibitin sannan likitocin suka futo, cikin sauri suka nufesu suna tambaya

Babban cikin su yace "kuyi hakuri Alhaji, ku kwantar da hankalin ku, amma Dan Allah ku kiyaye fadar abinda zai dinga tsorata mutum lokaci daya, yanzu haka danku yaji abinda ya tsorata shi ne sosai, shiyasa yasuma, kuma dama bugun numfashin sa ba normal yake fitaba sakamakon ciwon da zuciyar sa take son kamuwa dashi "


Daga Momy har Daddy hada baki sukai wajan fadin
" ciwon zuciya Doc.?

Kai tsaye yace "qwarai kuwa, amma tunda kunzo asbiti insha Allah zamuyi kokarin ganin yasamu lafiya, yanzu za'a futo dashi a sauya masa daki"

daga haka ya juya yabasu waje

Momy kasa magana tayi daga nan, kawai de tana goge hawayen idonta, kuma har zuwa yanzu kokadan batajin haushin Nihla, fatanta daya, Allah yabawa danta lafiya


Daddy yakira Alhaji Basiru da Alhaji Baqir ya sanar dasu abinda yake faruwa, nan take suma suka Garzayo asbitin
Cikin lokaci qanqani jinyar Abba tacika family din Mazawaje



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️

Aslam yafi kowa shiga cikin tashin hankali, musanman daya tambayi Momy menene yake faruwa tafada masa komai bata boye masa ba, haka Yazauna yana tunanin mafita
Nihla ya hango tareda Ilham azaune agefe, tana riqeda lil Abba a hannunta

Ahankali yataka yaje wajansu Yazauna, yadubi Nihla tareda miqa mata wayarsa yace "qanwata temakamin da number Angon namu mana"

Murmushi tayi kadan, ta karbi wayar tasa tasaka masa number ya Yusuf aciki, sannan tabashi, ya karba yayi godia

Wayarta ce tahau qara, tana dubawa taga ya Yusuf ne, tadauka

Ilham da Aslam suka kalleta, cikin zazzakar muryarta yace "hello ya Yusuf , yakake yagida"

"lafiya amarya ta, nashigo kano fa, zanzo naganki inaso naji shirye shiryen dakika tsara, saina wuce daga nan"

"Ayya ya Yusuf ai bana gida, munzo asbiti ne, saide nayima kwatancen wajan saimu hadu anan, kaga sai Muje gidama nahadama wani abin kaci"

Be tambayeta waye baida lafiya ba yace "toki turomin adress din Inda kike yanzu"

Sunan asbitin kawai tafada masa yace yana kusa, tace to zata futo waje bakin titi Inda zai ganta

Wayar ta kashe tadubi Ilham tace "zanje waje nadubo ya Yusuf "

Ilham tace "to shikkenan"

Ahankali ta miqe tafuto, Aslam ya kalli Ilham yace "kibita mana, kidan bata shawara ko zata saurareki"

Kallan mijin nata tayi, duk yashiga damuwa, tarasa wacce irin soyaiya sukewa tsakanin su shida ya Abba, tace "to" sannan ta biyo bayan Nihla

Daga murya tayi ta kirata, Nihla ta tsaya ta, sannan ta qaraso sukaci gaba da tafiya
Ilham tace "ya Aslam ne yace nazo naraka ki"

Nihla tace "Allah sarki, kinga salihin miji, wallahi idan ya Abba ne bazai bar matar saba"

Murmushi tayi tace "nikam Nihla nabaki shawara mana"

"inajinki" cewar Nihla

Shiru Ilham tayi, saida suka qaraso bakin titi suna jiran ya Yusuf ya qaraso sannan tace "Nihla Dan Allah meyasa bazaki tausaya wa ya Abba ki aure shiba?"

Cikin sauri ta dago kanta ta kalli Ilham tace "aure fa kikace Ilham"

Hannunta Ilham takama hannunta ta riqe tace "eh, aure nace Nihla, to menene aciki idan kin aure shi? Nihla wacce irin zuciya gareki?yaushe kika koma haka? Mutumin nan yayi miki laifi kuma yabaki hakuri, babu wanda baya aikata kuskure acikin Rayuwar sa Nihla, saide na wani yafi na wani,kidinga tunawa ya Abba dan'uwana ne da'aka bar wasiyya cewa kuyi aure, Nihla ubangijin daya haliccemu ma muna aikata masa laifi muroqeshi gafara yayafe mana, haba Nihla, yanzu ashe bazaki iya tausayawa yaron Momy ba? Bazaki iya ceto yaron Daddy daga halin da yake ciki ba? Nihla wannan shine sakayyar dazaki nunawa Momy kenan? matar da tasoki Tun kina qarama kina gaban mahaifiyarki? Duk cikin yaran Momy Babu Wanda ya qyamaceki Nihla, kowa kokari yake yaga yafaranta ranki, Momy tana qaunar ki Nihla, Inda wata uwarce da tuni ta sauya miki, suna qaunar dansu fa, soyaiyar dasuke miki ce tasa bazasu iya nuna miki komai ba, idan kina tuna laifin dayayi miki bazaki taba yafe masaba, kuma bashi zaki dubaba, a a, iyayen sa zaki duba, kinji de abinda likita yace, zuciyarsa tana gab da kamuwa da ciwo, kuma komai yana hannun ki, idan kinso zaki iya ceto Rayuwar Dan mutanan dasuke kaunarki Kamar yarsu ta cikin su, idan kuma kinso zaki iya barin sa, amma kiyi tunani akai "
Tana gama fada mata tayi shiru tareda sakin hannunta

Zuciyarta fal da tunanin maganganun Ilham, tabbas maganar ta Babu ta yarwa aciki, Momy uwace abar alfahri ako'ina, to amma baban ta fa? Tayaya zata iya nusar dashi? Tayaya zata fuskanci ya Yusuf da wannan maganar? adede lokacin yaqaraso wajansu, suka gaisa cikin kulawa, ahankali suka qarasa cikin asbitin
Ya kalleta yace" yanaga jikinki yayi sanyi ne? Waye baida lafiya? "

Murmushi tayi tace" lafiya ta kalau ya Yusuf , ya Abba ne baida lafiya, dukanmu ma muna ciki, ko zaka qarasa ku gaisa da Momy duk suma suna ciki "

Yace" why not "

Ahankali suka qaraso cikin asbitin, cikeda kulawa Yusuf ya gaisa da kowa, sosai Momy ta ware suka gaisa dashi Kamar Babu abinda yake damunta

Suma su Daddy sun yaba da halin sa sosai, kowa dayake wajan yayaba da tarbiyarsa, babu laifi yanada nutsuwa

Likita ne yazo yace zasu iya shiga su ganshi yanzu, gaba dayansu kuwa suka nufi dakin

Yana kwance hancinsa sanye da oxygen, ga kuma na'ura agefen kansa tana aiki, dakuma wadda take nuna yanayin hawa da Saukar numfashin sa

Cikin sauri Momy ta qarasa wajansa, ta dora kanta agefen gadon tasaki wani irin kuka, tama kasa magana sai kuka datake sosai

Hajiya Farida ce tazo ta janye ta tana bata baki, gaba daya dakin Babu Wanda bai tausayawa Abba ba, ajikin hajiya Faridanma bata dena kukan ba, tari yafara Ahankali, duk hankalinsu saiya dawo kansa, Tun yana tari Ahankali harya dawo yanayi sosai, Aliyu yayi sauri yakira likita, likitan na zuwa yace Dan Allah su fita daga dakin, gaba dayansu suka futo

Aslam yaja Yusuf gefe suna magana, wadda Babu Wanda yasan akan me suke tattaunawa saboda sunyi nesa da mutane


Saida suka gama magana sannan Yusuf yakira Nihla, suka tafi zata rakashi wajan motarsa, har tana mamakin wacce iri magana ya Aslam yayi masa? Kuma menene dalilin karbar number sa awajan ta?
Har gaban motarsa sukaje yashiga Yazauna amma bai rufe motar ba, ta kalleshi tace " banji kace komai ba, akan maganar da mukai waya"

Memakon yabata amsa sai yace "Wancen gayen yacemin sunansa Aslam, yayi min magana akan ki, yace ma ya karbi number ta awajan ki zai kirani kuma sai akai sa'ah nazo, yafadamin saboda ke Abba yake rashin lafiya, kece maganin damuwar sa, yayi min bayani sosai akan hakan, kuma na gamsu da bayanin sa, Nihla why not muhaqura ki auri Abba?"















Mutara zuwa gobe insha Allah 🙏🏻




Sharhi please










Amnah El Yaqoub ✍🏻[7/12, 9:57 PM] El Yaqoub: ❣️DANGI 'DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub



Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493



51&52


Lokaci daya idanunta suka cicciko da qwallah, ta dubeshi muryarta na rawa tace "ya Yusuf... Mekake fada hakane? Meyasa zaka qini saboda shi?"

"ba saboda shi nafadi wannan maganar ba Nihla, kinsani ina son ki, tunda kina qarama, Tun bansan menene so ba nake tare dake acikin zuciyata, halin da suke ciki shida iyayen sa zaki duba, mutanan nan sun karbeni hannu bibbiyu Babu Wanda ya nunamin komai ko akan fuska, sunada karamci Nihla "

" yanzu me kake nufi kenan?"

" ki auri Abba Nihla"
Batare daya shiryaba hawaye yazubo masa yasaka hannu ya goge cikin sauri sannan Yarufe motar tareda dora kansa akan sitiyarin motar yana kuka

Kallansa tayi tasaki wani irin kuka tareda juyawa ciki aguje tana kuka


Usman dake zaune gefensu Daddy yace "yanzu Daddy ai sai a fadawa su baba Ibrahim adaga wannan aure na Nihla, mu dangin mahaifiyarta bamu shirya ba, saboda Abba bashida lafiya"

Alhaji Baqir yayi Murmushi yace "naga alama de Usman bakason wannan auren ko"

Kansa ya sosa yace "A a kawu, danaga wai hankali ba'a kwance yakeba"

Murmushi yasake yi, amma Daddy de yayi shiru baice komai ba, zuwa yanzu kam kodan ceto Rayuwar dansa yakamata yaje su Gana shida Ibrahim Mai hakuri, yakamata su shirya suje su sameshi


Cikin kuka tashigo wajansu, gaba daya hankalinsu yadawo kanta, Nihla kuwa bata zarce ko'inaba sai wajan Momy, fadawa tayi jikinta tana kuka sosai, Momy tace "me yake faruwa Nihla?keda waye?"

Shiru tayi takasa bata amsa, mezatace mata? Saboda ance na auri danki nake kuka kome? Dan haka tayi shiru, Momy tasa hannu tafara bubbuga bayanta alamar rarrashi, haka tayi shiru amma cikin ranta wani kukan takeji tanaso tayi, Ilham tataso tace" kitashi mukoma can "

Babu musu tabi Ilham suka koma gefe sai Jan zuciya take, Ilham bata tambayeta dalilin kukan ba, tabarta tagama hucewa tukunna

Nihla tayi shiru tana tunani, ita kuma tata qaddarar kenan, sai anzo auren ta afasa, yanzu gashi shima yace ta auri Abba, hakan yana nufin za'a sake fasawa kenan akaro na biyu



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Washe gari Alhaji Basiru da Alhaji Baqir dakuma Daddy da Alhaji habib mijin hajiya Farida suka shirya sassafe suka nufi Abuja
Saukarsu keda wuya Alhaji Isma'iel da baba sukayi musu masauqi acikin falon nasu, baba sai mamaki yake irin wannan zuwan nasu

Saida suka gama gaishe gaishe sannan Daddy yadubi ma hakuri yace "Ibrahim wajan ka mukazo gaba dayanmu nan da qoqon bararmu, haqiqa munyi maka laifi abaya, kuma muna qara neman kuskure, ba kuma komai ne yasa nina aikata hakaba saidon kaunar yar'uwata Aisha dakuma abinda kuka haifa, Awannan lokacin kokadan banaso nayima magana akan Zan dauki Nihla natafi da ita, saboda nasan yanda kake jin mutuwar Aisha kaima bazaka so karabu da yarka ba, nikuma ina qaunar yarinyar, hakanne yasa nadauke ta muka tafi, maganar aure kuma da bamu sanar makaba wannan ma mun dauki laifin mu, amma maganar gaskiya itace banine nayanke wannan hukuncin ba, iyayen mune, bawai ikona bane hakan, amma kayi hakuri "

Baba yayi Murmushi yace"haba Alhaji, ai Babu komai, komai yariga yawuce, rannan ma kuwa Shima Abubakar yazo shida Aslam"

Mamaki yakama su Daddy, ashe su Abba sunyi hankali, Alhaji Baqir mahaifin Aslam yayi Murmushi cikin ransa yace shikkenan ma sun rage mana hanya, yadubi baba yace "ai Abubakar dinma bashida lafiya, yana kwance a asbiti yanzu haka, zuciya ce takeson yimasa ciwo, amma batakai ga farawar ba"

Alhaji Isma'iel yace "subhanallah... Subhnllh, kode shine yaron da Yusuf yake fadamin bashida lafiya?"

Baba yadubi Alhaji Isma'iel yace "A a yaushe Yusuf din yaje kano?"

Alhaji Isma'iel yace "toni jiya yazo yake min kuka waishi afada maka sun hakura da aure shida Nihla, saboda akwai wani dan'uwanta dayake rashin lafiya akanta, wai kada ya mutu a dalilin su, toni kuma ban dauki zancen nasa serious ba, tayaya kuna tareda yarinya zakace kunfasa, ban yarda da maganar tasaba, shiyasa ma ban yiwa mai hakuri maganar ba "

Alhaji Baqir yayi Murmushinsu na manya yace" wallahi shine, ai mungaisa dashi jiya, Yusuf kenan, Yusufa yaron kirki "🤣

Alhaji Basiru yayi gyaran murya yace" ai jikin nasama da sauqi, har yanzu de bai farfadoba,"

Baba ya Jinjina kansa yace   " inafa lafiya kana cewa yaro har yanzu bai farfado ba "🤣

Alhaji Isma'iel Yace"Allah sarki, Allah yabashi lafiya, to amma ina ganin tunda yara sun fahimci juna harshi Yusuf din yayi jihadi, to ina ganin kawai ayi hakuri gaba daya tunda kowa ya fahimci kowa yanzu, sai adaura musu aurensu kawai, idan Allah yabashi lafiya duk wata bidi'ah da za'ayi suyi daga baya "

Farin ciki yakama Daddy, da kansa yasauko daga kan kujerar dasuke kai yafara yiwa Alhaji Isma'iel godia, Alhaji Isma'iel yace

"  Babu komai ai matar mutum kabarinsa "


Alhaji Baqir yace" toni ina ganin, tunda abin yazo da haka, memakon Muje musake dawowa, kawai asiyo goro yanzu adaura, shikkenan anhuta "

Alhaji Isma'iel yace" A a akwai goro, Muje masallaci anemi liman yadaura musu auren, ni Zan zama waliyin Nihla "

Baba yakasa magana ganin irin karamcin da Alhaji Isma'iel yayi masa, haqiqa samun irinsu a yanzu sai antona

Gaba dayansu kuwa suka futo, kai tsaye masallacin unguwar sukaje aka kira liman, da maqocin Alhaji Isma'iel Wato baban Nadiya, Alhaji Baqir yaje banki da kansa yaciro kudi, yace shine zaiyi wa Abba waliyi, nan take kuwa aka daura musu aure akan sadaki nera dubu dari, aka danqawa baban ta sadakin, kowa aka bashi goro,  suka yiwa limamin ihsani, sannan suka futo kowa zuciyarsa fes

Daga nan su Daddy sukayi wa su Alhaji Isma'iel godia, suka nufi Airport

Mamy da taji labarin abinda yafaru ta tausayawa Abba, saide wani bangaren na zuciyarta yana jimamin rabuwarta da Nihla, taso ace danta Yusuf yasameta, amma yaya za'ayi, matar mutum kabarinsa



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️




Zuwan su kenan asbitin itada Dida da Ilham, Diyana bata zoba tana fama da cikin ta, Ilham sai fada take mata "kintashi kinsaka wa kanki damuwa ina dalili? Tunda shine yace zaiyi hakuri yaya zakiyi dashi, amma Tun jiya kidinga kuka,Yaya zakiyi da qaddarar da Allah yadora miki, kokuma zuwa zakiyi wajan Yusuf din kijashi ta qarfi, kuma Momy tayi miki Tambayar duniya kinqi bata amsa, yanzu idan taji saboda Yusuf yace yafasa aurenne saboda danta ya warke kike kuka ai ba zataji dadi ba, menene amfanin rashin mantuwa da ruqo Nihla "

Itama Dida tace"wallahi de kam, idan ma kina tunawa da lokacin da yace baya son ki ne agaban family ai yakamata ace zuwa yanzu kisan cewa saboda ke dinne ya kwanta jinya, idan mutane kowa da kowa yaji ya Abba yace baya sonki to yanzu kowa ya shaida ya Abba yadawo yana sonki, kuma gashi Akwance baisan wake kansa ba saboda ke, duk cikin mu waye yasamu irin wannan soyaiyar? Yakamata ki godewa Allah Nihla "

Nihla tayi shiru tana jin maganganun yan'uwanta, ahaka suka qaraso cikin asbitin da hannunsu dauke da abinci, kasancewar ba'a barin kowa yashiga dakin dayake shiyasa suka nemi waje suka zauna, sai Momy ce kawai acikin dakin nasa

Daddy ne yashigo asbitin fuskarsa dauke da farin-ciki Kamar ba dansa ne baida lafiya ba
Su Ilham suka gaida shi, sannan Nihla takira wayar Momy tafuto daga cikin dakin

Gaisawa sukai dasu Ilham suka qara yimata, yamai jiki sannan suka bata Abincin, Momy taji dadi sosai tayi musu godia sannan sukai mata sallama suka tafi, sukabar Nihla awajan

Tazauna tana duba wayar hannunta, Momy dake gefe itada Daddy tace "Alhaji yanaga kanata Fara'ah ne? Allah yasa lafiya"

Murmushi yayi yace "daga Abuja muke"

"Abuja kuma Alhaji, meyake faruwa"

Hannu yasa a aljihunsa yadauko goro yace "riqe wannan goron"

Momy ta karba tace "na menene Alhaji?"

Yace "goron daurin auren Takwarana ne shida yarki"

Momy ta zaro ido tare saka hannu abaki cikin mamaki, takai Kallanta wajan Nihla taga hankalinta yanakan waya
Tace "Alhaji da gaske kake?"

"da gaske nake, ga shaida nan kingani, shikkenan Abba sai hankali ya kwanta"

Momy tasaki ajiyar zuciya tace "Alhamdulillah... Allah nagode ma, to Alhaji binka zanyi mutafi gida nayi wanka nahuta nima, tunda ga matar sa nan ita saita zauna ta dora daga ina na tsaya"

Daddy yayi Murmushi yace "to zo mutafi"

Abincin hannunta takai wa Nihla tace "Nihla riqe wannan Abincin, idan Allah yasa yau yafarka shikkenan sai kuci, akwai kayan Tea aciki, idan kuma bai farkaba sai kici, ni natafi gida sai munyi waya"


Mamaki yakama Nihla, tace "Momy gida kuma? Ba anan zaki kwana ba?"

Momy tace "a a, aina dena wannan zaman Nihla, yanzu kam saike" 🤣

Jikinta yayi wani iri, tayaya Momy zatace tazauna da ya Abba bayan tasan hakan bai kamata ba? Tace "to Momy kuma...."

Cikin sauri Momy ta katseta, "Nihla bafa Zan zauna ba, yau kema ki d'ana"

Tadubi Daddy tace "Alhaji Muje"
Har sun fara tafiya Tajuyo tace "yawwa Nihla Karki Manta likita yace kullum dasafe ana goge masa jikinsa da ruwa Mai Dan dumi, duk abinda kike buqata yana cikin dakin, idan baki ganiba saiki kirani"


Nihla ta kalli Momy takasa cewa komai, wai me Momy take nufi ne, ya za'ayi takama taba jikinsa bare har dasu goge jiki? 🤔

Momy kuwa bata jira amsar taba, suka tafi itada Daddy











Kuyi hakuri da wannan ba yawa

Sharhi please 🙏











Amnah El Yaqoub ✍🏻
[7/14, 2:19 AM] El Yaqoub: ❣️DANGI 'DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub


Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493


53&54



Jiki a sanyaye tajuya cikin dakin, ahankali ta tura kofar dakin tashiga, idonta yasauka akansa, babu oxygen din ancire masa, amma fuskarsa tayi wani irin fari, Dan qaramin lips dinsa ta kalla duk yafara bushewa, gashin idonsa sun kwanta gwanin sha'awa

Kujerar dake gefen kansa tazauna ta ajiye Abincin, sannan tayi shiru tana tunanin irin wannan zaman jinya, ko yaushe zai farka? 🤔

Ya Yusuf ne yafado mata, Allah sarki, tunda sukai maganar rabuwa dashi basu sake waya ba, tana mamakin yanda lokaci daya yace zai sadaukar da soyaiyar ta ga ya Abba, bayan tasan ya Abba da kishi idan shine ba lalle ya'iya hakura da itaba

Haka tazauna shiru ita kadai a dakin, lalle idan hakane Momy tayi kokari, amma tarasa Inda Momy tasa gaba, tayaya zasu barta daki daya da ya Abba?

Ajiyar zuciya tayi tajuya ta kalleshi, saikuma ta dauke kanta cikin sauri Kamar tana tsoro karya kamata



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️



Mutanan gida kam, kowa labari ya sameshi, saboda su Alhaji Baqir kowa daya koma gida yafadawa iyalansa, Aslam Kamar yayi me saboda murna, Ilham kuwa bakinta Yaqi rufuwa, haka tadinga d'aga lil Abba sama tanayi masa wasa Yaron kuwa sai dariya yake shima Kamar yasan abinda ake

Aslam Yazauna yanemi number Yusuf domin su tattauna kuma yaqara yimasa godia amma kiran duniya ya Yusuf bai dagaba, haka ya hakura, ya shirya da daddare domin suje asbitin shida Ilham, Ilham tazuba musu abinci, sannan tahada wa Nihla wani maganin mata, tatafi mata dashi, cikin ranta tana cewa gara tafara bawa qawar tata Dan abubuwan nan tanasha, tunda auren yazo a qurarran lokaci, kuma tasan halin Nihla yanda batason ya Abba yanzu tsaf zataqi sha, Dan haka gara tana zuwa dashi tana bata tanasha a gabanta

Zuwan su asibitin kenan suka kira wayarta tafuto, fuskarta Babu yabo Babu fallasa, ya Aslam sai Fara'ah yake yace "Amarya kinsha qamshi"

Nihla bata kawo komai ba, tunda kowa yasan ansa mata rana Dan haka tace "na'am ya Aslam"

Yace "yaya marar lafiyar naki kuma"

"ya Aslam namu de"

Yayi Murmushi yace "A a, mun barmiki, keda dan'uwanki, kinga ai yanzu yazama naki"

"duk da haka de ya Aslam, kaima ai dan'uwanka ne"

Ilham ce tajata gefe tace "ke rabu dashi, zomu zauna"

Tabashi Abincin tace "ga Abincin nasu, ka shiga musu dashi ciki tunda zakaga jikin nasa"

Abincin ya karba yawuce cikin dakin

Yau Tun safe ransa fari tas, Baqin cikin sa daya yanda Abba yake kwance bai farkaba, yaso ace shine mutum na farko dazai fara bawa Abba labarin aurensa da Nihla , amma yaya zaiyi? Wayarsa yafara dubawa yaga batanan, da alamun agida akabar masa wayoyin, yar drower din gefen gadon yafara dubawa cikin sa'ah yaga biro da wani littafi, cikin sauri yayagi qaramar paper yayi rubutu aciki, sannan ya linke takardar yaqaraso gaban gadon na Abba yana dube duben Inda zai saka takardar ko Allah zaisa Abba yagani batare da Nihla ta lura ba, hannunsa ya kalla, yadaga hannun yasaka masa takardar aqasa hannunsa, yasan ma Nihla zata gani, amma duk da hakade yana fatan karta gani din

Awaje kuwa Ilham ta   dubi Nihla  tace "amarya, amarya, ah ah, kaga amarya kinsha qamshi"🤣

Tsaki taja tace "keni ba wannan ne yake damuna ba, Ilham yanzu Dan Allah tayaya Momy zata tafi gida ta barni tareda ya Abba, bayan tasan surutun wannan family din yanzu sai kiji ankasamu a faranti ana qananun maganganu akan mu"

Ilham tace "Babu wani maganar da za'ayi, to waye ma ya'isa yace muku wani abu?" 🤣

"Ilham bazaki ganeba, bafa muharrami na bane sannan wai Momy harda cewa wai...." shiru tayi takasa qarasa wa

Ilham tayi Murmushi tace "kinga, ki kwantar da hankalin ki Nihla, babu abinda zai faru, tome zai miki shida bashida lafiya? Kisaki jikinki kiware ki kula da dan'uwanki, karkiji komai tunda su Momy sunsan kina tare dashi, kifa saki jikinki dashi" 🤣

Cikin sanyin jiki tace "to Ilham, amma de.."

Ilham tace "kinga, karbi wannan hadin kisha, kinga yanzu bawani zaman gida zakiyi ba bare Momy tadinga baki kina sha, kuma mazan yanzu saida gyara, ke masu gyaran ma yaya aka qare dasu, Dan haka gara kije gidan mijinki tsaf"

Babu musu takarba tace "to Ilham nagode"

Dariya sai cin Ilham take, Nihla kuwa bata kulaba

Fira sukaci gaba dayi har ya Aslam yafuto sannan sukai mata sallama suka tafi, ita kuma tajuya cikin dakin

Wajan shadaya na dare likita yazo ya dubashi yace "idan akwai matsala zaki iya kiranmu"

Tace "to"


Likitan nafita tadauki wayarta tafara kiran ya Yusuf amma baya dauka, Tun tana yin na marmari harta gaji da tadena, sai message ta tura masa

Tashi tayi tadauro alwala tazo ta shimfida sallaya tatada sallah, data idarma addu'ah kawai tayi tayi sannan tatashi ta linke sallayar takoma kan kujera tazauna, zuba masa ido tayi, gaskiya ya Abba qarshe ne, yahadu iya haduwa, halin sa ne bai haduba, ajiyar zuciya tasaki ta kalli girarsa datake kama da tata girar, Allah de yabashi lafiya tadena wannan zaman shirun

Tun tana kallansa tana tunani harta gaji tadan dora kanta agefen gadon nan take bacci ya kwasheta



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


"Rahma sai murna kike Tun safe"

Momy ta kalli Daddy tace "Alhaji ai dole nayi farin ciki, yau Abba na yasamu abinda yakeso, koda na mutu nasan yarana dukansu sun samu mata nagari"

Jinjina kansa yayi yace "hakane, Allah yabasu zaman lafiya"

"Amin Alhaji, ni dama nasan Dan bakasa baki bane, amma inde an fahimci juna ai komai Mai sauqi ne"

"hakane, yabata min raine yaron, haba yaro sai taurin kai"

"Hmm Alhaji kenan, kowa yasan de halin Abba gaba daya naka yadauko, kuma kaga laifin yaro?, amma Alhaji yanzu ai sai afara gyara musu gidansu, idan komai ya kammala saisu koma can"


Daddy yace "Haba Rahma, korar yaran nawa kuma kike? me zaisa sukoma wani waje Rahma? Da badamu suke zaune ba? Yanzu ma ai sai suyi zaman su"

Cikin sauri Momy tace "um um Alhaji, kayi hakuri da wannan maganar, ba zaman gidan kake bane shiyasa, amma nida nake zaune dasu nasan abinda yake faruwa, Abba bashida kunya gara su tafi kawai"

Murmushi Daddy yayi yace "to bansan de mekika ganiba, amma tunda kince haka, idan angama gyare gyaren komai saisu koma ai"


Tace "yawwa yanzu naji batu"


Asuba tagari Daddyn Momy 🙏🏻



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️




Karfe hudu da rabi na dare yaji kansa yasara, Ahankali Ahankali yafara bude idonsa

Hasken dayagani adakinne yasa yasake runtse idonsa sannan yasake budesu Ahankali, Nihla kuwa bacci yayi bacci kanta yanakan dantsan hannunsa tayi fillo dashi

Kallan kansa yayi anan ya tabbatar da asbiti aka kawoshi, ahankali yafara tariyo abinda yafaru dashi harya tuna komai, yana gama tunowa yaji wani irin Baqin ciki aransa

ga kansa dayake masa ciwo,qirjinsa nauyi idan yanajan numfashi, jin alamun mutum akan hannunsa dakuma gashinta daya bazu akan hannun nasa shiyasa yakai dubansa ga hannun damansa  anan yayi tozali da dogon gashin kanta, babu dankwalin yazame yafadi qasa
Gabansa yafadi,meyakawota nan?

Ahankali yafara motsawa zai tashi yaji hannunsa na hagu akan takarda, komawa yayi ya kwanta sannan yadauki takardar Ahankali baiyi tunanin komai ba yabude, mamaki ya kamashi, wannan ai rubutun Aslam ne

Ahankali yafara karantawa :
 _Ango mijin amarya, congratulation_ _Abokina, Allah yasa kada wani_ _yarigani sanar dakai cewa_ _Nihla tazama mallakinka_ , _but ka kiyaye batasan komai ba "_

Cikin sauri yatashi zaune Kamar ba marar lafiya ba, sai yaji yana nema yanemi ciwon kan nasa yarasa, ita kuwa Nihla jin kanta ya koma kan katifa yasa ta danyi motsi, sannan tasake gyara kwanciyar ta tajuya taci gaba da bacci

Dube dube yafara yana neman wayarsa amma bai gantaba, wasiqar yasake karantawa, ya karanta ta yakai sau biyar
Yajuya yasake Kallanta tana bacci hankalinta kwance, Hawaye ne suka zubo masa, yasaka hannunsa duka biyun ya share, sannan yadaga hannunsa sama yana yiwa Allah godia, domin kuwa yasan cewa banda addu'ah Babu abinda zaisa yasamu Nihla cikin sauqi


Alerm din wayarta ne yafara qara, Ahankali ya koma ya kwanta Yarufe idonsa Kamar me bacci, nan take masallatai suka dauki kiran sallah

Saida Alerm din yaqare yasake bugawa sannan tabude idonta, bacci takeji sosai
Kallan kanta tayi Babu dankwali tace "subhanallah," tadauko shi aqasa ta daura dankwalin ta sannan ta kalleshi, tasaka hannu ta gyara masa fillo din da kansa yake kai sannan tashige toilet, yana jin alamun shigar ta toilet yabude idonsa yatashi zaune yana daga hannu yana ta murna 🤣

Haka yaita murna saida yaji zata futo sannan ya koma ya kwanta, harta idar da sallah duk yana jinta, wayarta tafara qara, tadauka yaji tace "Hello Momy"

"Nihla kuna lafiya deko?"

"lafiya kalau Momy, yanzu na idar da sallah ma"

"toya jikin nasa"

"gashinan nan de Momy, har yanzu shiru"

"to Allah yasawaqe, Karki Manta da goge masa jikinsa de anjima, akwai Ruwan zafi a flask, anjima za'a kawo muku abinci"

"to Momy sai anjima"


Tayi shiru tana azkar, har gari yafara haske, ganin idonsa biyu kuma ga lokacin sallah yana wucewa shiyasa yafara bude idonsa Ahankali, ya kalleta da gefen ido yaga tayi tagumi tanajan carbi

Ahankali yafara cewa "Momy!, Momy!! Momy kaina"

Cikin sauri ta zabura tayi kansa "ya Abba! Katashi? Sannu, bari akira Doc."

Tajuya tafice daga dakin cikin sauri
Wani irin murmushi yasaki, yana jin wani masifar dadi aransa yabi bayanta da kallo, wai yau shine Nihla take nuna masa wannan kulawar, aikuwa in hakane Babu shi Babu warkewa🤣


Tare suka dawo da likitan, ya dubashi, yasake kallansa yace "abin mamaki, ya akai ciwon naka yaragu haka sosai?"

Maida kansa yayi majinyacin sosai, ya langabe yace "qirjina yana min ciwo kadan, kuma ko'ina ma ciwo yake min na jikina"

Doc. Yayi Murmushi yace "insha Allah Ahankali zaka dena ji"

ya kalli Nihla yace "please ki goge masa jikinsa idan zai iya saiyayi sallah ma, idan ma zai iya wanka saiyayi ko zaiji qarfin jikinsa"


Jikinta a sanyaye tadaga masa kai, yafice daga dakin yarage saisu biyu

Kallansa tayi, cikin sauri takawar da kanta tafara linke sallayar datake kai
Shikuwa sai binta yake da wani irin kallon soyaiya , badan kada ya to nawa kansa Asiri ba da Babu abinda zai hana tajita ajikinsa

Toilet tashiga tahada masa ruwa, sannan tafuto tazo wajansa tana kallansa qasa qasa tace "Anhada Ruwan wankan ko zaka shiga kayi?"

"Ai bazan iyaba, saide nagoge jikina"

Cikin sauri tace "to" sannan tahada Ruwan zafin agabansa, tadauko qaramin towel takai masa gabansa ta ajiye tace "gashinan ankawo"

Kallanta yayi har yana lumshe idonsa alamun jin jiki yace "bazan... Iyaba fa"

Shiru tayi, tarasa meyake mata dadi, shikuma yana Kallanta yanaso yaga yaya zatayi

Ajiyar zuciya tasaki ta qarasa wajansa ta matsar da Ruwan gefe, ta kalli rigar jikinsa tace "to dan gyara"

Sarai yagane nufin ta sai yace "jikina ne Babu qarfi, bazan iyaba"

Wannan karon kam kawarda kanta tayi gefe, itade wannan zama baiyi mata ba kokadan, sai hura hanci take, takasa yin komai 🤣

Kamar wadda aka tsikara Tajuyo takama rigar jikinsa Ahankali tafara yin sama da ita, babu musu yadaga mata hannunsa ta cire masa rigar duka, gabanta yafadi ganin yanda hannunsa yake a murde, ga gashi daya kwanta akan qirjin nasa,lokaci d'aya yacika idonta yayi mata masifar kwarjini, fat... fat... fat... takejin bugun zuciyarta nayi, ta ajiye rigar sannan tadauko towel din dake cikin Ruwan ta matse, tadora shi akan qirjinsa

Zirrr yaji wani irin abu acikin jikinsa, cikin sauri ya lumshe idonsa yanajan wani irin numfashi
Satar kallansa tayi taga idonsa arufe, dan haka tafara goge masa cikin sauri, shikuma wani irin dadi yakeji Kamar karta daina abinda takeyi, bayaso yadena jin abinda yakeji din

Ita kuwa sai kawarda kanta takeyi, har wajan wuyansa saida ta goge masa, sannan ta ajiye tace "nagama"

Ahankali yabude idonsa yasauke su akanta, meyasa Nihla ta kasance damuwar sa dakuma maganin damuwar tasa? Meyasa yakejinsa Kamar ba marar lafiya ba? Tabbas dole ne yayi azumi domin nuna godiyar sa ga Allah

Gari kam har yayi haske sosai, ahankali yafara kokarin tashi yadubeta tareda miqa mata hannu cikin shagwaba yace "kikamani natashi"

Kallansa tayi, tadauke kanta, inaga yamanta itace atare dashi ba Momy ba shiyasa yake mata wannan shagwabar
Ahankali ta dora hannunta cikin nasa, yanajin haka yariqe ta sosai, saboda yanda yaji hannun nata da taushi, yatashi tsaye yadora kansa akan kafadarta, yasaka dayan hannun yariqe waist dinta

Yanayin yadda ya tura saqon nasa kuwa ya karbu, nan take tayi taga zatayi baya, amma saiya sake riqe waist dinnata sosai, cikin shagwaba yace "Uhm... Uhmm.... Nifa bazan iyayin wankan ba"

😳Zaro idonta tayi, sannan tazare jikinta Ahankali, ta kalleshi tace "tome kake nufi? Ban fahimta ba?"

Saura kadan tasaka  shi dariya, amma saiyayi Dan murmushi yakawar da fuskar sa, yadafa bangon dakin harya shige cikin toilet din Ahankali

Wata irin nannauyar ajiyar zuciya tasauke sannan takoma kan gadon ta zauna tareda dafe kanta🤦🏻‍♀️
Inda yariqe mata dinnan wani iri takeji


"Zoki gani"


Ta tsinci muryar ya Abba yana kiranta

Dak.. Dak.. Gabanta yafara faduwa, Innalillahi.... mekuma zataje tagani? 🤔

Abba dake toilet yaji shiru, yasaki yar qaramar dariya yasake cewa "Kizo kigani"


Nihla kuwa mayafin ta tayafa, tana jiran likita yashigo tagudu gida, sarai tana jinsa tayi shiru, da yasan zai iyayin wankan amma shine zaisata wahalar goge jiki















Masu cewa naqara yawan typing suma su qara yawan Comments, dama nafada more Comments more typing 👌🏻











Amnah El Yaqoub ✍🏻
[7/15, 12:34 AM] El Yaqoub: ❣️DANGI 'DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub


Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493



55&56


Jin bata amsa masa ba yasa yayi Murmushi yafara wankan sa, yasan cewa sarai tana jinsa

Bai dauki lokaci Mai tsawo ba yafuto, yana sanye da kayan jikinsa, Nihla tana jinsa yafuto amma bata daga kai ta kalleshi ba, idonta aqasa, ya kalleta yayi Murmushi yasaka hannu yadauki sallaya sannan Yazauna abakin gadon yayi qasa da muryar sa Kamar Wanda yake rada yace "please yaushe mukazo asbiti?"

Yatsun hannun ta take wasa dasu batare data dago ta kalleshi ba tace "Shekaran jiya"

"kwana biyu kenan?" yasake yimata Tambayar

Kanta tadaga masa alamun hakane

Kansa ya Jinjina alamun gamsuwa sannan yatashi yatada kabbarar sallah

Yasha addu'ah sosai acikin sallar tasa, yana qara yiwa Allah godia, bayan ya idar ya ajiye abin sallar sannan yafara kokarin hawa gadon

Cikin sauri tatashi takoma kujera tazauna, Sam taqi yarda suhada ido dashi

Shikuma kwanciyar ta isheshi, haka Yazauna yasata agaba yana Kallanta, tanaji a jikinta ana Kallanta Dan haka koda wasa taqi yarda suhada ido dashi

Wayarta tadauka takira Momy, Momy na dagawa cikin shagwaba tace "Momy yaushe zakizo"

Momy tace "Nihla me zaisa nazo asbiti bayan gaki nan? Menene yake faruwa?"

"Momy Babu komai"

"A a ki sanar Dani idan akwai abinda yake faruwa"

"Babu komai Momy, dama ya farka ne"

Momy tace "to Alhamdulillah, Allah mungode ma, yana ina Abban?"

Satar kallan Abba tayi daya zubawa lips dinta ido yana kallo tace "gashinan"

"to bashi wayar"

Ahankali ta miqa masa wayar, memakon ya karbi wayar kadai sai da yahada da hannunta yariqe sannan yazare wayar yayi qasa da murya yace "Momy...."

"Abba na ashe jiki yayi sauqi, to Alhamdulillah bari mu shirya muzo"

"A a Momy, kiyi zaman ki, banajin ciwon sosai, sonake ma yasallame mu"

"to shikkenan idan kana buqatar wani abu de karka yi shiru ga Nihla nan"

Murmushi yayi yace "to Momy"

Wayar ya ajiye gefensa, a lokacin likitan dayake aiki da safe yadawo yadubashi,shima yayi mamakin yanda Abban ya warke

Abba yace "Doc. Ai ina ganin ma dazaka temaka daka sallamemu, saboda banajin komai yanzu, inajin karfi ajikina banajin ciwon komai"


Likitan yace "ka tabbatar?"

"da gaske nake Doc."

Yace "to shikkenan, zaku iya hada kayan ku, zanje nadawo yanzu"

Yana ganin Fitar likitan ya kalleta yace "madam kira min Abokina mana"

Kallansa tayi, taga wayar tana gefensa, tace "gata nan awajan ka"

"eh nasani, kinsan wayar yanmata, saisu"

Ahankali tamiqo hannunta zata dauki wayar yabi hannunta da kallo gwanin sha'awa dogaye dasu
Tadauki wayar tadannawa ya Aslam kira

Ringing din farko kuwa yadauka, batayi magana ba tabashi wayar

Cikin aji yace "Abokina"

Cikin murna Aslam yace "kaga Ango, Ango kasha qamshi, kace kanajin qamshin amaryar taka kamiqe"

Murmushi yayi kawai yace "naga saqon ka ai"

"Hmm ai addu'ah nayi tayi kada Nihla tagani, amma yanzu de jikin da sauqi ko"

"babu komai, na warke"

Aslam yasaka dariya yace "toganinan zuwa"
Daga nan sukai sallama, doc. Yazo yabasu takardar sallama, sannan Nihla tafara hada musu kayansu, ko minti goma ba'aiba Aslam yazo, suka tafi, sun shiga cikin Mota su agaba ita kadai abaya, wayarta tafara qara, tana dubawa taga baban tane, cikin ladabi tadauka "Baba ina kwana"

"lafiya Nihlan Diddi, Yaya su hajiya"

"suna nan kalau baba, inasu mamy"

"mamy tana nan lafiya, bakya wani abune yanzu ko"

"eh baba"

Gyaran murya yayi yace "to abinda nakeso dake shine ki saurari abinda Zan fada miki,jiya su Alhaji Abubakar sunzo andaura miki aure da Dansa Abubakar"

Gabanta yafadi, cikin sauri tadafa qirjinta tace "Aure kuma baba"

Abba da Aslam dake gaban Mota suna jinta, Aslam aransa yace to fada mata ake kenan
Abba kuwa shiru yayi yana jinta

Daga daya bangaren baba yace "eh aure, Yusuf da kansa shiya fara yiwa mahaifin sa magana akan ya hakura, saide bai yarda ba, saida sukazo jiya muka sake tabbatar wa, ga sadakinki ahannu na dubu dari cif,kiyiwa mijinki biyaiya sannan kiyiwa Yusufa addu'ah Allah yabashi mace tagari, mahaifin sane ya tsaya akai komai aka gama, sannan Alhaji Abubakar yanemi yafiyata da kansa, Dan haka banason wani tone tone, kiyi hakuri Allah yabaku zaman lafiya "


Hawaye suka silalo daga idonta, muryarta ta sauya tace" to baba "

" yawwa Allah yayi miki albarka "

"amin baba"

Daga nan sukai sallama, tayi shiru tana goge hawayen idonta, yanzu ashe dama shiyasa Momy ta barta awajan ya Abba, wani hawayen yasake zubo mata, Allah sarki ya Yusuf, haqiqa tayi rashin masoyi, yasha wahala akanta, tasa hannu tashare hawayen

Ahankali Abba yadubi Aslam yace "dan tsaya Aslam"

Babu musu kuwa ya tsaya, yabude gaban motar yafuto yadawo baya wajan ta Yazauna, Aslam yayi Murmushi yadauke kansa yaci gaba da driving

Sake matsawa yayi jikinta, tanajin yanda jikinta yake gogar nasa, yasaka hannunsa ta bayanta ya rungumota jikinsa, batada zabin daya wuce ta dora kanta akan faffadan qirjinsa

Bayanta yafara bubbugawa Ahankali, yasunkuyo da kansa dede kunnanta cikin rada yace "kiyi hakuri kidena kuka kinji, kukan ki yana tabamin zuciyata, kiyi shiru, kinji?"

Ahankali tadaga masa kanta, wani irin dadi Abba yaji, yanda yaga lokaci daya taji maganarsa

Cikin kunnanta yadora bakinsa yace "kin hakura?"

Wani irin abu taji yana yawo a jikinta, kode ya Abba ya Manta da ya Aslam ne, ahankali  ta janye jikinta daga nasa

Shima sai murmushi dayayi, yamatso kusa da Aslam yace "Abokina ina Abba nah"

Aslam yayi Murmushin waskewa yace "kaiko, Hmm"

Dahaka suka qarasa cikin gida, suna zuwa tabude motar tafuto jikinta asanyaye, tayi part dinsu

Momy da Daddy na zaune afalo, Adala tana gefen Momy tanayi mata lissafin abubuwan dazata siyo mata, haka Nihla tazo ta samesu, cikin ladabi ta gaishe su tareda zama aqasa

Momy tace "a a, yana ganki yanzu, yanxun nanfa nake cewa Alhaji yatashi mutafi"

"Momy ai an sallamemu, yace yawarke"

Daddy yayi Murmushi, a lokacin suka shigo falon shida Aslam, suma gaida su sukai suka zauna aqasa

Daddy yace "Abba ashe jiki yayi sauqi"

Lallausar sumar kansa ya shafa yace "eh Daddy"

Yace "to Alhamdulillah, Dafarko de kayiwa Allah godia, sannan ka godewa Aslam,idan da hali ma kayi masa Babbar kyauta 😃sannan kaida Aslam din Idan jikinka yagama warware wa kushirya kuje can Abuja kuyiwa yaron nan Yusuf godia, yayi mutuqar kokari kuma yayi maka halacci, sannan dazu mahaifiyarka tayi waya da Ibrahim ta sanar dasu ka farka, sunce asaka musu lokacin da za'ayi biki yan'uwan mahaifin ta zasuzo daga jigawa ahadu anan, na Abuja ma zasu so gaba dayansu duk ayi komai anan, nikuma nafada musu nasaka sati daya, saboda haka sai kayi kokari zuwa next week din kagama shirya komai, saiku tare a gidanku "

Cikin farin-ciki yadan sosai qeyarsa yace" to Daddy insha Allah"

Sannan yakalli Nihla yace "kinji abinda yafaru ko?"

Tace "naji Daddy"

"to kiyi hakuri, ki qara akan Wanda kikai abaya, Allah yabaku zaman lafiya"

Tace "amin Daddy"

Momy ta miqe tace "Nihla taso Muje kitchen"

Bayan Momy tabi abaya, suna zuwa kitchen Momy tabata wani magani tace "kisha wannan yanzu, sai kici abinci kishirya kitafi gidan gyaran jikin"

Cikin ladabi tace "to Momy" tadauka tafara sha tana tunani aranta, Ilham tabata, Momy tana qara mata wani itakam yaya zatayi?
Momy ta kalleta tanajin tausayin yarinyar, gani take Kamar ba'a kyauta mata ba, Allah yasa de taso Abban nata, koda yake tasan Abban ma da naci, zai rarrasheta

Bayan tagama sha tawuce dakinta tazauna agefen gadon tana tunani, yanzu haka aure ne akanta fa, ashe yaya Abba yasani shiyasa yake min wasu irin abubuwa a asbiti, tatuno lokacin da ya Aslam yake cemata yaya marar lafiyarta, Hmm ashe duk sun sani, wayarta tadauka takira Anty Nadiya tabata labarin komai, nan take Nadiya tace zatazo bikin itama domin ta nemi yafiyar sadeek, tayi musu ala sanya alkhaairi, bayan sun kashe tatashi tashiga wanka, tafuto ta shirya tsaf taci abinci, sannan tayiwa Momy sallama tatafi driver yakai ta gidan



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Sai bayan sallar ishsha'i tadawo gida, zaune suke afalo su biyu shida Momy, Momy tana bashi coffee abaki, sallama tayi tashigo cikin falon idonsa yasauka akanta, doguwar riga ce a jikinta Mai godon hannu amma rigar abaje take sosai, ya dinta yanada santsi Kamar na abaya, da mayafin rigar tayi amfani tayafa akanta sauran kuma ta zuba shi baya, dukda fadin rigar hakan bai hana ka hango bajajjan hips dinta, yayinda cikakken qirjinta yadago ,hakan yasa cikinta shafewa, da yar qaramar jakar ta a hannunta

Cikin ransa yafara magana

ya'ilahi! Yanzu haka duk anganta ahaka, amma yaya zaiyi? Bazai iyamata magana ba tunda shine yake neman sulhu

Zama tayi akujera kusa da Momy, tace "wash Allah Momy nadawo"

Zaman datayi awajan kawai wani irin qamshi na daban yake tashi, ahankali ya lumshe idonsa sannan yabudesu

Momy tace "Sannu Nihla, ai gara da Allah yakawo ki, zanje in dubawa Alhaji wasu takardu, karbi wannan coffee din kibashi"

Baki taturo gaba alamar bataso, ita Momy batasan halin ya Abba ba, kawai shagwaba ce take damunsa, amma aiya warke
Haka tasa hannu ta karba Momy tashige dakin Daddy tabarsu anan

Gyara zaman sa yayi akan kujerar ya dauki fillo din kan kujera yadora a cinyarsa yazuba mata ido yana murmushi
Gaskiya yaji dadin abinda Momy tayi, wani irin nishadi yakeji aduk lokacin dasuka kasance su biyu shida ita

Kallanta yayi yace "zeyi sanyi fa"

Dago idonta tayi ta kalleshi, ta janye idonta, sannan tamatso kusa dashi ta diba a Spoon din takai bakinsa, Dan qaramin bakinsa yabude tasaka masa Spoon din, yanasha ya lumshe idonsa, haka taci gaba da bashi yanasha harya qare tas, bedena bude mata bakin ba, ta kalleshi tace "yaqare"

Murmushi yayi yace "bazan samu qari ba?"

Tashi tayi tsaye kanta tsaye tace "eh"

Cikin sauri yasauko daga kan kujerar yace "kawo nariqe miki jakar to Muje dakin"

Babu musu tabashi handbag din nata , shikuma yabita abaya har cikin dakinta

Abakin gado tazauna shikuma Yazauna aqasanta tareda dora mata jakar akan cinyar ta, bayan yadora mata jakar a cinya memakon yadauke hannayensa sai yabarshi akan cinyar tata, bayaso kokadan yadena jin wannan qamshin nata dake rinjayarsa

Nihla tarasa yaya zatayi dashi, ahankali tace "inaso ne nashiga wanka"

Yace "akwai maganar danake so muyi"

Fuskarta Babu yabo Babu fallasa tace "to"

Kallanta yayi yafara tunani, yarasa meyasa har yanzu taqi sakin jikinta dashi, idan yadubi qwayar idonta yana hango rashin sabo atattare da'ita, kokuma har yanzu bata yafe masa bane bai saniba

Ajiyar zuciya yayi, cikin maganar sa Ahankali cikin sigar rada, Wanda dagashi sai itane zasuji yace "ina qara baki hakuri akan abubuwan dasuka faru abaya .... Nihlaaa! "
Yaja sunan nata
Sannan yaci gaba da cewa "Wallahi yawancin kowanne dare bana iya kwanciya harna samu nayi bacci saboda tunaninki, koda yaushe jinake inason  ganin ki a kowanne lokaci, duk lokacin dana kasance tare dake inajin wani irin dadi acikin zuciyata, abaya nayi kuskure dana kasa bawa wadda nashaqu da'ita kulawa harta hakura dani,domin kuwa nagama ganewa shaquwa ce kawai tasa na furta mata kalmar soyaiya, amma soyaiya daya Tun ta yarinta ta kena bawa Nihla..... a yanzu nayi miki alqawarin Zan kula dake fiyeda yanda Zan kula da kaina, kiyi hakuri kiyafemin kisaki jikinki dani please "

Shiru Nihla tayi bayan tagama jin duk bayanin sa, Kamar ba shiba wani lokacin idan Yazauna yana yimata wasu abubuwan

Ganin tayi shiru ba tace komaiba yasa shi motsa hannunsa dake kan cinyar ta, ahankali yafara shafa cinyar ta, kasancewar rigar jikinta me santsi ce saitaba shi damar shafa cinyar tata dakyau

Ta kalli fuskarta yace "kinji"

Gaba daya yafara kashe mata jiki da salonsa,
Cikin shagwaba tace "ya Abba nide kabari"

Yace "to kin yafemin?"

Ahankali tadaga masa kanta, sannan tace "Allah yayafe mana baki daya"

Yayi Murmushi yace "Amin, kinga wani abu"
Yabude wayarsa ya nuna mata wasu pictures
Kanta ta matso tafara ganin pictures din, shima yaturo nasa kan domin su gani tare,tana gani tace "laaaa pictures dina"

Murmushi yayi ya kalleta, yanda kansu yahadu ne yasa yaji Kamar yayi kissing Dan qaramin bakinta, musanman yanda ta bude shi dinnan tace laaaa, amma bazai yiba, gara yabi komai Ahankali

Yace "yes, Tun lokacin da mukaje garinku nayi miki pictures din, kin tuna? Abakin ruwa, har ruwa yadakemu"

Cikin murmushi tace "wallahi na tuna, bani na gansu gaba daya, waye yatura ma?"

Dadi yafara kama Abba, yanda yaga tafara sakewa dashi, yace "ya Usman ne yatura min"

Tace "wayyo,lokacin banda qiba wallahi"

Kallan qasa qasa yayiwa cikakkun nashanunta yace "yanzu ai kinyi" 🤣

Nihla bata gane komaiba tace "wallahi sune, zaka tura min kuwa"

Kallanta yake yanda take jin dadi sai yaji dadi shima, gashi shiba wani surutu ba, kuma bayaso firar taqare,bayaso yadena jin daddadan qamshin dake tashi a jikinta, bayaso yayi nesa da'ita, yarasa mezaice mata domin tasake jin dadi shikuma yaga farin ciki akan fuskarta, ya kalleta yace "nagoyaki?"

Cikin sauri ta kalleshi, cikeda mamaki, wanne irin goyo kuma ana zaune lafiya? Saikace Wanda zai iya goyon, tasan kawai fada yayi, amma domin taga gudun ruwansa sai tace "eh"

Cikin sauri yace "to zo ki hau"

Yadauke hannunsa akan cinyar ta ya tsugunna a gabanta

Mamaki yagama kashe Nihla, anya ya Abba ne kuwa wannan? Yau ya Abba ne zaice tahau bayansa ya goyata? Ta ajiye wayar tasa agefe sannan tafara tattare rigar jikinta, tad'ane bayansa, lokaci daya yamiqe tsaye, beji nauyin taba kokadan, hanyar kofar dakin yanufa da ita yace "muje nakaiki falo saina dawo dake?"

Zaro ido tayi tafara girgiza kanta tace "laaaa a a babu ruwana"

Ganin yanda ta tsorata yasa yayi Murmushi yace "Allah Muje"

Riqeshi tayi sosai tace "dan Allah kar Muje"

Lumshe idonsa yayi, numfashin sa yafara sauyawa, qarfin jikinsa yafara raguwa, kasala ta lullube shi sakamakon jin nashanunta agadon bayansa yanda tasa hannu ta rirriqeshi

Nihla taji shiru, tayi tunanin bai haqura ba, tasake jijjigashi tace "dan Allah"

Nan take yaqara daukan caji, yashiga cikin yanayi, yaji qafafunsa suna neman gaza daukarsu, sai gyara kafafunsa yake, ita kuma takasa gane komai

Yana motsawa kuwa suka tafi kan gadon nata gaba dayansu suka fada kai

Nihla tayi tunanin da niyya yayi hakan, batasan yanayi ne yasa ba 🤣
Nan take tafara dariya, yajuyo da kansa yana Kallanta, yajima rabon daya ga tana dariya Kamar haka, ahankali yadago hannunsa ya dora shi akan dimple dinta












Sharhi, share please 🙏









Amnah El Yaqoub ✍🏻
[7/15, 11:04 PM] El Yaqoub: ❣️DANGI 'DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub


Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493


57&58



Juyowa tayi tana kallansa, cikin murmushi tace "Aidama nasan bazaka iya daukana ba, shiyasa nahau banyi ma musu ba, yanda nake d'innan"
Ta qarasa maganar tana jijjiga jikinta

Shima murmushin yayi mata "nayi tunanin zan'iya ne, bansan haka ake jiba"

Nihla kwata kwata bata gane maganar dayayi ba, Dan haka tayi shiru, hannunsa dake kan dimple dinta yadauke yadawo dashi dede karan hancin ta, yace "kinada kyau"

Cikin sauri ta kalleshi, tayi Murmushi sannan ta yunqura tatashi zaune, ta kalli Agogon dakin tace "kaiiii shadaya saura, ya'akai lokacin yayi gudu haka, bari de in shiga wanka"

"to kitashi kishiga mana"

"to ai baka fita ba"

"idan kika shiga Zan fita, kona kaiki?"

Cikin sauri tace "a a, tsaf zaka sake kayar dani" tashige toilet din da kayan ta a jikinta tareda rufo kofar

Yana ganin shigarta ya lumshe idonsa tareda yin ajiyar zuciya, yatashi jiki a mace yafuto daga dakin nata, har lokacin Momy bata falon, ya kashe kayan kallo sannan yawuce dakinsa, cikeda begen matarsa



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Acikin satin su Abba sukaje Abuja suka yiwa Yusuf godia, Abba har kunyar sa yakeji akan abubuwan dasuka faru abaya Sosai suka fahimci juna

 Tundaga lokacin Nihla tadena zuwa wajan gyaran jiki, dede da falo Momy hanata futowa tayi saide dole, kullum tana cikin hijabi, hatta qafarta akwai safa, data zauna aqasa kuwa Momy zata sata tatashi takoma kan gado ko kujera duk saboda kada sanyi ya shige ta
Magunguna kuwa Momy bata take iri-iri masu inganci, Nihla qwarai ta yaba irin sonda Momy take wa ya Abba, haka kuma duk cikin surukanta Nihla ta daban ce, dama Tun tana qarama soyaiyar Nihla take cikin Zuciyarta, kokadan Momy bata qyashin yiwa Nihla abubuwa, domin kuwa tayi alqawarin zata riqeta Kamar itace ta haifeta, shiyasa take mata duk wani abu da uwa zata yiwa 'yarta

Abba da Aslam Babu zama, danma wani lokacin su Adam da Fawaz suna yin wani abun ta wani bangaren, gida kam komai yaji, sun qawata shi yanda yakamata da kayan kamfanin A&A Furnitures, yayinda Anty Salama matar ya Usman da hajiya Farida maman su Dida suka shirya sukaje Dubai suka hadowa amarya kayan lefenta

Anty Firdaus kuwa matar ya Aliyu itace tashiga tafita wajan kawo anko, dayake abune na kudi nan take kowa yayi, duk Wanda kaduba yana cikin farin ciki, kuma doki yake wannan rana tazo, andade ba'ayi wani taro a wannan family ba, ko bikinsu Aslam da akayi Babu wani biki da akayi, kasancewar kowa yasan Babu Wanda yake son auren, kowa dole aka masa

Ana sauran kwana biyu biki 'yan'uwa na nesa dana kusa duk sunzo, yan'uwan mahaifin ta duk sunzo, kuma family anhadu anyi musu kara duk Inda suka so anan suke kwana, yan Abuja ma duk sunzo, mamy kam wajan Momy ta sauka suka hadu suke gudanar da Komai

Yusuf yana wajan angwaye, saide duk abinda yake yana kokarin danne zuciyarsa ne kawai, saboda kada yazobe ladansa, bayan badan komai yayi ba saidon Allah



Ranar kamu kuwa kowa ya shirya, amarya tanata sauya shiga kala kala, Acan gidan sheik Adam kuwa Diyana kuka tasaka masa da qaton cikin ta na wata shida, gaba daya dinku nan sunyi mata kadan, haka tasa Adam agaba tana masa kuka, yarasa yaya zaiyi da'ita haka yadauko mata wasu kayan suka Taho gidan bikin, Dida kuwa normal take harkar ta, domin kuwa har yanzu batada komai 🤣

Washe gari da rana amare suna zaune a part dinsu Ilham, cikin tsohon dakin Ilham datake ciki kafin tayi aure, bayan angama yiwa amarya kwalliya, zuwa dare za'a tafi wajan dinner

Diyana tana gefe, da ciki agaba tana karanta wani littafi, Nihla ta kalleta tace "meciki"

Diyana tace "saura ke ai"

"A a, aini ya Abba yana sona, saiya qara reno na, sannan"

Gaba dayansu suka saki dariya, Dida tace "tab, ina Ruwan yaudaran kai"

Dariyar dasuka sa ne yasa lil Abba kuka, Nihla tace "kai Innalillahi... Dan Allah Ilham ki dauke wannan yaron naki, gaba daya ya ishemu da kuka"

Ilham tace "angonki nede, yanda kuka sashi kuka yasin kema lokaci yana zuwa saiya saki kuka" 🤣

"ni Ilham Dan Allah kidena min irin wannan maganar, Allah banaso"

Wayarta ce tadauki qara, Dida tabata tace "ga Ango yana kira"

Karbar wayar tayi, ashe yanada number ta, betaba kirantaba, rage murya tayi tace "Hello"

Saida yaja wasu second sannan yace "Amarya bakya lefi kokin kashe Dan masu gida"

"to waye Dan masu gidan?"

Murmushi yasaki Mai aji yace "farouq mana"

"Hmm kaiko, shiyasa kullum kuke fada ai"

"muna gidan Aslam, kuma suna jin yunwa"

"toooo, to saide Ilham din tadawo tadafa muku abinci"

"A a, kece zaki kawo mana"

"yanzu ya Abba fisabilillah tayaya Zan Taho ni kadai, idan Momy ta ganni ma zata hanani"

Shagwaba yafara yi yace "uhm.. uhm.. Allah nide yunwa nakeji"

🤦🏻‍♀️Kanta da dafe da hannunta tace "to naji"

 qit takashe wayar sai mita take, mutum ana tabashi sai shagwaba, saikace shine autan duk duniya, nida nake wajan iyayena ni kadai banyiba saishi, haba ni wallahi nagaji 😔

Mesu Diyana zasuyi inba dariya ba, Dida tace "wai Dan Allah ya Abba ne yake miki shagwaba?"

Tace "tab, ai saide in bamu zauna ba"

Diyana tace "ya birgeni, yanzu ba kowanne namiji ne yake wa matarsa shagwaba ba, saide ke mace kullum ki daddage kiyi, duk saboda ki faranta musu, maganin mata ne, mata ne suke nema, maganin tsumi ne mata ne, shagwaba ce mata ne, ke mace kullum kede kina kokari kiga kinyi Dan ran mijinki yayi fari, amma Ba kowanne namiji ne zaisha magani ba, saboda matarsa taji dadi, komai de saimu, saboda haka idan yafara miki shagwaba kema ki masa, zai dinga tattalinki, Dan kowanne namiji dakike gani Babu Wanda zaice bayason yasamu mace wacce ta'iya shagwaba "

Ilham tace" wallahi gaskiya ne kam "


" salamu alaikum "

Gaba dayansu suka juya suka kalli kofar dakin, baquwar fuska suka gani,yarinya ce qarama da alama zatakaisu shekaru, wata shegiyar gown ce a jikinta datahau jikin nata sosai, kallo daya zakayi mata kasan cewa lalle mace ce har mace, haka kana ganin hancin ta zaka tabbatar ita din bafulatana ce, duk yanda doguwar rigar ta baiyanar da hips dinta hakan baisa tasaka Babban mayafi ba, Dan qarami ne sai tayi rolling dashi

 ganin yanda suka zubo mata ido suna Kallanta yasa ta qarasa shigowa cikin dakin ta ajiye jakar kayanta, sannan tazauna agadon ta cire mayafin datayi rolling tana firfita dashi
Tace "ku qaramana esin mana" 🤣

Ilham tana kallan ikon Allah tace "aqure yake ai"

Tace "to inaga Dan daga rana nake ne shiyasa,"

Ta kalli Nihla tace "amarya, wai baki ganeni bane? Naga duk sai kallona kuke, naje wannan part ance bakwa nan, naje wannan ance bakwa nan, saida nazo nan nayi sa'ah akace kuna ciki, ina qawayen naki naga saiku hudu kawai?"

Nihla tace "banfa gane kiba"

Dida ma tace "amarya batada qawaye, qawayenta yan'uwanta, mune kuma"

Itama tace "to gani naqaru, Rafi'ah cefa, yar gidan yayan baban ki Abdullahi na lagos"

Nihla tace "kut, au Rafi'ah wai kece? To ina Zan gane ki, kinga yanda kika koma kuwa"

Ta kalli su Ilham tace "cousin sister nace, yar gidan yayan babanmu ce, alagos suke dazama, babansu yana canji"

Gaba dayansu sukai murna,Dida tace "to yanzu ai kinga kinsamu qawa yan'mata"

Nihla tace "to Rafi'ah ko zaki kaiwa angwaye abinci, suna gidan Ilham"

Rafi'ah tace "angwaye? Sunada yawa?"

Ilham tace "gaskiya bazasu rasa yawa ba"

Tace "a a toba lalle nashiga ba gaskiya, dade mu biyu ne,bari na gyara fuskata,nikam Nihla ina yusuf Dan unguwar ku? Kwanaki naji baba yana waya da baban ki naji yace kuna Abuja agidan su"

Murmushi Nihla tayi "ya Yusuf, shima yana wajansu ai, idan kinje saiku gaisa dashi"

Tashi Rafi'ah tayi tashige toilet taqara gyara fuskarta dakyau, sannan tafita wajan Momy domin karbar Abincin

Tana fita Diyana tasaki ajiyar zuciya tace "kai duniya akwai kyawawan mata gaskiya, Wato Nihla wannan sister naki Babu qarya tahadu, kice muqara rike kazajenmu hannu bibbiyu" 🤣

Dukansu sukai dariya, " oh Diyana uwar kishi" cewar Ilham



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Suna zuwa gidan iliya driver ya tsaya, tafuto tace "ga Abincin kashiga kakai musu, ni ina jiranka anan"

Iliya yayi dariya yace "ranki yadade aida Kinshiga"

Tace "a a, idan kakai musu kace ana magana da yusuf"

Iliya yaje yakai musu Abincin, yafadi saqonsa, yana fada kowa yafara yiwa Yusuf kallan kallo, Adam yace "iliya kace mace ce take sallama dashi?"

Yace "eh, tare muke da'ita ai, itace tabani Abincin tace na kawo muku, budurwa ce"

Dariya sukayi, Aslam yace "to kode munyi kamu ne" 🤣

Yusuf yayi Murmushi kawai ya cewa iliya "Muje"

Suna futowa yaganta a tsaye daga nesa, begane taba, cikin ransa yace anya kuwa shi take nema? To Wacece wannan saikace aljana saboda qira? 🤔

Wajan ya qarasa, ta kalleshi cikin murmushi tace "baka gane niba ko?"

Yace "gaskiya kam, kiyi hakuri bangane kiba"

Tace "Rafi'ah cefa, yar garinku, Wanda suke lagos"


Saida yayi jimmm sannan yace "okeyyyyy nagane ki yanzu, to Rafi'ah aikin girma ina Zan gane ki idan akan hanya ne?"

Tayi Murmushi tace "na tambayi Nihla ina kake, kuma ance min a gidanku suke zaune a Abuja, shine dana tambayeta tacemin kaima kana nan gidan"

"wallahi ina nan, Yaya school, meyasa baki shigoba kuma?"

"ai ance min angwaye suna ciki, nasan kuma suna dayawa,gashi ni kadai ce, shiyasa nace idan yakai muku Abincin yaturo ka mugaisa "

Yace "gaskiya kin kyauta, Allah yabar zumunci, zakije wajan dinner din ai anjima ko?"

Tace "eh zamuje tareda amarya"

"to shikkenan idan bamu wuceba saimu dauke ki mutafi"

"to shikkenan nagode, sai anjima"

Tajuya wajan iliya dake jikin Mota yana jiran su, tashiga suka tafi, Yusuf yabi bayan motar da kallo, ikon Allah, ashe yanzu ana samun yanmata masu sada zumunci haka, Wato ita haka kawai dansu gaisa ta kirashi, amatsayin sa na Dan garinsu
Yayi ajiyar zuciya tareda komawa ciki, yana shiga kuwa duk suka bishi da kallo, Fawaz yace "Malam Yusuf irin wannan dadewa haka, kode kasuwa ta tabbata ne"

Yayi Murmushi yace "yar garinmu cefa"

Abba da tunda aka fara magana baisa bakiba yace "to menene ai ana auren yar gidama" 🤣

Aslam yace "Kamar yanda kayi ko"

Adam yace "mukayi de" 🤣



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Wajan dinner yayi kyau sosai, an qawata shi yanda ya kamata, kujerun da Amarya da Ango suka zauna sunacan sama, sauran mutane kuma anshirya musu nasu wajan zaman, iyaye mata duk sunzo, nan take aka fara gabatar da Komai bayan shigowar Ango da Amarya, gown din da tasa launin light green tayi masifar yimata iyau, yar qaramar posting din hannunta kadai ma abin kallo ce, yayinda Ango yasaka farin kaya yaci Babbar riga Kamar ba shiba, hannunta yana cikin nasa, mc yafara gabatar da mutane sannan aka umarci amarya da Ango sufuto su yanka kek

Rafi'ah tana gefen Nihla sai tafi ake musu ga kida yana tashi, Dan qarami ta yanko tasaka masa saikawar dakai take taqi yarda suhada ido, waje yadauki ihun murna, shikuwa daya yanko nasa saida yasa hannunsa yariqe waist dinta sannan yamatso da bakinsa dab da nata Kamar zaiyi kissing dinta yace "haa"

Murmushi tayi, takai masa dukan wasa a qirjinsa "sannan tabude baki yasaka mata"

Su Momy suna ganin haka, suka miqe daya bayan daya suna barin wajan, akabar iya yaran su kadai 🤣

Ana kiran mutane suna fita suna rawa, Diyana tayi tagumi tanajin haushi, taso tayi rawar amma Babu hali,saboda cikin ta 🤣

Nihla tana zaune awajan dasuke ta hango ya Yusuf da Rafi'ah suna Selfie, taji dadin yanda Rafi'ah take kulashi, ko banza hakan zaisa tarage masa wata damuwar, ita har yau Yaqi bata dama ma suyi magana, amma tunda yakula yar'uwarta ma taji dadi sosai

Hadari ya gangamo agari amma kasancewar suna ciki ga qaran kida shiyasa basuji ba, sai wajan goma da rabi aka tashi, hannun Nihla  yana cikin na mamy, mahaifiyar Yusuf suka futo kai tsaye aka wuce da Amarya gidan ta

'yan'uwa kowa ya yaba da gidan amarya, ganin Hadari yasa kowa yatafi gida dawuri akabar amarya ita kadai, bayan fama da akai da'ita akan tayi hakuri ta daina kuka



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️



Shadaya da rabi suka qaraso gidan shida Aslam, ruwa ake sheqawa Kamar da bakin qwarya, ahankali motar take tafiya kasancewar ana ruwa, har suka qaraso cikin harabar gidan, Aslam yayi Parking Abba yafara kokarin fita

Dasauri Aslam yariqe shi "haba Abba, haba, irin wannan saurin fa? Kagafa ruwa ake, kabari yadan ragu mana"

"Aslam yazan zauna anan matata tana ciki ita kadai" 🤣

"Abba wallahi de kabi 'yar mutane Ahankali, idan kana nan ana ruwa ai itama tana ciki, mezai sameta? Katsaya Dan Allah"

Dawowa yayi Yazauna yace "gaskiya kana takuramin wallahi, kabarni naje wajan amarya ta kawai"

Aslam yayi Murmushi yace "bade acikin Ruwan nanba, kayi hakuri kawai, inkuma ana ruwan zakayi naka amarcin ga hanya nan"

"Hmm Aslam waidan Allah meka daukeni ne? Kace nabi yarinya Ahankali, kace zanyi amarci acikin Ruwan sama, haba, yarinyar da ko gama sakewa dani batayi ba"

Dariya Aslam yayi yace "ai gaskiya ne, hali nasani"

Wayar Aslam tafara qara, yana ganin sunan matar sa yadauka, tace "ya Aslam dagani sai Abba fa a gidannan har yanzu baka dawoba, baku gama siyan bakin bane?"🤔

Yace "ruwa ne yatareni, amma ganinan zuwa, bari nataho" yakashe wayar

Abba yace "tab, tosu dasuke su biyu ma takira ka awaya, amma ni kahanani tafiya" yana gama fadar haka yabude motar yafuto

Aslam yana dariya yadaga murya yace "ledar, kamanta ledar taka" 🤣

Dasauri yadawo ya karba yayi ciki, duk yanda yake sauri saida Ruwan yadakeshi,yashigo cikin falon sannan Yarufe, kai tsaye dakinta yashige, tanajin shigowar sa ta kalleshi ta cikin mayafin da'aka rufe mata kanta dashi Mai shara-shara, tana ganin yanda yajiqe tayi Murmushi

Ledar hannunsa ya ajiye, yafara cire Babbar rigarsa ya ajiye, sannan ya kalleta yace "amarya, angon naki duk yajiqe saboda yana zumudin son ganinki"

Nihla tayi shiru batace komai ba

Ahankali yataka yazo gaban gadon ya tsugunna, sannan yasaka hannu ya janye rigarta data rufe kafarta aciki, Jan lalle da Baqin da akayi mata ya baiyana, cikin ransa yace wow! Shafa wa yayi ahankali

Cikin sauri ta janye kafarta batare datace uffan ba

Kallanta yayi, sannan yasaki wani irin murmushi, wacce irin godia zaiyi wa ubangijinsa daya mallaka masa Nihla?
Hannun nasa yasake maidawa ya janyo kafar tata, yakama yatsun kafar yanajansu daya baya dayan,qunshin da'aka yi musu yayi mutuqar kyau, kokarin janye kafar take, amma sai Yaqi bata damar hakan, daga qarshe ma saiya dora bakinsa akan Dan yatsanta guda daya yana sha

Wani irin abu taji yana mata yawo a jikinta, takasa gaskata wa kanta cewa Shin ya Abba ne kokuma wanine daban, sunkuyarda kanta tayi tadorashi akan gwiwar ta tanajin wani irin yanayi yana shigar ta

Saida yakai kusan minti uku yanasha sannan yazare bakinsa, muryar sa harta fara disashewa yace "please ko zaki temakamin incire kayana, duk sun jiqe"











Sharhi please











Amnah El Yaqoub ✍🏻
[7/17, 1:57 AM] El Yaqoub: ❣️DANGI 'DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}


Writing by Amnah El Yaqoub

Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493



59&60



Nihla tayi shiru tana jinsa batace komai ba, ahankali yatashi yahau gadon tareda yaye mayafin nata, cikin sauri tasa hannu biyu tarufe fuskarta, yayi Murmushi yace "masha Allah,"

Yasa hannu ya shafi fuskarta yace "kinyi kyau sosai,"

Tayi Murmushi kadan batare data kalleshi ba, yace "kunya ta kikeji kuma? Toki dena, tashi mana, tashi kitayani mana"

Ahankali tace "saikace wani Yaro"

"yes, ai qaramin Baby ne awajan ki"

Nanma batace komai ba, yafara kokarin tashi yana mata wasa "amarya amarya, kisaki jikinki fa" 🤣

Nihla de tana jinsa tayi shiru, tasan cewa yau me rabata da ya Abba sai Allah, yanda yake wannan rawar kafar Allah ne yasan yanda zasu kwashe dashi
Agabanta yafara cire kayan jikinsa, cikin sauri ta runtse idonta, ya kalleta yayi Murmushi, kunyar Nihla tana birgeshi sosai, yadawo dagashi sai gajeren wando yadubeta yace
 "zanje nayi wanka, yakamata kema kiyi shirin kwanciya, nasan kin gaji"

Ahankali ta daga masa kanta, shikuma yafice daga dakin da kayansa

Bai wani dade ba a wankan yadawo dakin nata yana sanye da kayan bacci,dakuma jallabiya a hannunsa, a lokacin harta kwanta da kayan ta a jikinta 🤣

Wata yar qaramar dariya yasaki yace "kisakko muci abinci"

Girgiza kanta tayi tace "naqoshi"

"mene? Banason musu, sauko kawai, kuma wannan kayan najikinki aida kin ciresu, damunki zasuyi idan kina bacci" 🤣

Kokarin tasowa take daga kan gadon tace "Babu komai, bazai dameni ba"

Ajiyar zuciya yayi yace "kozakiyi alwala mufara yin sallah?"

Tace "to" sannan tayi hanyar toilet dinta dake cikin dakin, yabi bayanta dawani irin mayen kallo

Tare suka gabatar da sallah,bayan sun idar yadinga kwararo musu addu'ar zama lafiya dakuma samun zuri'ah tagari, bayan sun shafa ne  yabude musu ledar dayazo da ita, kaza ce aciki babba saikuma fresh milk, shida kansa yafara bata taci taqoshi sannan shima yaci, itace takai kayan kitchen har lokacin ana zabga Ruwan sama

Dakin tadawo tarakube agefen gadon, shikuwa kwanciya yayi harda dora kansa akan fillo, yana riqe da wayarsa🤣

Yadago kansa yadubeta yayi Murmushi, yaga alama gaba dayan ta atsorace take dashi, idan kayi mata kyakykyawan tsawa zata iya zurawa da gudu 🤣

Yace "kizo ki kwanta mana"

Ahankali tahau gadon can gefe ta kwanta tareda juya masa baya, tashi yayi ya kashe wutar dakin yadawo kan gadon kusada ita ya kwanta, gabanta yafara faduwa sosai

Yace "Ruwan nan anayin sa dayawa yau, yayi albarka sosai, Allah yasa muma auren mu yayi albarka"

Tayi shiru 🤣

Yayi Murmushi yasake cewa "bakice amin ba"

Sai a lokacin tace "Amin"

Hannunsa yasa yajanyota jikinsa Ahankali, yace "meyake damunkine, naga kin takura kanki"

Girgiza kanta tayi alamun Babu komai, kafin yayi magana aka fara walkiya sosai, sai cida tabiyo baya, har hakan yatsoratar da'ita, cikin sauri tashige jikinsa

Shikuwa Babu musu yasakata acikin faffadan qirjinsa, cikin kunnanta yaradama ta, meyasa ne kike tsoron cida Tun kina qarama? "

Cikin rawar murya tace" Babu komai "

Shiru yayi, yasaka hannunsa ya zagaye ta dasu, jiyake Kamar ya maida ta cikin jikinsa, yace" to kiyi baccinki, babu abinda Zan miki "

Wata irin ajiyar zuciya tasauke har yana mamakin irin yanda take tsoron sa haka, shikuma dama bashida niyyar yimata komai, gara tasake dashi sosai yanda zaifi jin dadi, amma kana ganin tsoron ka a'idon mace qarara haka tayaya zaka nemeta

Addu'ah yayi musu sannan yayi shiru yana tunani, wai yau Nihla ce suke kwance amatsayin ma'aurata

Jin numfashin ta nasauka a qirjinsa yasa yagane cewa tayi bacci, amma shi sam yakasa baccin, yana jin lokacin da aka gama ruwa, har karfe biyu da rabi idonsa biyu

Sai motsi yakeyi yana matse kafafunsa, ahankali yasaka hannu yazuge mata zif din rigarta, ya cire rigar gaba daya, a lokacin ta farka, tsoro yakamata, nan da nan tafara hawaye, bai saurareta ba ya cire mata siket din jikinta, daga ita sai breziya da under wear a jikinta, ahankali yadora bakinsa dede wuyanta yana kissing dinta, yayinda hannunsa yasauka akan qirjinta nan da nan ya rikice, babu bata lokaci ya cire breziya din yana shafa matasu, muryar sa harta fara sauyawa yace "ki.. Kiyi shiru.."

Kafin ma yaga tabashi amsa yadora bakinsa akan qirjinta yanasha, Dafarko wani irin dadi tafara ji saboda yanda yakeyi Ahankali, amma da al'amari yaci gaba da wakana saita fara kuka Ahankali

kukanta ne yaqara volume, daqyar ya'iya Dagowa yace "kiyi shiru mana"

gashi yariqe breast dinta a hannunsa yana matsawa


Cikin kuka tace "ni zafi nakeji"

Numfashin sa gaba daya ya sauya, daqyar ya'iya cewa "toshknn nadena, kiyi shiru kinji"

Ahankali ta daga kanta, daqyar suka samu suka rintsa gaba dayansu shida ita
Amma matsananciyar sha'awa kam yana cikin ta



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Da asuba kam, kasa hada ido tayi dashi,shikuwa gogan daqyar yake aiwatar da Komai, Dan gaba daya jiyayi ma dama yasani bai tabata jiyan, saida yayi wanka sannan yatafi masallaci sallah

Kafin yadawo gida kuwa Nihla harta koma ta kwanta, shima Babu musu ya kwanta, sai a lokacin yasamu bacci Mai dadi ya daukeshi
Tarigashi tashi dasafe, tashiga toilet tayi wanka,taci kwalliya cikin riga da siket na leshi, ta gyara Inda yakamata ta gyara sannan tafuto falo tazauna tana tunanin abinda yayi mata adaren jiya, abin de in Ahankali ne akwai dadi, amma yanda ya Abba yadage yanayi abin ba sauqi, amma ta tabbatar ya Abba yana sonta, ita kanta tasan cewa ya tausaya mata jiya

Har karfe goma tayi tana falon azaune, har lokacin Abba bai tashi ba, dirin motar da taji yasa ta kalli bakin kofar, amma batasan kowaye yazoba, Rafi'ah ce tazo bakin falon ta tsaya tana sallama, Nihla tace "ki shigo mana"

Tashigo falon hannunta dauke da flask din abinci, tace "kinsan gidan amare gara munayi muna doka sallama"

Nihla tace "Allah ya shirye ki Rafi'ah, yagida"

Flask din ta ajiye tace "ga abinci nan inji Momy, yana ganki afalo azaune, nida nake cewa qilama kina cikin bargo kina kuka"

Harararta tayi tace "har wani, kukan me, ni rainona ya Abba yake"

Rafi'ah tace "um kaga masoya, tare nake da ya Yusuf fa, shine yakawo ni"

Adede lokacin yafuto daga dakin ya shirya cikin qananun kaya yayi kyau sosai, maganar Rafi'ah tasauka a kunnansa, yace "meyasa bai shigo ba to"

Rafi'ah ta gaida shi, ya amsa mata yace "kije ki shigo dashi mana"

Rafi'ah tace "tab, ya Yusuf din, saida nace yashigo Yaqi yarda"

Abba yace "to mu bari mubishi," ya juya ya kalli Nihla batare dayace mata komai ba, nan take ta gane nufin sa,maganin kar ayi kar afara, danhaka tanemo hijabin ta tasaka sannan suka futo 🤣

Yana cikin motar ya hango su sun futo su ukun, yabude motar yafuto, tareda bawa Abba hannu suka gaisa, Nihla tace "ya Yusuf ina kwana"

"Alhamdulillah qanwata, ya amarci"

Murmushi tayi masa tace "nayi ta kiran wayarka baka picking meyasa?"

Murmushi yayi yace "a inasan abinda yasa kike kiran, babu komai, Allah yasa hakane yafi alkhaairi, amma yanzu nide kitayani kafa fada ta awajan madam Rafi'ah"

Kunya takama Rafi'ah, tajuya cikin motar da gudu tashige, gaba dayansu sukai murmushi sannan sukai musu sallama suka tafi

Ciki suka koma Nihla tazuba musu Abincin suka faraci, Nihla tayi mamakin duk kishin yaya Abba amma bai nunawa ya Yusuf fa, taji dadin hakan sosai, shikuwa sai Kallanta yake qasa qasa, can ta tsinci maganarsa yana cewa "ke dama rayuwa ce bansaniba"

Kallansa tayi tace "ragwantar me nayi"

"gashinan jiya daga fara abu kika kamamin kuka" 🤣

Spoon din hannunta tasaki tareda rufe idonta, yace "idan kin gama kunyar, Muje nafara koya miki motar ki"

Tace "ya Abba A'ina, bade acikin gidaba"

"ai unguwar nan Babu mutane sosai, mufita kawai"

Lokaci daya tafara murna tace "to ya Abba"

Suna gamawa kuwa, suka futo, motar tata suka shiga Wanda dama already ankawo mata ita gidan, sai kwarara gudu yake Kamar yasamu Babban titi, wannan shine karon farko daya taba yini driving da kansa shida ita
Cikin sauri ta kalleshi tace "ya Abba bafa acikin jirgi muke ba"

Murmushi yayi yace "yawwa, nanma yayi," yatsaya, sannan ya kalleta yace "Futo" 🤣, babu musu tafuto shikuma ya koma Inda take da Yazauna

Fara gwada mata yayi, cikin nutsuwa, tana jinsa tana kuma fahimtar abinda yake fada mata
Yabata umarnin ta gwada practical, gaba daya tsoro ya kamata, daqyar tafara driving din Ahankali, can nesa dasu suka hango wani mutum yana tafiya, amma Nihla data taka wata uwar giya, sai ganin mutumin sukai gab dasu, qiris yarage tayi ciki dashi 🙆🏻‍♀️

Daqayar da temakon Abba aka taka giya, sannan motar ta tsaya, tsoro yakamata, gabanta sai faduwa yake

Tuni ta dora kanta akan sitiyarin motar, Abba yafuto yabawa mutumin hakuri sannan yadawo cikin motar yaga yanda haki Kamar Wanda tayi gudu ya tuntsire da dariya
Dagowa tayi ta kalleshi, yaushe rabonda ya Abba yayi wannan dariyar? tace"wallahi na haqura, abarshi kawai "

Daqyar yadena dariyar yace" a a, manyan direbobi "🤣

Cikin shagwaba tace" Allah kadena min dariya "

Yace" to shknn naji, futo kigani "

Babu musu tafuto daga cikin motar, shima yafuto yadawo driving sit Yazauna, ya miqa mata hannunsa yace  "Taho"

Babu musu ta dora hannunta akan masa, babu bata lokaci yadora ta akan cinyarsa, sannan Yarufe motar yace "kina kallan yanda nake yi"

Nihla tayi shiru, tana kallansa, motsin dayake da jikinsa wajan riqe sitiyarin motar da kuma saka giya yasa itama datake zaune akan cinyarsa take motsi, hakan kuwa ba qaramin shiga yanayi ya haddasa masa ba, ahankali ya dakata da driving din yasaka hannu yariqe wais dinta, yadora kansa ajikinta, muryarsa harta fara canjawa yace "kina ganin yanda nake yi ko?"

Nihla Tajuyo ta kalleshi taga yanda gaba daya yanayin sa ya sauya, jikinta yayi sanyi, cikin ranta tace nikam naga koyon Mota 🤣
Afili kuma tace "ina gani"

Shiru yayi, yafara tura hancinsa jikinta yana shaqar qamshin dake tashi ajikinta, ahankali yafara yin sama da hannunsa harya sauka akan qirjinta
Cikin shagwaba Nihla tace "ya Abba awaje mukefa"

Daqyar yadago kansa sannan yabude motar, yace "to zagaya kishigo mutafi gida"

"to ya Abba koyon motar fa?"

Kai tsaye yace "kibari sai nanda wata shida"

Cikin sauri tace "wata shida"

"eh, sai nanda wata shida, zagayo mutafi"

Babu musu tafita takoma daya bangaren sannan yaja motar suka koma gida cikin salama



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️




Washe gari yaje yasiyo mata qananun kaya, afalo yaganta tana waya, ya ajiye jakar kayan Yazauna agefenta, sai yaji tana cewa "Babu komai Anty Nadiya, ai nasan dama akwai dalilin dayasa baki zoba"

Cikin ransa yace Nadiya! Ya Jinjina kansa

Nadiya tace"to shikkenan amarya agidan Sadiq Mazawaje, ki gaida shi "

" gashinan azaune ma Anty Nadiya, gashi "tafadi haka tana bawa Abba wayar

Kawarda kansa yayi yace" nagode "

Nihla tace" Anty Nadiya wai yace yagode"

Nadiya tace "nasan fishi yake dani, amma Dan Allah Nihla ki nema min yafita awajan sa"

"to Anty na, insha Allah" daga nan sukai sallama

Tajuyo ta kalleshi tace "Anty Nadiya tace kayi hakuri akan abubuwan datayi ma, kayafe mata"

"Babu damuwa, Allah yakiyaye, amma yakamata ki kashe wayarki, banason adinga damunki da kira, ga kaya nan nasiyo miki, kiduba kigani"

Tace "to ya Abba nagode sosai" tadauki jakar tabude tafara duba kayan ciki, gaba daya qananun kayane amma Babu na arziqi aciki, duk kayane na badala 🤣
dago kanta tayi tace "ya Abba yanzu wannan kayan Dan Adam zai saka?"


Yace "ba dan Adam zakice ba, cewa zakiyi wannan kayan Zansaka?"


Ta daga wata riga tace "ya Abba kagafa wannan rigar gaba dayan ta andebe gaban rigar" 🤣

Ajiyar zuciya yayi yace "to shikkenan" daga nan yatashi yayi cikin dakinsa

Nihla ta cigaba da daga kayan, yanzu saboda Allah tayaya zaice tasaka wannan kayan, tatuna yanayin daya tafi tasan fishi yayi, itama ta shareshi tadauki kayan takai dakinta

Har azahar bai futo daga dakinsa ba, itama batajeba, wanka taje tayi adaki ta shirya cikin atamfa, sannan ta gabatar da sallah, kwalliya ta tsara Mai kyau sannan tafuto falon, anan taganshi yana kwance dagashi sai gajeren wando, ya kunna tv yana kallo, kitchen tawuce taje ta debo masa snack takawo gabansa ta ajiye, ya kalleta baice komai ba, amma cikin ransa baiji dadiba yanda taqi saka kayan, shi mutum ne dayake son ganin matar sa cikin qananun kaya, sannan kowanne lokaci yaji matar sa akusa dashi, amma yaya zaiyi tunda bataso, dole haka zai haqura bazai yi mata dole ba

Nihla Tajuya cikin daki tazauna agefen gado, tafara tunani da gaske de fishin yake kenan, to yanzu in banda rigimar ya Abba tayaya zata saka wannan kayan? Wata zuciyar tace da ita to menene idan kin saka dinma? Bayan Babu abinda yake miki, illa iyaka yataba jikinki shikkenan, shawarar zuciyarta tabi, ahankali tatashi ta cire kayan jikinta, ta duba kayan ta dauko wata yar qarama Tsawon ta bai wuce gwiwar taba, gaban rigar kuwa abude yake



Sosai kake hango albarkatun qirjinta, haka tafuto daga dakin salalo salalo sai hannu take sawa tana kare jikinta, yana hango ta ta miqa mata hannu, ta kalli yanayin dayake ciki, takawar da kanta sannan ta dora hannunta cikin nasa, kai tsaye ya fuzgota tafado jikinsa, kanta yana kan qirjinsa, dis yaji hawaye yadiso akan qirjinsa, yasaka hannu yana bubbuga bayanta yace "nineko?"

Daga masa kai tayi, yayi Murmushi yace "to kiyi hakuri, dama inaso naganki da kayan ne shiyasa"

Kanta tasake gyara wa akan qirjinsa tayi luf,hakanan ta tsinci kanta da sakar masa kukan shagwaba, cikin ransa yace yasalam! Tareda lumshe idonsa
 yasaka hannu yaqara rungumeta sosai ajikinsa, fatar qirjinta tahadu da tasa fatar jikin nan take yafara shiga yanayi,kwana uku, ai yayi kokari, kullum saide yadan rage zafi da'ita ta hanyar wasa, gaskiya yau kam bazai iyaba, bazai iya daga mata kafa ba,

Idanunsa a lumshe yayi qasa da murya yace "nakoya miki wani abu?"

Tadaga masa kanta

Ahankali yabude idonsa, sannan yasaka hannunsa biyu yadago kanta dasu, dif yahade bakinsu waje daya

Lips dinta nasama yakama yana sha sosai, idonsa a lumshe, saida yasha sosai sannan yasaki yakama na qasan yanasha, ita kanta taji dadi domin kuwa batasan lokacin data lumshe nata idon ba, kusan minti uku yayi yana kissing dinta sannan ya cire bakinsa daga nata yace "kin koya yanzu?"

Cikeda kunya tadaga masa kanta

Yace "Ok try"

Ganin Babu abinda yake mata yasa tasaki jikinta dashi gaba daya, babu tunanin komai ta dora bakinta akan nasa, tafara kissing dinsa Slowly, nan take hankalin Abba yafara gushewa


Baisan lokacin daya cafke bakinta ba, yafara yimata wani irin mahaukacin kiss, Tun suna kwance akan kujera har suka kusa faduwa, daqyar tasamu tazare bakinta daga cikin nasa tace "ya Abba ga snack fa na kawo ma bakaci ba"

Wani irin numfashi yake Fitar wa, Idanunsa duk sun sauya launi, yace "zaki bani?"

Tace "eh, tashi nabaka"

Daqyar yatashi daga kan kujerar, tsautsayi yasa ta kalleshi, cikin sauri takawar da kanta ganin yanda komai nasa ya baiyana Kamar Babu gajeren wando ajikinsa

Da kanta tafara bashi abaki,yanaci, amma yanda taganshi kadai yasa gabanta faduwa, tab!

Shikuwa sai Kallanta yake, yanacin snack din, daqyar yagama yamaida matar sa jikinsa suka fara kallo, yana fada mata idan yasamu lokaci zasuje shopping, saita dubo abaya wadda zatake sakawa akan uniform dinta idan zatake zuwa wajan datake service, taji dadi sosai, tace "Allah yakaimu"

Daqyar Abba yayi hakuri har zuwa dare, Nihla de bata gane komai ba, tunda taga tunda akai auren baiyi mata komai ba, tasan yauma zai iya qyale ta, Dan haka tasake dashi sosai sukayi kwanciyar su, shima daya ga haka yajata jikinsa cikin dabara yafara janta da fira

"kinsan me?"

Tace "a a ya Abba"

Yasaka hannu cikin dabara ya cire mata hannun yar qaramar rigar jikinta sannan yace "fatarki tanada laushi sosai, wanne irin Mai kike amfani da shi ne?" 🤣

Nihla taji dadi anyabeta cikin nishadi tace "kaima zakake shafa wa ne?"

Abba yayi Murmushi, yakai hannunsa ya kashe musu wutar dakin, sannan yasaka hannunsa zuwa qasan rigarta ya cire mata ita gaba daya, yace "akwai zafi garin yau" 🤣
Sannan yadan fara shafa bayanta yace "idan zamuje shopping to nima saiki dauko min irinsa, inaso"

Lumshe idonta tayi, yanda takejin hannunsa yana shafa jikinta Ahankali, tace "to"

Breziya din dake jikinta ya cire 🤣yace "kidena kwanciya da wannan abin fa, zaisaki ciwon qirji"

Nihla tadaga masa kanta Ahankali tace "to"

Bayanta yaci gaba da shafa wa da niyya yake tabo mata gefen qirjinta, sannan yace "nakoya miki wani abu?"

Nihla tayi shiru tana tuna dazu abinda yafaru, tace "a a, karka koyamin" 🤣

Shagwabar tasa yafara yimata yace "uhm uhm bafa wani abu baneba, kinji... Nakoya miki?"


Jikinta ya kashe mata, sakamakon yanda yake mata wannan Shagwabar Babu musu tace "to" 🤣

Ahankali ya birkitota daga jikinsa, batayi auneba taji Saukar hannunsa akan qirjinta, lokaci daya taja wani numfashi tareda lumshe idonta, ahankali yafara matsawa yana kallan yanayin ta, wani irin numfashi tafara fitarwa, tanaso ta hanashi amma abinda takeji yasa tayi shiru tabarshi yanayi, tasan ba komai zaiyi mata ba, Dan haka tasaka hannunta akan nasa hannun alamun kada yadena

Wani irin yanayi yake jinsa aciki, ga wani irin laushi dayaji, lokaci daya jikinsa yafara karkarwa, yace "inci gaba kina koya?"

Batasan lokacin data daga masa kanta ba, ganin haka yasa yasunkuya tareda dora bakinsa akan breast dinta guda daya,sha yafara yi Ahankali Kamar wani jariri, dayan kuma yana matsawa

Lokaci daya Nihla ta rikice, gaba daya taji bataso yadena abinda yake mata, daqyar ya cire bakinsa yasake Kallanta yace "akwai dadi ne inci gaba da koya miki?" 🤣

Bata iya bashi amsa ba, saima hannunta da tasa akan lallausar sumar kansa, tafara kokarin maida masa kansa Inda yadago, yana ganin haka ya cire kayan jikinsa, duk batasan abinda yakeba, tadaiji yasaka hannunsa duka biyun yahade breast dinta waje daya sannan yamaida bakinsa kansu yanasha sosai, ahankali tasaka hannunta ta rungume shi

Gaba daya Abba yafita ahaiyacinsa, ko'ina rawa yake ajikinsa, cikin nutsuwa yafara neman hanyar sa, amma bata samu ba, Awannan halin dayake ciki kuma bashida niyyar hakura, haka yasake gwadawa yanaso yashiga still shiru bawani labari, daga qarshe sai tausayin sa yacire ya daddage yashiga, wata irin qara Nihla tasaka, kasancewar gidan sabo ne nan da nan yadauka

Hannun data rungumeshi, shi tasa tafara dukansu, da hannu bibbiyu 🤣🙆🏻‍♀️
Amma Abba, jinsa yake awata irin duniya

Gaba daya bayajin dukan datake masa, kawai abu daya yakeyi, gefen kafadarsa tasamu ta cijeshi, tana kuka, hawaye sai ambaliya yake akan kuncinta yana gangara wa kan fillo, cikin kuka tace "ya Abba zaka kasheni, nashiga ukuna, Momy ya Abba zai kasheni"

Tasaka kuka sosai, shi kansa zuwa wannan lokacin hawaye yake, yakasa controling kansa gaba daya, yana hawaye yana kiran sunanta "Nihla... Nihla.. Bansan haka ake jiba"
Wasu maganganun shi kansa bayasanin meyake fada, jijjigashi take tana yaqushi, cikin sauri yamaida bakinsa cikin nata, hawayen idonsa yana sauka akan fuskarta, yayinda idonta yayi jajir, suka kumbura saboda kuka

Wani irin dumi yakeji da masifar dadi, Wanda kozai mutu bazai iya raba kansa da'itaba

Nihla Babu damar kuka saboda Yarufe bakin,amma wata irin azaba takeji Kamar ta mutu, tunda tazo duniya bata taba jin wannan bala'in ba irinna yau

Saida yadauki Tsawon awa daya, yana abu daya, sannan yarirriqeta Kamar zai ballata, lokaci daya kuma jikinsa yasaki,nan take zazzabi Mai mutuqar zafi Yarufe ta, banda ciwon kan nan take daya kamata 🤣
ahankali yafara zare jikinsa daga nata, har lokacin bai daina kuka ba, ahankali yasaka hannunsa ya janyo ta jikinsa, yamaida kansa cikin wuyanta ya fashe dawani irin kuka, yace "i luv u Nihla,i luv u so much my Soul'












 
Kunsamu Nihla da Abba ko jajen gidansu Dida da Diyana bakwayi ? 🤔





Yanda kuka samu typing dayawa yakamata nima nasamu sharhi please 🙏










Amnah El Yaqoub ✍🏻❣️DANGI 'DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub


Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493



61&62



Wani irin haushi yakama Nihla, yama za'ai bayan kuka da tasha, tanayi masa magiya yaqyaleta amma yaqi hakura zaizo yana mata kuka, ahankali tafara kokarin janye jikinta amma takasa, jikinta zafi sosai, ga wata uwar gajiya da takeji, shi kansa yagane hakan, cikin sauri yasake matse ta ajikinsa sannan yashare hawayen idonsa yace "Allah yayi miki albarka, nagode, ina qara yiwa Allah godia daya yimin kyautar mace Kamar ki, nagode da irin yanda kika kawomin mutuncin ki lafiya, i luv u"

Yana qarasa magana yadora bakinsa akan nata yana kissing, lokaci daya ta fashe da wani irin kuka, ahankali ya cire bakinsa sannan yatashi ya kunna wutar dakin, yana ganin halin da take ciki yace "Innalillahi 😳
Nashiga uku"

Hawaye yanata zuba a'idonta, ahankali tarufe idonta, bazata iya kallansa hakaba
Cikin sauri yadauketa sukai toilet, Ruwan dumi yahada mata tashiga sai ihun zafi take masa, shi kansa kawarda kansa kawai yake, amma yasan cewa yayi mata barna dayawa, saida sukai wankan tsarki sannan ya gyara musu gadon tareda canja bedsheet din suka kwanta, har lokacin Nihla bata dena hawaye ba, haka kuma batace dashi uffan ba 🤣

Idonta arufe taqi kallansa, cikin tausayawa yace "kiyi hakuri dan Allah, wallahi ni bansan haka ta faru ba, Dan Allah kiyi hakuri kiyafemin, bazan sakeba"

"dan Allah ni kamin shiru, zazzabi kake qaramin" 🙆🏻‍♀️🤣

Abba baisan lokacin daya saki wani irin murmushi ba, ahankali yatashi yaje dakinsa yadauko mata magani yabata, daqyar tasamu tasha ya kalleta yace "to kiyi shiru mana, sai hawaye kikeyi"


Wani irin kuka tasaki, tasaka hannu tarufe fuskarta dashi sai kuka take masa sosai, cikin kuka tace "mugu kawai , dama ai nasan baka qaunata,Inda kana sona zaka qyaleni, amma nacema kabari kabari zaka kasheni, shine karabu dani"

Dariya tanason kamashi amma yagagara yinta saboda karya jawowa kansa,shagwaba yafara yimata "inason ki mana, to... ba wannan ne soyaiyar ba"

Dago kanta tayi ta kalleshi tace "Amma ai cewa kayi abu zaka koyamin" 🤣

Yace "abun me? Kifada mana, ai sunansa zaki fada" 🤣

Tayi shiru tarabu dashi tana kuka yace "to kiyi shiru, kinga yanzu dare ne, kibari idan safiya tayi sai Muje asbiti adubaki"

"niba Inda Zani, karabu dani kawai..." ta qarasa maganar tana daga masa hannu

Kukan shagwaba yasamata "uhm.. uhm... to kidena kukan mana, kinga fa nima Inda kika cijeni ciwo yake min... uhm wayyo Momy zafi hannu na"

Kallansa tayi ganin yanda yafara yimata halinnasa Wato shagwaba 🤣
Yayi mata laifi yazo ya isheta da wani kukan shagwaba,
banza tayi dashi ta qyaleshi, tajuya masa baya takwanta

Shiru yayi yadena mata kukan, sannan yayi Murmushi shima yaje bayanta ya kwanta tareda janyo ta jikinsa, wani irin nishadi yakeji Wanda bai taba jiba, haka kawai yakejin farin-ciki acikin zuciyarsa, ahankali yadora hannunsa akan qirjinta yana shafa wa

Tana jinsa amma yanda takejin zazzabi ga ciwon jiki, hakan yasa tarabu dashi, gaba daya jitake wani irin radadi wajan yake mata, zafi sosai takeji, ahankali hawaye yake diga daga idonta zuwa kan hannunsa, hakan ya tabbatar masa kuka take, hannunsa ya janye daga kan qirjinta, sannan yajuyo da ita yasaka harshansa yana share mata hawayen dashi, cikin sigar lallashi yafara lallaba matar sa



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️



Sun dade suna bacci dagashi har'ita Babu Wanda yatashi akan lokaci Tun lokacin dasukai sallar asuba, tasamu de zazzabin nata yasauka, amma gaba daya tayi laushi 🤣

Zaune suke afalo tana zaune a cinyarsa yana bata Tea tanasha, kanta yana kan qirjinsa saiya debo Tea din sannan zata dago tasha tamai kanta, hannunsa yasa akan wuyanta yace "har yanzu jikin naki dadan sauran zafi, kince kuma karmuje asbiti zaki warke, tayaya ki kasan haka"

Idonta ne yaciko da qwallah kafin tace wani abu wayarsa tafara qara, ganin me kiran yasa yadauka cikin sauri "Momy good morning"

"Abba ina yata take, Tun jiya ina kiran wayarta akashe"

"Momy wayar akashe take, damun ta ake da kira sainace ta kashe kawai"

Momy tace "um.. tonaji, bata wayar"

Kallan Nihla yayi yaga qwallar data cika idonta harta sauko tazama hawaye, kuma yasan idan Momy taji muryarta hankalinta zai tashi, yace "Momy tana bacci ne, bata tashi ba"

"wanne irin bacci ne wannan Abba shabiyu saura, tasheta kabata waya"

"Momy... ai, Momy ai ba dadi mutum yana bacci atashe shi, idan tafarka saita kiraki"

Momy tace "Abba, banason shirme, tunda aka kawo yarinyar nan bamuyi wayaba, kawai Rafi'ah tacemin ranar data kawo muku abinci taganta tana nan lafiya, ita bata kirani ba, nima sai yau nasamu nasallami mutane, tasheta kabata waya pls"

Badon yasoba haka yabata wayar, wayar takara a kunnanta cikin rawar murya "He.. hello Momy"

Momy tace "Subhanallah Nihla meyake faruwa"

Duk yanda taso danne kukan ta hakan bai iyu ba, saida tasake shi, Momy najin tasaki kuka tace "menene yake damunki yata"

Cikin kuka tace "Momy Dan Allah kizo..."

Abba ya kalleta da sauri yana zaro idonsa 😳

Momy tace "kiyi shiru kimin magana, nasan ba bacci kike ba yacemin kina bacci, mene yake damunki"

"Momy nide kizo ki daukeni mutafi gida, Allah bazan iyaba, ya Abba zai kasheni" ta qarasa maganar tana fashewa da kuka

Momy najin haka ta gane komai, ta sassauta muryarta tace "Nihla!, kina jina?"

Daga kanta tayi batareda tace komai ba, Kamar Momy din tana ganinta

Momy tace "Nihla, ki saurareni dakyau, ko wacce mace dakike gani da haka tafara, wannan shine auren, kuma wannan shine abinda ake kira hakuri, dole hakuri zakiyi, Nihla ki godewa Allah kinkai mutuncin ki lafiya gidan mijinki, wadda tarasa wannan damar ta hanyar bin samarin banza Nihla fargabar zuwan ranar take ma, kidinga tsarki da Ruwan zafi koda yaushe kinji ko, sannan kidinga zama aciki sosai "

Jan zuciya tayi tace"to Momy "

"bawa Abban wayar"

Wayar tabashi ya karba jikinsa a sanyaye,"Haba Abba, wanne irin rashin tausayi ka gwadawa yarinyar nan har take cewa azo atafi da'ita gida"


Sumar kansa ya shafa cikin kunya yace "Momy"

Daga nan yayi shiru yakasa cewa komai, sai shafa kansa yake yana yiwa Nihla wani irin kallo Mai kashe jiki

Tace "kunje asbiti ne?"

"A a Momy, taqi yarda"

"Abba amarya ai saida lallami, lafiyarta ce dole ko bataso haka zaka dauketa kuje, yanzu zanturo muku Doc tadubata, amma kadinga bin yarinya ta ahankali Abba, banason rashin hankali" 🤣

Murmushi yayi yace "to Momy"

Daga nan tayi musu sallama ta kashe wayar, yasa hannu yadauki Nihla yayi hanyar dakinsa da'ita yana cewa "bismillah... Bari mushiga daga ciki, Momy tace Muje aci gaba da gashi" 🤣

Kallansa tayi dasauri tace "nashiga ukuna, Innalillahi, Dan Allah Dan annabi kayi hakuri"

Murmushi yayi yace "keda kika hadani da ita, ai shiyasa tace naci gaba daga Inda na tsaya"

Hawaye yazubo mata tace "wallahi tallahi nadena"

"ke wasa nake miki, Doc zata turo adubaki tunda kinqi yarda muje asbitin, shikkenan?"

Wata irin ajiyar zuciya tasauke Mai nauyi

Yayi Murmushi yana girgiza kansa

Daga nan yayi ciki da'ita



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Tunda su Ibrahim Mai hakuri sukazo auren Nihla har suka koma Abuja Momy take ta tunani akansa, yakamata ace tabashi shawara Mai kyau ko Allah zaisa yayi amfani da'ita
Wayarta tadauka ta kirashi, bugun farko kuwa yadauka "hajiya yaya mutanan gida, ya wajan amare"

Momy tace "Alhamdulillah Mai hakuri, dama wata magana nakeso muyi ko Allah zaisa adace"

"to hajiya ina jinki, Allah yasa lafiya"

"lafiya kalau Ibrahim, saima alkhaairi, Wato Ibrahim gani nayi Tun rasuwar Aisha kusan shekara biyar zuwa shida har yanzu kana zaune Babu aure, mezai hana kasamu wata matar ka aura?"

Baba yayi Murmushi yace "hajiya kenan, to yanzu Awannan shekaru nawa, Wacece zata aureni, ai saide muci gaba da addu'ah Allah yasa mucika da imani, kuma Allah ya albarkaci Rayuwar yayanmu"

"Ibrahim kenan, wanne shekaru gareka da zakace ba zakayi aure ba? Yartaka qwaya daya jal Nihla? Yarinyar daba shekaru gareta ba? To gaskiya yakamata kasake shawara"

"to hajiya, wazan aura yanzu? Wacece zata zauna dani tsakanin ta da Allah Kamar Aisha ta?"

Kai tsaye Momy tace "Akwai Ibrahim, idan kabani dama akwai wadda nayaba da hankalin ta, kuma ni azamana da'ita dakuma binciken danayi batada matsala kokadan, sannan batada matsala da yarka"

"to Wacece wannan hajiya?"

"Adala, wadda take tayani da wasu ayyukan, nadade inama sha'awarta, tanada hankali sosai, tataba yin aure mijinta yasaketa saboda matsalar abinci, baya bata abinci, danta daya namiji kuma yana hannun ubansa, yanzu haka saida nafara tuntubarta da maganar sannan nazoma da'ita, idan ka amince kawai sai ayi, kodan mutuncin Nihla ma"

Murmushi baba yayi '' to hajiya, inde tayi miki ai shikkenan, nasan bazaki hadani da wadda halin ta yasha bambam dana Aisha ba, nagode hajiya, amma Kamar yanda kika fada dinne, zanyi ne domin mutuncin yata "

Momy tace" to Alhamdulillah, Allah ya tabbatar da alkhaairi, saimunjika "

Daga nan sukai sallama



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️



Tunda Doc tazo tadubata tayiwa Abba kashedi akan yarabu da'ita harsai ta warke, haka haqura yanaji yana gani har Tsawon sati daya, amma mutuqar matsuwa amatse yake, saide yayi wasa da ita kawai, ta hakanne yake  ragewa kansa zafi

Yauma da rana suna kwance a dakinsa, yadora kanta akan qirjinsa yace "bani labari mana"

Tace "ni banda labari"

"toni nabaki?"

Tace "inajin ka"

"kin tuna lokacin da Aslam yakawo ni gida asume?"

"eh natuna, meya faru?"

"aikece Sanadin suman nawa" 🤣

"nikuma? Tayaya?"

Murmushi yayi yace "a lokacin jinake Kamar nasaceki wallahi, inajin sonki a raina sosai, Aslam nafara fadawa amma bansamu goyon baya awajan sa ba, sai nace Zan gwada ki nagani idan kina kishi na, na shirya nace muku natafi zance, amma sai cemin kikai wai nagaisheta, Hmm dakinsan yanda kika sa kaina yasara ko, da bakiyi magana ba, naso ace naga kishina a'idonki, dama da ina fita Zan dawo na zauna muyi fira afalon ki kalli kwalliyar dana miki dakyau, amma sai kika hargitsa min lissafi na "🤣

Murmushi tayi kawai

Yakalleta yace" idan kina tareda maza fa kidena musu murmushi, domin kuwa ba qaramin kyau yake qara miki ba"

Murmushin tasakeyi tace "kaima haka"

Cikin sauri ya kalleta, lalle yana samun cigaba akan yanda Nihla take cigaba da yafe masa, yace "da gaske?"

Tadaga masa kanta

Yayi Murmushi yace "na koya miki wani abu?"

Cikin sauri tace "a a wallahi, nagode, kabarshi basai na koya ba" 🤣

"to yanzu sai a zauna haka Babu abinda ake koya?" 🤔

Tace "um"
Yace "kema to bani labari, tunda kinqi yarda nakoya miki"

"ni banda labari, saide kai kaci gaba dabani"

"nima Babu labari, namanta komai yanzu, ki bari nakoya miki abun saina tuno daga nan" 🤣

Tace "a a"


Hannunsa yadora kan qirjinta yana shafa wa, ya sassauta muryar sa yace "please"

Shiru tayi masa, amma gabanta banda faduwa Babu abinda yake, a mutuqar tsorace take, breziya dinta yacire gaba daya yaci gaba da shafa qirjinta, Tun yanayi ahankali harya dawo yida sauri,numfashin sa nafita dasauri yace "Nihlaaaa... Laushi.....

Azabar da tasha Dafarko tatuna tafara yimasa raki, be fasa abinda yake ba daga qarshe ma ya hade bakinsu waje daya

Duk yanda taso zillewa kasawa tayi, haka tabarshi yayi yanda yaso da'ita, amma kuka kam tasha shi, bataji banbanci ba tsakanin sa dana farko, kuka take masa sosai, shima kansa abin yabashi mamaki ganin wannan karon ma daqyar yashige ta, tana rungume a jikinsa yana lallashinta yace "kina shan wani abu ne?"

Girgiza masa kai tayi, yace  "kiyi hakuri to, zaki de najin zafin nan gaba kinji"

Ahankali tadaga masa kanta



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️



Haka Rayuwar taci gaba da wakana, komai yana tafiya yanda yakamata a kowanne bangaren, har Tsawon wata biyu da satittika, zuwa wannan lokacin Adala ta auri baba Inda Mazawaje family sukayi mata kara aka hadu aka rakata dakin mijinta dake Abuja bayan zaman sati biyu datayi awajan danginsa har suka Dan saba da'ita sannan tatafi abujan, baba yana jin dadin zama da matar sa sosai, haka Nihla tayi farinciki da auren mahaifin nata, kowa yanayin aure yana Dan murmurewa amma awajan Nihla, babu wannan sai wata uwar rama ma data qarayi, kana ganinta zakasan ta rame sosai, saboda har yanzu Muddin ya Abba ya nemeta tofa tanajin zafi sosai, shi kansa abin har mamaki yake bashi, kuma har yanzu idan zai shiga daqyar yakeyi, kullum sai yasha fama, hakan yasa tasaka abin aranta duk ta rame, ga ya Abba Babu wasa, ranaku daidai ne bayayi, idan tayi korafi yace ahakane ai zata saba, babu yanda ta'iya sai hakuri amma abin yana damunta sosai aranta, gashi bata fadawa kowaba ba



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️




"wayyo Allah ya Adam nashiga uku, cikina"

"Innalillahi maryam ko naquda kike ne?"yafadi haka cikin rikice wa

" ya Adam Zan mutu, Dan Allah ka yafemin kaji, mutuwa zanyi "

Idon Adam yacika da qwallah ganin irin wahalar da Diyana take ciki, gashi tana kiran mutuwa, yace" mariya kiyi hakuri, bari mutafi asbiti, ba zaki mutu ba kinji, kiyi hakuri "

Jikinsa na rawa yakira hajiya Na'ila awaya yafada mata, cikin tashin hankali tace suhadu a asbiti

Adam yasa hannu yadauketa gaba daya, yasa ta amota cikin sauri yaja motar sukabar gidan, yana driving yana juyowa yana Kallanta, ikon Allah ne kawai yakawo su asbitin lafiya

Suna zuwa hajiya Na'ila ta kamata sukai ciki, likitocin ma suna karbar ta sukaga haihuwar tazo kusa, Adam yakasa zama, sai zagaya wajan yake, hajiya Na'ila kuwa addu'ah take mata kawai
Bata dauki lokaci Mai tsawo ba kuwa cikin temakon ubangiji ta haifi danta namiji Mai kamada Adam sak

Hajiya Na'ila tarasa Inda zata dora ranta saboda murna, shi kansa Adam abin ba qaramin dadi yayi masaba, yau shine da dansa na kansa



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️



Bayan kwana shida suna zaune adaki ta dashi, tadubeshi tace "ya Adam nikam sunan wa zamu sawa yaron nan ne? Nasan sunan Daddynku zakasa ko?"

Adam yace "a a maryam, bazan sa sunan Daddynmu ba"

Tace "to ya Aslam zaka saka?"

"A a, bashi Zan sakaba"

Cikin mamaki tace "towa zaka saka?"

Ajiyar zuciya yayi yace "maryam, Aslam dan'uwana ne, dama can akwai zumunci a tsakanin mu, Karki Manta Allah ne yahadamu maryam, Inda danta iyayen mu ne ba zasuyi tunanin hadamu aure ba, amma gashi kakanninmu sunyi wannan tunanin, badon komai ba saidon su qara danqon zumunci a tsakanin mu, mu jikokinsu, kinga Aslam yasaka sunan Abba, dan haka nima acikin mu jikoki Zansaka sunan wani"

Ajiyar zuciya tayi tace "hakane kam, gashi yanzu atsakaninmu jikokin muna zumunci sosai, haqiqa auren zumunci akwai dadi idan har iyaye suka kauda kai akan yayan su, amma Muddin akace yara sun samu matsala, har aka samu rabuwar kai adangi wannan yana bayan wannan, wannan ma yana  bayan wannan, to tabbas dole aure ya lalace, kuma dole kan mutanan wannan dangi yarabu, yanzu de sunan wa zaka saka masa? "

Kai tsaye yace  "Fawaz"

Murmushi tayi tace "to Allah ya rayamana ya Fawaz, Dida tayi miji kenan" 🤣

Gaba dayansu sukai murmushi



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Washe gari sunan Diyana, Tun safe Dida take fama da tashin zuciya, komai taci sai amai, hankalin Fawaz yatashi, dan haka yadauketa suka tafi asbiti, suna zuwa kuwa aka gama yimata gwaje gwaje, doc din yafada musu abinda gwajinsu yabasu
Fawaz yace
"Doctor, da gaske kake mata ta tana dauke da ciki harna Tsawon wata biyu?"

"qwarai kuwa Fawaz, matarka tanada ciki, Allah yasauketa lafiya"

Cikin farin-ciki yayiwa Doc din godia, suka Taho, ahanya ma yana driving amma bakinsa yakasa rufuwa, gidan Diyana zai kaita wajan suna amma saiyai kwana suka tafi gida

Wannan ne karon farko daya taba kawota wajan ummansa tunda aka musu aure, ummah taji dadin ganinsu sosai

Suna zaune afalo shida ita, Umma kuma tatafi takawo musu ruwa, yadubeta yace "gaskiya ko Baby Dida, idan kika haifamin Baby me kama dake dakuma halaiyarki zanji dadi" 🤣

Ta kalleshi tace "ko"

"hakane, wannan shine fatana, naji dadi sosai, Allah ya saukeki lafiya, me kikeso nasiyo miki amatsayin gift ki fadamin pls?"

Kai  tace "bana son komai ya Fawaz, kawai sonake karabu da wannan abokin naka Wanda yake daukan hankalinka zuwa shaye shaye"

Murmushi yayi yace "angama hajiya ta, saime kuma?"

Saida tayi farrr da'idonta sannan tace "saikuma zancen aiki, ka daure kafara zuwa Kamar yanda kowa yake tafiya aiki, kadinga temakon Abbanku awajan ajikinsa, zaiji dadi sosai"


Murmushi yayi yace "angama Baby Dida, aini yanzu gaba daya nazama naki, sai yanda kikai dani"
Ya matso jikinta yayi kissing kumatunta

Zaro ido tayi tace "Allah idan ummah tadawo taganka ko Babu ruwana"

Dariya yasaka, adede lokacin ummah tashigo falon hannunta dauke da lemo, bayan ta ajiye musu suka qara gaisawa, Fawaz yace "ummah, please ki fadawa Abba na next week Zanfara futowa aiki"

Farin-ciki yakama hajiya Abida tace "Alhamdulillah, Allah abin godia, toshknn Fawaz, yana zuwa Zan fada masa insha Allah"

Sake dubanta yayi yace "am umma, daga asbiti fa muke, Doc yace Dida nada ciki" 🤣

Cikin sauri Dida takai Kallanta gareshi, sannan tarufe idonta cikin kunya

Ummah tace "alhmdllh, kuce niyau da labarai masu dadi kukazomin" ta kalli Dida tace "Dida? Allah ya saukeki lafiya kinji yata?"


Dida tayi Murmushi shikuwa Fawaz yace "Amin ummah" 🤣
Sun Dan dade suna fira sannan sukai mata sallama suka tafi gidan Diyana



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️



Taron suna ya qayatar, Diyana da danta Fawaz sun shiga sun fita, wannan karon ma hajiya Na'ila itace tayi kaka gida akan komai, ita ala dole sunan jikanta ake, Kamar de yanda tayi a sunan Ilham 🤣

Gaba dayansu yaran sukam suna dakin maijego sunata fira, sai bayan sallar magrib ya Abba yazo yadauki Nihla suka tafi gidan Momy
Suna zuwa Nihla tafada jikinta cikin murna, anan falo suka baje kolin firar yaushe gamo, shikam yana kawota yafice

Saida sukai sallar ishsha'i sungama cin abinci, Momy taje daki tahado mata wani tsumi takawo mata tace "ga wannan kisha, rannan Abba yazo namanta ban bashi yakai miki ba"

Jikin Nihla yayi sanyi ta karba tace "Momy ni wannan abun banason sha"

"shirman banza, meyasa zakice ba zakisha ba? Cemiki akai wannan rawar kan na Abba abanza yake miki?"

Cikin shagwaba tace "to Momy shima tambaya ta yakefa wai kona sha wani abu.. ni... ni wallahi Momy auren nan inaa" 🤣

Ajiyar zuciya Momy tayi, ta kalleta dakyau tace "Nihla, shiyasa naga duk kin fada, kinyi yar kama?"

Cikin in-ina Tace "a a Momy ni kawai...." saikuma tayi shiru

Momy tace "Nihla bakida Wanda ya fini kinji ko, kidena kallo na amatsayin mahaifiyar Abba, ki kalle ni amatsayin mahaifiyarki, fadamin menene yake damunki kika rame"

Ahankali tace "Momy ya Abba ne, kusan kullum fa... Allah Momy rana daidai ne bayayi nikuma zafi nakeji har yanzu, shine yace idan wani abu nake sha yake sake rufewa tona dena"


Momy tayi Murmushi tace "tokuma Nihla saboda wannan sai kiyi shiru? Yanzu kenan badon na tambayeki ba haka zaki zauna ko?, toki godewa Allah ma dayake tsallaken wasu kwanakin"🤣

Nihla tayi shiru kanta akasa, takasa hada ido da Momy


Momy ta dafata tace "Karki sake boyemin damuwar ki kinji ko? Bari inyi magana da wata qawata ta kawomin maganin dazaki dinga sha insha Allah zaki denajin zafin, tunda nasan ba yanzu Abban zai dawoba harta aikomin ma kafin kutafi, amma yanzu de dauki wannan tsumin kishanye duka "

Nihla ta daga kanta alamun to, sannan tadauka ta shanye shi tas


















(eh lalle Momy kin bawa Abba dama sosai 🤪



Najiya dayau kenan, Mutara zuwa gobe insha Allah 🙏🏻)





Amnah El Yaqoub ✍🏻❣️DANGI 'DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}

Writing by Amnah El Yaqoub

Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493



63&64


Saida Momy taga Nihla ta'ajiye cup din Babu komai sannan tadauki wayarta, takira qawar tata tatashi tayi cikin dakinta tana waya

Nihla tasaki ajiyar zuciya, tabbas barin damuwa acikin zuciya ma wata illar ce, yanzu gashi data fadawa Momy matsalar ta tana shirin tafiya

Tashi tayi daga kan kafet din falon takoma kan kujera ta kwanta tazuba wa tv ido tana kallo
Jitayi yanayin ta yanata sauyawa, kuma tabbas tasan cewa hakan baya rasa nasaba da maganin da tasha yanzu, shigowa cikin falon yayi bakinsa dauke da sallama, ta amsa masa tana kallansa

Kafafunta yadauke Yazauna awajan sannan yadora mata kafar akan cinyarsa yace "muwuce yanzu ko?"

Fuska ta yamutsa alamun tanason kuka tace "ya Abba Dan Allah mukwana anan kaji"

Wani irin shu'umin kallo yayi mata, yasaka hannunsa yana sosa mata tafin kafarta tareda shafa wa yace "kin tabbatar zaki iya?"

Idonta ta lumshe alamun jin dadin abinda yake mata tace "emana to menene"

Ganin bata gane Inda maganarsa ta dosa ba yasa yafuto mata baro baro yace "zaki iya rufemin bakina idan kika sani kuka ko?"

Cikin shagwaba tace "uhm.. To ya Abba basai muhaqura ba"

"muhaqura dame? Bari kiji dama can bansan haka akeji ba, Inda nasani ko kwana daya bazan bari kiyi batare danayi ba"

"to Dan Allah mukwana anan din kaji"

Wani irin kallan luv yayi mata, ahankali yafara shafa kafarta yana tura hannunsa zuwa cikin siket din dake jikinta har yazo kan cinyar ta yaci gaba da shafa wa cikin wani irin salo, lumshe idonta tayi tareda bude masa kafar ahankali
Kamar Wanda yake mata rada yace "nide bazan iya haqura ba, kuma yauma sainayi"

Shiru Nihla tayi masa, tanajin dadin yanda yake mata, ga kuma wannan maganin da tasha yana qara fizgarta, shi kansa yayi mamakin yanda take qara ware masa kafa,gashi dama amatse yake, Dan haka yaci gaba da sha'anin sa, gaba daya dagashi har ita sun Manta cewa afalon Momy suke, qarasa tura hannunsa yayi har can ciki.... Yana shafa wa yana kallan yanda take numfashi, ga kuma hannunta data dora akan siket dinta
Yasake cewa "zaki barni nayi sosai yau?"

Ahankali tadaga masa kanta

Adede lokacin Momy ta kunno kanta falon zuciyarta daya 🙆🏻‍♀️
Karaf idonta yasauka akan su, babu wanda yasan da futowar ta gaba dayansu, cikin sauri tayi baya tana dafe kanta 🤦🏻‍♀️
Wannan jaraba ta Abba har ina 🤣

Daga Inda take takara wayarta a Kunnan tana wayar qarya sai daga murya take yanda zasu jiyo ta, alamun gatanan zuwa wajan 😃

Cikin sauri Abba yazare hannunsa yana waya gyara zaman sa, itama Nihla ta sauri tajuya takwanta rigingine akan hannunta, sabanin da datake kallan saman falon tabude kafa ana mata Operation 🤪

Momy ta qaraso falon, kwata kwata bata nuna musu wani alamun tagane komai ba, taga de Abban nata yanata matse kafafunsa, amma tsabar miskilanci haka yake danna waya Kamar gaske 🤣

Tace "Nihla, tabayar akawo saqon naki, kujira minti goma haka"

Ahankali tace "to Momy"

Momy tayi Murmushi tace "Abba na ba magana ne?"

Sumar kansa ya shafa yace "Momy magana nake dawani abokin aikina"

Murmushi tayi tace "to kajira ta Zan bata saqo saiku tafi"

Babu kunya kuwa yace "to Momy"

Ba'a dadeba kuwa wani mutum yakawo saqon, Momy tayi cikin dakinta da ledar tana kiran Nihla, ahankali tatashi tabi bayanta, Abba yabisu da kallo yana shafa sumar kansa, yakamata tayi tafuto su tafi

Suna zuwa daki kuwa Momy tabata maganin tace "gashinan, kullum kidinga sha safe da dare, kuma ki qara hakuri, aure yaqin mata, wataran sai labari"

Cikin nutsuwa tace "to Momy"

Futowa sukai daga dakin, daga nan sukai sallama da Momy suka tafi, saida taga fitarsu sannna tayi ajiyar zuciya, gara da Allah yasa yaran nan ba'a gidan nan suke zaune ba



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️



Suna komawa gida yashiga dakinsa, itama nata dakin tashige tazauna tabude maganin da Momy tabata tasha, tunda taji yace zaiyi tasan bazai fasa ba, kuma itama dama yanda takejin jikinta Babu abinda takeso a yanzun sai shi, qara daga maganin tayi ta qara sha, sannan ta boye, tashige wanka, tanada futowa daga wanka ta kwanta tashige cikin bargo harda lumshe ido Kamar me bacci

Shigowa yayi jikinsa sanye da kayan bacci, yace "bade harkin kwanta ba"

Ahankali tace "um na kwanta ya Abba, nagaji ne, kasan sha'anin suna"

Gadon yahawo shima yashige cikin blanket din yace "bamu gaisa bafa"

Tabude baki tace masa "daw..." dif yahade bakinsu waje daya, atare suka lumshe idonsu suna sakin wata irin ajiyar zuciya

Hannunsa yasa yatallafi kanta yana qara shan lips dinta, yasaka hannunsa ta cikin bargon yadorasu akan breast dinta yana matsawa

Wani irin numfashi tasaki, ta qwace bakinta tace" washhh... "

Kallanta yayi sannan yamaida bakinsa kansu yanasha

Ahankali ta dora hannunta akansa tana shafa masa lallausar sumar kansa, cikin wani irin murya tace" ya.. ya. Abba.. Pls cigaba "

Mamaki yakama Abba, anya kuwa yau yarinyar nan kalau take? Matar da kullum yazo batada aiki sai raki? Ahankali yaci gaba dasha har Tsawon wani lokaci, Dan bude idonta tayi ta kalleshi tace" ya Abbaaah... to'isa haka Dan Allah, sun fara min zafi "

Bai takura mataba ya cire bakinsa ahankali, yana sauke wani irin numfashi, daqyar yace" nima kimin kinji "

Daga masa kanta tayi, ahankali ta qara matsowa jikinsa sannan ta dora bakinta akan qirjinsa, lokaci daya Abba yasaki wani irin numfashi " ahhhh... Yawwa Nihla.... Kamar haka..., Nihla ina son ki"

Jin yana mata wannan sumbatun yasa ta dage tanasha, gaba daya ta haukatashi da salonta, cikin zafin nama yamaidata ya kwantar da ita sannan yafara nuna mata tsantsar soyaiyar dayake mata, ihu yafara yana fadin "dadi Nihla... wallahi bazan iya rabuwa dakeba, Nihla tahhh... Nihla ta ni kadai...., meyasa har.. har yanzu yake shiga daqyar, wayyo Allah na"

Nihla tana jinsa, ita kanta tanajin dadin abin sosai yanzu, saide zafin da takeji idan zai shiga, shima yau kadan kadan takeji, gaba daya Abba ya haukace mata da ihu saida ta rufe masa bakinsa

Tun tana jurewa harta dawo tagaji tafara masa magiya yayi hakuri, amma bai saurara mataba saida yaji shi daidai, sannan ya qanqameta har tana sakin yar qarama qara

Wani irin wahalallan numfashi yake saukewa, daqyar ya'iya daga hannunsa ya janyo ta jikinsa yace "kinada dadi sosai, kullum qara suger kike" bai jira amsar taba yasaka bakinsa yayi kissing nata bakin, sannan ya kalli kumatunta yaga hawaye kadan

Kanta ya shafa yace "akwai zafin har yanzu ko"

Girgiza kanta tayi

Rungumeta yayi ajikinsa yace "kinfara jin dadin kema?"

Tace "eh, amma akwai zafi kadan"

Bayanta ya bubbuga yace "zaki daina ji, aide yanzu Babu radadi Kamar da ko"

Tace "um"

Shiru yayi mata, yaqara matseta ajikinsa, sai shafa kanta yake



Dasafe ma haka yasake yi, amma kafin yayi saida taje tasha wannan maganin da Momy tabata, tanajin dadin maganin sosai, domin kuwa yauda safen bataji wani zafi ba, saima wani irin dadi da takeji, shiyasa yanzu tadena fargabar komai
Ganin tagaji yasa yatashi da kansa yahada musu abinci, sunaci yajata jikinsa yace "sakewa fa zanyi"

Tace "uhm.. Ya Abba wai baka gajiya ne"

"ni bawata gajiya inde zaki bani, tunda kinfara jin dadi kema bagara muyi ba"

Shiru tayi masa, hannunta yanakan qirjinsa tana shafa wa
Yace "gara nadage musamu Baby muma, kina ganin Fawaz ma matar sa tasamu ciki, jiya suka sakani agaba da tsokana wai bana miki horo yanda yakamata"

Cikin sauri tace "su ya Fawaz din?"

Yace "emana, kinga ai gara naqara himma wajan bawa fulawa ta ruwa, kusan wata uku da bikin mu har yanzu ko batan wata bakiyi bafa"

Murmushi tayi tace "to menene ya Abba, ai lokaci ne"

Yace "um um wannan lokacin kam toya kamata yazo, namatsu naga abinda zaki haifamin, inaso naga dana danaki"

Tace "Allah yakawo masu albarka"

"amin, dazu fa munyi waya da Yusuf yacemin ansaka ranar aurensa da Rafia'ah nanda wata daya"

Cikin murna tace "wayyo Allah, amma naji dadi, kace zamuje Abuja biki, kokuma lagos din zamuje, daga nanma naga Anty Nadiya?" ta qarasa maganar tana kallansa

Yace "duk ba daya, gobe zamu wuce saudia kuma gaskiya daga nanma Honeymoon zamu wuce, bama nan za'ayi bikin, shima Yusuf nafada masa, saide idan mun dawo sai mukai musu ziyara"

"Amma ya Abba Honeymoon harya wuce wata daya?"

"wasa kika dauka ko, shiyasa fa naqi koya miki Mota ma, saboda amarcin mu, nace sai nanda wata shida kafin nan kinsake murjewa, amarci ya ratsaki" ya qarasa maganar yana dora bakinsa akan kunnanta, nan da nan yafara sha, hannu tasa tarufe kunnanta, yadago da kansa ya kalleta yace "please kibari na tabbatar da mafarkina dana tabayi kwanaki"

Batasan wanne mafarki yake magana akaiba, haka tasa hannu ta rungumeshi, nan take yayi ajiyar zuciya



Saida yaqara yin yanda yaso da'ita, sannan suka samu suka huta, washe gari kuwa suka lula qasar saudia, saiga Nihla har wajan tuqin jirgi itada Abba, yana nuna mata abubuwan sosai, itace harda yimisu pictures



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️



Tsawon wata daya sukayi a qasar saudia, babu abinda Abba yake sai addu'ah akan Allah yabashi yaya nagari, sunsha addu'ah sosai, ba subar kowaba, zuwa yanzu kam Nihla tafara murjewa, hankalinta Akwance yake yanzu, tunda tafara sabawa da Abba dakuma yanayin yanda yake, saida sukai wata daya da sati biyu sannan suka dawo gida, ta qara cika sosai, komai nata yasake futowa saima abinda yaqaru Wanda ada bata dashi, kana ganinta zakasan hutu Yazauna, jikinta Kamar ka latsa jini yafuto, dasuka dawo gida ma Abba baya barin ta haka kawai, kullum yana buqatar matar sa, satin su daya dawowa suka tafi Abuja gidan Yusuf

Gidan mamy suka fara zuwa suka gaisa da Adala dakuma mamy, sannnan suka tafi gidan Yusuf din

Abba kam amota Yazauna Nihla tashiga ciki kanta tsaye, sai sallama take kwalawa

Rafi'ah tana daga cikin daki tafuto, tana ganin Nihla tafada jikinta cikin murna, anan falo suka zauna Nihla tace "ke tareda ya Abba fa nake, yana compound amota"

Rafi'ah tace "kuma akan ki fadamin dawuri, bari na fadawa ya Yusuf yana ciki ai"
Cikin dakin tashiga tafada masa, yafuto suka gaisa da Nihla sannan yafita yashigo da Abba cikin falon
Rafi'ah takawo musu abun motsa baki, suna firarsu cikin farin ciki, kai ba zakace wani abu yataba shiga tsakanin suba
Cikin daki Rafi'ah ta janye Nihla, ta dubeta tace "ke naga auren ya karbeki Nihla, sai wata uwar qiba ma dakika hada"

Tace "ke wacce qiba, yanzu nefa nadan ciko, da baki ganni ba wallahi, duk na rame"

Rafi'ah tace "um abin kam Babu sauqi gaskiya, ga ya Yusuf ba haquri, ke ni Tun ina kuka yanzu nadawo ma na haqura"

Nihla tace "sai hakuri kam Rafi'ah, Allah dai yabarmu tareda mazajanmu"

"amin Nihla, kinga wani turare da aka aikomin shi daga lagos, kiyi amfani dashi zakiji da dinsa"

Tureren Nihla ta karba tace "nagode Rafi'ah"

Anan gidan suka wuni, sannan suka koma gidan mamy sukayi wa su baba sallama suka tafi gida

Basuzo gidaba kuwa sai wajan magrib
Gajiya tataru tayiwa Nihla yawa, nan take zazzafan zazzabi Yarufe ta, Abba yadawo daga masallaci da daddare yana zuwa dakinta yaganta cikin bargo, yana yayeta yaga tana rawar sanyi
Cikin sauri yace "subhanallah, menene yake damunki?" yafadi haka yana janyo ta jikinsa


Idanunta ne suka fara lumshe wa tazube ajikinsa, jikinta yafara tabawa yace "zazzabi ne ai yakama ki, kode mutafi asbiti"

Girgiza kanta tayi, tabude baki zatai magana wani irin akai yataho mata, cikin sauri tatashi tayi cikin toilet tafara kwara amai
Shima toilet din yabita yariqe ta yanayi mata sannu, tana Dagowa tazube ajikinsa, yasaka hannu yadauko ta, ya kwantar da ita yanayi mata sannu
Duk yanda yaso sutafi asbiti qin yarda tayi, yarasa menene tsakaninta da asbiti
Haka ya haqura suka kwanta tana jikinta, amma basu runtsa ba, kwana tayi tana amai
Da sassafe kuwa yasaka mata kayanta, suka tafi asbiti, sai kuka take masa ita batason allura
Suna zuwa kuwa aka daura mata qarin ruwa, sannan akayi mata text na jini dana fitsari, ba'a dade da saka mata ruwanba bacci ya dauketa
Doc. Yazo har dakin yabawa Abba sakamakon txt din, cikin sauri ya kalli fuskar Doc. Yace "Doc. Mafarki nake kokuma gaskiya ne? Kafadamin gaskiya da gaske Nihla tanada ciki?"

Doc. Yace "congratulation" sannan yafice daga dakin cikin murmushi

Jikin Abba har rawa yake yakira Momy da Daddy, dasu ya Usman yafada musu
Ruwan yana qarewa kuwa suka Taho gida, kai tsaye taga yayi hanyar gida da'ita, ahankali ta kalleshi tace "ya Abba gida zamuje?"

Cikin murna yace "gida Zan kai ki wajan Momy, daga nan nakoma nadauko mana kayanmu"

Kallansa tayi tace "meyasa zamuje?"

Cikin murna ya kalleta yace "kefa yanzu bake kadai bace, nakusa zama Daddy Abba, dan haka wajan Momy Zan maida ke mudinga baki kulawa harki warware"

Murmushi tayi, batace masa komai ba
Yace "kinyi shiru"

Cikin shagwaba tace "ya Abba ancefa haihuwa da wahala"

"waye yafada miki? to wasa suke miki"

Tace "Allah da gaske ya Abba?"

Yace "baki yarda ba ko?"

Murmushi tayi tace "um um"

Babu Wanda yasake magana har suka qaraso gidan cikin part din Momy, Momy na zaune afalo ta gansu sun shigo, tace "ashe baqi ne dani yau, sannu Nihla, zonan ki zauna"

Nihla ta kalli Abba, yasakar mata wani irin murmushi yana kashe mata ido daya, karde ya Abba harya fadawa Momy komai, tunanin tane ya katse lokacin da Momy take cewa "Allah yaraba lafiya, zoki zauna kinji" 🤣

Zama tayi, shikuma Abba ya kalli Momy yace "Momy, zanje nadebo mana kayanmu, mun dawo gida kenan saita gama warware wa zamu koma"

Momy ta kalleshi taga sai wani murna yake yana jin dadi, Wato za'azo abaje mata kolin rashin kunya agida, tatuna ranar da sukazo da daddare da abinda tagani, tace "kayan ta, kokuma kayanku?" 🤔









Comments
Share



















Amnah El Yaqoub ✍🏻❣️DANGI 'DAYA❣️
{Romance&Friendship luv}


Writing by Amnah El Yaqoub

Like my page On facebook 👇
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493


Nasadaukar da wannan shafi ga dukkanin masu karanta wannan labari, i luv u All 💋💋💋


65&66




Zuciyarsa daya yace "Momy kayanmu"

Momy tace "a a, kayan ta zakaje ka dauko mata, idan ta murmure cikin ta yatasa saita dawo, amma yazakubar gida Babu kowa duk kudawo nan"

Cikin sauri ya kalli Momy yace "a a Momy, to tatashi mutafi, dama fa abinda yasa na kawo ta nan din, saboda idan nafita karta rasa Wanda zai dinga bata kulawa, shiyasa na kawo miki ita, idan nafita gaki nan, idan nadawo kuma shikkenan"

Momy tace "bari kaji Babu Inda zataje, ai yanda tazo totazo kenan"

Shima yace "a a Momy, kiyi hakuri kawai, gara mutafi, to haka Zan zauna Acan din ni kadai"

Nihla tayi Murmushi ganin yanda suke yi shida Momy tace "Momy kibarshi yadauko mana kayan namu, can dinfa Babu kowa, Momy kibarshi yadawo nan shima"

Momy tayi saqare tana kallan ikon Allah, tace "to ai shikkenan tunda mijinki kikeso"

Nihla tayi Murmushi tatashi tabar wajan, shima fita yayi da sauri saboda kar Momy ta sauya shawara

Momy tayi Murmushi ganin kan yaran nata yanzu yahadu, dama kuma abinda take fata kenan, yanzu kuma fatansu Allah ya sauki Nihla lafiya


Da daddare suna kitchen itada Momy, suna gudanar da Abincin dare, zuciyarta tafara tashi, cikin sauri tafuto daga kitchen din  tana rufe bakinta datake shirin yin amai, dashi taci karo zai shigo kitchen din shima

Momy tabiyota da sauri tanayi mata sannu, Abba kuwa riqeta yayi yana cewa "ko aman ne?"

Kafin ma tabashi amsa tafara yin aman, duk ta bata masa kayansa da wajan

Momy tace "subhanallah, wai haka takeyi dama"

Cikin damuwa yace "Momy to ai yau da sauqi ma naga Tunda mukazo batayi ba"

Tace "kuje daki ta gyara kayan ta, bari agyara nan din"

Kafadunta yariqe yana mata sannu suka wuce dakinta
Kai tsaye suna zuwa yafara cire mata kayan ta, shima ya cire nasa kayan suka shige toilet
Wanka yafara yimata, sai kawar dakai saboda wannan shine karo na farko dasuka tabayin wanka shida ita atare, shikuwa Babu ruwansa shawa ma yasakar musu yariqe ta ajikinsa hannunsa kuwa yawo yake a jikinta yana goga mata sabulu, Tun suna wankan cikin hayyaci har suka fara Manta Inda suke, aka wuce Romance acikin Ruwa

Bai san lokacin da yasaki sabulun ba yacafki bakinta yanasha, daqyar suka gama wankan, suka futo, amma kana ganinsa kasan akusa yake, domin kuwa kalar Idanunsa ma kadai ta isa shaida

Haka de yake kokarin sharewa, har suka shirya suka dawo falon, Daddy yadawo gidan ya gansu yace "a a, kukuma yau kuntuna da kenan"

Murmushi sukai baki dayansu

Yace "Abba ai yakirani awaya dazu, Allah ya sauke ta lafiya"

Abba da Momy sukace "Amin"

Wajan dining Daddy yawuce, Momy ma tabi bayansa, Abba yamatso kusa da Nihla har jikinsa na gogar nata, yayi qasa da murya yace "ai yau adakina zamu kwana ko"

Cikin sauri ta kalleshi tace "wanne irin dakinka ya Abba, ka Manta agida muke ne"

Momy tana daga nesa take hango su, taga sai kallan fuskar Nihla yake yana magana qasa qasa, amma batasan me suke fadaba

Abba yace "to menene Dan muna gida, bafa haramun bane"

Tace "duk da haka, su Momy zasu iya tunanin wani abu muke"

Yace "to idan suka sani dinma ba dadi zasuji ba, bakiga yanda kowa yake murna kinsamu ciki ba?"

Tace "nide gaskiya kunya nakeji ya Abba"

"wai kunyar me, ko bakyajin dadinne?"

Shagwaba tafara masa tace "tokuma ya Abba Dan inajin dadi saimuyi agabansu Momy"

Kansa yadafe da hannunsa 🤦🏻‍♂️"to yanzu ke saboda kunya saimuqi yin abinmu, ai sunsan da hakan shiyasa suka mana aure ko, kinga Dan Allah tashi Muje kici abinci, babu komai acikin ki"

Haka tatashi ta nufi wajansu Momy amma bawai Dan ta yarda da maganar tasaba



Bayan sun gama cin Abincin falo suka dawo dukansu, yau harda Daddy azaman

Daddy yajuyo ya kalli Abba yace "Abubakar wata nawane cikin nata ne"

"wata daya ne Daddy, haka de nagani ajikin takardar txt din nata"

Daddy yayi Murmushi yace "to Alhamdulillah, Allah ya sauke ta lafiya"

Daga nan yatashi yawuce daki, itama Nihla Miqewa tayi ta kalli Momy tace "Momy saida safe"

"to Nihla saida safe"

Abba yazuba mata ido yana kallan dakin da zata shiga, kawai sai yaga tashiga nata dakin
Kallan sukaci gaba dayi shida Momy itama tagaji tayi masa sallama tatafi

Hamdala yayi daya ga tafiyar Momy, dama jira yake tatashi yabi bayan matar sa

Kayan kallon ya kashe, kai tsaye yatafi dakin Nihla, wutar dakin nata akunne, ya kashe, sannan ya cire kayansa shima ya kwanta

Cikin baccinta taji ana shafa ta, ahankali tafara bude idonta harta budeshi gaba daya, sai ganin Abba tayi yana kokarin dage mata riga

Kallanta yayi yace "kin tashi?"

Tace "ya Abba nide Dan Allah katashi kafita"

Rigar yagama dagewa sannan yatura hannunsa ciki yana wasa da Kirjinta cikin salon da yasan tanaso, ahankali yace "kibari mana to ko sau dayane muyi, kinji"

Babu yanda ta'iya haka tabarshi, saida tafiya tayi nisa yafara yimata ihu, yana kiran sunanta, sai sambatu yakeyi, tasan cewa su Momy ma sunji shi, dama kuma shine abinda take gudu

Hannu tasa tarufe masa bakinsa, amma saiya qwace yaci gaba da wasu irin maganganun da bai kamata ajisu ba, cikin dabara tahade bakinsu waje daya, to anan ne tasamu lafiya yayi shiru



❣️❣️❣️    ❣️❣️❣️


Washe gari kuwa haka yake ta al'amuransa ko ajikinsa, itace ma Dafarko take ta takure kanta, amma da taga Babu Wanda ya lura da itama kawai saita share, ta warware taci gaba da abun gabanta
Haka Rayuwar su take tafiya cikin kwanciyar hankali har cikin ta yacika wata hudu, a lokacin Dida haihuwa yau ko gobe, kowa yaga Dida saiya tausaya mata, saboda cikin yana bata wahala sosai idan tazauna bata iya tashi, awajan take wuni, saboda girma da kuma nauyin cikin nata

Nihla kuwa fitinar Abba ce tasa suka tattara kayansu suka koma gidansu, a lokacin cikin yadena bata wahala, saide kwadayi datake yi kawai
Shima idan akwai agidan zata tashi tayi abinta, idan Babu kuma zatayi wa Momy waya akawo mata

Yau Tun asuba Dida tatashi da naquda, Fawaz yarasa yaya zaiyi gashi gari anata kiran sallah, haka yakira mamansa awaya yafada mata, tace gatanan zuwa
Kafin ma ta qarasa gidan kan Baby yafuto, Dan haka tana zuwa tace Fawaz yabasu waje, haka yafuto yana jin ihun Dida, Tun yana daure wa harya kasa hakura yashiga dakin, ummah tanata mata sannu, shigarsa dakin kenan Allah ya sauke ta lafiya

Ummah ta kalli Fawaz tace "Alhamdulillah Allah ya sauke ta lafiya"

Fawaz yayi mutuwar tsaye ganin irin wahalar da Dida tasha, sosai yaji tausayin yarinyar, tasha wahala a rayuwa kuma tayi hakuri sosai, idanunta sunyi jaga jaga da hawaye, cikin sauri yayi wajanta yanayi mata sannu

Da qyar ta kalleshi tace "ya Fawaz, ka yafemin, jinake Kamar Zan mutu"

Umma data gama yankewa Baby cibiya tace "karna sakeji kin fadi wannan maganar Dida, kiyi hakuri keda Allah yasa bakiyi doguwar naquda ba" ta goge wa Babyn jinkinsa tamiqawa Fawaz tace "ungo riqe Babyn Fawaz, kayiwa Allah godia ansamu namiji"

Hannunsa har karkarwa yaje yariqe babyn yana kallansa, Dida tariqe hannunsa tace "ya Fawaz, kabawa Diyana shi ta kula min da yarona, wallahi ciwo nakeji Kamar na mutu"

Jikin umma yayi sanyi, tace "Dida haihuwar kenan, bazaki mutu kibarmu ba kinji, da kanki zaki kula da yaronki"

Cikin ciwo Dida tace "wayyo... Allah na ummah Zan mut...kafin ta qarasa wani gagarumin ciwon yakamata, Umma tataba cikinta tadubi Fawaz tace" tashi kuje falo kayi mata addu'ah, wata haihuwar ce "

Zaro ido Fawaz yayi 😳yace" ummah wai saita kuma shan wata wahalar? "

" banason shirme Fawaz, da abanza ake samun yaran? Tashi nace "🤣

Haka yafuto da yaron a hannunsa sai waiwayen Dida yake

Tun tana naquda cikin duhun gari, har aka idar da sallar asuba gari yayi haske, Umma tafara tunanin su tafi asbiti, domin kuwa qarfinta yaqare, haka lokaci daya tana qwaqqwaran nishi, wani Babyn yafuto

Sai a lokacin Dida tasamu damar yin wani bacci Mai nauyi, Umma ta gyara yaron sai kuka yake, sannan ta gyara Dida, Fawaz yana jin kukan Baby yamiqe yashigo dakin, hannunsa dauke da babyn, yaro yanata shan baccin sa 🤣🤣

Umma ta kalleshi cikin murmushi tace "to Alhamdulillah, tasauka lafiya, shima wannan din kaga namiji ne"

Hawaye yazubowa Fawaz, yasa hannu yadauki dayan yaron yazuba musu ido yana kallansu, yace "umma yanzu duk nawane?"

Tace "gashi kuwa Fawaz, Allah yaraya muku yaranku"

Tasa hannu ta karbi yaran tayi musu wanka ta gyara su tsaf, sannan ta kwantar dasu agefen Dida, itama ta zauna ranta fari tas
shikuwa Fawaz wajan Dida ya koma Babu kunya yasa hannu yana shafa kan matar sa 🤣

Babu Wanda ya tasheta acikinsu saida tasha baccinta sannan tatashi, tana tashi kuwa Fawaz yabata yaran yace "ga Baby's dinmu Dida, kinyi kokari sosai Allah yayi miki albarka"

Cikin farin-ciki tasa hannu ta karbi yaran tana kallansu, wata irin soyaiyar su tana qaruwa acikin ranta, Umma kuwa tashi tayi tsaye tace "to Dida kihuta sai Muje asbiti adubaki, bari naje nakira yan gida afada musu"

Daga nan tafice daga dakin domin ta basu damar sakewa, tana fita kuwa Fawaz ya rungumeta ajikinsa, sai kissing dinta yake, cikin shagwaba tace "ya Fawaz haihuwa akwai wahala"

Yace "ai mundena daga yau, wannan wahala haka har kina cewa abawa Diyana yara" 🤣

Murmushi tayi takai masa dukan wasa a qirjinsa

Yace "nagode sosai Dida, haqiqa ke alkhaairi ce acikin Rayuwar Fawaz, kin dawo dani hanya madaidaiciya, kinyi hakurin zama dani a lokacin dakowa yake fadar mugun halina, babu abinda Zan saka miki dashi Dida sai godia, Allah yabarmin ke amatsayin mata ta ke kadai aduniya dakuma lahira, Allah ya rayamana, Aslam da Adam "🤣

Dida tayi Murmushi tace"amin ya Fawaz, Wato harka huduba ko"

Yace "yes, Adam bai qyamaceni ba shida Diyana, basu qi halaiyata tadaba suka sakawa dansu sunana, kinga nima tunda Allah yabani ai sai nasaka sunansa, shikuma Aslam saboda zumunci nasaka, da sunan Abba zansa, but kinga already Aslam ya rigani"

Tace "hakane, to Allah yarayasu yasa suyi halin masu sunansu"

Yace "amin Dida ta"


Sunje asbiti andubata anbata magunguna, sannan an rubutawa yara madarar dazasu dinga sha saboda itama tadan huta wani lokacin

Kafin azahar kuwa gidan Dida yacika taf da jama'ar Mazawaje family

Ranar suna kuwa yara sukaci sunan Adam da Aslam, Babban shine Aslam, qaramin kuma Adam, wannnna karon ma hajiya Na'ila mamansu Aslam itace kan gaba akan komai, saboda anyiwa yayanta duka biyun takwara, gaba daya tahana iyayen Dida da Fawaz komai itace takeyiwa yarinyar abubuwan daya dace

Yaran kuwa basa zama ahannun Dida, kowa daukar su yake, da Dida da Diyana da Ilham da Nihla duk suna zaune awaje daya
Aka umman Fawaz takawo wa Dida yaran tana basu nono suna sha, sai runtse ido take

Nihla tace "tab wannan azaba har 'ina, sannu Dida"

Ilham tayi dariya tace "idan tasaba ai shikkenan, yanzu de saura ke, zamu ga me zaki haifa, Dan Allah ki haifo wa Abba na matar aure"

Diyana tace "a a wallahi, Fawaz dina yarigashi, haka kawai wani Abban ki, yaro yana tafe shiru shiru kana ganinsa kaga halin takwaransa" 🤣

Dariya sukasa Ilham tace "wallahi kuwa kamar kinsani, har mamaki nake, shegen son girma ne da lil Abba, haka kawai zaiyi wa ya Aslam shiru idan yana masa magana, shida kansa ya Aslam rannan haka yace yaga alama lil Abba de yadauko halin ya Abba"

Dida tace "to aiga yan biyu sunzo, saisu raba muku gardama, tana haihuwa sun samu matar aure" 🤣

Nihla tace "oh, Tun kafin na haihun har akewa yara kamu? 🤔
Abinda cikin watansa biyar bamusan mezan haifa ba?"

Diyana tace "insha Allah ma matar lil Fawaz zaki haifa" 🤣

Haka sukaita firarsu abin sha'awa, har dare yayi sannan kowa mijinta yazo yadauketa


Nihla suna hanya ya Abba yadubeta yace "dazu mudasu Aslam muke cewa kema yakamata ki haifi namiji, tunda duka jikokin Abubakar Mazawaje maza suke haifa, abin Kamar alamara kowa namiji namiji, shi Fawaz ma daya fimu aiki yasamu biyu" 🤣

Nihla tayi Murmushi tace "kuma ashe kunyi zancen, mumafa adaki haka suka sani agaba wai kowa sai cewa yake idan na haifi mace to wallahi dansa na haifawa mata" 🤣

Ya Abba yayi Murmushi yace "sunada gaskiya, amma ni idan namiji kika haifa ma sunan Yusuf Zan saka"

Tace "to Allah yakawo nagari"


Haka suka qarasa gida suna firarsu cikeda kulawa

Cikin Nihla yana cika wata tara Momy tace akawo mata ita gabanta, haka suka sake dawowa gidan Momy
Saida tayi kusan sati biyu agida, sannan Allah yakawo tata haihuwar, tana fara naquda kuwa Momy da Abba suka tafi asbiti da'ita, dakuma kayan Baby, amma da sukaje sai likitocin sukace haihuwa tukunna

Gaba daya Nihla ta jigata, ya Abba sai sintiri yake Yaqi zama, suda sukazo da azahar har wajan magrib tana abu daya, lokaci daya kuma suka fara jiyo kukan ta, Abba yatashi tsaye yanufi dakin haihuwar, Momy tayi sauri ta riqe shi, "ina zakaje haka Abba?"

Idanunsa suka cika da qwallah yace "Momy tanasha wahala wallahi... Sai sharrrr hawaye yazubo masa 🤣

Momy tace" toya zamuyi Abba, kayi mata addu'ah kajiko "

Suna tsaye shida Momy wata nurse tafuto hannunta dauke da Baby ta miqa musu tace" Hajiya tasauka lafiya, ansamu Baby girl "

Cikin sauri Momy ta karbi yarinyar tana murna, shikuwa Abba nurse din yanufa yace
" zamu iya ganin mamanta yanzu? "

Tace" kuyi hakuri tana dakin hutu, zaku iya ganinta anjima "

Dawowa yayi wajan Momy ya zubawa yarinyar ido, fara ce sol Mai mutuqar kama da Nihla, gata bulbul masha Allah, idonta abude sai kallansu take, sumar kanta yala yala da gashi

Momy tace" Alhamdulillah, yau su Abba anyi 'ya, karbe ta mana kayi mata addu'ah "🤣

Ahankali yamiqa hannunsa ya karbe ta yace

"Welcom to the world DIDDI nah "

Momy tace "kayi tunani Mai kyau Abba na, amma yanzu de share hawayen naka" 🤣

Murmushi yayi yasa hannu ya goge idonsa, saida suka dauki lokaci sannan aka basu damar ganinta, tana zaune akan gadon ya Abba yadora mata yarinyar acinyarta, Nihla ta kalli yarinyar taji lokaci daya wata irin qaunar yarinyar aranta, ashe haka iyaye sukeji akan yayan su, nan take tafara yiwa Allah godia

Sai dare aka sallamesu, kai tsaye kuwa gidan Momy suka koma
Yan'uwa suka cika part din Momy, Ilham kuwa da Diyana da Dida dasuka zo dauke yarinyar sukai kowa yazo saiya fadi albarkacin bakinsa akanta

Ilham tace "wallahi jinake Kamar na dauketa gaba daya"

Diyana tace "kekoni, Kamar yar larabawa yarinyar wallahi" 🤣

Dida tace "a a ni zaku barwa yan biyu na sun samu qanwa" 🤣

Saida sukai kai dare awajan ta sannan suka tafi gida, Momy tana ganin take taken Abba takafa ta tsare iya karsa da Nihla saide in falo tafuto 🤣

Yauda safe ya shirya zai fita wajan Aslam, yashigo dakin nata yaganta tana bawa Baby nono, zama yayi kusa da ita yasaka hannunsa ya riqo waist dinta, yana kallan yanda take yatsina fuska
Yace "Sannu"

Hararar wasa tayi masa tace "duk bakai neba, kuma itama gashinan zata qarasa ni"

Yace "sorry, mun tuba"

Yasaka hannunsa yana shafa qirjinta Wanda take bawa yarinyar, sannan yafuto da dayan waje, yasaka harshansa yana lasa, Nihla bata hanashi ba, tabarshi Tun yana lasa yadawo yanasha ahankali, yanda yake sha ne ahankali yasa ta lumshe idonta, cikin muryar jin dadi tace "ya Abbaaaa... Saika shanye mata abinta ko..."

Shiru yayi yana tsotsa harda lumshe idonsa shima

Adede lokacin Momy tashigo dakin,qaran bude kofar dayaji ne yasa cikin sauri ya cire bakinsa 🙊

Yasunkuyar da kansa qasa yana sosa qeyarsa
Momy tace "Sannu Abba, sannu kaji" 🤣

Tashi yayi Cikeda borin kunya zai bar dakin, Momy tasake cewa "Allah yakiyaye hanya, mujima da yawa"
Shide yayi wuf yafice daga dakin

Tadawo da Kallanta wajan Nihla tace "idan kika biyewa jarabar Abba ko shekara ba zakiyi ba zaki sake daukan wani cikin, kinde ji abinda akeji awajan haihuwar"



Nihla tayi shiru kanta aqasa, ga wata kunya data rufeta, shima kansa gogan yaji kunya bare ita

Ranar suna yarinya taci sunan Aysha, amma Suna kiranta da Diddi
A family house din akai taron sunan, gidan yacika sosai, kowa sai daukan yarinyar yake, Muddin ka dauketa sai kaji tashiga ranka, Mamy batazo ba amma taturo Rafi'ah wajan sunan da kayaiyakin barka, saikuma baba dayazo ganin jikarsa da kansa, kuma Sabuwar matar sa

 Rafi'ah ma tana dauke da nata cikin na wata shida, amma haka ta daure tazo tunda mamy bazata samu damar zuwan ba

Tunda aka gama taron suna Momy tafara gyara Nihla, ciki da waje datage tana gyara yarta

Saida sukai Arba'in sannan sukai shirin tafiya gidansu

Tun safe kuwa Abba yagama shirya wa su kawai yake jira, Momy ta kalleshi ta girgiza kanta tasan cewa yau sai Nihla ta yabawa aya zaqin ta 🤣

Saida suka futo, zasu tafi Momy tace "to kokun Manta da Little Diddi ne?"

Gaba dayansu sai kunya ta kama su, Abba yakalli Nihla yafara borin kunya, yace "Dama baki goyata ba kika futo?"

Nihla tayi masa wani irin kallo tace "ba kaine kake ta cewa nayi sauri ba"

Ta kalli Momy tace "Momy ina take?"

Momy tayi Murmushi tace "tana wajan Yayan ta"

Abba ya kalli Nihla yace "to kinji tana wajan Daddy kije kiyi sauri ki karbota mutafi"

Momy ta girgiza kanta tana murmushi, sai sauri yake Kamar Wanda zasu je wata qasa akace jirgi zai tafi Babu su 🤣

Daddy yafuto daga dakinsa hannunsa dauke da yarinyar yace "hajiya wannan qanwar tawa tacika kuka"

Momy tace "haka take Alhaji, da rana tasha baccinta da daddare kuma mu ta hanamu sakat"

Daddy ya kalli idon yarinyar yace "toki daina, danni ba haka Aisha na take ba"

Gaba dayansu sukai dariya, Nihla ta karbeta, su kayiwa su Momy sallama suka tafi gidansu


Awannan dare Nihla tasha baqar wahala awajan  ya Abba, domin kuwa Tun ana abu na marmari saida ya Abba yasa tafara kuka, sannan ya'iya hakura, amma badon yasoba



BAYAN SHEKARA TAKWAS

Zaune suke afalo suna yin game atv, gaba dayansu hankalin su yanakan game din, Acan gefe kuwa wani Yaro ne yana zaune yana kallan abinda sauran yaran suke

Little Diddi na gefensu tana wasa da teddy ahannun ta

Remote din lil Fawaz yayar aqasa yace "natafi wajan mata ta" 🤣

Yayi wajan Little Diddi

Yanbiyu ma dasuka ga haka sukai wajansa da gudu kowa yana cewa matar sa ce

Lil Adam yaron Dida yace "ai gidanmu zaki dawo ma ko?"

Tajuya ta kalleshi kafin tayi magana lil Fawaz yaron Diyana yace "a a gidanmu zata koma"

Shima tajuya ta kalleshi, duk sai kallansu take tarasa wazata yiwa magana duk sun sata agaba

Wancan na zaune agefe shi kadai shine yataso yazo wajan su yace "duk ba Inda zataje, gidanmu zata tafi" 🤣
Ya kalleta yace "ke Little Diddi gidanmu zaki tafi gaba daya, kuma nine Zan aureki, kinga nine takwaran Daddynki" 🤣




Abba da Nihla dake zaune akujera suna kallan yaran sukai murmushi, hijabi ne a jikinta ya Abba yatura hannunsa cikin hijabin ya shafa qirjinta

Kallansa tayi tace "ya Abba kayi ahankali fa ga yara nan"

Murmushi yayi yace "bakiji abinda suke fada bane? Kitashi Muje daga ciki anema musu wata Ayshan shikkenan kin raba fada" 🤣

Tace "um um,  sutafi Abuja wajan ya Yusuf yabasu Mai sunan Mamy"

Yace "a a, gara de kema ki haifo musu wata yar budurwar Karki hadasu fada" 🤣

Hannunsa ta cire daga kan qirjinta cikin shagwaba tace

 "ya Abba Allah zakasa yaran nan sugane fa"

Murmushi yayi yace "to Muje nakoya miki wani abu" 🤣

Murmushi tayi ta rungume mijinta, shima yasaki daria cikeda farin-ciki



Tammat Bi Hamdullah



Anan na kawo qarshan wannan labari Mai taken DANGI DAYA


Gaskiya tunda nake rubuta labari bantaba shan wahala ba Kamar yanda nasha acikin wannan littafin, saboda soyaiya ce data rabu gida gida kuma kowanne gida da irin nasa salon,dakuma irin nasa soyaiyar, babu wanda yaci karo da irin soyaiyar wani

Haka kuma duk cikin books dina Babu Wanda nasamu qarancin Comments Kamar sa, bantaba rubuta littafi nace Zan ajiye shiba sai akan DANGI DAYA saboda qarancin Comments
But Babu damuwa kowanne labari da irin nasa farin jinin

Amma abin mamaki shine bantaba tunanin inada masoya ba sai akan novel din DANGI DAYA ta yanda ina bude page a facebook masoyana suke ta ruruwar Like din page dina, Alhamdulillah mun fara labarin DANGI DAYA da mutum dari da hamsin mungama shi da mutum dubu biyu dawani abu, gaskiya naji dadi Babu abinda zance da masoyana sai godia,domin kuwa nagane ni akeso ba novel dina ba.

Dangane da al'amarin rayuwa nayau da kullum shima mun tabo matsalolin da ake fama dasu Awannan yanayin kuma mun fadi maganin su, misali magungunan da aka fada acikin labarin

Idan kuma labarin Rayuwar ki yayi daidai da irinna wannan ma'auratan, to ina fatan zaki samu solution acikin littafin DANGI DAYA.

Idan akwai wanda na batawa Sanadin wannan labari, yayi hakuri yayafemin, nikam na yafewa kowa,daga qarshe ina fatan duk masoyan Amnah El Yaqoub su kasance DANGI DAYA 🙏🏻








Amina Muhammad El Yaqoub jigawa state ✍🏻