DARAJAR 'YA'YANA1-01
Posted by ANaM Dorayi on 11:41 PM, 08-Mar-16
Under: DARAJAR 'YA'YANA
___________________NA
___________HALIMA K/MASHI
Cikin sauri sadiya take yin komai dan bata son
mai gidanta ya dawo ya sameta ba yanda idonsa
yake bukata ba.Tuwon (semo) tayi mashi miyar
kubewa danya, sai farfesun kafar sa, sanan ta
tanadifura da nono, tasa a cikin fridge don tana
bukatar yayi sanyi.Ta share ko ina na gidan fes ta
wada tashi da kamshi turare, taje ta fesa wanka
sanan ta bata lokaci a gun kwalliya.Kankwasa
kofar da taji ne ta tuna da 'yan yaranta, da sauri
taje ta bude musu, kai tsaye ban daki tace su
nufa.Wanka ta sake yi musu sanan ta shirya su
cikin sababin kayansu masu kyau ta feshesu da
turaruka.Ta dawo dakinta inda ta rasa wane
kayane ma zata saka, a karshe ta yanke shawarar
saka wani jan material riga da siket.Ta dubi
kitsonta kanana da ta yarfa a madubi, sanan ta
kashe daurin dan kwali. Tasan yau zata burge
mijinta, musanaman da ta kalli lallen hannunta
na fulawa da aka zana mata.Ta kalli agogo karfe
shida da kwata, wayarta wadda ta dauke saboda
rashin chaji, ta jonata chaji.Ashe garin sauri bata
sa dai dai ba, don haka bata samu chajin ba har
aka dauke wuta.
banda haka da taji yanzu mijinta yana dai dai
ina?Kwnkwasa kofar ne ya dawo da ita daga
haushin rashin cajin da wayarta bata da shi, ita
da yaranta suka diba da gudu don taryo
mijinta.Tana bude kofar shine tsaye, sanye cikin
kayan yansanda, daga ka ganshi kasan babban
jami'ine, ta fada jikinshi tare da rumgume shi,
amma me?Sai taga ya sabule tare da cewa sannu
da gida.Cikin mamaki ta amshi ledar hannunsa
tare da jakarshi, ya tsugunna yana sha kan yayan
sa cikin jin dadi da kewa, sadiya ta tsaya cike da
mamakin saboda al'amari da take gani a gurin
me gidan nata.Abin da tasani a duk lokacin da ya
dawo yakan iso ne a marmatse cike da kewarta,
da ya shigo burinsa kawai ya rungumeta tsam a
jikinsa kafin yaran, amma yau sai taga ita ce ta
rumgume shi har yana sabulewa, lallai wanan
sabon al'amarine a gurinta.To ko dai gajiya ce
take damunsa?Kokuma fushi yayi ya gaji da
kiranta bai samu ba?Ta dubi kanta, kokuma
kwaliyarta ce batayi ba?Ta sake wai wayawa ta
kale su inda yake rungumarsu daya bayan
daya.Da kausar ya soma, sanan Al'amen, sai
mama ta tuno yanda yake mata a duk juma'ar
da yazo, ya kamata ya fi dokinta a wanan karon
da ya hada saty biyu bai zoba.Abin duk ya
dameta, tana tsoron kada wata masifa ko annoba
ta ratso cikin kyakkawan zaman nasu, tana tuna
da yadda take makale a gefen damansa sannan
ya dauki mama da hannun hagunsa har cikin
falonsu.Yanxu dai ba zatace ganin yara bane,
domintasan yaransu sun taso sun samesu cikin
wata rayuwa da suka shinfida ta shakuwa da
kaunar juna.Sun saba ganinsu rungume da juna,
sun saba ita da yaran suyi ta kokuwa a jikinshi,
basa yin wani abu da zai kawo matsala ga
tarbiyar yaransu, amma sukan rungumi junako
yin falo da junan ana hira.Sun rigata shiga falo,
ta shigo nan ma ta sake kallonshi, mamaki ganin
ya zauna shi da ke zarcewa dakinsa, can suke
zuwa ya basu tsarabarsu.
Sanan ya basu ta iya ya ce su kai mata, sanan
kada kudawo in na huta zanzo in gaidata, sai mu
dawo tare.Su ce to Abba, su tafi suna
tsallensu.Shi kuwa suna fita wata ran ko wanka
baya yi zai rungumota ya ce Dear my choice a
matse nake.Ya wancin lokacin sai ya samu
natsuwa kafin ya ci abincin ba yan yayi
wanka.Dan Aliyu mutum ne mai matsanan ciyar
bukata.Cikin damuwa ta isa kusa dashi.Yaya Ali
yau kagaji sosai ko?Ya dubeta me kika gani?Ta
ce, baka saba zama cikin falo ba.Ya miko hannu
bani ledar nan in sallami yaran nan.Ya fada ba
tare da ya bata waccen amsar ba.Ta miko masa
kanta daure ta nufi dakinsa da jakarsa, ya ba
yaran tsarabarsu, kayan ciye ciye ne da na wasa,
sanan ya mike ya nufi dakin sa.Kausar tace, abba
yau ina tsarabar iya?Sadiya daga cikin dakinta ta
kaso kunne taji amsar da zai ba da.Ba tare da ya
waiwayo ya dubi kausar ba, yace kinga magariba
ta kusa, bari in anyi sallah sai muje ko?Ya shiga
daidai lokacin ta shiga ban daki dan hada masa
ruwan wanka.Ta fito yana zaune bakin gado yana
kwance igiyar takalminsa ta iso gurin.Da sauri ta
tsugunna tare da cewa abba kausar yau kuma
harda aikina zaka shigar min?Ta ci gaba da
kwance takalmi tana cewa, yau duk na ganka
wani iri daban, ko duk gajiyar ce?Ya ce gajiya
saikace ba jami'in tsaro ba?Ta soma balle masa
maballen riga, to baka jin dadin jikinka ne ko?
Yaja tsaki, dan Allah ki bar ni da tambayoyinnan
naki please, gabanta ya fadi, ta dubeshi da gaske
yake yi fuskarshi daure.Jikinta yayi sanyi, ta gama
balle botiran, ya mike ya nufi ban daki ta mike
zata taimaka mashi kamar yadda ta saba, ya
shiga sai ya banko kofar zata tura sai taji karar
makulli yana kulle kofar.Cike da tsoro taje dakin
tana kallon kanta a madubi, ko dai batayi kyau ba
ne yau?Ta duba ba wata makusa, ta kara jan
baki da turare sanan ta fito ta same shi yana
shafa mai,ta isa gurinshi, ta ciro masa kaftani da
wando na shadda mai ruwan sararin samaniya,
ta ciro hular da zata dace da kayan ta ajeye
masa, amma sai taga ya janyo jallabiya mai
dogon hannu fara sol ya saka.Daga nan sai ta
koma ta jingina da bango dan jiran ganin
sarautar Allah.Ya fita, ta bishi ganin zai fita waje
ta ce, tabban kausar abincin fa?A sanyaye tayi
maganar.Ba tare da ya waiwayo ba ya ce, sallah
zan yi tukunna.Kausar ta ce,Abba ina kayi sallar
ka dawo kaje damu gidan iya, kada kaje daga
can.Ya dubi yaran da murmushi zan zo muje
kunji?Suka ce to Abban mu, bari muyi muma
sallar.Ko da tayi sallar sake zama tayi gaban
madubi tayi sabuwar kwalliya sanan tayi canjin
kaya daga jan yadin zuwa leshin ruwan dorawa
mara nauyi .Ba kamar ko yaushe da yake kashe
waya baina zasu ci abinci wayarshi kunne kuma
jifa jifa yana amsa kira.Guri daya taji dadi ya
zage ya kwashi abinci kamar yanda yake yi ko
yaushe, haka nan
haka nan 'ya'yan shi yana ta surutu da su.Amma
ita ya dauke wuta da lamarinta har ta kasa cin
abincin ma, so take ta tuno kurun laifin da tayi
masa dan kawai ta bashi hakuri.Bata saba da
wanan yanayin da suke ciki ba, zuciyarta ta ce ko
ya ta kiran wayarki ne ba a ji?Da sauri ta dube
shi.Abban kausar nasan kayi ta nema na layi naa
kashe ko?Ya dubeta ban nemi layinki ba, ba wuta
ne ta ce eh ba wuta.Kutashi muje gidan iya,suka
mike cikin murna,Ku ziyarci blog dinmu domin
karanta Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Kausar ta ce,Abba, momi bata dauko hijabinta
ba.Ya ce, bata son zuwa ne, tayi aiki ta
gaji.Wanan ya nuna mata ba a son zuwa da ita
tunda ba a tambayeta ba bare a ce ita ce tace ba
za ta je ba.Sun barta cikin tunani da jimami, ta
gyare gidan musanman gurin da suka ci abinci,
tayi ta jiransu tana zaune a falo tana kalon TV
amma inda zaka tambayeta abinda ake yi a TV
din ba zata fada maka ba.Ita burinta kawai ta
san laifinta, amma ina ta tuna da cewa anjima da
yazo dole zai sauke ko mai dan tasan cewa ba
zasu taba kasancewa gado daya da shi ba ya iya
kauda kai daga gare ta.Itama zata ja aji lokacin
har sai taji dalilinsa, ganin sun kai har sha daya
sai kurum ta cire tayi shirin bacci, kayan baccin
bakake masu matukar daukar hankali, ta dora
hijabi saboda da yara zai shigo.Kausar ce kurun
batayi bacci ba, Al-Amin yana sabe a kafadar
dama, mama a ta hagu, kausar din tana biye
dashi suka shigo.Kai tsaye dakinsu ya nufa da su,
tabi bayan su yana kwantar da su, ya fita ita
kuma ta gyara su, sanan tayi musu adu'a taja
musu kofa.Dai dai lokacin kausar tana cewa
momi sai da safe, sadiya tace, Allah ya kaimu
kausar.Dakinta ta nufa ta sake fesa turare, sanan
tanufi fridge don ta dauki furarshi wadda ta riga
ta dama.Shiru ta tsaya dan ya riga ya dauka, ta
nufi dakin shi.Yana zaune bakin gadonshi sanye
da kayan bacci, laptop ce a gabanshi kan dan
tebirin da ake ajeye mai fura.Kofin yana
hannunshi yana kurbar furar, idonsa sanye cikin
farin gilashi ta ce, tace ashe har ka dauko furar
ka?Ba tare da ya dubeta ba ya ce eh.Ta zauna
kusa da shi wai abban kausar nayi laifi ne da ake
ta share ni?
Ban gane na neke ta share ki ba?Ta ce na gane
yau duk ka canza ko na ce abubuwa sun canza
kamar ba mijina ba maita rairayata?Ya dago ya
dubeta baki min komai ba.Ta dora hannunta a
kan cinyarsa, abba kausar to naganka ne ni yau
irin kamar banyi kyauba din nan.Ya kalleta Dan
Allah ki barni ina yin abu mai muhimmanci ne.Ta
ce, amma dai da aka saurare ni bai fi abin da ka
ke yi muhimmanci ba?Ga mamakinta sai kawai
taji ya daka ma tsawa,kin san me kike fada kuwa
dan Allah tashi ki bani guri a nan,ta zaro ido,
mikewa tayi ta nufi kan gado ta kwanta a ranta
tana cewa ka gama kazo ka same ni ina nan
kwance.Abin ta'ajibi ranar dai haka ya raba dare
yana harkokinshi a internet sabon abu ga Sadiya
mutumin da in yazo satin karshen mako hatta
wayoyin shi kashewa yake suna manne da juna
har sai ya tafi yana cike da kewarsu.Ko da ya
kashe laptop ya kwanta juya mata baya yayi,don
Allah babban kausar me yake faruwa ne?Dan
Allah in wani abu ya faru ne ka sanar dani zan
baka hakuri, ban saba da wanan rayuwar
ba.Cikin zafin rai wanda banta ba ga ni ba ya ce,
nace bakiyi mini komai ba, kina son dole sai nayi
maki karya ne?Dan Allah ki bar ni in huta ki barni
na ce.Ta rike kai to banyi maka laifiba me yasa
ka canza min?Nasanka kai mutun ne mai bukata
a marmatse ka ke zuwa in kayi saty daya, wanan
satyn har saty biyu kayi amma sai naga kazo
bana gabanka.Ya zoro ido to yau ban da bukata
ko dole ne?Ya ja tsaki, tashi dan Allah taf dakinki
bana son jaraba kada ki dameni.Kuka ne ya
subuce mata, ta fita a dakin tunda aka kawota
gidan yau ce rana ta farko da zata kwana a
dakinta ita daya.Dan ko haihuwa tayi basa raba
makwanci, ta fito falo ga mamakinta sai taga
kausar tsaye a falo tayi saurin dai daita fuskarta
tare da share hawayenta ta nufi kausar.Me kika
fito yi?Kausar me kike so?Ta ce, mome naji abba
ne yana fada ne, me kika yi masa?Ta kama
hannun yariyanyar suka nufi dakin yara.Kan
katifarsu ta kwantar da ita ta kuma ta kwanta a
bayanta tare da rungumeta, kausar ta sake
tambayarta momi kinyi laifi ne Abba ya ce ki fita?
kasa magana tayi don al'ajabi ne ke dankare cikin
ranta, ta danne hawayenta ta ce kausar laifi nayi
masa.Kausar ta ce, momi ki bashi hakuri
mana,'to' Sadiya ta ce zan bashi sai da safe in ya
huce kinji?Kausar tace, eh.Sadiya ta ce ki daina
tashi cikin dare kin ji, tadinga shafa kan yarinyar
tana lallashinta hartayi bacci ita kuma ta koma
duniyar tunani tuno farkonsu.Iya mahaifiyar Aliyu
ya ce ga mahaifiyata, uwarsu daya ubansu
daya,su 'yan asalin jahar jigawa ne, a karamar
hukumar Hadeja.Mahaifiyarsu ta rasu ta barsu su
hudu mazabiyu mata biyu, kawu Adamu da kawu
Dauda duk iya ce babbar su.Lokacin da
mahaifiyata ta na budurwa, dan haka iya ta
dauketa lokacin suna zaune a Dutse da mai
gidanta da yaranta hudu.Yaya sulaiman
yayazakari, yaya sani, sai cikin yaya Aliyu.Mijinta
ma'aikacine a ma'aikatar gona ta jahar Jigawa,
daga baya yayi ritaya inda ya dawo kaduna da
zama sana din dan uwansa dake noma.A
unguwar mu'azu ya sai gida madaidaici a ciki aka
haifi Aliyu kuma a nan aka aurar da mahaifiyata
inda ta auri mahaifina wanda yakasance
ma'aikacin gidan Raidio kaduna.Amma dan zariya
ne kuma zariyar aka kaita,yana da mata biyu da
yara kusan goma, ko a lokacin.Maimuna
mahaifiyarta ta kasance mai hakuri da juriya, duk
da cewa bai kasance mutum mai cika hakkokin
iyalansa ba.Amma bata taba kawo kararshi gurin
iya ba,don tasan iya tana da fada sam bata da
wasa.Shekarar da yaya sulaiman yayi aure
shekarar ce mujin iya Allah yayi mai rasuwa,sunji
mutuwar ta farat daya yana cikin sallah yayi
sujjada a masallaci har aka idar bai dago ba.An
dago shi sai gawa, ashe mutuwar kenan.Yaya
sulaiman koyarwa yake yi a makarantar yan mata
dake Tudun wadan wada wato Sai yaya zakari
kasuwanci a babbar kasuwar kaduna, duk da
cewa ba wani babban dan kasuwa bane,Sani
kuma da ya gama secondary sai kurum ya shiga
wurin gyaran motoci dan a lokacin babu halin ci
gaba saboda yanda karatu ya zama a kasarmu sai
yayan masu shi.Talaka yana so yake hakura.Ya
Aliyu karamin su kuma suna tallafa mashi don
ganin ya samu karatunshi, kwanci tashi suma duk
suka yiyyi auransu.Lokacin da mahaifiyata tana
dauke da da tsohon cikina don ta jima bata haihu
ba, har lokacin iya bata gane yar uwarta tana
cikin matsala ba, sai bayan ta haife ni.Lokacin da
taga komai babu, abin ci a gidan gashi ya sake
yin aure ya ciko mace ta hudu,iya ta same shi ta
ce, yanzu tsakanika da Allah Abubakar hakan da
kake yi dai dai ne?A ce ka ajiye mata babu
kulawa ba abinci badai baka da shi ba sai don
zalunci?Ya ce ai za a siyo.Tace, gara ma ka siyo
don ba zan dauki zama da yunwa ba, in an ganka
a waje kwas kwas har da mshin din hawa gareka
amma a gidanka da yunwa.A daddafe akayi suna
inda aka rangada min Halimatu Sadiya, iya ta tasa
mahaifiyata ta tafi da ita, tace ba za a bartaba
haihuwar fari ba kulawa ba,Ita kenan gareni dan
wadan can yan uwan namu sai munyi tafiya mai
tsawo kan mu gansu.Sai da mahaifiyata tayi
kusan wata shida lokacin ni da ita munyi bulbul
tamkar kada iya ta bari mutafi, amma yanda
mahaifina ke ta suntirin zuwa yana kuma turo
mutane don baiwa iya hakuri sai ta hakura tace
mu koma.Amma ta ja masa kunne sosai, to dan
saukin yanzun ba kamar da ba, hakan yasa ki
shiyoyin jin haushinta suna ganin ya fifitata shi
ko tsoron karr a dauke ta ne don iya ta tabbatar
masa in tazo taga ba daidai ba to zata tafi
damu.Shakarata biyu ta sake samun wani cikin
tun yana karami take fama da laulayi iya tana
zuwa tare da yayanta akai akai suna duba
mahaifiyata tare da kawo mata abubuwa.Iya taso
ta tafi dani amma lokacin an ce inna da kalafucin
uwa, kulafaci gareni sosai ta hakuraKu ziyarci blog
dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Gurin haihuwarta kuma taji jiki da kyar ta haifi
yar bubu rai.Sanan itama jini ya balle mata ya
dinga zuba kafin aje Asibiti rai yayi halinsa, ance
iya taji mutuwar nan kaman me.Bayan anyi
bakwai aka raba dan abinda ta bari sanan iya
tace ba zata barni ba dani zata tafi da kyar
mahaifina ya yarda don shima yaji mutuwar yayi
kuka tamkar ranshizai fita , to mafarin zamana a
gun iya kenan.Na taso cikin gata da tarbiya duk
da irin son da iya take yi min, bai sa ta kasa bani
tarbiya ba.Lokacin da aka kawoni gidan yaya Aliyu
yana shekararshi ta karshe a makarantar kwana
ta barewa kwaleji dake zariya.Sam yaya Aliyu
halinsa ba iri daya bane da yayyansa, don su
suna da sakin fuska da fara'a, amma shi kullun
rai a hade ta bakin iya in tana masa tsiya takan
ce na rasa inda ka gado wanan halin naka na
shegen miskilanci, kullun cikin bacin rai sai kace
jakadan yan wuta. Tunda nake gidan bai taba yi
mun wasa ko hira ba, magana in ta hada mu to
bata wuce yazo bai ga iya ba, yace Sadiya ina
iya?Tare da haka ba shi dai raini ko rashin kunya,
sai dai kafi ya ga saurin fushi gami da zafin
zuciya. Yanada matsananciyar tsafta da ibada Iya
na yaba masa a nan, tunda na taso Allah baitaba
nuna mun bacci iya na dare ba, sai dai na rana,
bayan azahar. Duk lokacin da na farka zan ganta
tana yin nafilfilu.
Yaya Aliyu akwai iya saka kaya, bani manta
kawayena in sun biyo mini makaranta suka ganshi
sai kiji suna cewa, sadiya yayan nan naki dan
kwambo ne, ya cika yanga gashi baya
fara'a.Nakan ce kurufa mini asiri kada yaji.Burin
yaya Aliyu aduniya bai wuce ya zama police ba,
kalmar da Iya ta tsana duk lokacinda ya ce mata
shifa in ya gama karatunshi zai shiga makarantar
horar da yansanda.Sai ta ce masa ya daina
wanan tunanin don ita bata son dan sanda, wai a
nata ganin sharri kullun ake koya musu, kullin
suna kan titi suna karbar cin hanci.Wani lokacin
tace, dan sanda da aka ce ko ya mutu gawarsa
tana fita da ban, dan baki take to ban amince
ba.Shi kuma sai yace, iya kiyi min adu'a buri na
kenan zancen zancen ace kaza kaza duk sharri ne
babu ma'aikatan da babu na gari, kuma babu
inda ba battace.Kimin adu'a in zama mai kawo
gyara a cikinsu kuma in na zama dan sanda in
sha Allahu sai kinyi alfahari dani.Takan tabe baki
ta ce, uhm ni rabu dani da wanan zancen, ni dai
insuna yi sauraransu kurun nake yi, don sam in
yaya Aliyu yana fira da iya bana sa baki, domin
tsawa zai daka min ko ya harareni, haka nake
rayawa a raina ba wai dan haka ta taba faruwa
ba.Iya tana yin wainar saidawa a cikin gida,
muna yin ciniki sosai, wani lokacin har da
sha'anin buki suna ko walima duk muna yi da
sana'ar ta take yi mana dawainiyar karatu ni da
yaya Aliyu, sai dan abin da sauran yara suka
kawo mata.Dan suma yanzu ko wanensu yana
nan da dawainiyar iyalansa, karatun ya Aliyu
shine mai cin kudi, dan Alokacin yana karatun
digree sa ne a jami'ar Ahamadu bello dake
zariya.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Yana karantar (Engineering) ban san yanda zan
kwatanta muku ra'ayinsa ba, amma shi mutum
ne mai babbancin hali da ra'ayi.Bayan ya
kammala karatun sa ne ya dagewa iya yayyinsa
shifa sai yaje police Acadamy, wato makarantar
horar da manyan yansanda dake wudil jahar
kano, dakyar ya sha kansu.Ko da yake har sai da
kawunsu kannan iya dake Hadeja,Kawu Adamu
ne yaje har gida ya lallashi iya.Bayan ta yarda
tace, to ita fa bata da kudi,yaranta kuma suna
fama da iyalansu, dan haka yaje ya nemi
kudi.Aliyu ya ce, iya ai na fada miki asaida gona
ta, ta gadonmu da aka raba mana.Nan ma da
kyar ta yarda kawu Adamu shineya saida gonar
Aliyu yaje ya amsa, haka yayita zirga zirga
tsakanin kano da kaduna har sai da yayi nasarar
shiga police Acadamy.Ranar farko da yaxo ni
kadaice ina cikin wanke kayan waina bayan mun
tashi, iya bata nan taje kai kudin kayan miyan
wainar gobe, sai kurum naji sallamar sai naga
mutum tsaye kyam da kayan dan sanda riga blue
mai haske wando baki, ga wanan takalmin na su
da hula.Nikuwa dama gani da tsoron Dansanda,
sai naji cikina yana kugi, fuskarshi daure yace,
bakinki yana ciwo ne, bakya iya amsa sallama ko?
Cikin in-ina nace, wa...alai...kassalam.Ya zuba
min harara, yau ne kika fara ganina ne da har
zaki tsareni da idanu ko na can za maki ne?Na
sunkuyar da kai, a'a ya nufi dakin nace bata nan
ta je wurin Isa mai kayan miya, ya ciji ya tsa to
dauko min makullin dakina najena duba inda na
san iya tana ajewa na dauko masa da zan bashi
sai da na dan rusuna.Ya amsa ya nufi dakinshi
nazo na karasa wanke wanken na gyara gurin ya
fito cikin gajera wando da yar T-shirt irin ta
yansanda,Ina cikin kicin zan dora tafashen kashin
waina, yace baki san mutun yazo kiyi mai tayin
abinci ba, kenan ina ganin rowa zakiyi?Nace nayi
zaton ko kana azumi ne, na ga kullun kana yin
azumi,yace, oh, dama kina samun ido ne har kika
san cewa kullum ina Azumi?To yau ban yi.Nace,
duk abincin ya kare sai sauran tuwo kuma baka
cin dumame, sai dai in ko na dafa maka wani
abu.Yace barshi nasha cornfilakes,ya juya ya nufi
dakin sa.Na sauke ajiyar zuciya ban san meyasa
ba yaya Aliyu in yana guri bana so in tsaya a
gurin sai in ga duk ya cika gurin,gashi tsananin
tsoransa nake bai dai taba duka na ba watarana
ne dai da yake iya gadanga take ce masa sai tace
in kira mata shi, ni kuma naje nace iya ta ce kazo
gadanga.Wata tsawa da yayi min kadan ya rage
in saki fitsari, ya dora yatsinsa a dan manuni a
goshi na.In kika sake ce min gadanga sai na
zaneki tas kinji ko?Jikina yana bari nace, kayi
hakuri.Don tsoro lokacin har fitsari nayi a
wando.Lokacin da iya ta dawo tai murna da
ganin autanta, nan suka zauna suna yin fira, cikin
hirar ne naji tana yi masa zancen aure, inda ta ce
gadanga dan Allah ka nemi matar aure kasan
shekarunka nawa yanzu?Yayi dan murmushi ni
kwan nasan shekaruna, muke nan kullum cikin
rubuta date of birth ba dole in rike shekaruna
ba?Talatin da uku ne kacal.
Iya tayi dariya talatin da uku shine kacal?Ai dai
cikin sa'anninka ina tsammanin kai kadai ka rage
ba kai aure ba.Ya ce iya ba ni kadai na rage ba,
kin manta da usman?Ta ce, usman bikin shi kafin
Azumi ba kuyi waya bane?Aliyu ya zaro ido, iya
da gaske?Tace, ko jiya na kira shi na fada masa
yau zan shigo shi ne zai ki sanar dani?Iya ta ce
kila sai kazo din za ka ji zancen.Ya ce, iya kiyi
adu'a kawai amma ayanzu ba mata a ga bana,
kokari na in hada wanan course din nawa.Ta ce,
Allah ya taimaka.Ya ce sauran mu wata shida.Ta
ce, to Allah yasa a gama cikin nasara, ni dai fata
na ka zama mai gaskiya da amana, kayi aiki a
kasarka da kishi.Ya ce in sha Allahu, na gode.Duk
ina jin su har suka gama ya dube ni ita waccen
sunyi jarabawar J S. C.E din?Iya ta ce, tin yau she
har sun amso yan zu kici kicin shiga SS din ta
muke yi, ya ce zo ki bani saka makon na ki in
gani, dan nasan bawata kwanya ce da ke ba.Iya
ta ce, in ji wa?Sadiya boko da islamiya tana da
kokari.Na dauko gaba na yana faduwa na bashi
ya duba sanan ya kalleni babu laifi, amma kina
jin turanci?Na sunkuyar da kai, amma ban iya
bada amsa ba.Ya ce shirmen yaran hausawanmu
kenan, kuna jin tsoro ne kada kuyi ba dai dai ba
ayi muku dariya, to ai gara ayi muku dariyar
sanan a gyara muku.To ni dai daga yau kada ki
kara mun hausa.Har in koma duk kuma zuwan
da zanyi in baturanci zakiyi mun ba bana son jin
maganar ki.Iya ta ce, kuji mun fin karfin hali
gurin gadan ga, wanan ai mugun horo ne.Yare ba
na uwarka ba, ba na ubanka ba kace dole sai tayi
maka magana da si.Ya ce, in ba haka ba yau she
zata iya ga yanda zamanin namu ya zama sai da
karatu, ko da ta gama scondary zaki mata aure?
Iya ta ce, tana samun miji zan sallamata, don
haka kar ka takura mata.Ni dai nayi ciki na barsu
nan suna ta jayayya, yana cewa ilimi ko dan
tarbiyar yara ai ko ni ba zan auri matar da bata
ta shiga jami'a ba.Iya ta ce Allah ya taimaka ni
tawa tana samun miji zan turata can gidan
mijinta shi ne babbar jami'ar ta.Ku dai yan
zamani baku da magana sai dai in kun tashi aure
kun fi son yan boko sabo da tarbiyan yayan ku.To
amma kada ka manta ni banyi boko ba, amma
duk in da kuka shiga yabon ku akeyi ana sha
awarku.Aliyu yayi dariya, to iya in kin lura ai
baban mu yayi boko, kefa kika ce mun lokacin su
yaya sulaiman suna yara sun zo da home work
shi yake musu.Nima lokacin da na taso sune suke
yi mun ba, tace to wanan ce tarbiyar?Ban ce ilimi
baya cikin tarbiyya ba, amma bashi ne
gundarinta ba.Gun darin tarbiya shi ne ka dora
dan ka kan hanyar Allah da monzo (S. A. W) su
rinjayi komai a kan mazaunin shi.Sanan ka cusa
musu Tauhidi su iya rike Amana,Cika
Alkawari,Tausayin na kasa da taimakonshi,
Girmama na sama, in dan ka ya san wanan sai
ka hada masa da ilimin zamani da na adini shi
ne tarbiyya.Kai in dan ka ya san wadancan ya
rike ko bai je boko ba zai yi rayuwa
ingantacciya.Aliyu ya ce, haka ne zancen ki Iya,
Allah ya sa muma muyi tarbiyar yayan mu kamar
yanda kuka yi mana.Ta ce ameen.Ina da ga ciki
ina jin su na ce, in dai Iya ce duk musun ka da
gardama tana yi maka baya ni sai ka
fahimta.Abin da ya bani al'ajabi da mama ki, da
dare na je kai masa abinci dama fakon sa na yi
tayi dan ba zan yar da wata magana ta hada mu
da shi ba, tunda ya ce sai da turanci, niko dan
tsinta tsinta na iya.Dan haka ina ganin shigarsa
ban daki na dauki abincin na nufi dakin sa na
ajiye zan fita sai na hangi wata mujalla can kan
katifar sa, ni kuma da shegen son kalon hotunan
yan film.Na zata irin tasu ce yan fin din India, sai
na koma na dauko na bude jiki na ya dauki
tsuma ganin mata tsirara.Da sauri na rufe wato
dai mujallar ta tsiraici ce, na sake bude wani
shafin da sauri na rufe, ina fitowa yana isowa
kofar dakin.Ya ce cikin harshen turanci me kike
so na cecikin hausa, dama abinci ne na kawo
maka.Ya matso ya damki kunne natamkar zai cire
shi.Ba na ce kada ki kara yi mun hausa ba?Nayi
shiru dan ina tsoron yi masa turanci ya ji ba dai
dai ba ya ci uba na.Ya sake matse kunnan, cikin
turancin da zaniya na ce yayi hakuri.Ya saki kin ci
sa'a daga yanzu ba hausa tsakanina da ke.Duk
cikin turanci yake maganar.Ni dai nayi daki ina
Al'ajabinshi, mutum kamar na Allah ashe dan
iska ne, ya tasa hotunan batsa yana kallo.Shi
kuma da ya shiga dakin sai yaga kamar an jawo
mujarlar daga inda ya ajiyeta, a ranshi yace wato
dai yarinyar nan ta bude mujallar nan kenan,In
ko haka ne ban ji dadi ba, amma sai wata zuciyar
ta ce, kada ka zargeta, domin bata da rawar kai,
tsoranka ma takeji ba zata taba maka komai ba,
sai kurun ya samu natsuwa tare da gaskata
hakan.Kwana biyu yaya Aliyu yayi ya tafi, niko
cikinkwana biyun nan binshi nake da kallon
mamaki.Bayan tafiyar shine na samu ci gaba da
karatu na a makarantarmu ta maimuna
gwarzo.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Kwanci tashi su yaya Aliyu an kammala wanan
karatun, buki sosai akayi ko na ce walima dan su
yaya Sulaiman su har can suka je nan gidan mu
kuwa mun aikatu.Anyi wainar shinkafa, da su
zobo da kunun zaki, daga can suka turoshi
kaduna (headquarter) a matsayin A. S. P Aliyu
Tukur.Ranar da ya zo gida na jima a uwar daki
ina tunanin fitowa saboda tsoron maganar da zan
masa da turanci, gashi a fallon iya suna fira.Na
zauna ina bitan abin da zan fada masa da turan
ci, can iya ta kwalo mini kira na amsa, ta ce me
kike yi?Na fito, ya kalleni dama tana ciki, kin wani
kunshe kamar wani munafiki?Na ce, sannu da
zuwa. Cikin turanci na yi maganar, shi sai lokacin
na tuna mai da batun wani turanci.Ya kalli iya
sanan ya kalle ni ya amsa, na ce ina taya ka
murna, ya ce ya gode.Ya tambayi nawa karatun
na ce lfy lau.Da sauri nayi waje ina tsoron kada
ya daukowani zancen da va zan iya amsawa ba, a
rai na na ce, baka sanan wannan ba na fi sati ina
haddar su.Bayan na fita ya cewa iya, to kin ga
dai yarkita soma zama baturiya, iya ta ce, eh, ai
hakan yana da kyau.Tunda ya dawo kullun
zancen shi da iya ba ya wuce kayi aure gadanga,
ka fito da mata sai dai in bai zo gidan ba,
kokuma bai zo mata fira ba.Har ta kare ta ce yaje
gidan hajiya talatu ya nemi diyarta Jamila, yace
iya kiyi hakuri har inga wacce ta yi mun da idona,
bana son cushe cushe.Ta ce, duk fadin unguwar
Mu'azu har yau baka ga wacce kake so ba?Sai ya
ce, ina nan dai ina binkitawa, har dai ta hakura
ta zura mashi ido.Daga baya naji suna hira da
yaya sulaiman wai ta sama mashi magani tana
ganin kamar bashi da lafiya, niko da naji wanan
xancen lokacin cewa nayi a raina, ras yake kila
ma neman matan shi yake yi a waje tunda mai
ya hada mara lafiya da hotunan tsiraici?Kuma
bayan nan ina zaton yana kalon fina finan tsiraici,
don lokuta da yawa in yana kallon in nayi sallama
dakin zai kai abinci ko wani abu sai yayi sauri ya
kashe, sanan ya ce in shigo.In kaset din arziki ne
menene na kashewa?Amma na sa a raina wata
rana sai na kama shi.
Haka kuwa watara na xan kai masa abinci darana
lokacin aikin dare yayi da safe ya dawo,Iya kurun
ya gaisar muna aikin waina ya shige daki ya
kwanta.Sai kusan sha biyu sanan ya farka,
lokacin Iya ta tafi gurin sabo mai shikafar waina,
ta ce in ya farka in kai masa ruwan zafin shida
waina in kuma bredi zaya ci to in kai masa.Ya fito
ya shiga wanka, da sauri na dauki dan flask din
sa na ruwan zafi na nufi dakin, ko mai a kashe
yake amma na san zan kunna in gani tunda
wanka ya shiga saboda shi mutum ne mai
dadewa a wanka.In dai ya shiga tamkar zai canza
fata, don haka ina lokacin sallah ya katato xai
shiga ban daki iya kance bari muyi alwala dan in
ka shiga sai lokacin salla ya fita baka fito ba.Na
jona komai ya kawo na ce oji bulumme can kasa
dan muna funci aikuwa CD yana gama login sai
ga mata da maza tsirara suna aikata masha'a.Da
sauri na kashe na fita naje na ci gaba da aikina
abin da na gani ya girgiza ni kuma naji haushin
kaina da karan bani na.Na fito na dauki waina da
bredi naje nayi sallama ya ce in shigo na shiga na
ajiye xan fita ya ce tsaya, me kika shigo yi nan
dakin?Gaba na ya fadi na ce ni flask na kawo, ya
ce daga nan sai kika yiyi me?Cikin in ina na ce,
banyi komai ba ya Ali.Ya tsareni da idanu, bashi
da tabbacin nayi wani abu amma yana shigowa
yasan an shigo.Ya kalleni, jiki.Na fita sanan na
harari dakin na tafi.A raina na ce dan iska, amma
wani lokaci sai ya kure wa'azi sai kace na Allah.
Kwanci tashi ba wuya, muna cinye kwanakinmu
har mun kammala (SS3) mun zana jarabawa
kuma lokacin ya zo dai dai da saukar karatun mu
na alkur'ani.Munyi komai cikin nasara, kuma nayi
walimata a gidan mu inda iya ta matsawa ya
Aliyu sai ya buga mun memo wanda zan rabawa
kawaye na.Sauran yayyansa ma sun taimako,
baba na kuwa da naje zaria na fada masa dubu
biyarya bani wai inyi hakuri da yake ina zuwa
danhutu can wani sa'in iya tace inyi sabon dinki
da kudi na.Dangi kam sun xo babu laifi, har yan
uwa na na zariya, babanmu ya zo da su komai
na yayi babu laifi.Da yamma ni da kawata Aisha
muna kwashe kujerun da muka zauna akai
mukayi walima a waje da kawaye na.Mun hada
su guri daya sai naga guda biyu wanda ya Aliyu
da wani abokin sa suka zauna su na hira.Ta ce,
kije ki amso wadancan cikin zolaya tayi maganar,
don tasan ina jin tsoron shi.Na ce, ke kije ki
amso.Tayi yar dariya bari inje.Tayi tamkar zata
nufi gurin sai ta fasa.Muyarshi ta katse maganata
da zanyi lokaci daya kuma gaba na ya fadi, Ke!
Na wai waya, zo nan.Naje na rusuna na gaida su
cikin in ina ya ce, ke daga jin maganar ki baki da
gaskiya ko?Na ce, a a.Ya ce, to me nene nayin in
ina din?Nayi shiru, ya kalli abokinsa ga ta.Abokin
ya ce, ina yi muki murna da yin saukar alkur'ani
mai girma, Allah yasa anyi na tsoron Allah.Na ce,
amin.Ya Aliyu ya ce, jeki dama murnar zaiyi
maki.Ina tafiya ya kalli Aliyu ya ce, kanwar nan
taka tayi fa.Ya Ali ya ce, ok, iskancin naka har
agida ma zaka yi?Auwal ya ce bada wani abu na
ce ba, cewa nayi tana da kyau.Kai da ma ka
shiga kayi yar gida tunda duk matan dake sonka
baka kallon su.Ali ya ce don me zan tsaya kallon
yayan mutane, alhalin na san cewa ba auran su
zanyi ba?Auwal ya dan yi masa dukan wasa a
kafada tare da cewa, ko jiya munyi gulmarka da
Sajen Bello, wai ina ma shine mata keyiwa wanan
shishshigin, da sai ya more kuriciyarshi son
ranshi, amma kai kullun cikin Azumin dole, in
kaga mata sai kace kaga Abokanan gaba.Aliyu ya
ce, ban ga anfanin zina ba, koda ba haramun
bace mutum ya gujeta, ya kyamace ta, dan kare
kansa daga cututukan zamani.Ina fada maka ina
da kyama ba zan iya hada jiki da wayan can ba,
kuma dole in naga mata in hada rai tun da ba
halali na bane, kuma ba muharramai na
bane.Kullun dai ina adu'a Allah ya bani mace ta
gari mai kamun kai, kuma da kuke bin matan
Allah ya shiryeku, kai gashi kayi auran ma amma
ba ka daina ba.Kayi hattara duk abin da ka shuka
shi zaka girba, kana kallo wani can zai bata
rayuwar yayan ka yadda ka fada ta yayan
wasu.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Auwal ya ce , ka samu cikin adu'a abin ne
dawahalar bari, mata ne nishadin rayuwa, hira
da su ma a kwai dadi ne.Tsaki Aliyu ya ce in kaso
kaji dadin ba?Ni kuwa bana fatan in ji dadin fira
da mace wadda ba tawa ba, ina nufin
halalina.Auwal ya mike, bari ni in tafi kai dama
malami ya kamata ka zama ba dan sanda
ba.Sam Aliyu be mike dan raka shi ba, daga nan
suka yi sallama.Shi kam tunani ya shiga, shima
yana sabo wajen kallon fina finan batsa da
karantar mujallan batsa, duk da cewa bai taba
aikata zina ba ya san wanan laifi ne babba.Kuma
in mutum bai daina ba wata rana zai kai ga
aikata zinar, kuma tunda Allah ya rufamini asiri
tsawon lokaci yana yi ba wanda yataba ganinshi,
ya kamata ya daina.Ya tuna lokacin da ya fara,
wata rana yaje dakin su Auwal da rana lokacin
suna jami'ar Ahmad Bello ta Zaria, ya ga wani
novel a dakin ya dauka ya karanta, ashe na batsa
ne.Daga lokacin sai yaji yana so ya gani, ya ko je
wani shago a kasuwa ya siyo kaset din tare da
mujallar tun daga nan lokaci zuwa lokaci sai ya
siya ya kalla, sanan ya kona su ya sake siyan
wani.Shi da kanshi ya sha fada wa kanshi cewa,
yanda yayi Imani zai tsaya gaban Allah haka yayi
imani za a tambaye shi yanda yayi ya sami kudi
da kuma hanyar da yabi gurin kashe su.Me zai ce
game da wanan kudin da yake sawa yana siyan
batsa?San nan baya karanshi da komai sai karata
da masu hankali?Lallai wanan abune da ya
kamata yayi makansa tun kafin ya mutu.Ya mike
tare da kudircewa daga yau ya tuba,ba zai kara
ba.
Dai dai gwargwado ba xa a ce bani da kyau ba
tunda Allah bai halicci mumuna ba matsawar
mutum yana da kyan hali, balantana a ce mutum
musulmine.Aina ya ga kyau sai dai kuma in ba
tsafta, ni fara ce sol amma bani da dogon
hanci.Wanan baisa fuskata muni ba, haka
idanuwa na matsakaita ne, ni mutum ce mai
tsananin kwalliya ko alwala nayi sai na sake
sabuwar kwalliya.Haka nan iya bata gajiya da
siyan mun kayan kwalliya, sanan bata ganin
bekena duk lokacin da zan bata gurin kwalliya.A
cewarta ya mace doki ce sai da kwalliya, abinda
kawai bata yarda da shi ba shi ne, ayimini dinkin
da zai nuna surata, nan ne zata ce ba zata bada
kwamasho ba gurin yada zina.Ta ce, shigar da
yawancin mata keyi ita ce ke haifar da zinace
zinace sannan zata zuba ko nawa ne ta yankan
mini yadin hijabi amma mayafi dai sai dai inyi
asusu in siya.
Shima din ban isa in siya karami ba sai babba,
kuma mai kauri ban taba jin haushinta ba dan
nasan tana kare nine daga afkawa cikin
shaidan.Dai dai misali ina da farin jinin samari
masu sona, dan ma iya bata bari in fara fita
zance da wuri ba sai da na kai SS2 duk masu
zuwa gurina da aure suke sona.Sai dai ni cikinsu
banga wanda yayi mini ba irin injishi kane kane
cikin raina din nan ba, fada haka iya take cewa
maza ki tsaya ruwan ido daga karshe kowa ya
gudu kizo kina nema.Ai yanxu lokacin ya mace
mai hankali ake dubawa wanda yake da hali mai
kyau sanan ba jahili ba kuma ya kasance yanada
yar sana'ar da zai rikeki, to ki kamashi.Allah
shine mai azurtawa, in da rabo sai kuyi arzikin
tare, ke in ma baku samu anan ba to ya baku na
gobe kiyama.Yawan yi mun wanan nasihar yasa
nake ganin zan iya tsaida Idris kuma zan iya
auransa amman sai mun zauna da kawata
aminiyata Aisha.Mun zauna da ita ita ma tace,
gaskiya duk cikin masu sona babu kamar Idris a
hankali.Mun yanke shawarar in tsaida shi ita
kuma dama akwai makocinsu Bello dake sonta.Ku
ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Wata safiya Iya tana kwance ba lafiya dole na
fasa zuwa makaranta tunda mun riga mun hada
kullun waina, sai kuma ciwon cikin dare.Ya Ali ya
shigo da shirin fita, don bai san bata da lafiya ba
sai da ya shigo dakin, ya girgiza da ganinta
kwance cikin bargo dakyar take magana.Arude ya
ce, ya babu lafiya ne?Tace, eh, yace meyasa ba a
tashe ni ba a gida fa na kwana?Ita wacen
sakaryar ba sai ta fada min ba.Iya ta ce ni na
hanata ta ce bari ta taso ka, ya cire hula, bari
muje Asibiti, bari in samo mota, ta ce, a a naji
sauki.Fita yayi sai gashi da likita wani dan nan
unguwar ya duba ta sai gashi hadda ruwa a dora
mata.Ranar dai bai fita bahar rana, bai taba
birgeni ba irin ranar, duk wani abu sai yayi, hatta
bata magani a baki da abinci sai gurin la'asar
sannan ya fita.Su yaya Sulaiman,Zakari da Sani
duk sun zo da matan su, sanan makota na ta
zuwa.Da yaje gurin aiki ya bada uzirin shi sai ya
dawo kusan shabiyun dare, jikinta yayi sauki.Ina
jiyo hirarsu,rokonshi take yayi aure ta ce Aliyu
bani da wani burin da ya wuce inga auranka, kai
na fuskanci kafi son sai na mutu sanan zakayi
aure.Jikinshi yayi sanyi, dan ya kasa tuna ranar
da ta kira shi da Aliyu, cikin tautasar murya da
lallashi ya ce, zan yi iya, in sha Allahu kina
raye.Ta ce, kayya, gadanga kullun haka kake
cewa, ni dai ai tuni na cire rai ka tashi katafi na
yafe maka Allah yayi muku albarka kai dasauran
yan uwanka.Yarinyar nan sadiya dan Allah ko ban
tashi ba kada ku bari ta koma zaria ta zauna
gurin wannan yaron hardai ta sami miji kuyi mata
aure.Ya ce, iya ke ce da kanki zaki aurar da ita
insha Allahu, ta ce shi kenan tashi kaje ka
kwanta.Hankali tashe ya fita bayan ya tai maka
mata ya kawota cikin daki, na tashi idona
naxubar da hawaye, na taimaka mata muka
kwanta.Ina kuka kasa-kasa ta ce,Sadiya lafiya?
Tace iya bana so inji kina cewa zaki mutu ki barni,
ta ce in fada ko kar in fada sadiya ba zan kara
lokaci ba sai dai in ajalina bai zo ba.Da kyar bacci
ya daukeni, lokacin iya tayi nisa da bacci.Shima
Aliyu tun da ya koma dakin shi fa ya kasa ko
zama, lallai dole ne ya nemi mata, sai dai
matsalar shi ta ina zai fara?Bai taba yin budurwa
ba, bai taba soyayya ba, shi kuma yana ganin
kamar raini zai ja masa in yaje kofar gidan su
yarinya.Amma bari gari ya waye yaje wajen
usman amininshi.Kafin ya wuce masallaci sai da
ya fara lekowa dakin mu ni da iya duk muna
sallah, sanan ya wuce,dan Allah ya kawo mata
sauki a cikin daren daga masallaci gidan Usman
ya wuce, ta wya ya kira shi cewa gashi a kofar
gida,Usman ya ce, lafiya?Aliyu ya ce, lafiya ba lau
ba, fito kaji.Da sauri usman ya bude gida ya fito,
sama sama suka gaisa.Usman ya ce, aboki lafiya?
Aliyu ya ce ina fa lfy, jiya tsohuwa ba lafiya, ta
fara bar mun wasiya, sannan tayita jaddada min
burinta kawai nan duniyar shine inyi aure.Usman
yace aboki ba ita kadai ba, ni kaina buri na
kenan, to tunda kaga tsohuwa ta tsananta gara
kayi ko kwa rabu lafiya.Aliyu ya ce, ai baka sani
ba, tunani na yanzu ina zanje nemo mata?Na
rantse maka banda budurwa...
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
DARAJAR YAYANA1-02
Posted by ANaM Dorayi on 08:55 PM, 09-Mar-16
Under: DARAJAR 'YA'YANA
___________________NA
___________HALIMA K/MASHI
Usman yayi yar dariya sanan ya ce, ni da zakaji
shawarata wanan sadiya ta gidanku?Aliyu yace,
ah haba?Usman yace, naga yanda ake yabon
hankalin yarinyar, ko a gida tana da matsalane?
Aliyu ya ce, sam ko a gida bata da matsala
gaskiya, amma ban taba jin koda alamar sonta
ba, to wanan yarinyar ma ina ganin ta tsaida
wanda take so, in ma ba ta tsayar ba sai inga ta
yi mun yarinya.Shekarunta sha bakwai fa yanzu
in ban cika ma ba, usman ya ce, dai dai.Nafi son
wacce ta shiga makarantar gaba da scondary a
kalla ta mallaki hankalinta, ta san yadda zata kula
dani sai nine zan koma in kula da ita.Usman ya
ce, ba yaran yanzu ba, tunda kaga bata yiba in
kaga wata da tayi maka ko a unguwarku ko a
kafatanin unguwar mu'azu ka fada min yanxu
anjima sai muje, kaga yanxu sai kaje wa iya da
kwarin gwiwa.Aliyu yayi shiru yana tunani can ya
ce, aboki kasan Allah?Nifa ba wai ina kallon mata
bane, na layinmu ma ban sansuba balle na
unguwa.Usman ya ce, to aboki ka tsaya a Sadiyar
mai hankalice,Sadiya tayi.Aliyu yace inda ta kaicin
yake sai kuma in kirata ince ina sonta?Usman ya
ce in baka iyawa bi ta sama mana ka samu iya
ka fada mata kana son Sadiya, nasan zatayi
murna.Aliyu ya ce, aboki daina cewa ina sonta,
zadai ayi aure amma ba wai ina sonta ba, Aliyu
yace kuma ba zanyi karya ba tunda banji cewa
ina sonta ba,har Aliyu yaxo gida tunani yake anya
kuwa zai amince cewa yana son auren sadiya?
Lokacin da ya shigo dai dai na bare magani na
mikawa iya, ta afa tare da kora ruwa, ya tsaya ya
rike kugu yana kallon mu, tunaninshi a wanan
lokacin lallai babu wanda ya dace ya auri irina,
bisa hujjarshi tacewa ba zai sami matsala ba
wace take tsakanin iya da matan yayanshi ba.Iya
tana kuka cewa cikinsu matar yaya Sulaimance
kawai ta san darajarta, kuma tabbas hakane
domin sai suyi wata uku basu zo sun gaida ta
ba.Ita ba wai tana kwadayin abin hannunsu ba
ne, a a ko ba komai taga yan jikokinta yayi,
amma Sadiya bata da uwar da ta wuce iya.Dan
haka yana nan ko baya nan zata zamo a
karkashin kulawarshi, burinshi yaga ya daukewa
iya duk wani matsalarta, su kuma yayinshi suji da
iyalinsu.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Tunaninsa ya katse lokacin da iya ta ce, gadanga
ka shigo ne?Yayi firgigit, na shigo iya.Na gaida shi
na fita, shima a ranar bai iya yi mata zancen ba,
karshe ma tunani yayi ya samu yaya sulaiman
suyi shawara.Haka kuma bayan sallar isha'i ya
nufi gidan yayan nasa bayan sun gaisa sai ya
sanar dashi abinda ke tafe dashi.Yaya sulaiman
yaji dadin zancen da Aliyu yazo dashi, sanan yace
sai ka samu yarinyar ku daidaita, Aliyu ya ce, ina
ga ba sai na sameta ba, indai iya ta amince shi
kenan.Yaya Sulaiman ya ce, iya ba zata ki ba,
yarinyar ce abinji, in ta ce bata sonka fa?Aliyu ya
ce, ai nima ba wai ina sonta bane, dacewar
auren kurum nake dubawa, shi yasa.Ya Sulaiman
ya ce, shirme kenan, to kai in kaje wajen iyar ce
mata zakayi ba sonta kake ba?Aliyu yayi
murmushi ce mata kurum zanyi ina so na auri
Sadiya, Sulaiman ya ce, Allah yayi mana zabi na
alkairi.Ka bari zanje gurin iyar, duk yanda mukayi
zakaji.Aliyu ya ce to.Yayi godiya yayi masa
sallama ya tafi..Sulaiman ya sami iya cike da
karfin gwiwa, ganinshi babu wanda zaikai iya
murna kai yasan har goron albishir zata
bashi.Amma ga mamakinshi yana gama labarta
mata dalilin xuwansa sai yaga tayi kicin kicinda
fuska ta ce kaine kaga sun dace ka bashishawara
koko shine ya sameka da zancen?Yace, a a dazu
ya zo mun da zancen sai kuma naga dacewar
haka.Ta ce, to ka koma ka fada mashi ban
amince ba, kace mashi ya nemo matarshi can
itama ta nemo nata mijin.Jikin Sulaiman yayi
sanyi ya sake tausasa murya ya ce, iya ban san
dalilinki ba, kokuma akwai abinda kika hango
wanda ba na Alkairi ba?Ta ce, na farko dai kasan
halin gadanga, zuciya ce dashi ga saurin fushi, ga
miskilanci tsiya, ga shegen jin kai.Sanan na sha ji
ko in ce ya sha fada min cewa shi yar jami'a yake
son aura.Niko tawa ko secondary din bata gama
ba.Sulaiman ya ce, iya in kin duba tunda shi din
ya ce ta mashi ai ina ganin ba za a sami wata
matsala ba.Fir iya ta ki zancen, duk ta inda
sulaiman ya bullo sai iya tabi ta wata hanyar,
haka nan yaya sulaiman ya hakura ya fita rai
babu dadi.Aliyu ya sunkuyar da kai yana
sauraron sakonshi a gurin yaya sulaiman, sam bai
zaci jin haka ba, amma sai ya ce, ba komai Allah
yasa haka shine mafi alkairi, na shi ganin ba zai
damu ba, tunda dama ba wai yana sonta
bane.Sai dai kuma yanda ya tsammaci abun yafi
haka, samun kanshi yayi da shiga damuwa, ko ba
ya son yarinyar hakika ya tsananta dason
aurenta.Ya samu iya da kan shi wata safiya yaxo
gaida ta bayan yayi shirin fita cikin dakin sa.Ya
ce, iya me yasa ba zaki bani auren sadiyaba? Ta
lissafo mashi dalilinta kamar yanda ta lissafawa
yaya Sulaiman takuma fada masayaje ya nemo
mata can.Ranshi ya baci amma bai nuna ba, sai
dai cikin sanyin murya ya ce, to shikenan iya na
hakura, amma ba zan taba xuwa ko ina neman
aure ba saboda ina da munmunan halayen da
ban can canta a bani mataba,tace, ni ban ce
ba,ya ce to iya tunda ba a bani a gida ba in naje
nema a wani gida suka bani na cutar dasu tunda
ba su san hali na ba,yana kai aya ya mike tare
da cewa, sai na dawo.Ita kuma lafuzan nashi
suka hanata magana.Ita zahiri ba wai bata son
auren ya Aliyu da sadiya bane, na farko ta san
halinsa, sanan tana tsoron ta tursasa min.Kullun
Aliyu sai yayiwa iya naci amma taki ko ta ga zai
dauko zancen sai ta hade fuska.Wata safiya ina
kwance kangado ina fama da matsananciyar
ciwon mara, dama mun rabu da yin waina tunda
iya tayi rashin lafiya.Ya Aliyu ya ce, a daina yin
wainar duk wata nake wanan ciwon marar.Yaya
Aliyu ne ya shigo gaida iya, bayan sun gaisa ta
ce, har ka shirya fita kenan?Ya ce mata eh, akwai
wani case a hannunsane yana son ya kammala
dashi kafin fitowar(AC) ta ce, to Allah ya taimaka,
a can zaka karya?Ya ce, eh.Sanan yayi shiru ta
ce, da magana ne?Ta sani in har yayi haka to da
magana a bakin sa, ko da yake ta san zancen na
sa daya ne, bai wuce na sadiya ba.Kuma tana
son Sadiyar ta ji ma kunnenta in ta amince
ruwanta don haka ta ce yaya autana?Yace iya dai
maganar Sadiya, Allah iya ba maganar yabon kai
ba, ina da kamalar da za'a bani mata, ya ko ta
gidan waye 'yar taki ai ba kyau tafini ba,ya fada
cikin sigar wasa, ta ce,duk da haka ba zan baka
ba, kai ita fa tarigata fidda mijinta.Yace dan Allah
iya ki fada mata kinji?Ta ce, au, nice ma zan fada
mata?Lallai ba ma son auran nata kake ba.Ya ce,
ni iya in na fada mata sai naga tamkar zata
rainani ne.Iya ta ce, kun ji girman kan ba?Don
Allah kayi hakuri nifa ka tayar dani,ba zan yarda
ba.Aliyu da ya gaji ya fita.Tun daga lokacin da
naji ya Aliyu ya ambaci sunana na mike zumbur
hankalina atashe,ni Sadiya yaya Aliyu yake nufi
ko wata?Kai in ko nice na more, dan gaskiya yaya
ba irin mijin da zance bana so bane, tab!Wanan
shine tsintar dami akala.A a iya kada kyi min
bakin ciki, ina jin fitarshina fito da sauri ina
kallon iya, ko zata ce wani abu, amma sai ta
shareni, na ta nufintadaga yanda na dauki
al'amarin tunda ta tabbatar naji.Ko daga irin
fitowar da nayi, ganin iya ba zatayi magana ba
sai na ce iya ta dubeni, wai ya Aliyu wa yake so?
Ta tabe baki dan Allah rabu da shi, wai ke, na
dafa kirji da karfi na furta da gaske?Ta ce, zan
maki karya ne?Na ce to iya shine zaki ce mashi
ina da wanda nake so?tace, au.Sharri nayi maki
kenan?Ina ce ke naji kina cewa kin tsaida Idris?
Na ce, ai ban fada mashi ba.Ta ce, meye nufinki
yanzu?Kina so ki ce min kina son Gadanga?Nayi
shiru tare da hade fuska, mamaki ya cikata, ta
ce, Sadiya dama can kina son Gadangan ne?Na
ce, nifa ban ce ina sonshi ba, amma ke meye
dalilin da kika ca baki yarda ba?Iya ta shiga tafa
hannu tana salati.Kin tirke nine lallai sai kinji?To
ba wani dalili bane sai na kare mutuncinki,
gadanga yana da zuciya, gadanga yana da fushi,
sanan ga miskilanci,ina tsoron ki shiga matsala,
gaki karamar yarinya, shi kuma shekaru sun dan
soma ja.Da sauri na ce iya in dai dan wanan ne
na yarda kinji?Ta ce, wai me ya burgekine a dan
sanda duk jikinki ya hau bari?
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Na ce, to iya gaskiya ya Aliyu ba irin mutumin da
za a ce ba a so bane .Ta ce, ni dai na ce a a ban
yarda ba.Na mike cikin fushi na fita tsakar gida,
da kallo iya ta bini, matuka ta ji mamaki
musanman ta sanni bani da rawar kai.Ni kuma
kicin na shiga na zauna banyi aune ba sai kurum
naga hawaye suna zuba a ido na, ni kaina har
naji mamakin kaina.To da bai ce yana sona ba
fa?Ranar haka na yini har dare, kusan mutum
uku suka aiko kirana naki fita, iya duk tana lura
dani tana kallona ranar bai dawo gida ba sai sha
biyun dare, sanan tunda a subahi ya fita.Yau
sam na kasa sukuni, iya sai kallona takeyi tana
salla, can bayan ta idar ta ce sadiya!Nayi shiru, ta
ce, nasan kina jina ta shi kawaiki tashi, na tashi
zaune ta ce, sadiya ina ganin baki gane nufina ba
game da zancenkike da gadanga shi yasa har kike
fushi dani.Gadanga bahogon mutum ne, ni na
haifeshi na sanshi tun yana dan karamin shi,
gadanga bashi da dadin lamari, amma in kinji
Allah ya baki sa'a.Sai dai ina so ki sani in da
wanda zaiyi farin cikin aurenki da gadanga to ya
biyo baya na,sai dai duk da haka ba zan kasa
fada maki gaskiya ba.Shawarar da zan baki kuma
ki rage rawar kai in ya fahimci kina doki kimarki
ta zube.A zaton iya zan hakura amma sai taji na
ce, in sha Allahu ba zan sami matsala ba.Ta tsura
mini ido haka kika ce?
Nayi shiru ta ce shi kenan, to da sharadi ba zuwa
kawo kara.Da sauri na ce, to,da kallo tayi ta bina
ni dai na tashi na koma makwancina ina
murna.Na zaci da safe zata neme shi ne ta fada
mashi ayi sai kurum ta share, ko da dai ya fita
da wuri, wasa wasa sam taki zancen inaji lokaci
da yawa da ya dauko zancen zata ce don Allah ya
rabu da ita.Sai dai abinda ke bani mamaki,
kullum yanda yaya Aliyu bai can za min yanda
yakemin ba , amma nakanyi uziri cewa kila sai
iya ta amince sanan za mu soma yin tadi.Cikin
haka ne har aka dauki tsawon lokaci muka shiga
shirin zana jarabawa (SSCE) duk na kori samari na
babu wani mai zuwa tunda na fada musu na
tsaida miji.Shikam ya Aliyu bai san na sani ba,
kullum ya zo gurin iya sai yayi mata nacin shi fa
yana nan yana jira ita kuma takan ce mishi kar
ya dame ta, ba ya ce ya fi son yar jami'a ba?Ya
je ya nema.Ni kuma in ya tafi wani sa'in in ce iya
don Allah ba kince kin hakura ba, tunda na
yarda?Sai ta ce min sakarya, dubi fa ko kallo baki
isheshi ba, amma duk kin tsamgwami kanki don
fitina, ni dan kare mutuncinki nake kin abin nan.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Usman abokinsa yaji shiru batun maganar Aliyu
da sadiya, sai ya zo gurinshi musanman don
zancen , dama ya kirashi a waya yaji cewa yana
nan.Bayan sun gaisa usman ya ce, aboki wai
haryanxu ban sake jin batunka da yarinyar nan
sadiya ba, in mun hadu baka yimin zancen ba, ni
kuma ban tambaye ka ba.Aliyu ya gyara zama
yayi sanan ya lumshe ido don haushi ya ce,
kabari kawai abokina, haushin maganar nake ji,
shiyasa ban taba yi maka zance ba.Ya miko
hannu ya dafa gyiwar usman abokina ban taba
samun abinda ya bani matsala ba kamar
maganar yarinyar, ni abin haushi duk lokacin da
nayi kudirin hakura dazancen sai na kasa.Kullum
adu'a ta Allah ya yaye min ita daga raina, amma
abin ya faskara.Ko son yarinyar ne ya kamani?
Usman yayi murmushi lallai sonta kake yi, Allah
yasa ita ma ta soka hakan.Aliyu yace ina ruwana
da ita?Iyace kurum damuwata, in da ta amince
shi kenan, amma baiwar Allah nan wai zan cuci
yarinyar ita ba zata bani yarinya karama
ba.Ranar harda cewa na tsufa.Usman yace zanje
in sameta aboki, kada kadamu.Aliyu ya ce, ko
kaje matarnan ba zata yarda ba, na dai fada
mata ni na hakura da yin auren.
.Usman yayi ta dariya tare da zolayar Aliyu da
cewa, aboki ka dai shiga da yawa, to da ka ajiye
duk wani girman kai ka dinga kiran yarinya hira
in taga haka zata fi yarda cewa da gaske kake
yi.Aliyu ya ce ka yarda ni ba zan taba iya kiran
yarinyar ba, ko ba Sadiya ba, kuma sanin kanka
ne ban taba ba, so bansan ta ina zan fara ba.Ba
ta ita fa nake ba, in iya ta yarda tayi hakuri ta
aureni dan da cewa auren sai kuma ya ja tsaki
kada ma ta hakura.Tama ji dadin zancen ta samu
miji irina, Usman ya ce, yabon kai?Aliyu yayi
dariya aboki ka fadi gaskiya, ni da ita wa yafi
kyau?Bai jira amsa ba ya ci gaba na farko dai
kaga ita fari ne kurum ya ceceta..... Usman ya
katsishi au, wai dama haryanzu akwai
mummuna?Ni dai yanzu na daina ganin
mummunaai tunda naga alamun kai ya waye, ba
a zama da kazanta, Aliyu ya ce, haka ne, amma
wani wan wani ne a kyau.Usman ya ce, duk da
ka fi ta kyau dai ita zuciyarka ta zaba, zanyi
maka kokari, zanje in samu iya.Aliyu yace tunda
ka dage jeka din, duk yanda kukayi zamuji.
Kamar yanda Usman ya alkawarta yazo ya samu
iya wajen la'asar ina yi mana tuwo, itakuma tana
zaune a kofar dakinta.Na gaida shi sannan na
dauko masa tabarma ya zauna, na kawo masa
ruwa sanan naje na ci gaba da aiki na.Daga inda
nike ina jiyosu suka gaisa sanan ya fara yi mata
zancen da ya kawoshi.Iya dama akan batun
abokina ne da yar uwarsa sadiya, iya dukkan su
naki ne, a ganina wanan abin farinciki ne.Iya ta
tsuke fuska,Usman ina ganin kimarka, zaifi kyau
ka bar zancen nan bana jin cewa zan
amince.Usman yayi shiru yana tunanin yanda zai
bullo mata.Can ya ce, to shi kenan, amma na so
ki amince domin yana cikin wani hali na son
yarinyar nan, nasan halinshi kin san halinshi,baya
daga cikin mutane ma su magana biyu.Yayi mun
rantsuwar ba zai taba aure ba in ba Sadiya ba,
duk duniya ita yake so.Zaman shi haka nasan
yana damunki.Ta ce in duk duniya Sadiya yake so
ita Sadiyar ya tambayeta ta ce tana sonshi? Nifa
ba zanyiwa yata auren dole ba, don in faranta
masa.Daga inda nake a kicin na da ga hannu ko
nace ya tsa tamkar mai bada amsa a cikin
ajinmakaranta, sanan na kwalawa iya kira!!Ta
kalleni tare da yi mun da kuwa, shi dai baisan
dalilin dakuwar ba, tunda ya bani baya, ita kila
ya zaci laifin nayi mata.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Usman ya fahimci nufin iya, shi yasa ya ce mata
Aliyu ya dinga kiran yarinyar suna fira.Ya dubi
iya, to in sha Allahu za mu tuntubi yarinyar, idan
bata amince ba shike nan.Yana fita ya dauko
waya ya kira Aliyu, bugu uku ya dauka. Usman ya
ce, Aboki da farko fara bani goron albishir.Cikin
sauri Aliyu ya ce kada dai ka ce mun
tasaurareka? Usman ya ce, in sha Allahu munyi
nasara Aliyu ya ce shi kenan sai na xo aboki,
gidanka zan sauka kaitsaye daga office yanxu ina
kan wani aiki.Suna cin abinci a falonsu Usman
yana koro mashi bayani duk yanda sukayi a
karshe yace yanzu kaga tana nufin ta yarda sai
dai amma tana so ka kira yarinyar ka nemi
amincewar ta.Aliyu ya tsirawa Usman ido, sanan
ya ce, ai wanan shine mai wahalar, gaskiya a boki
ba zan iya kiranta ba.Usman ya ce, tsoronta kake
jine?Raini ne bana so, yanxu dai kai kaje ka
sameta kuyi magana.Usman ya ce, nima ke nan
zan yi maka yakin neman sonta?Aliyu ya ce, duk
yanda ka ce amma ni in na kira tafa ba ra'ayinta
zanjira ba, umurni xan bata.Usman ya ce, shi
kenan ka bari xanje.Bayan sallar isha'i muna
zaune ni da iya muna cin abinci tare kamar
yanda muka saba, yaya usman yayi sallama shi
da matarshi Anty Abida da yaran shi guda
biyu,tsam na mike daga cin tuwon ina yi musu
sannu da zuwa, suka zauna na kawo musu abinci
da ruwa, sukace yanxu suka tashi daga kan cin
abinci.Na koma tsakar gida bayan na dauki
yarinya wato Ummulkhairi, yarinyar tana da wayo
yar mai kyau taji kitso, na ce Ummulkhairi kina
makaranta? ta ce eh mana, kuma Abban mu yake
kaini har ma da Abulkhairi, nace, iye, to koya
mun karatu.Ta ce, na islamiya ko na boko?Na ce,
a a islamiya dai.Ta gyara zamanta a cinyata ta ce,
in miki sunayen Allah kyawawa?Na ce, eh,ta fara
kenan babanta ya fito, ya kallemu karatu kuke yi?
Na ce, eh, tana koya mun ne.Yayi dan murmushi
ya ce ummu jeki wajen umman ki, ki ce mata ta
jira ni ina zuwa.Ta na shiga daki ya ce, kanwata
zo mana.Na mike na bishi zuwa kofar gida,
nasake gaisheshi nayi , bayan mun tsaya ya
ce,Sadiya nasan ba zakiji mamakin kiran da nayi
maki ba ko?Na ce ba wani mamaki, kila zaka
aikeni ne.
Yyace bahakabane na kiraki ne dan in sanardake
wani abun alkairi, ko da yake ban san yanda zaki
amshi abun ba.Na gane zan cen ya Aliyu, ya
duba duk cikin matan da ke garin nan yaga babu
wadda tayi masa sai ke, tamkar bai san zancen
ba na furta da karfi so!!!Usman ya ce ba wani
abun mamaki bane, dami ne kika tsinta a kala.A
raina na ce lallai ma yaya usman din nan, to bari
in latsa shi.Na ce, ya Usman ka ce masa yayi
hakuri kawai dan na riga na tsaida mijin aure
wanda nike so.Ya Usman ya ce, kin kai shi gida
ne?Na ce, gobe ne iyayan sa zasu shigo gidan
mu.Usman ya ce, in har zan baki shawara ki
yarda zan so ki dakatar da su domin kowa zaki
aura na tabbata bai kai Aliyu ba, samunsa sai an
tona, ko na ce irinsa.In kika sameshi a matsayin
miji tabbas zakiyi alfahari samun muji kamarshi,
mata da yawa suna sonsa, kila sun fahimci
nagartarsa, amma ba matsi in baki sonshi zan
koma in fada masa cewa baki sonshi da aure.Na
kalleshi bance bana sonshi ba, saboda duk
abinda iya ta haifa dole ne in soshi, kai ko wani
ne can ba danta ba in dai ya mutunta ta to zan
soshi bare dan cikinta, na riga na zabi wani
ne.Usman yayi shiru, ya zaci da yayi mun
magana zan amsa da murna, can ya ce, to yanxu
mai zanje in ce masa?
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Na ce, ka fada masa zanyi tunani zuwa gobe. Ya
ce, shi kenan, zan kiraki amma kiyi shawara da
kawarki wadda ta sanshi, na san zata fada maki
qualitie din Aliyu. Na ce, ba damuwa. Ya ce, shi
kenan gobe zanzo naji. In kin shiga kicewa Abida
su fito mu tafi daman na sallami iya. Na ce, to.
Bayan tafiyar su iya tashiga yi mun fada wai ai
gashi nan saboda bai daukeni da muhimmanci ba
abokinsa ya turo min, ta san jikina yana bari na
ce na yarda. Na vata fuska tamkar zan saki kuka
na ce, ni fa iya banyi fa rawar jiki ba, ce masa
kawai nayi zanyi shawara zuwa gobe. Ta ce, ato
in kin kimanta kanki yaga darajarki in kuma kinki
ni dai na fada maki babu zuwa a kawo mun kara.
A waya Aliyu yaji duk yanda mukayi, mamaki ya
dinga yi wai wanan yarinyar ce zata ce sai tayi
shawara, dawa zata yi? Kuma ita ce wa? Usman
ya ce ita ce mace. Aliyu ya ce, shi yasa kaga ba
zan iya kai kaina ba ga wata ya in ce ina son ta
ba, bare tayi mun yauki, nidan oya-oya ne.
Usman ya ce ka barni da itakawai na san jan
ajine zamuyi nasara cikin jin haushi Aliyu ya ce,
in taki ka kyaleta kawai, yarinya sai kace wata ta
gold sai ga ruwa nake yi a kanta. Ya ja tsaki nan
ya kashe wayar ba tare da ya sake jin mai
Usman zai ce ba. Kwana Aliyu yayi da zullumin
halin da zai tsinci kanshi, in yarinya taki
amincewa da shi. Da safe ina shara ya fito daga
dakinsa ban san me ke sani faduwar gaba a duk
lokacin da na ganshi ba.Na gaida shi ya amsa
cikin isa, kuma a ta kaice kamar yanda ya saba.
Sanan bai ko kalleni ba sai dai nice na bishi da
kallo. Namiji ne sosai ko tafiyarshi ta shaida
haka, daga ganinshi baka ga rago ba, dama abin
da ya dace dashi kenan jami'in dan sanda. Iya
daga daki ashe tana kallona ta ce, in kin gama
kallonshi sai ki ci gaba da sharar ko? Cikin kunya
da shauki na ci gaba da sharata. Da rana naje
gidansu Aisha kawata nake bata labari duk yanda
muke ciki, tace, tabbas! Sadiya idan zan fada
maki gaskiya ki amince kawai, kada ma ki tsaya
wani jan aji,sau nawa nake fada maki Aliyunku
unique ne?Allah in kika yi sake kin tsaya yauki
kya zo kina na dama, kin san shi da zuciya ya ce
yafasa.Kash!Ina ma nice ya ce yana so?Jin haka
yasa na kagu dare yayi.Har na debe tsammanin
xuwansa dan tara ta kusa, duk na tsure kar dai
ya Aliyu ya hakura da gaske.Can sai na tsinkayi
muryar wani yaro yana sallama ni ina cikin daki a
kwance kan kujera.Iya ce ta amsa salamar don
tana tsakar gidan, ya ce an ce sadiya ta zo inji
wani a waje.Ka fin ya rufe baki na mike, zaraf na
suri mayafi na fita.Iya ta ce, kai jama'a!Kai
jama'a!!Ni wanan yarinya ko dai zaki kai kanki
ne?Na ce ban fa san ko wane ne ba, ma ai
iya.Cikin gatse iya ta ce, ina zaki sani, shiyasa
kike ta sintiri tun daxu kin kosa ko wanene maya
zo?Na ce, sai na dawo.Ta ce, kada ma ki dawo ki
kwana can.Usman yana tseye a gurin da muka
tsaya jiya, na sameshi da sallama, muka gaisa ya
ce to kanwata nazo jin me kika yanke?Na danyi
shiru kamar mai nazari, ya ce, kada ki damu in
har baki sonshi ya ce babu komai.Na ce, ai ba
zan iya cewa bana sonshi ba ko dan iya, don
haka ka ce masa na amince.Usman ya ce,
Alhamdulillah, sai kin ji mu.Ranar nayi farinciki
har nafila nayi don godiya ga Allah, iya ta ce yau
kuma ibadar ce ta motsa har da nafilar dare?Ni
dai ban tanka mata ba, ta ci gaba, Allah ya sa a
dore, ina ta samun gadanga ce akayina san daga
yau shi kenan.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Washe gari yaje ya samu yaya zakari da yaya
Sulaiman yayi musu bayani, su kuma suka sami
dan uwan mahaifinsu dake nan layin kasuwa, a
nan unguwar mu'azu.Nan dai suka sa ranar zuwa
zariya gurin mahaifina don jin zance, Aliyu da
zasu tafi ya bada dubu hamsin ya ce har sadaki
duk yanda ta kaya shi kenan.Mahaifina yayi
murna har yana cewa wannan abu ai da ba sai
anxo ba, ita iya Sadiya tata ce, Aliyu ma nata ne,
da ba shi kenan ba sai dai muzo a yan
gayyata.Kawu ya ce, a a kun wuce haka, kuma
dole abaku hakkinku.Baba yayi ta godiya kafin
daga bisani ya ce bari ya kira dan uwansa.Sun
yanke sadaki dubu talatin sanan aka basu na
gaisuwa goma, sai dai suna dawowa suka fadawa
iya duk yanda akayi.Iya ta ce sam yarta tafi
talatin, su kawo goman nan hamsin ne sadakin
yarta, sanan gadanga ya ciko goma kudin
gaisuwa.Da kyar suka shawo kanta ta amshi
goman, sadaki arba'in kenan.Aliyu dai yana
zaune yana jin su yana kallonsu amma bai ce ko
mai ba.Suka ce an tsaida rana watan tara sha
biyar da shi, lokacin kuma ana watan shida.Aliyu
ya ce yaya Sulaiman lokacin nan bai yi tsawo ba
kuwa?Anawa ra'ayin nafi son wata biyu, iya ta ce,
har ka gama shiri ne zaka ce wata uku yayi maka
kadan?Aliyu ya ce, wane shiri ne mai zafi?Ba lefe
bane ko meye ne kuke cewa ya rage ba?Ta ce,
kana da gurin zama kenan ko nan zaka gyara mu
zauna?Ya ce, a haba dai, zan nemi gurin zama
duk a cikin wanan lokacin.Ta kalli Sulaiman ni fa
in nayi auran nan zataci gaba da karatunta ku
shaida wanan, in ya ce a a za a jimu.Aliyu ya ce,
na sani iya, nima ina son ta ci gaba da
karatun.Ta ce, to batun aure a barshi wata ukun,
sai kaga lokacin ya zama ba ka kammala da wani
abun ba har kake raina lokacin.Ya ce Allah ya
kaimu.Ina zaune cikin ajinmu bayan mun gama
zana paper din mu ta karshe, ina kallon yanda
yaran ajinmu suke ta jin dadi da murna tun da
muka baro hall din.Ta gumi na zabga ina
mamakin irin halin ya Aliyu, yau kusan sati hudu
da sa muna rana amma ko sau daya bai taba
kirana ba, haka nan kuma ko cikin gida ya shigo
ban isheshi kallo ba.Nima fa yanxu na soma
sarewa, anya kuwa mutumin nan yana sona?
Kullum iya sai tayi min gori, yau kam zanje in
nemi ya Usman.Bayan nan na cewa Anty Abida in
yadawo tace ya zo, ina son magana da shi, ta ce
to zata fada masa na ce ina su Ummulkhairi?Ta
ce suna makaranta.Da daddare kuwa sai gashi
ana sallama dani, na mike har ina tum tube.Iya
ta ce, sai karaftu kike sai kace a dakin Ajantina,
na san dai ba wanda kike son gani bane, dan
nasan shi ya fi karfin ya kiraki.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Nace, iya to ai ina so ne na ga ko wanene.Ta ce,
oho ke dai kika sani.Ina fita yaya Usman ne
kamar yanda nayi tsamani bayan mun gaisa ya
ce, Abida ta ce kin zo nema na.Na ce, eh.Na
sunkuyar da kaina ina wasa da yatsuna, na ce
dama nazo ne a kan maganar mu ne da ya Aliyu,
in abin ba zai yuwu ba gara mu hakura tun
yanzu.Ya gyara tsayuwa wani abu ne ya faru?Na
ce to ya Usman a haka ne za mu fahimci juna in
san abinda baya so yasan abinda bana so?Na ci
ga ba, bai taba kirana da sunan muyi zance dashi
ba, ko gida ya shigo ban ko isheshi kallo ba, shi
bashi da wani lokaci ne sai na aikin shi?Usman
yace ba wai zan goyi bayan shi bane amma
ninasan kina ranshi,ki fahimce shi, shi mutum ne
mai kishin kasarsa da aikin sa, shi yasa baya
samun lokacin kansa.Amma da zarar kin zama a
gidansa na san dole ya baki dukan lokacinki.Nayi
shiru kamar maganar ta shigeni, ammada na
tuna ko kallo na bayayi na ce, yaya Usman ka
san Allah ba dan aikin shi bane, ko kallo fa ban
isheshi ba.Usman ya ce, to bari zanyi mashi
magana.Na ce, don Allah kada ka ce nayi maka
magana, kada yayi tsammanin na damu da shi
ne.Usman ya ce, zanyi masa maga na da ma ai,
ba zan ce kece kika sani ba.Kusan sha dayan
dare Usman ya daga wayar Aliyu tare da yin
sallama, bayan sun gaisa Usman ya ce aboki
dazun ina ta kira baka daga ba.Aliyu ya ce, bari
kawai aboki, lokacin ina tsakiyar wani case ne
abin nan yana matukar daga hankalina tare da
bani mamaki.Ka san wani mutum dan kimanin
shekara arba'in aka kama yayi wa yar shekara
hudu fyade.Usman ya zabga salati tare da cewa,
wai aboki wanan wace irin masifa ce?Ko dai wani
tsafi ne?Aliyu ya ce, wa ya sani?Wannan fyaden
na kananan yara yayi yawa.Kullum sai mun sami
wanan case din wlh yanda abin nan ke mun zafi
a raina zan iya kashe irin wadannan mutanen,
don mugaye ne.Idan mata ne su je mana ga
karuwai nan,Usman ya ce, to Allah ya shirye su,
ya tsare mana daukacin musulmi.Aliyu ya ce,
amin aboki to kaji halin da nake ciki, lokacin da
ka kirani lafiya lau dai ko?Lafiya lau dama zance
ne ya kamata mu shirya muje muyi hira da
yarinyar nan ko?Aliyu ya ce, wace yarinya ke
nan?Usman ya ce, sai karinka yi kamar baka san
da zancen ba bayan nasan tana ranka.Aliyu ya
ce, tsakani da Allah sai ka tuna min.Usman ya ce,
ok, tunda yanxu iya ta yarda dole ka manta.Aliyu
ya ce subuhanalla? Dama wai Sadiya kake
magana?To wacce hira kuma zamuyi tun da na
rigaya an gama magana, sai jiran lokaci.Usman ya
ce, ai duk da haka za aje ayi hira ta san abinda
baka so don a samu zaman lafiya.Aliyu yayi yar
dariya.To ni ba haka tsarina ya ke ba, ina zaton
in har zanje gurin budurwa zan jene don ina
tallata kaina in in samu shiga,tonina riga na
samu shiga babu dalilin da zan matsawa
kaina.Usman ya ja tsaki kai dai bahago ne wlh, to
sai ka sai mata waya ko ta waya kunyi
magana.Aliyu ya ce, to yan zu dai kaine sarkin
yakinta ko?Suka sa dariya.Usman ya ce, da gaske
nikeyi, akwai wata waya da ake saidawa mai kyau
nan kusa daoffice din mu (MTN OFFICE) ya ke
aiki.Aliyu ya ce, ka suyo mata in kazo sai na baka
kudin, sanan kai zaka bata don har karshen satin
nan ban san lokacin dawowata, kafin ita ta tashi
na fita.Usman ya ce shi kenan.Washegari da
daddare ya usman yazo ya kawo mun waya wai
iji yaya Aliyu, inyi hakuriza mu rinka waya aikine
yayi masa yawa.Bani da zabi dole na hakura
tunda ga waya har da layin (MTN) ko da na nuwa
wa iya baki ta tabe sanan ta ce Allah ya sa
alheri.Tun da na karbi wayar ko flashing ba a
taba yi mun ba, ga dai lambarshi a ciki ya usman
ya samun duk da cewa har da kudi a layin nawa
nima cewa nayi ba zan kira shi ba.Sai dai in ta
kiran kawaye da yan uwa wadanda nake da
number su.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Wata rana da dadare naji Iya tana yi masa fada
cewa yana zaton haka za ayi auren ba lefe, biki
saura wata daya da kwanaki, amma ba a ga yana
motsi ba.Ya ce, abin ne ya shige masa, amma
gobe zai je ya sami matar ya sulaiman.Ita da
matar Usman Anty Abida sukai ta zaryar zuwa
kasuwa, saura sati biyu lefe ya kammala da dinki
da komai.Iya ta ce ya Aliyu ya bada kudin mota a
kaisu zariya, ni kuma nan kawaye na sun matsa
da batun anko, lokaci yana tafiya gashi ba zan iya
yi mashi magana ba.Aisha ta ce, kiyi wa iya
magana.Na ce, iya kwana biyu bata sana'a , bata
da kudin anko?Tab! Ba zai yuwu ba.Wayata na
dauka inyi kamar zan kira shi in fasa, Aisha ta
amsa na ce kada ki kira shi dan bai taba kira na
ba, ba wani kiranshi da nima zanyi Allah aisha ni
auren nan tuni ya fitan min daga rai.Ace kai kafi
karfin kazo sai dai abokinka?Aisha ta ce, Allah sai
na rubuta masa tex.Ina kallonta ta rubuta
masa.SALAM.INA FATAN KANA LAFIYA?KAYI
HAKURI KILA YANXU KANA CIKIN AIKI NA TSAIDA
KA, DA MA NAYI MAKA WANAN MESSAGE DIN NE
DON NA TAMBAYEKA A KAN MAGANAR ANKO,
DONKAWAYENA SUN DAMU SABODA LOKACI YANA
KAREWA.NA GODE, KA HUTA LAFIYA.Tana gama
rubutawa ta tura masa, maji amsa-maji amsa
shiru, nace kin gani ko?Ke ayi biki haka bani kara
masa batun anko.Aisha ta ce, niko yanda yake
nashi salon birge ni yake, na ce, au!Wulakancin
da yake min din ne yake burgeki?Tayi dariya, ai
ba wulakanci bane rayuwar sa ce haka.
Lokacin yana office din commissiner ya je a kan
nemansa da yayi tsam ya kame kamar yanda
yake al'adar yan sanda, sanan ya soma magana
cikin natsuwa ranka ya dade an ce kana nema
na.Commissioner ya dube shi cikin natsuwa
sanan ya ce da ma na kira ka ne a kan maganar
barawon shanu din nan da aka ce kaki yarda a
bada belinshi.Aliyu ya sunkuyar da kai don
girmamawa, yace ranka ya dade haka ne, naki
bada belinshine saboda bincike ya nuna shi din
ba karamin mai laifi bane.Daji suke shiga da
motoci suna kora shanayen fulani suna kwashewa
su kai kudu su saida, wanan kamawar ita ce ta
goma sha uku amma ba a taba mikashi kotu ba,
azzalumine na gaske,Commisioner yayi dan
murmushi sannan yazo ya dafa kafadar Aliyu ya
bubbuga alamun jinjina, san nan ya ce, Dan
Sanda mai kishi, lallai kasan aikin ka da ka tsaya
binciko wannan files din, ka tattarosu ka miko
min nan, ni nasan yanda zan kawo karshen
lamarinsa.Zan shigo gurinku anjima kaje.Aliyu ya
sara masa, sanan ya fito.Gaskiya in son samu ne
case din nan ya tsaya a hannunsa dan kam zaiyi
gogaiya da zalunci.Shigarshi office din sa kenan
sako ya shigo wayarsa, sai da ya zauna sanan ya
duba.Murmushi yayi bayan ya karanta, a fili
kumaya ce, ko me nene anko?(hahaha,kunjifa
dan rainin hankali inji,shin kuna ganin zai yuwu
ace baisan Ankoba,ai dai kayan yansanama
Ankone,kuma kala biyu, wasu su sa baki
kawai,wasu kuma baki da light blue ko? Cewar
ANaM Dorayi)
Ya kira layin Usman bayan sun gaisa ya tambaye
shi ko menene Anko? Usman yayi murmushi wato
kai dai in kaje ka shige caji ofis dinku shi ke nan
baka tuna meye a cikin garin.Aliyu ya ce, aboki
mu kuwa dake wanan ofishin mu muke da
labarin abunda ke cikin garin, amma ba wanda
ya shafi biki ba.Usman ya ce zaka bata kudi ne
kurum ta shiga kasuwa da kawayenta su zabo,
haka su ke yi.Aliyu ya ce, gashi ni kuma bana son
yawo bare kuma xuwa kasuwa, in dai zani ne in
zan je gidan zan tsaya nan wani super market in
sayan masu, guda nawa ake siya?Usman ya ce,
da ka basu kudin.Aliyu ya ce, ba zata kasuwa ba,
wanan shine ra'ayi na, zan siyo musu zani.Usman
ya ce shi kenan, sai ka suyo musu mai kyau.Aliyu
ya ce ina ruwa na da zabe, ni dai kawai in dau
zani.Don haushi Usman ko sallama babu ya
kashe wayar.Aliyu ko da wuri ya bar office din ya
bi ta kasuwa ya sai zaunnuwa kala uku ko
wanneguda bibbiyu ya nufi gida.Iya tana zaune
tana yankan kubewa ni kuma ina daga kicin ina
kwashe tuwo ina mulmulawa a leda ina sakawa a
kula ya Aliyu ya shigo da sallama.
Kusan kwana hudu ban sashi a ido na ba , da ya
zauna yana gaisheta.Ta amsa ya ce, ga zaunnuwa
anko ne suka ce ko menene ma?Ta dauki ledar
tana cirowa ta re da fadin kaine ka siyo ankon
gadanda da kanka?Ya ce, to duk ba zani bane,
shi nan sai su zaba.Ina kallo daga ciki kuma ina
jin su, tun kafin in fito zaunuwan suka tafi
dani.Ya ce, naki ne da nata.Iya ta ce, to mun
gode, da ma ina so inyi maka zancen gidan ne, a
ina kasamu?Ya ce, to ni dai nafi so a can kasan
layinku, gefen makabarta din nan, to ba a samu
ba sai na dawo neman na siyarwa, kudina
dakekasa yanxu za su iya semin gida, amma
albashin wanan watan da na wancan watan hada
mana za ayi.To ganin kurewar lokacin sai kurum
na barshi yanxun anjima zamuje mu ga wani gida
da yaya Sani da Usman wai ciki da falo sai kichin
da ban daki dubu dari da hamsin.Iya tayi shiru
tana nazari, can ta ce ina nufin kasan gidan su
babba ne?Ya ce ciki uku ne da kicin da ban daki
sanan ga filin da mutum zai iya fakin din mota
har biyu.Iya ta ce kuma nawa?Da sauri ya ce wai
miliyan daya da dari takwas.Ta ce, ina ganin zaifi
ka siya gidan in yaso sai a daga bikin.Ya dubi iya,
ai saboda bana son dagawar shiyasa na hakura
da siyan gidan.Iya ta ce siyan xai fi maka sauki
ka huta da biyan haya, auran kurum za a daga
ba.Ya ce ba dagawa za'ayi ba, abinda ya sa in an
daga za ayi asara da yawa.Abokaina sun kashe
kudi gurin kati mai tsada tare da wasu abubuwan
abokan aikina suma sun kashe kudi gurin shirya
bukin.Iya ta ce to, kana ji ko, yanda za ayi kawai
a daura auren da buki, sai ta zauna gida kafin a
gama gyara tunda dai nan a gida ne ba a dawa
ba, bana so ka rasa gidan nan ne muhalli a bariki
ba karamin rufin asari bane
Aliyu ya ce, shi ke nan sai ayi haka din bari zan
kira yaya Sani sai muje dake ki ga gidan sai a
biya.Lumshe ido nayi cikin jin dadin an fasa daga
bikin, kai naso in tare a gida na ranar amma baji,
buri na dai a daura auren, amma da iya ta so
kwafsawa wai a daga.Ya mike ya juya da nufin
fita ida nunsa sukasauka a kichin a inda nake, da
sauri na ce ina yini?Sai da ya dauke kai sanan ya
ce, lafiya.Har ya fita ina kallonshi.Iya ta katse ni
da cewa, wata rana sai kin gaji da kallon shi.Na
sunkuyar da kai kunya ta rufe ni, ban santana
kallona ba sa karya, in dai gadanga ne gaki ga shi
nan.
Pink din muka zaba ni da Aisha, sai dai muna
zuwa kasuwa aka ce dubu uku ce gashi kudin
aisha bai kai ba.Sai muka dawo gida da kyar
mamanta ta cika mata muka koma muka
siyo.Muka roki mai shagon ya ajiye mana da mu
siya da yawa.Yamma tai mana a kasuwa gashi
ana wahalar mota.Muna tsaye a kan titin kano
Road, na ce bana son magariba tayi mana tun
daya muka fito gashi iya ba ta san mun koma
unguwar mu'azu mun dawo kasuwa ba.Aisha ta
ce, sai dai muje mushiga dambancen ko za mu
samu, na ce zamuje.Ta kan legas street wani
lokacin ba a wahalar mota.Muna tafe wai wani
mai mota ya tsaya, 'yan mata kuzo mana.Na ja
tsaki tare da kara sauri, Aisha ta ce, lafiya?Ya ce
rage muku hanya zanyi.Na ce Aisha, kema kika
tsaya tambayarshi.Haka mutumin nan ya ci gaba
da bin mu yana magiya, duhun magariba ya
shigo na ce Aisha ko dai mu tsayar da mutumin
nan ya kai mu gida?Don ina tsoron fadan iya.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Tace, nima hakan zan ce,dai dai lokacin ya sake
cewa ku kuwa tunda na ce Allah ya kamata ku
saurare ni, dan kun san mugu dai ba zai yi muku
sallama ba.Aisha ta ce unguwar Mu'axu muke.Ya
ce, ai hanya ta ce ni kuma Nasarawa zanje.Cikin
far gaba muka shiga motar ya ce mun a'a ke
dawo gaba dai ki nuna mun hanya , na koma ga
ba.Ya tam bayi sunayen mu, ina shirin xollo masa
karya sai naji Aisha daga bayana ta ce, ita Sadiya
ni kuma Aisha .Ya ce, masha Allah , sunaye masu
ma'ana.Ya dube ni, Sadiya dan ke fa nake ta
wanan bibikon sai aka ci sa'a kina da sunan
matata, ni sunana Auwal.Hakika jin sunanki ya
kara samun sonki Halimatu duk wace ta amsa
wanan sunan takan zama mai hakuri da hange,
bata rani bata daukar raini, macen rufin asiri zan
so na sake samun ki.Na ce matar taka ta hada
duk wanan halin shine zaka yi mata kishiya?Ya ce
jin dadin halinta yasa zan kara.Aisha ta ce bakai
mata adalci ba, au, ke fa sunan uwata ne ke da
zaki tayani yakin neman shiga?Aisha ta ce, nan da
sati biyu ita ma tana dakin angonta.Da sauri ya
ce, da gaske?Ta rantse mashi tare da fada mashi
ashobe muka zo siya.Daga nan nayi shiru bai
sake magana ba harya shigar damu layin kasuwa,
na ce sauke mu a nan ma mun gode.Sai mu
karasa.Ya tsaya muka fito, ya ce marya ba
godiya?Na dawo dai dai saitin shi na ce, mun
gode, na ce kayi hakuri muna sauri ne dare
yayi.Ya ce shi kenan, Allah ya baki zaman
lafiya.Juyawar da zanyi in tafi tare da cewa amin,
sai maganar ta tsaya, sa kamakon ya Aliyu da
nagani tsaye yana kallon mu.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
Darajar Yayana 1-03
Posted by ANaM Dorayi on 10:51 PM, 14-Mar-16
Under: DARAJAR 'YA'YANA
__________________NA
___________HALIMA K/MASHI
Duk da kasan cewar duhun magariba ba zai sa in
kasa gane bacin ran sa ba.Gaba na ya fadi, irin
wanda ban taba yi ba.A fili na furta na shiga
uku!Aisha ta ce, me nene?Bakinta yayi shiru
sakamakon ganindatayiwa abin da nagani.Kusan
minti biyu yana kallo na, ko da banga fuskarshi
sosai ba na san a daure take .Sai yaja tsaki sanan
yayi babban titi abin shi.Muka kwashi sauri ni da
Aisha inayi ina waiwaya shi, a zuciyata ina cewa
yau na kade, Aisha ta ce muyi wa ni kin ga da
sauki tunda mama ta san mun xo mun koma
ne.Munyi sallama iya tana tsaye tsakar gida tana
cewa, kai ni wadan nan yara ko ina suka shige
ne?Kai Sadiya bata da hankali, ki fita tunda
hantsi har magariba, to ko kasuwar kwari ta kano
suka je?Ko jiran mu gama sallamar bata yi ba
bare ta amsa ta hau fada, Aisha ta shiga jero
mata dalilan mu, ta ce ku refa mun baki, ko
kasuwar kano kuka je ya ci a ce kun dawo tadubi
Aisha ta ce uwaki ta ganki hankalinta ya kwanta,
masu shegen rawar kai.Ta bini ke kuma, sai ki
jira xuwan gadanga don tun yamma yake shige
da fice bai ganki ba, har dai ya kare ya ce ita
wanan yarinyar ina tayi ne?Ina son ta hada mun
abin shan ruwa ina azumi, na dafa kirji na ce, to
me kika ce masa?Ta harare ni karya zan masa?Ce
masa nayi kinje kasuwa sayan anko, yayita fada
me yasa na barki don baya son xuwanki kasuwar
ne yasa shi siyo ankon dakansa.Na ce, na
kade.Na dauki buta dan yin auwala, a xuciyata
inatuno yanda ya ganmu muna fitowa a motar,
da nayi salla nayi addu'a Allah ya yayyafawa abin
ruwan sanyi.Da a zamar sa ya shigo da sallama
ga ba naya fadi da sauri, don haka ma ban iya
amsa sallamar ba, dakinsa ya shiga bayan wasu
mintina ya fito tsaf tsaf cikin shirin fita.Ban taba
ganin dansanda da kaki yake masa kyau matuka
ba irin ya Aliyu, kan cinya ta na dora fiskata
ganin ya nufo dakin Iya.Ga zato na da ya karaso
zai zabga min mari,ina jiyoshi yana cewa iya ya
tafi sai da safe, ta ce, can zaka kwana?Ya ce eh,
ta ce, Allah ya tsare mun kai, ya kuma bada sa'a
ka yawaita adu'a.Ya ce to ina yi iya, zan kara
kulawa.Ya sake wuce ni ya nufi fita, da kallo na
bishia raina na ce, zaki na maza sarkin jin
kai.Nan ya tafi ya barni da kamshin sa sai dai da
dukkan alamu yana fushi dani.Da dare ina cikin
daki kwance kan gado, juyi kawai nake zuciyata
tana mun nazari a kan kallon da ya Aliyu zai
mun, ganin da yayi mun a motar wani kamar in
kira shi in bashi hakuri, sai na fasa.Na rubuta
sako kamar haka:YA ALI DON ALLAH KAYI
HAKURI IN NA BATA MAKA RAI.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ban jira amsa ba don nasan ba samu zanyi ba,
amma ga mamaki na sai naji sautin shigar
sako.Da sauri na bude na soma karantawa.KUL!
BANA DAYA DAGA CIKIN MUTANEN DA SUKE
DAUKAR LOKACIN AIKINSU, SUNA HADA SU CIKIN
LAMURANSU NA DABAM.SAI KI RIKE WANAN DAN
GABA.Na lumshe ido ina son yin nazari a kan
kalaman nasa, na san dai kul! Dan gargadi ne ya
yi mun kenan ba ya bukatar a shigar masa
lokacin aikin sa.Nayi juyi ina mai yiwa kaina jajen
auran ya Aliyu, yanxu auren ya fi ban tsoro fiye
da birgeni.Washegari sukuku na tashi,Iya ta ce
jiya kuna can kuna gararin yawon ku mahaifinki
ya zo yayi ta jiranki har ya tafi.,na ce kash!Ko da
yake na san dole ya dawo kafin bikin.Ta ce ba
dole ne ba , kudi ne ya kawo sadakin ki da akayi,
sai gudumawar su dubu hamsin.Na ce hamsin
iya?Yaushe hamsin zatayi mun kayan daki?Ta ce,
ina laifi, mahaifinki fa yanxu ba aiki yake yi ba,
tunda yayi ritaya sai dai dan noma.Shi ko noma a
kasarnan yanxu dai ba a dauki maiyinsa da
mutunci ba, shine koma baya a gurin gwamna
ti.Su ba ga taki ba ba ga tallafi ba, dan
gurarenda suke nomawan ma kwanaki
yakecemun gwamnati ta ce zata amshi wurin.Na
ce iya gurin da ma ba nasu bane?Ta ce, Sadiya
kenan, dama talaka yana da guri ne a a wanan
karnin?Sai wanda Allah ya taimaka ya kuma tsaga
da rabonsa.Gurinka da takardu da komai za a
amshe maka,dubu hamsin ai yayi kokari.Na ce
haka ne Allah ya rufa asiri, duk abindaza ayi dai
dai karfinmu za muyi.Iya ta ce, in sha Allahu sai
kin zaba yata.Jugun nayi ina kallon Iya, baiwar
Allah nan tana sona fiye da yayan da ta haifa,
abin da take min ko ita ce ta haifeni sai
haka.Kusan duk dare sai bacci na ya katse, in yi
kiri kiri ni kadai cikin xullumi irin zaman da zanyi
gidan ya Aliyu.Na gama duk hashashen da zanyi
ban hango jin dadi ko kulawa a cikin auren ba, sai
yanxu na gane nufin iya ta guje mun wahala ne,
gashi lokaci ya kure mun bani da damar in ce
bana so.Kusan karfe uku na rana ina zaune ina
yankan farce na tare da gyarawa, sautin shigowar
sako naji, sharewa nayi amma naki dubawa don
nasn MTN ne.Sai kuma wata zuciyar ta ce mun in
duba, gaba na ya fadi ganin sunan ya Ali, na
duba cewa yayi.KI SAMENI A DAKI NA
YANXUN.Duk da cewa ina fargaba sai da na dan
sakemurza hoda tare da man lebe, sanan na
fesaturare.Iya ta kalle ni tana zaune gefe tana
gyaran goron ta da yayi tsutsa
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ta ce, to mai aljanun kwaliya don a sarar turare
ana zaune kin hau feshe feshe.Na ce, iya yaya
Aliyu ne yake kira na, ta ce ya shigo ne?Na ce ina
zato, amma ta waya ya turo min.Na suri hijabi na
na nufi dakin gabana na matukar faduwa.Nayi
sallama ya amsa, na shiga kallo daya nayi mashi
yana sanye da gajeren wando da(t-shirt) fara sol
na sunkuyar da kai sanan na tsugunna tare da
cewa gani yaya.Sam bai ko kalleni ba, hasalima
danna wayarsa yake abinsa, nayi kusan minti uku
sanan ya ce (ba tare da ya kalli inda nake ba).Ya
sunan saurayinki da na ganku jiya ya sauke ku a
mota?Ban san lokacin da na zauna ba don tsabar
tsoro.Sanan na ce, ba saurayi na bane.Lokacin ne
ya dubeni cikin wata irin harara da murya ta isa
ya ce, ba karamin zunibi ba ne wajen dan sanda
mai laifi yaki amsa laifinsa.Kar ki raina hankalina
kokaryata ni, sunansa kurum na tambaya.Murya
ta ta soma rawa alamun kuka zai kubuce min, ya
dora yatsansa dan manuni akan leben shi ta re
da cewa, shhhhhi!Kul!Kika min kuka, ko rawar
muryar nan bani son ji.Ya ci ga ba duk da
dadewarku da shi baki san sunan shi ba?Nayi
kokari na kalaci miyau na hadiye shi tare da
kukan da ke son kwace min.Na ce, yau ne na
soma ganin shi, yana ta binmu yana rokon mu
wai mu tsaya muka ki, toda muka ga duhun dare
muka yarda ya kawo mu, don ana wahalar mota
kuma kudin mu ba zai ishe mu mu hau achaba
ba.Ya maida kanshi ya kwanta rigingine, ya kuma
ci gaba da danna wayarshi.Kusan minti biyu
sanan ya ce, wa yake so cikin ku da yake ta
binku?Da dama yana ta binku ne kawai ya rage
muku hanya duk da dimbin jama'ar da ke jiran
mota a gurin?Tsoro ne da faduwar gaba suka
karu gareni, cikin in-ina na ce, am.. Em.. Haka ya
ce wai ni yake so.Da sau ri ya tashi zaune, cikin
daga murya ya ce, menene?Da sadakin nawa a
gurinki?Da sauri na ce, ai Aisha ta ce mashi aure
za ai min.Ya zuro kafafunsa kasa, oh, da ke baki
fada mashi ba?Na ce, ta rigani yin mga na ne
shine dalilin da ya tsareni da idanunsa.To me
yace da ta fada masa?Haka ya ce Allah ya sa
alkairi.Ya sake komawa ya kwanta.Jeki zan
bincika, in na samu zantukanki ba gaskiya sai kin
sani.Zaraf!Na mikexan fita sai ya sake cewa, me
ya fada miki lokacin da zaki tafi ya kiraki?Na ce,
ya ce ne ba godiya?Shine na ce mun
gode.Tamkar ba shi na bawa amsa ba, don bai
komotsa ba bare ya dubeni.Ina ta tsaye har
lokacin da ya kula dan kansa, sanan ya ce, kina
da wata maganar ne?Na ce, a a.Ya ce, to kin
tsaya min a kai.Na tabe baki a raina na ce,
masiffafen ikon ka zan dauke shi kuwa?Tsuntsun
dayaja ruwa......ANaM)Na fice, duk da ba lokacin
zafi bane jikina sharkaf da zufa, kan kujera na
zauna ina maida numfashi.Iya ta ce, me ya ce
miki ne?Ko abinci zai ci?Na ce a'a mun dai yi hira
ne.Ta ce, shine kika yi wujiga wujiga sai ka ce
kunyi dambe?Sakon da ya kara shigowa wayata
shi ne ya hana ni baiwa iya amsa, ko da yake
dama bani da amsar.Sunan shi na kara gani na
bude sakon, cewayayi.NA MANTA BAN
GARGADEKI BA, DOMIN KE TAWA CE TUN KAFIN
NA BADA SADAKI, BARE NA BIYA KUDINKI.Naaje
wayar a gefena, na zari buta zuwa ban daki ba
don zanyi wani abu ba sai dan inkaucewa tam
bayoyin iya.Sauran sati daya biki iya ta zauna da
duk yayanta, sun shirya yanda za su gabatar da
komai cikin tsari.Ina tsakar gida ina jiyo su, iya ta
kwala min kira sadiya!Na amsa, zo kije gidan
Hajiya Umma Rimaye matar Likita Hassan ki ce
mata tayi wa maiyin alkaki magana?In sunyi
maganar nawa ne kudin?Na ce to.Na shiga dakin,
kaina sunkuye dan harda ya Aliyu a gurin, ta ce
maza-maza ki dawo, dukkwanakin nan na kula
baki son aike.Ina shiga uwar daki na tura mashi
sakon cewa iya ta aikeni, ya bude ya gani amma
sai ya ajiye wayarsa, sanan bai ce mun kala
ba.Neko sai nayi zamana gefen gado, jin shiru
ban fito na ta fi ba iya ta ce, kin tsaya kwalliyarki
ta jaraba ko?Na ce, a a.Ya san shi nake jira, sai
ya ce ba aikenki akayi ba kina jiran menene?Na
fito na tafi.,ya Usman ne ya kawo mun katinan
bukin a ranar da dare.Lallai su na kula biki zasuyi
na sosai.Farko zasuyi walima bayan daurin aure,
sai kuma dinner, sanan akwai police day, shi
kuma washe garin daurin aure zasuyi shi,
damisalin karfe uku.Ni da Aisha da Fatiman ya
Sulaiman muka shiga rabon kati.Ana saura kwana
hudu biki, Anty Abida matar Usman ta kirani ta
waya naje, bayan mun gaisa ta ce, kina dan
gyaran jikinki ko?Na ce da me?Ta ce dan shirye
shiryen mu na mata.Na ce, a a ni bani da kudi
anty.Anty ta ce, baki tambayi ango ba?Na ce
anty, ni ba zan iya tambayarshi ba.Nan take ta
kira wayarshi ta sa handsfree, ya daga tare da
amsa sallamarta, ya ce madam ya akayi ne?Ta ce
ango, ango ka sha kamshi.Ya ce bansha ba
tukunna.Suka yi yar dariya, ta ce dama maganar
gyaran jikin amarya ne, ka san anayi.Ya ce ban
sani ba gaskiya wane irin gyara kenan?Ta ce
dogon bayani ne yanzu dai kudi muke bukata.Ya
ce nawa ne?Ta ce talatin ne kacal ba yawa.Ya ce
madan kuna so sai kun tsotse ni tas! Ya fadi? Ta
ce tashi muje gidan Hajiya Umma Rimaye.Na ce,
a a, ita ce mai gyaran jikin?Ta ce, eh.Nace na ga
iya gurinta ta aikeni in kai kudin alkaki.Ta ce, eh,
ai kawarta ke yin kayan buki, ita dai ke gyaran
jiki.Na ce gaskiya tana da kirki.An hada kayan
dilka masu kyau an lailaye ni da su, duk da
kasantuwata fara ba karamin kyau nayi ba,
kwana uku zanyi ina zuwa.Kuma ran na uku za
ayi mun lalle.Iya da kanta tayi ta yabon kyan da
nayi, haka naita zuwa ranar da na cika kwana
uku ta kira mai zanen lalle inda aka zuba min
fulawa.Abinka da fara, kowa sai tanka ni yake ta
ce,tunda gidan su yana da girma kawaye na suzo
nan a yi masu na su lallan na ce, to na
gode.Abida ce ta amso kudin ta bada, Usman
shine ya bamu kudin walimar mu.Wani abun da
ban gane ba duk dare sai iya ta dama mun wata
fura wace ita ta hada kayan hadin da kanta,
sanan ta va inno yar sokoto ta daka mata.Furar
tana da danko, furar sai kace magani gashi duk
yawanta in ta dama sai ta tsare nina
shanye.Sanan da safe ta xuba gero a turmi ta
surfe shi, wai zata tara na dama kunun safe
saboda yan buki, amma tana gamawa zata wanke
shi ruwan farko ta tsareni sai na shanye ina kuka
ina komai.Tun ana jibi daurin aure wasu suka
soma sintirin taya aiki, makota dangi duk sun cika
gidan, yan gefen su iya da na baba na.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
An yi mini kamu inda aka feshe mu da turareni
da kawaye na kamar yanda muke yi a nan
Kaduna.(Ina yan kadunan,yakukeyi kubamu
Labari,ANaM) Gidan matar yaya sani mukakwana.
Zariya za a daura aure amma an ce ni ba saina je
can ba, tunda ba tarewa zan yi ba.Na nufo gida
dan kwasan kayan da zanyi anfani da su in nayi
wanka.Su ya Aliyu na ta shirin tafiya gurin daurin
aure, an kawo motoci.Ya Aliyu ba ya gurin sai
abokanan sa sun taru a kofar gidan mu, kunya ta
kamani, na ja gefen hijabina na rufe fuskata.Ina
jin wani cikin su amaryarmu ki bude idonki kada
ki fadi mana.Sai naji muryar Usman yana cewa,
sarkin kunya kenan.Zan shiga soro (zaure) naji
mun zabga karo da wani, da sauri na bude
fuskata, gaba na ya fadi.Ya Alyu ne har wayarsa
da ya na magana tafadi.Da saurina tsugunna dan
dauke, tare muka hada hannu zamu dauki wayar.
Hannunshi ya taba nawa.Ba ni kadai ba, na kula
harshi yaji abin da naji, tamkar wutar lantarki ta
jamu.Shi ne ya janye hannunsa, na dauki wayar
na mika masa tare da furta kayi hakuri.Kala bai
ce ba, sai amsar wayar da yayi ya tafi, na bishi
da kallo yayi matukar kyau cikintsaleliyar shadda
mai ruwan suminti, tana tamaiko.Kamshinsa ya
cika zauren, a fila na ce na more muji, na juya na
nufi ciki.Sai tsiya ake min Amarya-amarya.
Munyi walimama inda nai ta canjin kaya, kusan
karfe hudu Aisha ta miko min wayata, sa ko ya
shigo na bude kamar yanda na zata ya Aliyu ne,
in da ya ce, "Alhamdulilla" na kalli Aisha dubi
abin da ya ce, ta karanta da murmushi ta dube
ni, kin zama tashi dole yayi hamdala ga
Allah.Nace, Allah ya sa haka yake nufi, wanan
danjin kan?Sakon shi ya sake shigowa musalin
karfe bakwai na safe, na idar da sallah ke nan,
ya ce kije gidan Usman da ga can za a dauke mu
ni da ke dan zuwa dinner, kawayenki kuma su
xama cikin shiri su tsaya a kofar gidan mu,
please, banda marasa hankali, bayan sallar isha'i
za a tafi.Na ce, Aisha kinji mutuminki ko?Ta da
fani, me ya ce?Na mika mata wayar ta karanta ta
dube ni.Ki dauki kayanki da zaki sa ki tafi can ki
shirya, ni kuma zan kula da sauran kawayenmu a
nan dan mu shirya cikin tsari.Kinsan su ya Aliyu
masu aji ne ba irin tarkacen nan suke so ba.A
gidan Abida nayi salar isha'i sanan na shirya da
taimakon abida da yake ita ma in dai kwalliya ne,
matirial ne na saka riga da siket ruwan madara
da ratsin kore.Sai nesa kore takalmi da jaka duk
koraye, sarka kuma ja sai muka yi anfani da ja a
kwalliyar fiska ta gashi ya sha gyara, da ta shiga
fesa mun turare sai da na soma atishawa, kaloli
ta samun masu kamshi.Da na kalli kaina a
madubi sai na ce Alhamdulillah ni ce haka?Ita ma
sai yaba ni take yi, ta shirya, sun zo daukarmu
Usman ya ja motar suna gaba shida Abida ni
kuma a ka bude mun baya ashe ya Aliyu na cikin
motar.Sanye yake cikin lallausan yadi ruwan
madara, kalar kayana ke nan hular kube ce kai
yayi kyau matuka, sam bai kalleni ba.Waya ma
yake yi motar tana tashi wutar motar motar ta
dauke dai dai lokacin kuma ya gama wayar.A
hankali motar ke tafiya motar shiru sai sanyin
(AC) da wani dan sauti dake tashi a raidiyon
motar mai sanyaya rai, ban san ko wacce zabiya
bace mai wakar ba, tunda ba sauraran wakar
turanci nake ba.Sai dai wakar tamasoya ce,
kalamar zabiyarsun haddasa min shiga wani irin
yanayi, na lumshe ido tare da jingina baya na a
kujerar motar.Kamar daga sama naji saukar tafin
hannunsa a saman nawa, da sauri na ware
idona, a zatona bayanan zabiyar ne suka sani
dan karamin mafarki.hhhhh,kujita da shiririta..
Amma sai naji yatsunsa suna ratsa tsakiyar nawa,
lokaci guda kuma ya matsatse su tsam.Na dube
shi da sauri sam ba zaka ce shi bane.Don har
yanxu yana fuskantar inda dama yake fuskanta,
na kalli hannuwa na ma duk da cewa a kwai
karancin haske bai hana ni ganin sarkakun
hanuwan namu ba.Na sake mai da baya na jikin
kujerar tare dasauke yar karamar ajiyar
zuciya.Lumashe ido nayi ina tuno karon da
mukayi dashi da zun, goshi na da hanci na suka
dakikirjinsa.Na tuna hanuna da nasa suka hadu
wajen daukar wayar.Hannuwa na farare sun sha
lalle, na lura da yanda ya tsurawa hannuna ido
na yan sakwanni a lokacin. A raina ina ta mamaki
da tam bayar kaina, shi wanan ya canza daga jin
kan ne?Koko isa ce tasa shi yin haka?Wata zuciya
ta ce koma me nene mijinki ne a yanzu.Tsayuwar
motar ne yasa ni bude ida nuna.A zatona in zai
fita dole ya sakar min hannu,amma har muka fito
hannuwan mu sarke, a haka yayi ta daga waya
na kalli gurin da muka zo, an rubuta Cristal
Garden da wani rubutu mai yi kala kala na
wuta.Usman ya shiga ciki ya fito sanan muka
shiga tare.Dam gurin ya cika da mutane an
wadata ko ina da kayan ciye ciye da na shaye
shaye, naga muta ne manyan mutane da banyi
tsammani ba.
Anci ansha kuma anyi wasa da kudi, sai dai duk
yanda abokan ya Aliyu suka so muyirawa yaki ko
mikewa tsaye.Dan haka duk wanda ya matsu da
ya yi mana liki sai dai ya ishe mu a kan kujerar
mu, abokan shi da kawaye na sun sha rawa.Sai
kusan sha daya a ka tashi, mu kam sai sha biyu
sanan muka tafi don sai da aka kwashe kowa.A
kofar gidan mu motar ta tsaya, na yunkura zan
fita, sai naji ya dafa hannuna, wato ya dora
hannunshi a kan nawa.Na kalleshi shima ya kalle
ni, dai dai lokacin Usman ya fita, da ma mun
sauke Abida a gida.Aliyu ya ciro wayarshi ya
haska fiska ta, ya cire hannunshi da ke kan
nawa, ya dora a kan kuma tuna ya shafa har
zuwa dokin wuya na.Sannan ya juya bayan
hannunshi ya shafi haba ta, dole na lumshe
idanuna abin sai kace a mafarki.Ya tsansa dan
manuni ya saka ya gewaye lebuna na, na bude
ido ina kallonshi, murya kasa kasa ya ce, ki bar
wayarki a kunne zan kira ki.A jiyar zuciya na
sauke, sanan na amsa a kasalance to.Tsakar
gidan mu cike da mutane duk sunyi shinfida sun
kwanta, kasancewar lokacin damina ne amma
anyi kwana biyu ba ayi ruwa ba.Don haka gari
duk ya dauki zafi.Na nufi uwar daka, nanma duk
jama'a ne kwance, gado na dai ba kowa.Na cire
kayan jikina nai daurin kirji sanan na fada kan
gado.Iya can na varo ta a falo tana yin sallar
nafila, a rai na na ce iya koda biki ba a daga
kafa.Filo na dauka na rumgume ina tuno
abubuwan da suka faru yau, tamkar almara ji
nake yau na zama mace sosai.Karar ringing din
waya ta shi ne ya dawo dani cikin hankali na, na
dauka cikin faduwargaba na ce salamu a
laikum.Muryarshi can kasa kasa ya amsa sanan
yace ke da waye ne a nan?Na runtse ido dan
yanda muyarshi take ratsa dodon kunnena, na ce
ni da mutane amman sunyi bacci sunyi shinfida
ne a kasani a gado nike, ya ce ok, kin san me
yasa na kira ki?Na ce a a ya ce, saboda mu
fahimci juna...
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347.
A raina na ce abin da ya kamata a ce shine a
farko ya koma karshe.Tamkar ya shiga raina.Ya
ce kila kiga abun babu tsari ko?Kafin na bashi
amsa ya ci gaba.Ni irin nawa tsarin kenan, kina
jina?Na ce eh.Yace to yanxu sai ki fada mun
dokokinki kafin kiji nawa.Da sauri na ce ya Aliyu
ai bani da wata doka sama da ta Allah da
manzonsa, wada suka tsara ita ce abin bina doka
ta ni kadai in bika.Gud to me kike so me bakya
so?Zan so in soma jin naka yaya, tunda kaine
babba.Ya ce, to da farko dai bana son kazanta,
duk inda zan shiga a gidan bana so in shaki wani
wari.Kuma bana so in ganki babu tsafta ko in
shaki wani wari daga jikinki, sannan ina son
komai a kan lokaci.Na san kin fi kowa sanin ni
dan oya oya ne, komai cikin hanzari bani son
kasala, bana son musu ko gaddama.Abu na kusa
da karshe bana son duk wani abu da zai shiga
lokacin aiki na, ina fata kin fahimta?Na ce eh.Ya
ce yan zu sai inji naki.Na ce, ni dai bai wuce uku
ba, duka da zagi ne bana so.Sai nayi shiru.Ya ce,
ina jinki, saura daya.Na ce imm.... Bashi kawai
ma.Ya ce a a, ki fada in nayi maki cikin rashin
sani fa?Bana son mu munafunci juna,fadamin
duk abinda ke ranki da xuciya daya.nace
amm...dama kishiya ce bana so dai,kuma bamuyi
sabo daxan fada maka ba.shi kanshi shiru
yayi,nasan yana mamaki ne don bai zaci jin haka
ba,a zuciyarshi shi kamshiru yayi saidai bai ji
wani mamaki ba saboda yasha samun case din
mata akan kishiya.ganin kishiya ce abu na karshe
da mata suka tsana.nima shiru nayi gabana yana
ta faduwa,tsai din dana ji araina na raya cewa
magana xai dankaramin mara dadi,can yace ba
xan yi miki alkawari ba in na duba cewa komai
na rayuwata rubutaccene tun fil'axal kamar
yanda yake ga kowa.kifahimta,baxan taba yi miki
karya ba,don kawai kiji dadi.sai dai shawara daya
xan baki,kiyi kokarin tsare duk hakkokina,ta yiwu
in kinyi hakan bazaki rage gurbin wata ba
Kuma kila baxan ji sha'awar karawa ba.(Lallai
yaya kazama abokona,muna da ra'ayi daya
dakai, dan haka me sona nima namiki nasiha
makamanciyar ta Yaya Aliyyu,kiyi kokarin
kyautatawa,tayanda zaki rufe idanuna daga ganin
dukkanin wata mace da matsayi irin na soyayya
bayan ke. ANaM Dorayi)
Nayishiru tabbas nasan gsky yafada,amma kishi
ne daninasan wanan tundaga ranar da kunnena
yaji ya Aliyu ya furta yana son aurena.can kasan
xuciyata tunani ne kada wata rana yace xai so
wata har ma ya aureta.duk sauran samarina da
duk wanda yaxo da niyyar aurena nakan fada
mishi koda na aure ka banason kishiya fa.Toh shi
xakin nawa ina naha fuskar fada masa,shine sai
yanxun...ya katse tunanina da cewa,nasan baki
fahimce ni ba akan batun kishiya,don haka a aje
zancan gefe muyi mai amfani.nima naji abinda
bakiso zan kuma kiyaye insha Allahu.kiyi baccinki
sai dasafe kar ki manta gobe akwai ranar yan
sanda.bikin da suka shirya mana,ina fatan zakiyi
shiri?muryata sarke nace Allah yakaimu goben.
shine ya katse wayar sannan nakashe tawa na
kwanta,kalamansa ne ke yawo cikin kaina na
damu da bai min alkawari cewa baxai min
kishaya ba har bacci yayi gaba dani.(kabwata duk
lokacin da saurayi yace bazaimiki kishiyaba to
kisani hakan mafificiyar karyace a hasashena,pls
kabwata karkisa saurayin yayimiki wannan
alkawari kawai dan gudun bacin ranki,ANaM)
Ya aliyu ya iya magana cikin natsuwa,kai inason
gayen sosai.
Dasafe kin fitowa nayi ina yin sallah asuba dama
komawa nayi nacigaba da bacci. da Iya ta tashe
ni sai na langabe nace mata kaina ciwo yake yi
nan ko banason tashine in ta aiki ga mutane. sai
kusan sha biyu sannan na tashi nayi wanka na
karya.Aisha taxo muka sha hira anan ma muka
xabi kawayanmu da zamu je bikin anjima
dasu.yau kam shigar Green da Golding nayi
nawani leshi mai kyan gaske,abinka da farar
mace kayan sun dauke ni duk da cewa wai farin
ne yacece injiwasu
Duk yau ban sa shi a idona ba sai yanzun da za
mu tafi., yau kam gadanga kusar yaki kakinsa
yasha na yansanda, ya iya aje hularsa a kai
tamkar sai da ya yi course din sata,wani dan
sanda ne ya jamu zuwa wajen, guri yayi
guri,Usman shi ya taho da sauran kawayena,
Police band sai tashi take ga wasu yan sanda
suna ta bin kida fareti. gurin zamanmu na
musamman muka nufa înda masu kidan suka
dafo bazanmu da kida. ya Ali da abokansa da
fareti suka yi tafiyar har zuwa gurin zaman har
wani yana cewa yakamata matar dan dan sanda
ta îya fareti itama . sun yi wasa kala kala har
wani wasan su wai lokacin suna makaranta suna
cin garin kwaki,anci ansha anyi rabon
abubuwa.sai bayan magriba muka dawo
gida.karfe sha biyun dare dai dai wayata ta soma
ruri da sauri natashi nadaga yace xo mana
natashi xaune na kalli shashin da Iya take, tadan
rumtsa kafin lokacin sallarta ya karato,Na tashi
sadaf-sadaf tamakar munafuka nafita, a kofar
daki nayi sallama, ya amsa na shiga.Kwance
rigingine na same shi yana danna wayarshi,
jikinsa sanye da farar singileti tareda gajeran
wandonta.Nayi saurin dauke kaina don kunnyar
ganinshi a haka.Na rusuna kaina a kasa ga ni
yaya ba tare da ya dube ni ba ya ce, tun cake
din da kika bani a baki dazu gurin party nan ne a
ciki na,yun wa nake ji.Na dube shi me zaka ci?
Shima sai lokacin ya dube ni, me kika ga ya dace
in ci?Na ce, ko za ka fara shan ruwan zafi tun da
ka jima baka ci abinci ba, saboda cikin ka
yawarware?Ya ce to yaya za ayi, na samu ruwan
zafin?Na ce sai na dafa maka, na mike tare da
ajiye wayata a gefe na nufi kicin, ina kunna risho
naji takun tafiya, sai ga iya tsaye a kaina ta ce,
na farka ban ganki ba lfy kika kunna risho?Na ce,
yaya ne ya kirani a waya wai yana jin yunwa shi
ne zan dafa mashi ruwan zafi , ta ce, hum!Ki dai
kiyayi kanki, kuma ri rage wanan barin jikin,
sanan kiyi maza ki dawo daki na ce, to.Ina
komawa dakin dauke da dan flaks dinsa na
ruwan zafin na same shi yana danne danne cikin
waya ta, na juyo na jawo kofi zan zuba masa ya
dube ni baki da numbata a she?Na ce ina da ita
mana.Ya ce in gani.Ya ciro number ya miko min
wayar, na amsa na danno sunansa inda na sa ya
Ali, ya ce ok, bani ruwan zafin, na zuba a kofi na
hada masa sanan na mika masa.Sai da ya amsa
ya kurba sanan ya ce, amma na zaci cewa na
wuce wanan matsayin na yaya.Na kalle shi eh
haka ne.Ya dauko wayarshi ya danna ya nunu
min numbata a wayarshi.Yayi saving dinta da
suna my choice, a fili nafurta my choice, ya ce
nima sai a canja min suna ko?Muka kalli juna
cikin ido sannan na soma danna wayata, ya ce
zauna sosai mana, sai kace ba dakin mijinki ba?
Na zauna sannan na soma rubutawa na sa
honey, sai na goge na sa darling, shima na goge
sai kuma na rubuta sweet Aly.Zan goge yayi zaraf
ya amshe wayar ta re da cewa in gani me kike
rubutawa kina gogewa?A fili ya ce sweet Aly.Yayi
dadi ki barshi haka.Ni kuma tuni na sunne kaina
cikin cinya ta don kunya.
Ya ce ai babu wani sauran kunya tsakanin mu,
kinyi alkawarin za ki rinka kirana sweet dinki har
gaban kowa?Na dubeshi cikin kunya sanan na
sunkuyar da kai ina wasa da gefen hijabina na ce
ba dai ga ban muta ne ba, yace to ni gaban kowa
zan ce maki my choice, sunan ya da ce?Na saka
yatsa a bakina ina dan wasa da shi,na ce me
yasa ka zabi ka sanya min zabin ka?Ya dan kara
matsowa, dan duk duniya ke kurum zuciyata ta
zaba har mamakin ki tai lokacin da muka taya
wai saida kikaimana yanga kafin ki amsa.Na
yunkura bari inje in kwanta, ya ajeye kofi bakya
jin dadin firar tamu ko?Ya ci gaba, kiyi hakuri
dani ban taba fira da mace ba shi yasa, na dube
shi tare da dan zare ido ya ce baki yarda ba ko?
Nace naga kana dan sanda ka ce baka taba fira
da mace ba?Amma ba wai ban yarda bane yayi
dariya gaskiya bana yi, tsakanina da mace sai dai
in matsalar da ta shafi aikina ne ta hada ko har
yanzu baki yarda ba?Na ce na yarda na mike
tsaye ya ce, firata ba dadi ko?Na ce, da dadi
mana.Ya ce to shi yasa kike so ki gudu? Iya ta ce
kar na dade,yace ta manta ni mijinki ne ya ce ok
sai da safe?Na ce tam, har na kai bakin kofa
yace, gaki dai baki son kishiya sai ina ganin ba
zaki iya kula dani ba.Ina tsoron kada hakan ya ja
maki kiashiya. Cak!Na tsaya cikin wata murya
wacce ban san ina da ita ba na ce, sweet Aly,
Allah zan iya kula da kai fa ka ji?Kasa amsa ni
yayi don jin irin muryar da nayi anfani da ita.Na
ruga da gudu cikin kunya shi kam shiru yayi yana
mama kin mata.Lallai mata abokan nishadi ne,
dubi yar hirar nan da yayi da yarinyar nan ya
shagaltar dashi ya koma kamar sakarai, yayi
murmushi sanan ya kwanta.Nima kwanciya nayi
ina tuno abin da ya faru tsakaninmu duk da
kallon da Iya ta bini da shi, da na shigo sai dai yi
nayi kamar ban lura ta ji haushin dadewar da
nayi a wurin yayan ba.Washegari ban tashi da
wuri ba sai wajen tara lokacin baki suna ta shirin
tafiya gida jen su.Sha biyu kowa ya kama gaban
shi, sai mu munata aikin gyaran gida ni da
iya.Kusan karfe uku na yamma ya kirani wai a
kwai fura ko?Don anzowa iya da fura da nono
lokacin biki, na ce masa nono yayi tsami, sai dai
in ya siyo yogot ya shigo da shi ya ce to.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Tunda na idar da la'asar na zauna zaman zabar
kayan da zan saka iya dai tana kallo na na sauke
akwatuna na zabo atamfa cikin kayan aure na.Da
na idar da sallar isha'i kuwa na shiga zabga
kwalliya ina ta feshe jikina da turaruka.Iya ta
shigo ta zauna bakin gado ta tsareni da idanunta
ko da bata fada ba nasan abinda kallon nata
yake nufi.,don haka nakoma nima bakin gado na
zauna tare da ajiye dan kwalin da na dauko zan
daura.Ta ce sadiya ni ba wai ina hanaki ki lura
da mijinki bane ko ki shige masa a ana fi so ki
bari sai kin tare, shi fa namiji babu ruwan sa da
zancen kunya, in baki ji nauyi na a matsayin
mahaifiyar Aliyu ba ai kyaji kunya na a matsayina
na uwarki.Saboda iya shege ko watsewa yan biki
basu tafi ba kin tafi dakin miji kin raba dare
saboda rashin kunya?Na sunkuyar da kaina rai
bace a zuciya ta na ce, har ga Allah shi yasa na
so in tare a daki na, ta ce daina bata rai, daraja
nike nemamaki da kima in kin tsare kanki har sai
kin tare kifi kima a idonsa, ga dai misali a gidan
ku.Kiji tsoron abinda ya faru da yar uwarki ta
zariya Harira ya faru dake, kan ta tare tayi ciki a
gidan mijin nata ya shiga yi mata wulakanci.Kin
manta banda ubanku tsayaye ne ai cewa zaiyi
cikin ba nasa bane, shi yasa in andaura aure ba
a tare ba mace ta mika kanta ba karamin so
mijin keyi mata ba za ya daraja ta.Wani dama
sha'awa ce ta kawosa gurin mace da ya biya zaiji
baya sonta, amma in tana gidansa fa?Ai yasan da
kunya ya ce yayi aure sati daya ya kori
matar.Jikina yayi sanyi, tabbas babu ja a batun
iya,kuma haka ne batun Harira, tayi goyon ciki a
gida ta haihu a gida ba ta tare ba.Kuma ya
saketa da kyar ya amshi cikin amma har yanzu
dan yana hannun uwarta agidan mu ita kuma
tayi aure a Hunkuyi.Na saka kaya a sanyaye na
zauna ina kara nazarin abubuwa.Har dakin iya ya
shigo suka gaisa ya ce, ina yarinyar nan?Ta ce,
tana ciki.Kamar daga sama sai naji ya ce, my
choice.Na fito da sauri tare da amsawa, duk da
nasan iya bata san me yake nufi ba.Amma tana
da saurin dago abu, zata san cewa suna ne na
musanman ya sa min, na amsa sannu tare da
gaishe shi.Ya miko min yoghot din in kin gama ki
kawo min.Na ce to,ya dubi iya bari nayi wanka.
.Na shiga da sallama, yana zaune kan sallaya da
alama salla ya idar, na ce baka sami jam'i bane?
Yace, shafa'i da wutiri nayi.Zan tsugunna ya ce
zauna a bakin katifa mana.Kina yi ya ce, sai kace
ba dakin mijinki ba.Ya gyara zama kan sallayar,
sanan ya dauko wata laide dake gefe ya bude ya
ciro kunshin takarda ya warware yana fadin.Kin
ganni da son kilishi shi yasa na saimuku
Balango.Ya dauki daya ya saka a bakin shi, zo in
baki a baki. Nace na koshi ni na ci abinci tun
dazu.Yace wanda kika ci da ban nawa nama ne,
matso kiji.Na dan sunkuyo ban sauka daga kan
katifarba, shima ya matso ya miko nannu ya sa
min abaki, na amsa tare da rufe fuskata cikin
tafukan hannaye na.Ya ce fada min gaskiyarki, ni
dake yanzu ba wani batun jin kunya. Kin kosa ko?
Na daga kai alamun eh, yayi yar dariya kinyi kyau
da wanan kwalliyar ta wace?Nasake makale kaina
cikin cinyoyi na, na ce eh.
Ya matso sai kurum naji ya kama ka fada ta, ya
saka dan yatsansa yana bin zanen fulawar, jikina
ya dauki bari don ji nake tamkar susa yake
min.Shima nasan yaji abin da naji don naji
muryarshi ta dan sarke.Ya ce wata gwana ce ta
zana maki wanan fulawar?Na ce wata yarinya
ce.Ya ce, yayi kyau.Ina son farar mace na dan
ware ido ina duban shi.Me yasa?Ya saki kafada ta
Ra'ayi nane kawai ba dan komai ba, ke fa?Na
sun kuyar da ka, kalar ka nafi so a cikin
maza.Yayi yar dariya, wace iri ce kala ta?Na ce,
wankan tar wada baka cikin farare kuma fara
cikin bakake.Ya tashi daga mazaunin shi ya dawo
kusa dani kan katifar.Kina nufin duk mun dace da
zabin mu?Ban iya amsawa ba saboda yanda ya
kusance ni, jiki na da na shi har suna haduwa.Ya
saka hannun shi a kafada ta ya manno nijikin sa,
fada mini gaskiya can dama kina sona?Duk da
halin da nake ciki na faduwar ga ba sabo da irin
yanda ya makale ni, bai hana ni tunanin wanan
mutimin ya cika tam baya.Ko yana zaton nima
mai laifin ce?Ya dago fuska ta, kalli cikin ido na ki
fada mun. Zan gane in kinyi karya kwa yar idonki
xata nuna mun.Naji mamakina lokacin da nake
furta can dama ina son ka kai fa kana sona?Cikin
wata ma yaudariyar murya nayi maganar.Kurum
sai na fuskanci le bunan shi a kan nawa yana yi
mun sumba, lamarin ya zo min sabo, ko na ce
bako.Ya dinga yi mun wasu abubuwa masu
firgitani har na zama bani da karfi.Tsoro na daya
kada ya gota daga haka, saboda ina tsoron
Iya.....zandakata Anan,muhadu a lokaci nagaba
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
Darajar Yayana1-04
Posted by ANaM Dorayi on 10:48 PM, 16-Mar-16
Under: DARAJAR 'YA'YANA
_______________NA
_____HALIMA K MASHI
Nayi karfin halin zame jiki na daga na shi,
yakwanta rigingine na mike sai da safe.Ya miko
hannu ya riko nawa hannun, cikin wata rikitaciyar
murya ya ce, ki zo nan mu kwana.Da sau ri na
ce, tab Iya ba zata yarda ba.Ya ce, ina ruwanta,
ni ba mijinki bane?Na ce to ai ban tare ba.Ya saki
hannu na.Da sauri na fice.Na tabbata in na shiga
daki haka iya zata fahimci wani abu, don duk
kwalliyar fiskata ya goge min.Don haka sai na
bige da sabar buta na nufi bandaki, na zo nayi
alawala.Ina shiga uwar daki ta bini da kallo tana
kwance kan gadonta.Na cire kayan jiki na dauko
rigar sallata nayi shafa'i da wutiri.Ta tabe baki
bata dai ce min komai ba ko takula duk na
tsargune?Oho.Da kyar na samu bacci ya soma
dauka ta sabo da tunanin abubuwan da suka
faru tsakani na da shi.Shigowar sakonshi dan
sautin ya farkar dani, na bude na duba cewa
yayi, kin hanani bacci my choice kixo ki taima ka
min please.A raina na ce mai zanyi maka sweey
Aly, ka dan bani lokaci mu tare, kiranshi ne ya
katse tunanina,sa sauri na farka dan ina tsoron
kada ringing din ya farkar da iya, duk da cewa na
san tana jina don bata da nauyin bacci.Can kasan
makoshi na nayi sallama ya amsa muryarsa a
raunane, har mamakinsa nake ina girman kan?
Ina isa da jin kan?A she dai mace dai ita ce
namiji.In ba mace rayuwar namiji ragaggiya ce.Ya
katse mamaki na da cewa, kizo kinji?Ba zan iya
bacci ba ki taimake ni.Nace iya fa tana jinmu ka
bari sai tayi bacci.Ya ce dagaske zakixo in jira ki?
Na ce eh.Sai ya yanke niko gaba daya ma sai na
kashewayar, na amsa masa cewa zan xo ne
kurum amma ba dan zan je din ba, sai don ya
barni.Kuma ko ba dan iya ba ina tsoro, tunda
ban san yanda abubuwan suke ba.Na makele fulo
ina tunanin ko a wane hali yake ciki yanzun, na
jima kafin bacci ya tafi dani.Nayi mafarki kala
kala masu dadi wai muna ta shawagi a cikin wata
duniya ni da ya Ali.Ku ziyarci blog dinmu domin
karanta Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Da safe kuwa fuskarshi a murtike, don ko amsa
gaisuwata baiyi ba, lokacin da yazo gaida Iya ina
gai da shi,hakan bai yi min dadi ba, na kunna
waya ta na tura masa sakon ban hakuri tare da
ce masa jiya naso inzo Iya ce bata bari na fito
ba.Ko ya gani ko bai gani ba oho, bai dai bani
amsa ba, na dafa ruwan tea na kai mai na same
shi ya gama shirin fita yana daura ta kalmi.Na
shiga da sallama ciki ciki ya amsa, ina shiga ya
dubeni fuska daure ya ce, lfy?Cikin wata murya
irin ta a salin jarumin maza.Jiki na ya dauki bari
na ce, dama....dama tea ne.Ya ce fitan min da
shi ina azumi, fargaba na ya karu, iya ce jiya ta
fash....Ke!Ya katse ni, fita a nan dan Allah.Na fita
da sauri, zugun na zauna ina tunanin yanda ya
Ali yake canza launi tamkar hawainiya...
Kimanin kwanaki uku kenan yayi mun dif, inna
gaida shi baya amsawa, haka nan in abinci na kai
mai ko yaushe sai ya ce yana azumi.In iya tayi
mashi magana ke nan, in nice ma na kai mishi ni
abu sai ya koro ni, ina girki a kicin iya ta fita
lokacin sai ga Aisha kawata.Naji dadin zuwanta ta
tayani,muna fira na bata lbr duk halin da nike
ciki na kara da cewa, ya Aliyu gaba yake dani, iya
ta sa ido sosai dan ganin ban bada kai ga miji na
ba, ba tare da mun tare ba.Don Allah Aisha ki
bani shawara, ta ce, ni dainawa ganin in har zan
fada maki gaskiya kibi mijinki, daga lokacin da
aka daura muku aure da shi dukkannin hakkokin
shi sun hau kanki.Nayi ajiyar zuciya tace, nasan
kin san komai ma kina yi ne kamar baki sani ba
nace Aisha nasani,Iya fa idonta yana kanmu.Ko
daki na shiga sai kiga tana kai kawo, in na fito
kuma tayi ta yi mun kallon tuhuma, to ki bashi
shawarar ku fita wani wurin mana.Nace tap nice
ma zan bashi shawarar?To an ce maki iya za ta
barni in fita ne?Aisha ta ce, yanda kika gani,
amma in nice zan bi miji nane.Rayuwar nan ta
yanxu mata suna bin maza har inda suke,
balantana mijinki dan kwas irin wanda basu da
yawa a cikin jama'a?Ku ziyarci blog dinmu domin
karanta Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Na ce nima ina tuna haka, shiyasa wlh ban so ba
da ban tare ba, kamar yarda ko wace Amarya
take tarewa a dakinta. Ki tayani da adu'a don sun
sani a tsakiya ita tana kallo na a mai rawar kai
na shige masa,shi yana kallo na mara
biyayya.Aisha ta ce, abu ne fa mai sauki ke ce
kika dauke shi da zafi, in kin bi mijinki kinga dole
ta barku.Na dubi Aisha ta ce, fa ba zai dubi
mutuncina ba, Aisha ta ce, in bai sameki a
mutuncenba ba?Kin bi maza ne?Na kai mata
duka, kinji ki da wani zance, in na bi tare muka
bi kenan.Ta ce ke ce da wani shirme, in kin ga
namiji yaga rashin mutuncinki ya sameki kin bi
wasu....(Biri fa kuma yayi kama da
mutum,watakila irin haka tafaru da yar uwarki da
Zaria,shiyasa mijin yayi inkarin kasancewarvcinkin
a matsayin nasa,hartakai ga saki ANaM Dorayi)
Kalu bale ga masu saida mutuncinsu a banxa.
Aliyu tukur ya tsaya a gaban shugaban shashin su
na binciken manyan laifuka, mataimakin
Commissioner.Ya ce ASP Aliyu zanfi so idan kana
tsayawa a kan aikinka, ina nufin ka rinka
dakatawa a madakatarka.Sanan ka rage kishin ka,
domin kasar mu a yau in kace haka zakayi lallai
ba zaka kai ko ina ba.Ina yi maka magana ne a
kan barawon shanu din nan, mutumin mai girma
commissioner ne, na tabbata da yana gari baza
ka kamashi ba bare tsarewa.Inma kayi nasara ka
kama shi, ba zaiyi minti talatin a tsare ba kai ba
a taba kama shi ba, yaranshi kurum ake
kamawa.Da sunyi waya da commissioner zaisa a
sake su, nayi mamakin ma da commissioner bai
tsawatar maka ba, ya ce kawai ka bar case din a
hannunsa.Ran Aliyu ya baci, shi da ya shiga aikin
dan sanda kishin kasarshi da kawo gyara, sai
kuma su rinka ganin barna suna kauda kai?Ya ce,
yallabai ina rantsuwar da mukayi da alkur'ni
cewa zamuyi aiki tukuru bisa amana da gaskiya,
idan dannanda bai zama mai kishi da gaskiya me
za a kirashi?Idan dan sanda zai rinka amsar cin
hanci yana hulda da manyan azzalumai yana
daurewa barayi gindi suna zalunci, za a kirashi
mai tsaron lafiya al'umma.AC ya dagawa aliyu
hannu, dakata ASP, wannan tambayoyin zasu fi
dacewa kayiwa CP su, ni shawara na baka.Da
akwai mutane irinka da yawa wadanda suka
nuna kishi, wasu anyi musu canjin gurin aiki zuwa
wasu garuruwan da ba zasu sami irin wanan
barnar ba bare suyi gyara.Wasu anyi musu sharri
an koresu, kai wasu sun mutu yayin da wasu da
yawa suka ajiye hularsu.Ban hanaka yin kishi da
gaskiya tare da kin karbar cin hanci ba, sai dai
ina mai baka shawara ka dinga tsayawa ga
kananan masu laifi, jeka abinka.
Aliyu yana zaune a office din shi, kansa ya dauki
zafi yana tuno sa'insa da sukayi da Barawon
shanun, inda barawon yace, kai yaro wanan ba
wani bakon abu bane satar shanun da muke
yi.Haka nan mu nan Headquarter gidan mu ne
kaine mutum na farko da na taba bawa cin hanci
ya maido mini.Nafi tunanin kana daga cikin
mutanen da basu da rabo, amma kai bako ne
ko?Aliyu ya ce, ba jin tarihi ko maganar cin hanci
na xo ba, nazo nan ne dan in kama ka,a
matsayinka na mai laifi, ni kuma na hukuma.Duk
wadan nan baya nan zasu biyo baya in munje
office, yaranka muka kama kuma suka ja
sunanka.Barawon ya zaro ido tare da daga murya
ya ce, kai bako ne shiyasa baka sanni ba amma
muje.Aliyu ya ce nasan ko ban sanka ba, bako ne
ni bako ne wannan ba damuwata ba ce.Ku ziyarci
blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Sun san Aliyu bai san wanene wanan barawon
ba, shi kanshi barawon cewa yayi zakayi da
nasanin kamani.Aliyu bai ce kala ba, ya nufi
Office din sa zuciyarshi cike da son nunawa
wanan baron cewa hukuma bai bar
kowaba.Amma me? daidai lokacin da yake bada
ummarnin ashigar da kara ne shugaban shashin
su AC ya ce, kajira tukunna sai an sami ummurni
daga commissioner.Dafawar da akayi mashi itace
ta dawo dashi daga dogon tunaninsa.Ya dago
kai.Insperctor kamal kaita ne ya ce Sir, ka daina
damuwa da irin wadan nan matsalolin, sanan ka
ci gaba da yanda kake, Allah zai kawo maka
dauki dan yana tare da irinku.Sai dai dama baku
cika farin jini ba a cikin yan sanda, saboda kowa
yana ganin cewa zaku toshe masa kafar
samu.Shawarata ka bar batun Barawon nan ko
ba komai kayi namiji tunda ka kamo shi, ka kuma
tsare shi.Sanan Allah ya doraka a kan CP bai
dauki zafi a kanka ba.Aliyu ya mike tsaye, na
shigo aikin dansanda cike da kishi da buri, gami
da kwazo.Manufata insamu waddanda zasu
fahimci niyyata don mu kawo gyara cikin
hukumar yan sanda.Na tabbata ko cikin
headquarter din nan akwai masu kishi da yawa
wadanda suke jin irin abinda nake ji yanxu a
zuciyata. Inspector ya ce, hada dani, sai dai ina
mai bakin cikin sanar da kai cewa ba zamu kai
labari ba, tunda daga sama a ake tadiye mana
kafa.Aliyu yace inko haka ne zaya ci gaba da
faruwa, watarana zan iya ajiye hulana.Inspector
ya ce, ranka ya dade kada kasaka haka a ranka
tun yanxun, kaji a cikin xuciyarka cewa burinka ya
cika, Allah yana tare da mai gaskiya.Ranka ya
dade ka duba tashin farko bin diddiginka yasa
sashinmu na bincike suke shakkarka, ina son
mutum irinka.Aliyu ya lumshe ido tare da cewa
zantukanka sunyi mun allura inspector, zan kara
kaimi.Da wanan ya cigaba da aikin sa.Daf da zai
tashine aka shigo da wani da ake zargi, ya kalle
gobjejen mutumin sanan ya dubi yan sandan.Me
yayi shi kuma wanan? Sajan Ado ya ce, ranka ya
dade, kato kamar wanan aka kama yayiwa yar
shekara takwas fyde,ran Aliyu ya tunxura, ya
runtse ido cikin takaici, ya ware ido ya kalli
mutumin cikin tsana ya ce, wai wane irin
zaluncine wanan kuke yiwa jikokinku?Cikin rawar
murya mutumin ya ce ranka ya dade na rantse
maka ba ni bane, sharri sukayi min, na rantse
maka.Aliyu ya harareshi, ba kowa bane yake
amsa laifinsa da sauri.Ya kalli yan sandan suwaye
suka kama shi?Sajan ya ce ranka ya dade ga
mutanen da suka kawoshi can, sune suka
kamashi da yarinyar a shagon shi tana ihu.Yace
ina yarinyar yanxu?Sukace an tafi kaita Asibiti.Ya
kalli mutumin yaja tsaki ya ce, ya ce ku rufe shi,
yanxu ba wani sausauci ga irin mutanen nan
masu cutar da kananan yara ta ta hanyar fyade
Ya koma office din sa cikin ta kaicin fyadan nan,
kullum sai sun samu irin wanan case din da yar
da jarirai yafi yawa, amma yanzun yanaga zasu
xo daidai.Ya kira sajan ya ce, ya kawo masa
takardar tuhumar (statement) da ya duba tsaki
yaja, ya dubi sajan.Kullum dai abin iri daya ne.Ya
tabe baki, sanan ya dubi a gogonsa, yau shida
zan bar nan, duk wanda ya nemeni
saidasafe.Sajan ya sake kamewa tare da fadin
yes sir!Sai kuma wanan mutumin yaya za ayi da
shi?Aliyu ya ce, ba maganar beli ko wani ya zo
zuwa gobe za a hada bincike a turashi kotu.Sajan
ya sara masa sanan ya fito.Da dunbin wanan
damuwar ya iso gida, daga ganinshi kasan akwai
abin da yake damun shi, kan katifarshi ya zube
rigingine bata re da ya cire koda ta kalmi
ba.Lokacin da ya shigo ina zaune a kan kujera a
kofar daki ina karatun wani littafi (SIRRIN BOYE)
na Anty Bilkisu.Ga al'adarshi in ya shigo dakin Iya
yake fara shiga kafin ya dawo dakinsa, ya cire
kaya in sun gaisa.Ya shiga wanka.Amma yanxu
tunda ya shigo shiru, iya ta fitodaga bayi (ban
daki) na dubeta na ce, yaya fa?Ya dawo yanayin
shi kamar na mara lafiya, ko baya jin dadi ne?Ta
ce, ba wani ke dai kina sonzuwa gurin mijinki ne,
kuma ba zan hanaki ba.Na hade fuska, Allah iya
nifa ba wai zanje bane fa.Ta ce, kije ki duba ko
lfy,naki tashi, dan dama ina tsoron inje yayi mun
wulakancin shi, ya ce nafita shiyasa naki
zuwa.Ganin da iya tayi tabbas ba zan shiga ba
kuma tabbas bai fito ba sai ta shiga dakin. Yan
da ta ganshi warwas a katifa batare da ya cire ko
takalmi ba, sai abin ya bata tsoro.Cikin saurin
muyar ta ce, Gadanga!Ya dago kai da kyar ya
dubeta, wani matsanancin ciwon kai ke damun
sa.Ya ce na'am Iya sannu.Ya tashi zaune,
ciwonkai ne ya hanani shigowa ciki.Ta ce,
matarka nema ni take ce mun ka shigo cikin wani
yanayi, bari a kawo maka magani ka sha.Yace
zanje Asibiti in anjima bayan magariba.Duk
kwanakin nan da haka nake ta yawo da ciwon
kan nan.
Ta ce, to kasha maganin yan xu sai kayi sallar da
dan karfin jikinka, kaje asibitin da dan kwari.Ya
ce, to.Ta kwala min kira Sadiya.Na amsa ta ce,
dauko min magani panadol kizo da ruwa.Naje har
gabanshi na ajiye da ruwan ina yi mashi sannu
yaya, ya jikin?Ko kallo na baiyi ba bare ya amsa,
mamakin yanda naga iya tan gutsi gutsi da
maganin, ta dubeni dauko mun cokali.Na dauko
ta jika ta bashi a baki tare da fadin, shiyasa nake
fargaban ciwonka gadanga.Duk da dai ba yawan
ciwon kake ba, amma kin maganinka shi ke
wahalar da kai a ciwo dai dai yake da na yaron
goye.Shi yasa duk lokacin da katashi ciwo bama
jita dadi.Ya sha ya koma ya kwanta, dai dai
lokacin aka kwada kiran magariba.Ta dube ni,
bari inje inyi sallah, nima na biyo bayanta.Ta
dakatar dani da cewa, jira tukunna muga yanda
jikin zaiyi.A raina na raya cewa dan ta ga ina
fashin sallah, shi kuma bashi da lfy.Shi kam yana
kwance, na isa gurinsa gabana yana ta faduwa,
duk da ina zaton zai daka min tsawa ban fasa yin
abin da nayi niyya ba.Gabansa na tsugunna ina
kwance masa takalmi, na cire su na aje gyafe,
sanan na kwashi kafafunsa na zubasu a kan
katifar.Har lokacin idanunsa biyu amma suna
lumshe, haka nan hannunsa yana dafe da
kai.Kusan minti shabyar ina zaune can gefe, ya
tashi zaune yana kici kicin cire rigarsa, na taso na
balle masa boturan, sanan na sabule rigar sai
farar singiletin, ita ma ya kama ya cire.Na kalli
kirjinshi gashi ne kwance na kauda kai don sai da
naji wani iri.Ya sabule wandonshi, sai gajere na
ciki, shima na kwashe su na zaba su a cikin
kwandon da yake zubawa.Naga yana kokarin
tashi nace mai zaka dauko in dauko maka?Ka
zauna kawai.Ya ce, bani jallabiyata.Na bashi fara
kal mai dogon hannu, ya mike zai fita, na ce ina
zaka je?Ya ce masallaci.Yana fita na shiga gyaran
dakin, ban taba yi masa gyaran daki ba sai
yau.Ko yaushe da kansa yake yin gyaran dakinsa,
nayi zaton zanga mujallun da na taba gani da, sai
kuma ban gani ba, har na gama.Iya ta idar da
sallah, ta sake lekowa ko ya tashi, na ce ya je yin
sallah, shiru shiru ashe daga can ya tafi
asibiti.Har kusan tara gashi bai fita da waya
ba.Iya da kanta ta fita har masallaci layin mu,
wanda suke sallah tana nemanshi.Duk wanda ta
tambaya sai su ce mata tare dai suka idar da
sallar isha'i.Da ta dawo sai na ce mata ko dai
yatafi Asibintin da ya ambata ne?Ta ce zata iya
yuwuwa ya tafin, tun da ya ambata.Nan dai
muka zauna zaman jiran tsammani,mun kasa ko
cin abinci.Sai sha dayan dare da yan mintuna
dan acaba ya sauke shi, ni da iya har rige rigen
fita muka yi, shi ne muka yi masa sannu ya
amsa, iya ta ce, muna ta neman ka.Ya ce, natafi
Asibiti ne shi yasa ciwon kai ya matsa min da
yawa.Amma na sami allura da magunguna, kuma
na kwanta canne kamar yanda likitan ya ce in
dan huta, Alhamdulillahi kai yayi sauki.Ta ce to
me zakaci yanzun?Ya ce, nasha tea a can kafin
ayi min allura, muka shiga dakin shi ya zauna
bakin gado.Iya ta fita nima na mike zan fita, sai
ta ce ki dan tsaya ke saboda dare ko?Na koma
na zauna ya kwanta tare da lumshe ido.
Wayarshi tayi ringign, ya daga ya kalla sannan
yaja tsaki, bari na kashe wayar nan ina so in dan
huta.Har zai kashe sai ga ma bari yayi anfani da
wanan damar ya nunawa sadiya anafa ribibin shi
har da take masa yan ga.Don haka sai ya daga ni
dai naji yana fadin yaya mati na me ya faru ne?
Ban zaci jin muryarta ba, ashe ya saka
hanfree.Sai kurum naji ta ce, lafiya lau sir, ban
gankaba ne an ce ka tashi tun six, ya ce akwai
wata matsala ne matina?Ta ce babu, naso in
ganka kawai, kayi hakuri kasan ganinka kawai
yana cire min damuwa dayawa, dayawa, amma
sir sai kanayi kamar baka san haka ba.Yace
matina yanzu bani da lafiya ne, ban dade da
dawowa daga Asibiti ba in nafito da safe zamuyi
maganar.Ta ce to Sir, nagode Allah ya kawo
sauki.Raina yayi mugun baci, a gabana yake
magana da wata arniya har take ce masa ganin
shi yana sata sukunni da kwanciyar hankali?Yana
ajiye wayar ya kalleni, na hada rai matuka na
mike ya ce, ina zaki?Nace zanje in ci abinci ne, da
kyar nake magana.Ya ce, au dama baki ci abinci
ba?Kamar in kai masa duka don ta kaici.Mutumin
da yayi nasa guri bai fada muna ba muka yi tsuru
tsuru cikin damuwa.Shine zai ce dama ban ci
abinci, ya mai maita tambayar nace um, ya ce
kina ciwon baki ne?Nayi shiru yace in kin ci ki
dawo, tunda Allah yasa yau naji da kunnena ba
iya ce take hanaki zuwa wurina ba, karya kike yi
mata.Ban tanka shi ba na wuce, a raina na ce ba
zan dawo baCan kusan daya saura ina ta tubka
da warwara na kasa bacci, ni nasan kaina ina da
mugun kishi, sai ga sako ya shigo cikin wayata
cewa ba zaki dawo bane?Na tura masa amsa da
cewa eh, ka kira Matina.Yana ganin haka yayi ta
dariya, sakonshi ya kai ke nan, don haka shima
kurum sai ya kashe wayarsa ya kwnta.Da Asubahi
iya taje dubashi ta sake shiga dan duba shi, sai
ta samu jiki yayi sauki, har ma ya tafi
masallaci.Don ya Aliyu ba rago bane namiji ne, ga
juriya da izza, matsalarsa daya in yana ciwo kin
magani,yayi tawa iya shagwaba sai kace karamin
yaro, shi a dole auta.Nikam har gari yayi haske
ban tashi daga makwanci na ba, tunda ina fashin
Sallah ba wai ina bacci bane kurum takaici ne ya
hanani tashi.Jiya ko baccin kirki banyi ba, saboda
takaicin ya Aliyu.Iya ta shigo, ke ba zaki tashi kije
ki gano mijinki ba?Ko da nafito kin xuwa nayi na
debi ruwa na shiga wanka.Ina fitowa nayi zaman
shafa mai duk ina jan lokaci ne don yayi abinda
zaiyi ya kama gabanshi.Bana ma ko son ganinshi,
lokacin da na shirya na nufi kicin a tsammanina
ya fita.Ina tsakiyar kunna risho sai naga mutum a
kofar kicin tsaye.Na rasa dalili in zan ga ya Aliyu
sai gabana ya fadi.Na kalli fuskarshi, gaskiya har
ya dan rame na ce ina yini?Ya ce ban yini ba, ni
yanxu zafiya ce, sanan ba zan amsa ba tunda
baki san hanyar daki na da bazakije ki gaida ni
ba.A raina na ce ina matina?Ita batazo ta duba
ka ba?Ya katse tunanin da cewa,ruwan zafi nake
so zanyi wanka.Na kalleshi, ban taba ganin yayi
wanka da ruwan zafi ba, nace to bari in dora
yanzun, bai ce, kala ba ya koma daki.Da yayi zafi
na sirka na kai masa ban daki, sai naje na ce
masa ga ruwa can.Lokacin yana waya, da hannu
yayi min alamar cewa in je yaji.Na tsargu da wa
yake waya, don haka da nasaki labule sai na
tsaya.Ji nayi yana cewa, kada ki damu, yanzu
zanfito.Jikina yayi sauki, ai da tunaninki na kwana
araina.Na girgiza kai tare da yin kwafa.Tabbas da
matina yake yin waya, nayi kicin ina yin magana
ni kadai, na ce to ita wanan shegiyar matinar me
ke tsakaninsu?Nemanta yake yi ko me?Wata
zuciyar ta katseni da cewa, ba kina gudunsa ba?
Ai ga Matina zata maye gurbinki. Jikina ya sake
mutuwa, na shiga tambayar kaina mafita.Wunin
ranar sukuku nayi shi, na kasa tuna yanda zan
bullowa abin.Duk jin su iya nake ko da can da
suke cewa ba ruwanshi da mata, ni nasan da
ruwanshi tunda ni naga mujallun batsa a dakin
shi.Wanda baruwanshi da da mata me ya
ruwanshi da irin kallon tsiraici?Dole ke nan inyi
yakin rabashi da matan banza.Wata zuciyar tace
haka ba zata yuwu ba, sai in zakiyi aikinki a
matsayin matarsa, lallai saikin mika kanki a fili na
ce ya na iya?Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Muna zaune a falo da iya washe gari da safe,
yazo yiwa iya sallama zai fita, nima na bude
baki da nufin ce masa sai ka dawo.Amma da
yake matina ce a raina sai kurum naji na ce
masa ka gaishe mun da matina.Har ya juya sai
naga ya tsaya cak, sanan ya waiwayo fiskarsa
dauke da murmushi ya furta cewa zataji in sha
Allahu.Ya juya ya tafi, ni kam kamewa nayi
tamkar gunki, a zuciyata tambayar kaina nake
dama mutun na iya kuskuren magana ya furta
abinda ke son zuciyarshi ya bar na saman leben
shi?Kash!Ban so nayi zarar bunun nan ba, abin
takaici harda murmushi na ambaci sunan
masoyiyarshi.
Kwana uku suka shude ina cikin damuwa,na san
Iya ta lura banza kawai tayi mun,narasa abinda
ke yi min dadi, ni ba fita nake ko ina ba, ba TV
Garemu ba bare nayi kallo, ta lalace ni kuma ba
ma abociyar radiyo ba.Wani kayan haushi ko
littafi na dauka da sunan karantawa sai in kasa
fahimtar komai.Na san kaina ina da shegen kishi
na ban mamaki, ko saurayina naga suna yawan
gaisawa da wata budurwa hankalina kan tashi,
bare a ce miji na.Tabbas da Ya Aliyu ya skar min
fuska da tuni na same shi munyi ta, amma ya
Aliyu ya wuce haka.Ku ziyarci blog dinmu domin
karanta Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Cikin sauri sauri ya Aliyu ya shiga shashin su, ya
kalli sajan Ado ina barawon?Suka kaishi ya
shiga.Ya tsura mutumin ido, aransshi ya ya ce
kai wanan mutumin baiyi kama da barawo
ba.Ya kalli Sajan, kawo abin zama, sai da ya
zauna sanan ya kalli mutumin.Kaine barawon fili
ko?Hawaye suka soma kwarara daga idanun
tsohon, don bakin cikin sunan da aka kirashi.Ya
ce cikin rawar murya, ranka ya dade ni ba
barawo bane, ban taba sata ba.Aliyu ya juya
kulkin dake hannunshi ya dan jefashi, sanan ya
cafke.To baba ya akayi har ka mallaki filin da
kake gini?Ya ce, ran ka ya dade filin nan na
gajeshi ne a gurin mahaifiyata, don mahaifinta
manomine.To ina zaune a gidan haya ga iyali,
ina da mace daya ga yaya takwas.Yan samarin
yara na a makota na roka sunakwana, ganin
kullum nauyi na karuwa, sai nayake shawarar
gina fili na ko da daki biyu ne rak.Na soma gini
ni da yaya na, dan sana'ar mu ke nan ta
leburanci da yaran.Mun soma ginin kawai sai
ganin yan sanda nayi sun xo kamani, ban san
abinda nayi ba.Aliyu ya ce, to baba naga
takardar bayanin laifinka, naga cewa ana
zarginka da laifin yingini a filin da ba naka ba,
filin tsohon jami'in dan sanda ne.Tsoho ya ce,
dana wlh wanan filin nawa ne, kowa ya sani a
unguwar mu ina da takarduna ina da
sheduna.Kuma ni da aka kawoni nan ba a
tambayeni ankawoni nan aka jehoni ne
kawai.Babu wanda yaji ta bakina.Aliyu ya ce ka
tabbata kana da takardu da shedu?Tsoho ya ce
ina dasu ranka ya dade.Aliyu yace zamu mikaka
kotu kuma in sha Allah zan tsaya maka sai kayi
nasara.Cikin izza ya nufi wajensu Sajan Ado,
yace sajan, yace Sir, bayan ya kame.Aliyu yace
waye ya kawo wanan mutumin?Sajan ya ce,
barawon fili?Aliyu ya ce, eh shi.Sajan ya ce CP
ne yasa a kamo shi.CP da kanshi?Ya tambaya
cikin mamaki.Yace shi, amma AC ne ya tura.Kan
Aliyu ya daure, ina takardar bayanan da kuka
bani dazu?Sajan ya sake daukota, Aliyu ya kalla
ya sake karantawa, wanan rubutun kofur bala
ne ai, sajan ya ce, eh, Aliyu ya ce kira min
shi.Ya juyya ya koma office din shi.Ya tsare
kofur da idanun shi waddanda basadaukar raini,
kainne ka rubuta wanan takardar ko?Ya kame,
eh, nine Sir, ya juyya mishi baya, amma ai baka
tambaye shi ba ka rubuta da yawun shi.Ko
menene dalilinka?Kofur cikin daburcewa ya
ce,Sir ai nima AC ne ya ce na rubuta haka, sabo
da raini mutumin yake so ya kawo wa tsohon
mataimakin IG.Aliyu ya daga hannu da nufin
dakatar dashi, tsaya min kowa ya cuta sai a ari
bakinsa a ci mai albasa?Ya ninke takardar ya
zura cikin aljuhunsa, yace dauko wata kazo muje
ka sake rubuta ainihin bayanin da yake daga
bakinsa, mu masu kare Al'umma ne da
rayukansu ba masu danne masu hakkin ba ne
da kuma kashe su.Kofur dake biye dashi ya ce,
sir, wanan tsohon mataimakin IG yana yawan
kawo mana matsalolinshi a nan, kullum
maganarshi bata wuce an cuceshi.Ku ziyarci blog
dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Aliyu ya ce dan ya taba zama jami'in dan sanda
bazaiyi anfani da wanan damar ba, sanan yayi
anfani da mu.Alkawari na daukarwa kaina ba
zan bar zalunci ba, matsawar naganshi zanyi
yaki dashi.Aliyu ya tsananta bincike kuma cikin
kwanaki kadan yagano cutar tsoho wanan
jami'in ke son yi, don hakka ya tattara dukkan
bayanai ya turasu zuwa kotu.Gobe da safe ya
tabbata in anje can tsohon zai sami hakkinsa,
saboda bayanai da hujjojin da Aliyu ya
hada.Yana tsaye a bakin titi zai hau a caba zuwa
gida Inspector Kamal ya sameshi a gurin, ya ce
ranka ya dade zuwa yanzu yakamata a ce ka
mallaki abin hawa ko da mashin, amma in san
samu ne a ce kana da mota.Aliyu yayi
murmushi, kada kadamu, ko mai lokaci ne, ya
ce in dauko maka na aiki mana ba sai ka sha
mai ba?Aliyu ya ce, a a na aiki anyi shi ne dan
aiki kawai.Ispector ya ce, kana birgeni Sir, komai
kana barinsa a muhallinsa.Lokacin da aka raba
mana mashina baka zoba.Aliyu ya ce, ko ina
nan ba zan amsa ba, don bana son bashi.Ya
karasa zancen tare da tare dan acaba.Wayyarshi
ta dauki tsiwa, ya cirota cikin hanzari ya daga
saboda ganin sunan AC, hakuri ya baiwa dan
acaban, sanan ya komaciki kamar yanda AC ya
bukata a cikin officeya same shi, kai kawo yake
ransa a bace ya dubi Aliyu.Me yasa ba bada
damar a kai barawon filin nan kotu?Aliyu ya ce,
angama bincike ne sir, sanan doka ta hana a
tsare mutum tsawan lokaci ba tare da an kaishi
kotu ba.AC ya ce, na san dai na rigaka sa kaki
ko?Bai jira amsa ba ya ci gaba da cewa, don
haka kasan na rigaka sanin doka.Ya koma
kujerarshi ya zauna.Wanene ya hada binciken?
Kai kasan ma da wa yake rigimar?Kasan filin
wayake son kwacewa?Aliyu ya ce, nine da kaina
nayi binciken sanan nasan rigimarsu shi da
tsohon IG ne, kuma CP ne ya sa a kawoshi.AC
ya ce, gud, to zan sake mai maita maka, in an
kawo mai laifi da umurnin CP dan Allah ba
ruwanka da shi, in zaya shekara.Ran Aliyu ya
baci, ya ce, Sir, amma ba akan haka mukayi
rantsuwa ba.AC ya daga masa hannu ban ce
maka inason tunatarwa ba, sai dai ina son
kasani ka kusan kai CP bango, dan kana son
shiga cikin lamarinsa.Sanan kayi hanzarin cire
kanka daga cikin lamarin tsohon, ka barsa yayi
nashi binciken.Shiru Aliyu yayi, amma ji yake
tamkar ya kama da wuta don zuciya.AC ya ce,
ka iya tafiya.Aliyu ya fice da kunan rai.Matina ta
hangoshi cikin sauri ta bishi, yana tsayawa a
bakin titi tana tsayawa, ta ce barka da warhaka
yallabai.Ya furzar da wani huci mai zafi, sanan
ya ce barka dai.Tace ina tuni yallabai ya runtse
ido don yanason saita zafin da zuciyarshi ke
yi.Baya so ta fahimci yana cikin damuwa, sanan
ya budesu sun kada sunyi ja, sanan ya ce
matina zanfiso mu zauna a matsayin abokai, na
fada maki bani da sha'awar auran mata
biyu.Ina yi maki adu'ar samun mijin da ya
fini.Ta ce, samun kamarka ne yallabai sai an
tona, kunyi karanci a cikin al'umma.Ba duka
namiji mace kamata zata bashi kanta ya kauda
kai, har yanxu ina tuna ranar, ranar da na fada
maka ni da kai muyi soyayya koda bamuyi aure
ba.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Na fada maka cewa wata gara basa da zan
maka shi ne, zaka iya yin duk yadda kake
sodani na mallaka maka kaina, amma sai kayi
mun nasiha ka kuma nuna min cewa addininka
ya yi hani da hakan.Na sami kaina da sonka
tare da son addininka, sanan cikin aikinka kowa
yasan kana kwatanta gaskiya da amana.Ina
tsoron in auri wani cikin masu addininku ya sake
ni, dan ku hausawa ance kuna da sakin aure
amma kai nasan ba zakayi haka ba.Aliyu ya
kasa kallonta dan ta daureshi da jijiyoyin
jikinsa.Ya ce, Matina ki amshi addinina da zuciya
daya, sanan kisa a ranki zaki sami mijin da ya
fini, nima zan tayaki da adu'a.Ta gyara tsayuwa
kada ka damu, ni zan ci gaba da zaman samun
irinka, alfarma daya nake roko in zaiyuwu, in na
kiraka ka daga wayata.Sanan in kazo nan muke
rinka gaisawa.Ya ce dan mun hadu mun gaisa
ba damuwa,abin da zaiyi dan wuya ki rinka
kirana ina da mata, nasan bazata so hakan
ba.Ta rausayar da kai gefe, cikin raunaniyar
murya ta ce, na gode,ka fadiwa matarka cewa
ta rikeka da kyau, dan tana cikin matan da
sukayi sa'ar zuwa duniya.Murmushi yayi duk
lokacin da kuka hadu saiki fada mata da kanki,
na barki lfy.Yana kan mashin yana tunani ko me
yasa yake samun irin wanan matsalar?Mata suyi
ta sonshi suna binshi, amma shi bai damu da
su ba.Matina yana kulata ne saboda musulantar
da take sha'awar yi, ya san in yazama sanadiyya
zai sami ladan hakan.Daga nan tunanin sa ya
koma kan matsalarshi ta office, in dai da irinsu
AC da PC anya kasar nan zata gyaru?Lallai
kasarsa Nageria tana cikin wani hali, kullum
burin nasama ya danne na kasa, sam ba a son
gaskiya.In ka tsayawa halas dinka sai mutane su
rinka yi maka kallon dan kauye.Ya girgiza kai
sakamakon tuno tsohon nan da yayi, shi da
gaskiyarshi da filin sa da komai ba a tausaya
masa ba, kasancewarshi mai rauni ana neman a
zalunce shi.Mai dama yana anfani da damarsa
gurin cutar mai rauni, yasan in ba wani ikon
Allah ba tsohon nan ya rasa filinsa kenan, in
yasamu ya fita da ransa kenan.Duk lokacin da
irin wanan ta faru sai yaji tamkar ya bar aikin
dansanda, amma da ya tuna kudirinshi na kawo
canji da gyara, sai ya hakura, da wanan sake
saken ya isa gida.
Niko tun lokacin da na furta masa cewa ka
gaishe da matina cikin kuskure, ban sake yarda
mun hadu dashi ba.Kusan kwana uku wasan
buya muke yi har iya ta fahimci cewa na guje
masa, amma bata nemi jin ba'asi ba, yi tayi ma
kamar bata san me ni ke yi ba.Sam ban zaci
dawowarshi a wanan lokacin ba, domin cikin
kwanakin nan sai dare yake dawowa.Ni kadaice
a gidan,Iya tun bayan la'asar sun tafi Asibitin
dutse duba wata makociyarmu da bata da
lafiya.Sun tafine da ma da sauran
makotanmu.Na wanke hijabaina da na Iya ina
shanyawa,daga ni sai best, zanina kuma iyarshi
kugu.Ina shanya ina mitar cewa iya sunje sunyi
zamansu, nasansu da son tafiyar kafa, yanzu
haka ma da kafa suka tako.Banji sallamarshi ba
sai dai naji ya ce ina suka tafi?Na waywaya na
kalle shi, da gudu na shige daki dan kirji na duk
a waje yake.Dan murmushi yayi sanan ya shige
dakinsa.Ina zaune bakin gado ina kallon jikina
sai ganin shi nayi tsaye a gaba na har uwar
daki.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Naja hijabina, ya ce ina tambayar iya kina gudu?
Ya hade fuska tamkar bai taba dariya ba.Tsoro
ya darsu a raina, cikin in ina na ce,Asibiti suka
tafi.Ya ce, dan kada ki bani amsa shine kika
kwasa da gudu?Nayi shiru, ya ce kin min
banza.Nace yi hakuri dama zan dauko dan kwali
nein daura.Ya ce, ok, ni zaki boye min gashin
kanki?To ajiye hijabin in ga gashin tunda halas
dina ne.Gabana ya soma faduwa, na zame
Hijabina ya ce ashe ma ba wani gashi kike dashi
ba, cire hijabin daga jikinki in gani.Na kalleshi da
sauri ya kauda fuska yana yatsina baki, sai kace
zai ga abin kyama.Na cire hijabin na ajiye cikin
sauri kuma na sa hannuna na rufe kirjina.Ya ce
cire hannunki.Na cire tare da runtse idanuna.Sai
kurum naji yasa hannu ya turani baya, na fadi
rigingine na bude idanuna da sauri ina tsoro,
yasa hannu ya janyo best din sai ta yage, kirjina
ya bayyana.Tsayawa yayi yana kare mun kallo,
ya tabe baki, dama best din taki rubabiya ce?
Sallamar iya ta tsakar gida ce ta sani tashi
zumbur, na dauki hijabi saka.Cikin tsoro mai
tsanani na ce ga iya nan.Shi kam ko a jikinshi.Ya
tabe baki tare da daga gira sai me?A zato na bai
fahimci nufina ba, don haka sai nayi nufin
fahimtar da shi katafi da sauri kada ta ganka a
nan tayi zaton ko wani abu ne.Sai naga kurum
ya zauna bakin gado, na zaro ido dai dai lokacin
da ta shigo falo tana cewa Sadiya ina kika shige
ne?Kin ganmu sai ynzu?Da sauri na fito cikin in
ina na ce gani nan, kun...kun dawo?Eh, lafiya
na ganki a hargitse?Ta ce ba ko mai.Na yi
waje.Ita kuma ta nufi uwar daki, gabana yana
faduwa.Tana shiga ta ganshi zaune bakin gado
yanawaya, ta ce au, ka dawo?Ya ce, eh, na
dawo tun dazu, waye babu lafiya kika tafi
asibiti?Tace matar mai besfa ce a asibiti mukaje
duba ta.Ya ce, Allah ya bata lafiya.Ya mike bari
in karasa masallaci.Sai tin kunne na naji
maganar shi, a hankali yace sarkin tsoro.
Sam ya kasa bacci abin da ya kalla daga
yarinyar kurum yake tunanowa, juyi yayi har
gari ya waye sai ya dauki waya da nufin kiranta
dan yana togon cewa ita din halas dinsa ce.Sai
kuma ya tuna cewa yarinyar ba zatazoba, sanan
ga iya, kai!Shi fa ba zai iya jira sai sun tare
ba.Da safe naje kai masa abin kari, lokacin ya
gama shirin fita kawai zaiyi, ya amshi kofin daga
hannuna ya kurba.Sanan ya kalleni kin kawo a
latti, kin san da wuri nake fita. Na ce, a
shanarmu ce ta jike shi yasa, sai da masu shago
suka bude iya ta fita ta siyo.Ya ce my choice.Na
kalleshi zan sunkuyar da kai, ya ce a a kada ki
sunkuyar da kai, kalli cikin idona, bana son
wanan sunkuyar taki tana cutar dani.Na kalli
idon shi, ya ce yau ina bukatarki, na gaji ina da
mata kullum nine cikin azumi.Nayi kwalkwal zan
soma kuka, ya tsareni da idonshi, ya kuma
hanani sukuyar da kai.Cikin raunaniyar murya
na ce, kasan dai iya ba zata bari ba.Ya ce daina
karya da iya, na gano ma ba ita take hana ki ba
tun da ranar nan in an ji ta ce ki zauna da ni,
lokacin bani da lafiya.Ya mika min kofin tare da
cewa, zan fada mata, jeki abinki.Na tafi ina
mamakin shi, musanman da naji ya ce zai
fadawa iya zanso inji ko me zai ce mata na kasa
karyawa don zullumi, ina ta juya biredin dake
gaba na, kamshin turarenshi ne yasa gabana
faduwa.
Ya ce, iya na tafi.Ta ce to auta na, Allah ya
tsare.Ya ce, amin.Yana wucewa na sauke a jiyar
zuciya.Cikin jin dadi na gutsire biredi, na dago
kofin shayi na kurba sai naji takun sawunsa ya
dawo, take naji shayin ya sane.Ya ce au, na
manta iya.Ta ce, na'am iya za a zo a dauketa
taje ta gaida matar oga, ko bani ba wani zaizo
daukarta. Na kalli iya, shi dama vai jira amsaba
ya tafi, ganin kallon da take min sai na tsargu,
na taihashashen baki muka hada.Don haka na
ce, iya ke ce masa ba zanje ba,Allah ni bana son
xuwa.Ta harareni, bakya son zuwa ne kika bari
ya tafi baki ce ba zaki ba, sai nice zance karki
je? Bayan kun kitsa abinku?Ta taba baki haba
yayan nan, na fa rigaku zuwa duniyar har da
kuke son maidani wata sakara. Na ce iyya Allah
ba haka bane, ba mu kitsa komai ba, ni bansan
ko mai akai ba, ban san da wata magana ba sai
da yayi yanxun. Ta ce kwaji da shi, nifa bance
kada kije ba, ke da mijinki zan hana ki?Ta fada
cikin gatse sanan tayi tsakar gida tabarni zaune
cikin damuwa.Da naga har la'asar babu wanda
yazo nemana, kuma shi bai dawo ba, sai naji
dadi kuma na dan saki jikina. Cikin haka wayata
ta fara ruri, na daga a raina ina adu'ar Allah
yasa ya ce an fasa.Sai naji ya ce ki shirya
Usman zaizo ku taho.Sai da na daga murya
yanda iya zata jiyo, sanan na ce, yaya, Allah iya
ta ce bazanje ba. Iya daga inda take ta ce, a a
ba ruwa na ni Sa'adatu, ban hanaki ba ni ko
baku hada baki ba ni yar bada shawara ce.Yace
to najiyo abinda iya ta fada, don haka na baki
minti talatin ki shirya.Sai ya kashe wayarshi.Na
ce na bani yanxu yaya zanyi?Don Allah ku bani
shawara, inbi mijina ko in nunawa iya
harshashenta ba haka bane?
Taku Halima K/Mashi kemuku godiya. Awanna
gabarma Kanwarku Sadiya tana neman shawarar
ku, Saimun hadu a cikin littafi na biyu.Ku ziyarci
blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
Darajar Yayana4-01
Posted by ANaM Dorayi on 05:26 AM, 08-Apr-16
Under: DARAJAR 'YA'YANA
_________________NA
___________HALIMA K/MASHI
Na kalle shi cikin tsananin tsoro, na dafa kirjina.
Ni Yaya? In jiwa??? Saukar mari naii dau! Sannan
yace, Ba zan iya zama dakeba kina cin
amanata.Nadafe gurin tare da gigicewa, jina ya
gushe na wasu 'yan dakiku, jin abin nake tamkar
a mafarki,ahe kuka samun dama ne. Nasa ke
dago kai na kalle shi. Yaya mece ce hujjar ka da
zakayimin wannan zargin? Ya fita, na zauna a
bakin gado ina maida numfashi, cikina yanayi min
wani irin juyi. Ya sake shigowa, a fili nake furta
'Allahumma ajirni fimusibati..... Ya hada laptop
din shi ya dube ni cikin tsawa. Zo ki ga hujjar
tawa, na san kin san komai nema ki ke ki raina
min wayo. Kai tsaye ya shiga inbox din shi, Ki
karanta, duk da na san alaye kikeyi. Duk da dishi
dishin da nake gani na zaku in karanata,da farko
an rubuta.Sunana Sulaiman kuma bana bukatar
sai na fada maka in da nake, amma zan nuna
maka abinda matarka ke ciki da wani malami a
makarantar da take koyarwa. Kila kace ya akayi
nasani? To shi ne yake ba ni labari tare da yi min
forward din duk abin da suka tattauna, kuma
shine ya bani labarin cewa kana aiki ne a Abuja
dansanda ne kai.
Ga amsar da Yaya ya ba shi. "Me yasa ka ke son
fada min?"
Sulaiman. "Sabida tausayinka,sannan ina fatan
yanda na taimake ka nima Allah ya kawo mai
taimakona wata rana ko ba a kan irin wannan
matsalar ba."
Aliyu: "Ina jin ka."
Sulaiman: "To bari in maka forward."Sai ga
sunana ya fito:
Sadiya Abubakar. "Ina jin ka malam, ba nisa na yi
ba,na dan tashi ne savida banason a fahimci ina
tare da kai"
Malam: O.k, to me labari? Ina fata dai za ki shigo
gobe don na matsu inga fuskar ki tana burge ni.
Sadiya ina son ki fiye da matata dan kin fi ta
komai,wai ba za ki iya hada mana wata dabara
ba da za mu je wani guri mu kwana ba?
Sadiya Abubakar. Ba zai yiwu ba malam saboda
ciki,amma ka jira in haihu,ni kaina da a ce tuni
na same ka ba zan aure wannan mijin
nawaba,wanda da shi gara babu,kullum ba ya
gida,ga shi ya kara aure.
Malam. Hahhaha! Ki yi min irin wannan kunshin
da ki ke yi, kwanan nan zan sa a kara miki
matsayi a makarantar nan.
Sadiya Abubakar, turo min hoton sharabarki don
tana burge ni.
Ya kara yin sama kadan sai ga hoton sharaba an
turo. Gashi masoyina. Sulaiman. Kai! Ina jin dadin
kallonta,ina son yadda ki ke min shagwaba,in
muna tare,ina son hannuwanki masu laushi.
Sadiya Abubakar. Da gaske masoyina? Nagode,
zamu hadu anjima ina fata yau za ka yi min hira
cikin dare,zan sauka yanzun don yarana sun
dawo daga makaranta.
ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Jikina ya jike sharkaf da gumi,haka
fuskata,hawaye da majina sun gauraya, na dago
na kalle shi. 'Yaya ka yarda,wallahi ban san
komai kan wannan abin ba, hasali ma ni nawa
account din ba da sunana na bude shi ba.Ya
daka min tsawa, 'Ke rufe min baki! Wannan ba
sunan ki ba ne? Na ce, sunana ne. Ya ce, To,
inbox din ki ne fa,ko kina zaton wani yana shiga
inbox din wani? Na ce ni ban sani ba abin da na
sani kawai ba ni da wata masaniya kan wannan.
Ya ce, 'O.k, za ki ci gaba da raina min wayo
kenan? Ga shi nan kun yi labari a kaina kun
tattauna sirrin gidana, Allah Ya Isa Sadiya, ina so
ki sani zaman mu ya kare da ke. Na ce, 'Haba
Aliyu ka yi bincike mana? Jikina ya soma bari.
Yace, Abin daba zahiri ake yiwa bincike. Ya nufo
durowa ya yage takarda ya dauko biro daga
aljihun gaban rigarsa. Da karfi na furta. Yaya
Aliyu kada ka sake ni ba'a son sakin mace mai
ciki!!! Ban san cewa na rike hannunsa ba,sai da
na ji ya fincike ya miko min takardar,ban karba
ba sai dai idanuna sun haskomin in da ya ce
'SAKI DAYA. Na daga idanuna na kalle shi,sai na
ga yana dusashe min,ina kallon bakinshi yana
motsi,amma bana jin ,me yake fada,sai kuma na
ga ya soma juya min da shi da dakin a hankali
duhu ya mamaye idanuna sunfara dushi-
dishi,haka nan dana farka da dishi dishin na
farka,ban fahimci komaiba ban tuna komai ba
har tsawan dakiki.sannan naga Iya tsaye bakinta
na motsi,amma banajin me take fada.A sannu na
fahmci ina asibiti ne,sabida shigowar likita da
kuma ma'aikaciyar jinya(nurse)mai fararen
kaya,likitan ya dafa iya yana min magana da karfi
kinsan wannan?na kalli Iya,sannan na daga kaina
nace eh yace wacece? Dakyar na daga lebunana
nace mamana,ta kallon bkina ya gane abinda na
fada,naji yce Alhmdullh ta farfado yanda ya
kamata zata warware a hankali,kwatsam na tuna
cewar inada ciki nan take na soma tuna
komai,gaske ne yaya ya sakeni?na kai hannuna
na shafa cikina sainaji wayam,na yunkura zan
tashi sai naji Iya takamani ta maida ni nace iya
nayi 6ari ne?tace a'a kin haihu ne sai dai dan bai
cika taraba.
Nace y mutu? Tace a'a,yana can garinsu sun sa
shi a kwalba.
Na lumshe ido a fili na furta cewa,shikenan nayi
IDDA.
Wasu zafafan hawaye suka soma zubomin.
Iya tace Sadiya me kikace?
Na bude idanuna nima ina kallonta,take kuma
naji dan karfi na ciji le6e nace,iya ai in mace mai
ciki ta haihu tayi IDDA ko?Ta sake tattaro
hankalinta gareni,in an sake ta ba?me ya kawo
wannan tunani cikin kwakwalwarki?ta yunkura.
Bari in kira likinta nan ina zaton har yanxu b ki
dawo cikin hayyacinki ba Gam!nariketa iya! Ina
cikin hayyacina,na soma kuka,yanxu ni ba matar
shi b ce salati naji Iyar ta saka,sannan ta sake
tambayata,saki kuma sadiya?na kama
hannunta,kiyimin addu'a in cinye wannan
jarabawar.shiru tayi ta kasa magana sallamar shi
ce tasani lumshe ido,sam bana son ganinsa kojin
muryarsa.Iya ta subule hannunta daga nawa ta
fita,kuma cikin fushi,sanan taki ansa sannu da
yayan keyi mata.yabita da kallo har ta fita,y iso
kaina,na bude ido na kalleshi,kallon tsana,fuskar
shi babu alamar nadama yace.
Daga ganin yanda Iya ta fita rai a bace,nasan kin
fada matane,banso kikayi saurin fada ba,sabida
in rufa miki asiri,kamar yanda kikayimin.
Duk da halin da nake ciki ban san lokacin dana
tashi zaune ba,cikin kuka nace Aliyu bana bukatar
rufin asirinka,domin in kaji mutm yana neman
rufin asiri bashida gaskia,sai dai bansan mekazoyi
nan ba,tunda yanzu ba matarka bace,nayi
iddarka ka tafi banason sake ganinka,yace nasan
haka zuwa nayi in duba jikin ki matsayina na
yayanki kadai kuma uwar yarana,Nace,to
nagide,tafi yace yanxu kuwa,sai dai zan miki irin
halaccin da kikayimin,har abada iya bazata ta6a
jin dalilin sakin ba.nagirgiza kai,dole tasani,don ni
zan fada mata,ka tafi bana son ganinka,ka tafi,na
jefeshi da filo,Iya ta shigo,Gadanga fita daga nan!
ya juya ya fita.tazo ta kamani ina kuka ta
rungumeni a jikinta tana lallashina tana bni baki
har na hakura nayi shuru.
ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Kwana na 2 na dan murmure mutane suna ta
zuwa dubani,sunayimin barka,amma kishiyata da
yarana shuru bare yaya.tsakanin da da mahaifi
sai Allah,zuciyita tana can gurin yan yarana dana
tuno su sai inji hawaye yana bin kumatuna,Iya
tayi ta lallashjna.
Sati na 1 aka sallameni,Usman ne ke tsaye gurin
kula dani da biyan kudin Asibitina,sam baiyi
mana zanchenba,muma ba muyi masa ba,Anty
Abida kecemin wai yayi bakin cikin abunda Aliyu
yayine yasa shi jin kunyata.nace rayuwace kice
masa ba komai,shida yayi bai ji kunya ba sai shi?
Kai tsaye gidan Iya muka wuce,sun bani dana sun
mana gargadi banda jagwalgwalonshi.
Daran ranar Usman yazo kan batun sunan
yaro.Iya ta bamu wuri na mika masa
yaron,sannan na zauna muka gaisa,Ya dubeni
Sadiya,wallahi nauyi da kunya sun hanani in miki
jajen abinda ya faru,lokacin da Aliyu yazomin da
batun nan wallahi karkiga tashn hankalin dana
shiga,na tabbata an hado sharri ne don kawai a
tarwatsaku,hawaye suka soma kwaranya daga
idanuwana,na soma magana cikin kuka,
Yaya Usman wallahi bansan komai akan abinda
Abban Kausar yazo min dashi ba,sannan yaki
tsayawa ya fahmci hakan.A tunanina yafi kowa
sanin wacece ni,kuskurena 1 daya ce in rufe
account dina sai ban rufe ba,wannan kuma
mantawa nayi don ina ta kaina bana hawa.
Yace,kiyi hakuri ki dauki abin amatsayin
jarabta,Allah ya baki lafia,sannan ya raya miki
yaronki.wane suna za'ayimasa huduba dashi?
nace,ni bani da za6i a sa masa duk wanda
yakansance rabonsa.
Usman yayiwa yaro huduba da Abubakar,nace
sunan babana?yace rabon shine,Iya ta fito daga
uwar daki dama tanajinmu tace Allah yaraya
Abubakar Saddiku mukace amen. Ta
zauna,sannan tace,Usman abinda Gadanga yayi
sam bai kyauta ba,ba'a ta6a 6atamin rai b kamar
wannan tunda nazo dunia,Sadiyar ce bai sani ba?
in ya gaji da zama da ita sai yayi mata sharri?
abin da batayi da kuriciyartaba shine zatayi
yanxu wai tana bin wani Malami? Murya iya ta
soma rawa.Allah zai saka mata insha
Allahu.Usmn yace kiyi hakuri Iya,rashn bincike ne
kar kiyi masa baki.da sannun gaskia zatayi
halinta,nikaina baram baram muka rabu
dashi.ina kalln kiranshi dazu ban daukaba,
saboda ina son ya san cewa yayi laifi.nafada
masa in an bincika za'a gano duk wanda ya
shirya wannan sharrin sannu a hankali,mudake
aiki da internent muka san computer mun san
ana yin irin wannan sharri sai wani can ya bude
account din mutm ya kwace yayita aikata sharri
ko batsa ko kuma hotunan banza yayita turawa
da sunan mai wannan account mutane kuma su
zata shne.Inatasan inyimasa bayani lokacin
amma yaki'saida y iso gida ya aikata abinda da
yasha masa kai,amma insha Allahu komai zai
wuce a koma tamkar da.nayi yar daryar takaici
tare da cewa ta6di! Insha Allahu hakana bar
auren yaya.Iya tace insha Allahu kuwa,nidai
dama na guji hakan,amma ganin sun zauna lafiya
harda yan yaransu sai na saki jikina,ashe yace
tsiyar tana gaba,Usmn yace insha Allahu komai
ya wuce,yaba Iya yaron yamike tare da cewa
yana zuwa.jim kadan y dawo da manyan ledoji
dauke da kayan shayi zuwa su pampers.nace
yaya Usman dan Allah kabar dawainiyarnan dani
haka,yace haba dai ina abinyake?mukayi gidiya
tare da cewa ya gaida Anty Abida da yara,yace
zasuji.
Washegari da safe wayar Iya na kar6a na kira
Anty Abida nace mata kayan sawa na dana Baby
za'a kwaso min a gidan Yay Aly.iya tace ai ba
kayan sawa ba anjima zan nemi mota komai naki
za'a kwasomin tas.
Haka kuwa ranar a ka kwaso gadona da kujeru
dake falo tare da kayan kicin dina,iya da kanta
taje gidan.Mujidat sunata shewa da wadannan
yaren nasu,ta shigo da yaran makota da Anty
Abida suka kwashe.
ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Nace iya kingasu kausar tace a'a suna
makaranta.
Nasoma kuka,gaskia Iya zan kar6o yarana,wallahi
Mujidat bazata iya rikeminsu ba,Iya tce Sadiya!
nasan cewa da ciwo inaso ki danne ki kau da
kai,musawa Gadanga ido nace shikenan.
Cikin 'yan kwanaki duk na rame na kade ba na
iya cin abinci sai Iya ta matsa min da fada,sabida
tunanin yarana ina son in gansu. Wata rana Aisha
ta zo min yini, na ce don Allah ta je ta dubo min
yarana,amma tana zuwa gidan an datse shi da
kwado,cikin kuka na kira Yaya Usman ina
tambayar shi ina yaya ya kai min yara? Ya ce
Sadiya ki yi hakuri ya kwashe iyalan shi sun koma
Abuja. Na lura baniba hatta Iya ranta ya baci,
tace wato ban isa ma yace min zai bar garin
ba,shi kenan yayi in dai duniya ce ga shi ga ta
nan.
Nafi sati ina kukan yarana,sai da Iya ta saka aka
yomin rubutu wai na dangana,ni dai duk da haka
ban dangana ba.
Aliyu zaune a kan kujerar shi ta office,duk da
ayyukan da ke gabansa da kuma matukar son
aikin shi, ya kasa yin aikin. Baya ya tura kujerar
shi ya jingina da bango yana tuna tun daga
shigar sa dakin Sadiya zuwa yanda ta zube a
sume ya kwashe ta zuwa asibiti,ko da uban shi
ya mutu bai yi kukan da yayi saboda cin amanar
da Sadiya ta yi masa ba.A fili yake fadin,Sadiya
dame na rageki?meye bana miki,me yasa zakibi
wanina ina mijinki?Ya kalli saman silin,inasonki
Sadiya,saidai bazan iya zama dake ba,ya mike
tamkar an tsikare shi y nufi kofar fita,kai tsaye
gida ya nufa,kmar yanda ya zata yaran suna
zaune guri 1,Mama ta kwantar da kai a cinyar
Kausar shima Al'amin ta kafadarta yasa kanshi,ya
tsugunna gabansu.Kausar yaku ka zauna anan?
ina kayan wasanku?
Ta dubeshi da wayayyun idonta,Abba ka taimake
mu ka kaimu gurin Momy,kaga Mama kuka ta
gama yi yanzu,karya nayimata nace kaje
kawotane.
Ya rungumesu,nace kuyi hakuri zan kaiku ina
Auntynku?
Khausar ta ta6e baki,tana ciki.ya dafo fuskar
Al'amen ga mamakin shi sai yaga idon yaron biyu
yace kunci abinci?
Khausar tace a'a bama jin yunwa.yasa hannu ya
dauki Mama jikin yarinyar zafi rau ga dukkan
alamu bata da lafia. hankalinshi ya sake tashi,ya
kira Mujidat wadde ke can kwance kan gado da
yaranta tana faman yin sana'ar tata chatting da
abokanta,ta tura wayarta a kasan fiilo,sannan ta
tashi,yace yaya za'a bar yarannan?tace to ya
zanyi musu,suci abinci sunqi,na kunna musu TV
sunki,tome zanyi musu?
ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Yace ki dauko hijabinki mukai yarinyar nan
asibiti,bada son ranta ba suka tafi,,anbata
magunguna har da allura,sannan suka
dawo.ranar dakinshi yayiwa yaran
masauki,Mujidat anyo kwallia anzo dakin miji sai
ta tarar da yaran kwance kan gadonsa,ya tasa su
ya zabga tagumi,turus ta tsaya,Anan zasu kwana?
ba tare da yadubetaba yace eh.tsaki taja sannan
ta juya zuwa dakinta,Wannan ta zamar mata
baka,kuma tsanar yaran ta ninku a ranta,tana
murna ta kashe maciji ashe bata sare kanba,dole
ne tayi wani abu akan yaran nan,shikuma sam
bai runtsaba yatasa yaran yana kallonsu hawaye
na bin kumatunsa,bai san ko na mene neba
hawayen,na tausayin yaran ne ko na bakin cikin
da uwarsu ta kunsa masa?ckin haka Mama ta
farka,Momy kawai take kira,hankalin shi ya sake
tashi,zafin jikinta na nan,ya bata magani yasata a
kafada,Kausar ma tatashi ta zauna tsakiyar gado
tana kallonsu,itama kukan take amma na
zuci,dakyar Mama tayi barci,sannan yaje kusa da
Kausar ya dafata,'Yata kiyi hakuri kar karkiga
laifina,mamanku ce ta jawo hakan,Khausar tace
metayimaka Abba?intayi maka laifi ne Abba ka
yafe mata,kaji?yaushe zaka kaimu,Anty bata
sonmu Abba,yarungumeta,kiyi shuru zan kai ku
kinji,amma sai kunyi hakuri kun dan kara kwana
2 kinji?Haka yayita lallashinta har tayi bacci.
Hudu daidai aka bukaceshi wurin aikinshi,
sakamakon yan fashi da suka shiga wani
gida,dole y fice zuciyar shi cike da tunanin
yaran.Mujidat kuwa yana fita ta koma gurin dan
ta tare da cewa babu wanda zai hanani
bacci,tanajin lokacin da Mama ta tashi,tana ta
kuka amma matar nan taki fitowa,Khausar ta
farka taje ta dora kan Mama a kan cinyarta dan
bazata iya daukar taba tana ta jijjiga ta tana cewa
yi shiru Mama zan kira miki Momy,in kira miki
ita?tayi shuru.
Al'amin ma ya tashi ya zauna,kashi da fitsari
mama tayi,Khausar ta rasa yanda zata yi gashi
jikin Mama y saki,ba zata iya daukarta ba,haka
suka tasata suna kuka,har gari ya waye.Khausar
ta je dakin Mujidat ta same ta tayiwa danta
wanka tana bashi madara,ta ce, 'Anty Mama ta yi
kashi. Mujidat ta dalla mata harara, sannan ta
ce, 'To ina ruwana? Kije ki wanke mata. Khausar
ta dawo da kuka, suka ci gaba da zurawa Mama
ido.
Fitar Aliyu zuwwa takwas na safe ya kira Mujidat
sama da sau biyar yana tambayar yaran, tana
fada masa cewa suna bacci har yanzun basu
tashi ba. Badon ya kira ta cewa gashinan ba to
da zai samu yaran a yanda ya bar su, ko kuma
yanda suke. Jin cewa ga shi nan sai ta nufi dakin
da gudu ta dauki Maman zuwa bandaki inda ta
shiga wanke mata tana yi tana zagi,da ta fito sai
da ta rankwashi kan Khausar wai me yasa da ta
ji kashin ba ta kai ta bandaki ba?
Kausar din da Sadiya ke yi wa wanka yau ita ce
da yin wanka da kanta,sannan ta yi wa kannanta.
Maama tana ta rawar sanyi, Mujidat dama tun
da ta nade zanin gadon ta aje tare da cewa. In
ubanku yazo dole ya wanke ko inyardashi.
ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Tana hada musu tea ya shigo,duk suna zaune
rakube lungun kujera, Mama tana manne jikin
Khausar, ya isa gurin ya dauke ta.Mama ya jikin?
Khausar ta soma kuka, 'Abba don Allah ka kaimu
gurin Momy, kaga Mama bata da lafiya, tayi kashi
na fadawa Anty sai ta koreni, kuma har ta
dokeni. Ya kalli Mujidat rai a bace, da sauri ta ce,
'Ta shigone ba sallama, da yake ta san tun a
gaban uwarsu in sun shigo ba sallama yana
korarsu yace suyi. Khausar tace Allah Abba nayi
sallama. Nan yashiga ruwan bala'i, ya ce itamafa
zai iya rabuwa da ita kan yaranshi, ta soma kuka
duk abin da take yi baya gani, ta aje hada Tea
din ta nufi dakinta,nan ya hada musu kawai suka
sha da kyar, sannan ya shiga gurinta. Ya ce shi
dai ya roketa ta duba masa yaranshi amma in
har son datace tanaymaasa na gaskene, tsakanin
mata da miji nan da nan ya lallabata suka shirya,
kuma tayimasa alkawarin lura da yaran.Tun daga
ranar sai ta dauki salon da mata da yawa
sukeyi,in yana nan ta nuna kulawa in baya nan
sai zagi, hantara gami da kyara. Hakan ya sa shi
sakin jikin cewa zata rikesu, har ma ya daina
yarda da korafin Khausar na cewa ta musu kaza,
ta yi musu kaza.
Cikin wannan halin ya nemi makarantar boko
yasasu, sannan ya samo musu malamin
Islamiyya,sai dai sam yaran tamkar kurame ko
sun je makarantar basa magana bare karatu,in
an tashi break sukan hada kansu guri guda, kallo
daya zaka yimusu kasan suna da matsala.
Ni kam zuwa yanzun an samu wata biyu rabona
da yarana har na dangana da kukan fili sai na
zuciya. Haka nan kullum cikin tunanin su da
ambaton su tare da yi musu addu'a Allah ya kare
minsu. Wani dare nayi mafarki wai Mama ta rasu,
tun Asubahi nake kuka, Iya ta yi ta lallashina wai
taci ta koshine, duk da haka shida daidai na kira
Anty Abida nace tataimakeni tabani Yaya Usman,
tabani shi nace, 'Yaya ka taimake ni ka je ka
dubo min yarana, ina zaton akwai wadda ta rasu
a cikinsu,dan na yi mafarki. Ya ce, Sadiya nutsu ki
kwantar da hankalinki. Nace, Yaya don Allah
zakaje? To shi kenan zanje jibi ranar Lahadi. Na
ce, To yaya na gode.
ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ina ajiye wayar ya kalli Abida 'Wallahi ina
tausayin yainyar nan kinsan Allah banda ita,
wallahi bazani inda aboki yake ba,domin ranar da
zai bar garin nan sai da naje na sameshi, ba
yanda ban yi ba a kan cewa ya bar yaran gurin
uwarsu,sai ya ce shifa sam bazai bar mata yaran
shiba,tunda ita iskanci ta zaba,nace masa baka
da tabbas, kana yin abu sai ka ce bakaje
makaranta ba, wai kuma kana jami'in tsaro, ka
gaggauta maido da auranku ta hanyar sake daura
wani,domin idan ba matata ba ce nasan cewa ba
za ta iyaba. Kin san me ya ce? Abida ta ce, 'A'a.
Usman ya ce, Budar bakinsa sai cewa yayi ba zan
maida taba,kaima kana da dama bai haramtaba
inka shiga layin zawarawa,sai ka aure ta kasata
gidanka. Abida ta zaro ido tare da rike haba
'Lallai Aliyu ya dauki abin da zafi. Usman ya ce,
Shi duk ya manta abin da ya yi na zaci yarinyar
nan za ta tona masa asiri,saboda abin da yayi
mata, amma da yake 'yar halak ce. Abida ta ce,
In nice Allah saina tona. Usman ya ce mata, Da
yawama bazasu shanyeba, ita wannan yarinyar
daban ce, amma bazai ganeba sai nan gaba
(Nasan dayawanku kuma bazaku iya abin da
Sadiya tayiba ko idan kuma da wacce zata iya ta
fada muji! Duk da banayiwa kowace mace daga
cikin fatan makamacin wannan rayuwar...ANaM)
Abida ta ce, Inzaka je muje tare ina son ganin
yaran. Yace bari mugani. Har gida Yaya Usman
yazo yayi ta lallashina tare da daukar min
alkawarin zaije ranar Asabar ko Lahadi, sannan
ya ce ya yi alkawarin binciken duk wanda yayi
wannan kulli. Cikin kuka nake masa godiya. Haka
kuwa ranar Lahadi Anty Abida ta kirani ta sanar
da ni cewa gasu a hanyar Abuja,cikin raunanniyar
murya nace. 'Anty ki taimakeni in kunje ki kirani
mugaisa. Ta ce to. Na san ba kowa zai fahimce ni
ba, wasu za su ce na cika kawa zucin 'ya'ya,
amma duk wadda ta taba shiga irin wannan halin
ina nufin ta rabu da 'ya'yanta, ba wai ta yi
tafiyane tabarsu taje ta dawoba, ba wai sunje
hutubane, sakinta akayi,sannan aka kwashe mata
yaranta dole zata dandana irin abin da naji, ko
nake ciki yanzun.
Ina ta zaman jiran kiransu. Sha biyu da 'yan
mintuna Usman ya kira wayar Alliyu,a ringing na
biyu ya daga suka yi sallama a tare, Usman ya
amsa,sannan yace, Aboki ina zan same ka,ina
Abuja yanzun haka. Aliyu ya ce, Ina office ko
zaka karaso? Aliyu ya ce, Shi kenan.Sun sameshi
bakin hanya sannan suka karasa gidan.Abida sai
kallinshi take duk ya rame suka gaisa, sannan
suka isa gidan.kamar kullum yaran suna takure a
gurinda suka maida tamkar gurin zamansu,wato
gefen kujeru,Mama da Al'amin duk sun jingina
jikin Kausar wadda suke ganinta tamkar uwa a
garesu,domin itace take yi musu duk abinda
uwarsu take musu,in har kaga Mujidat tayi musu
wani abu to tabbas mahaifinsu yana gidan.
Ko da sukaji sallamar mahaifinsu basuyi wani
yunkuri tashi ba don taryarsa.sam Abida har ta
zauna bataga yaran ba,Aliyu ya kalli gurin.
ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Khausar ku taso mana,yaushe zaku daina zaman
gurin nan?
Abida ta zaro ido tare da mikewa"Khausar!yaran
suka mike da sauri dukkansu suka rugo da gudu
tare da rungume Abida sannan sukayi gurin
Usman,Aliyu ya cika da mamaki,ya manta rabon
dayaga yaran haka suna murna ya nufi ciki kiran
matar, Abida duk da cijewar da takeyi sai da
hawaye suka soma yimata sintiri,Usman ya kalle
ta ya girgiza kai alamun tadaina, amma ta kasa
saboda yanda yaran sukayi baki suka rame,gashi
ba wata cikakkiyar tsafta,kitson kan su Khausar
duk ya tsufa,ba'a ko ganin layin kitson.ta tuna
yanda yaran suke kansancewa tsaf cikin tsafta da
tsantseni kowa sha'awarsu yake,ta dauki mama
ta rungume.Khausar tace,aunty maman mu fa?
cikin rawar murya tace,lafiyarta kalau,tace a
gaidaku,Al'amin yace yaushe zatazo? Khausar
tace,kai sunzo tafia damu ne.ta kalli Usman
Uncle ai dai zaku kaimu gurin Momy ne ko?kafin
Usman yayi magana,Aliyu suka fito da Mujidat
tana sanye da riga da siket na shadda mai ruwan
kwai,shikuma yana sa6e da Abdul,wanda aka
tsafta ce shi ckin jeans blue da riga ja,sai wani
dacin rai takeyi.ta zauna tana gaida su cikin
yatsina, Usman ne ya amsa Abida kam ta kasa
magana don bakin ciki.
Usman yayi mata sako cewa don Allah ta
nutsu,sabida yaran sun soma kuka suma.Aliyu ya
kalli Mujidat,a kawo musu abinci da abin sha
mana,ta tashi can ta kwalawa Khausar kira da
sauri ta tapi,sai ga ta da pure water leda biyu da
dan kwalin juice,sai kofi 2,ita kuma ta fito da kula
yar madaidaiciya. Abida ko ruwa batayi burin
shaba,bare abinci,Usman dai ya dan kurbi Juice
din da Aliyu ya tsiyaya ta mika masa,daidai
lokacin ni kuwa na kasa hakuri nakira layin
Abida,ta dauka yanda naji muryarta sanyi
kalau,sai na soma kuka,nace Aunty ta mutu ko?
Abida tace a'a lafiyarsu lau,bari kijisu.
Ta kamo Kausar zoki gaida Mamanki,cikin doki ta
amsa tace Momy,nace na'am...'kukan yaki tsaya
min,cikin rishn nace kausar.ita ma yarinyar ta
saka kuka tana cewa Momy don Allah kizo ki tafi
damu,hankalina yakara tashi nace,Khausar kuyi
hakuri kinji?ki lura da yan uwanki kinji? Cikin
kuka mai tsanani tace,wayyo Momyna! don Allah
zamu zo Momy.
Abida cikin hawaye sharkaf ta amshi wayar ta
rungume Khausar,Sadia yaya zakiyi haka?kinsan
zaki kara tadamin hankali ne,kika kirani,nace yi
hakuri Aunty,Aunty kibani Al'amin da Mama.tace
a'a bazan baki suba dan ganin Khausar tana kuka
suma gasu nan sunayi.Khausar ta sake janyo
hannun Aunty Abida tana cewa,Momy don Allah
kinji Momy!!! Tilas na kashe wayar na dasa sabon
kuka,iya dake kallona itama hawayen take
sharewa tana cewa "Sadiya kidangana da 'ya'yan
nan. Na kalleta Iya kitayani addu'a Allah yaba ni
hakurin jure rashin su kinji Iya? Tace to Sadiya ta
taso ta kamani ta rungume tana lallashi tamkar
yarinya karama. Su kuma a can Aliyu ya kalli
Khausar meye abin kuka? Mujidat dake gefe ta
tabe baki tare dace " a to" Ta gatsina hanci gami
da hararar Abida tana magana kasa kasa Abida
tace Kuka ya zamar musu dole wadannan yaran
kanana a ce an rabasu da uwarsu? Aliyu na
rokeka arziki kayi hakuri ka bamu yaran nan
mutafi dasu Uwarsu tana cikin damuwa Yatabe
baki Kadan tagani ma kin san Allah bazan bada
yarannanba ko zasu mutu daga ita har su,Usman
yadagawa Abida hannu alamun tayi shiru sannan
yakalli Aliyu Aboki zamu tafi daman munzo ganin
yarane,ya dauko ledar gefenshi Khausar yi shiru
ga tsarabarku tana sheshshekar kuka ta amsa
tana ji da dan nauyi har ya mike ya cewa Abida
tashi muje sai kuma ya tuna da binciken shi
yadawo yazauna yace Aboki ina son wani taimako
daya Aliyu ya kalle shi inajin ka. Yace zaka bani
sunan wannan account din zanyi searching zan
gudanar da wani bincike Aliyu yaruntse ido
wallahi bana son a tunamin komai game da ita
ban san tuna account din nan. Usman yace bazan
samu ba kenan? Aliyu yakalli Mujidat dauko min
laptop dina sun kunna inda suka fito da komai.
Aliyu yadauke kai inda Usaman yashiga bincike
cikin sa'a akwai lambar kuma ta MTN sannan
shima Malam din ya dauki lambarsa haka nan
yadauki ta wanda yakawo gulmar wanda yace
sunan shi Sulaiman yakulle komai sannan yamike.
Mujidat tazaro ido tana kallon Usman cikin
zuciyarta tana tsine masa, suka mike suka tafi
Abida tana kuka su Khausar na kuka haka aka
rabu yaran suka ruga daki suka dora sabon kuka.
Mujidat da gudu tashige daki lokacin da Aliyu
yatafi rakasu Usman takira layin Jamilu daya
dauka yace lafiya? Ina ta kiran layinki kin ki
dauka don kada ki bani cikon dubu 2 na koh?
Tace zan baka mun tashi daga kaduna ba shirine
zan aikowa Anty Ramata zata baka amma kana
ganin asiri bazai tonuba? Yayi Tsaki Sungama su
hkr Mujidat ta sauke ajiyar xuciya sannan takashe
wayar.
ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Aliyu yakalli Usaman Aboki na godefa tunda
abinnan yafaru banga wani nawaba sai yau ga
tunanin Iya a xuciyata bansan ya zan tunkaretaba
dan nasan Sadiya ta fadamata abinda nabinne.
Usman yayi murmushi, ay Sadiya mutumce
wallahi har yazu Iya batasan wancen zancenba
kayi mamaki koh? Aliyu yayi ta kallon Usman
tunanin cewa zata fada shiyasa ya tattara ya bar
kaduna ya maimata bata fadaba? Usman yace ko
daya Aliyu yace Uhm duk na zata ta fada. Usman
yace shiyasa nace kayi bincike kan wannan laifin
dakake zarginta. Aliyu yace tafa aikata laifinnan
bazanyi mamakiba sabida shaidan ba rago bane,
nima nazaci zan tsinci kaina acikin haka?Usman
yace inma gaske ne bazakayimata adalci ba? Aliyu
yace adalcin kenan nayi mata na saketa kalau ba
tare danayi mata dukan hauka ba sannan banda
ta fada na so in ramawa kura aniyarta wato in
bar zancen tsakaninmu inkuma dauki nauyin
zunubin zagin da za'ayi min na sakinta batare da
tayi min laifi b kawai sai ta tona. Usman yace
Aliyu kenan bari muwuce Allah yabayyana gaskiya
inga yanda zakayi Aliyu yace wahala kawai zaka
sha amma gaskiyar ce tabayyana in kalura da
hirar data gudana atsakanin ta da malamin.
Koda suka tafi ya jima bai shiga gidanba yana
mamakin yanda Sadiya taci gaba da rufa asirin
shi yayi ta ganin kiran kiran yayunsa. Yaya
Sulaiman, Yaya Sani, Yaya Zakari, kai har kawu ya
kirashi amma ya ki dagawa nashi ganin asirin
shine yatonu zasu kira suyi Allah wadai dashi to
shi in ya dauka dabatun sakinnan ze kare kanshi
Aliyu Kenan.
Koda Anty Abida ta dawo sam bata nunamin
cewa yarana suna cikin matsalaba, illa fadan da
tayimin na kukan danayi tace shine yasa su kuka.
Jin hakan sai na kwantar da hankalina kadan, don
har Usman ma yace min kada in damu suna
samun kulawa. Haka na dangana sai dai duk na
rame yarona kawai ke tafka kibarshi har mukayi
kwana 70 nace baxan koma aykiba,Iya tazare min
ido dole nakoma yanzun mota nake hawa zuwa
gurin aiki dan ban waiwayi motarshiba.
Ranar asabar ina zaune a tsakar guda yarona
yana cinyata na kifa shi ina karanta dan karamin
alkur'ani mai girma suratul Bakara kamshin
turaren yaya naji kafin sallamar shi tabiyo baya
badon na san mahimmancin amsa sallama ba da
baxan amsaba, sannan banko dago kainaba bare
nadube shi yayi sallama dakin Iya tana ciki can
kan gado don haka bata jishiba shima din be
tankaba yashiga dakin. Natashi nagoya dana naja
Hijabina a igiya na dauki pose dita da yan canjina
napita sai gidan Aysha, taganni hankali tashe tace
lafiya har yanzu baki kwantar da hankalinkiba?
Haba Sadiya. Naxauna hawaye suka soma zuba
daga idona nace ni na hakura Aysha yayane yazo
gidan yanxun, wallahi shine yafama min bakin
cikin daya cusamin,ta dapani yi hakuri meyace?
Nace bamu ko kalli junaba fitowa nayi dan ko
ganinshin shi banasan yi. Aysha tayi ta lallashina
tana bani hakuri tace kin fadawa Iya shima
abinda yayi? Nace har abada baza aji daga
bakinaba wannan ya wuce saidai taji gurin wani.
Ina gisan har dare sannan suka rakoni ita da
Bellonta, itama dai tana tayi min korafin cewa
Bello yanzun sai bakin halaye yake shigo mata
dasu, ya soma doguwar hira sai yakai sha daya
bai dawo gida ba yayi ta 'yan daure daure da
fadace fadace. Nace lallabashi zaki Aysha kiji ko
kin masa wani laifi ne kar ki dauki fushi da
mijinki karamar matsala tazama babba, kar kiyi
sanadin dazaki nesanta kanki da yaranki ni na
isheki misali Aysha 'ya'ya sune rayuwar uwa
kamar yanda uwa take rayuwar 'ya'ya yanxun
duk macen da bata tare da 'ya'yanta ina tausaya
mata dan na dandani ciwon dataji. Cikin bacin rai
nasamu Iya nace, Iya ya ne? Tace Sadiya ina
kikaje? Nace gidan Aysha natafi kiyi hakuri
banfada miki ba wallahi ganin yaya ne naji bazan
iya zaman gidanba shiyasa natafi. Tace baki
batamin raiba Sadiya bacin ran Ali ne yaron nan
na zata yayi nadama ne ashe zuwa yayi yabani
hakuri, nace me kayimin? Ni awa zakazo bani
hakuri? Ali banzaci zan sake sakaka a idona ba.
Yace sabida me zaki ce haka Iya? Na tafine don
ki huce sannan inzo in baki hakuri dan na san
cewa babu wanda zai fahimceni ko yabani
gaskiya akan sakin danai wa Sadiya duk kuwa da
cewa yin hakan ba laifi bane. Iya tace sai na tari
numfashinsa cikin gatse nace to dama Ali waya ce
kayi laifi? Ko guda banga laifin kaba don ka auri
mace kana sonta lokaci guda kuma kaga ka daina
sonta ko ta maka tsufa ka sake ta sai ace kayi
laifi? Laifin da kayimin daya ne bata min ita da
sharri wai tana bin maza wannan kazafi yayi min
ciwo sosai domin yarinyar nan har ta gama
kuriciyarta a cikin gidan nan kaganta kace kana so
ka aura bata taba dauko min maganaba. Iya tace
Sadiya yau har nauyin na aje gefe na tsakanin da
da mahaifi na tambayi gadanga cewa ko ba
budurwa kasame taba? Sai ya sunkuyar da kai
nace in ba budurwa kasameta ba sanar dani.
Yace Iya duk ba wannan zancen bane ai mutum
yakan canza kuma ni fara koyarwar ta dinnan ne
ta hadu da abokan banza. Iya tace na ce dakata
bata tare dakowa nabanza kai dai ka gaji da ita
ka saketa ka kuma hada mada da sharrinka na
'yansanda to kaje Allah ze sakamata ina raye sai
naga sakayya sannan 'ya'yanta in kun lura dasu
kuda Allah inma kun wulakantasu kuda Allah. Ya
kasa magana sannan wai ina jaririn? Nace yana
gurin uwarsa ai danaga baka waiwayeshi ba na
zata zakace ba danka bane? Yace ni bance ba
Iya, yaciro kudi ya aje wai gashi kibata sabida
siyan wasu abubuwan na yaro Iya tace dauki
kudinka babu abinda muka rasa yayi shiru can ya
sake cewa. Ina kara baki hakuri iya nace kai ne
da hakuri amma dauki kudinka in ba so kake
kaga bacin raina ba,ya dauka yafita.Na sauke
ajiyar zuciya nace, Iya na gode dabaki karba ba
na sani sosai Iya cewa bashine yayi min sharriba
wasu ne daban amma takaicina yanda yakiyin
bincike kuma yayarda cewa nice, kobe sakeni ba
aure baya yiwuwa da zargi.Iya tace ay na gaya
masa nace lokacin daka fito da abunka kana
ganin ya maka tsufa sabo kake so, lokacin wani
kuma zai ga cewa na kannan shine sabo agurinsa
Allah yayi miki zabin Alkairi, nace amin.
Daren ranar su Yaya Sulaiman suka zo da shi su
hudu wai iya tayi hakuri tayafe masa sannan
suka matsa masa cewa ya maido da matarsa
kuma ya yarda amma da sharadin zata daina
koyarwa. Ina kwance kan gado a uwar daka ina
jin su tamkar in taso in fito in ce bazan koma ba
amma sai na tsaya inji me iya zatace? Ay kuwa
sai naji Iya tace da farko dai kamar yanda na
shaida masa dazun ni bai min laifi ba bare ya
bani hakuri in da ace ni wata ce lokacin da
rigimar tafaru yaneme ni mana sai kurum yatafi
ya aikata son ransa yanzun yazo yana ban
hakuri,ni a wa? Batun kome kuwa ga matarsa
nan adaki tazo in zata koma bazan sata ba kuma
bazan hanata ba, Tadaga murya Sadiya na'amsa
tace zo nafito da dana akafada na zauna
gefe.tace nasan kinji komai dan haka in zaki
koma sai ki fada musu, shidai sun bashi baki ya
yarda,Budar bakin da nayi sai kuka nace yaya
kuyi Hakuri da abinda zance in Yaya Aliyu ne ya
rage namiji a doron duniya wallahi tallahi bazan
aure shiba bana kosan ganin shi ya fita a raina
sam.Iya tace tashi ki koma ciki sannan tace kunji
koh? To kuma na roke ku da kar ku sake
zuwamin da wannan zance ko gaba an rufe
wannan babi in dansa ya isa yaye yazo ya
dauka,bansan lokacin da nace Iya harda wannan
ma za'a rabani tace Allah ya baki wani mijin na
gari ki haifi wasu yayan Sadiya,sai lokacin Aliyu ya
dago ya dubi Iya sabida yaji zafin kalmarta
sannan ya sake sunkuyar da kai Aliyu yaba yaya
Sulaiman kudin yadan matsa yace iya ayita hakuri
shin ina Sadiyarne? Na fito ya miko mini nace a, a
yaya muna da komai na koma ciki yace ke Sadiya
zoki karba hakkinkine da danki Iya tace tunda
tace bata so saiku barta ko ku tashi kuje zamu
kwanta...zamudakata anan,fatan zamuyi sallar
juma'a lafiya
ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
Darajar Yayana4-02
Posted by ANaM Dorayi on 12:11 AM, 12-Apr-16
Under: DARAJAR 'YA'YANA
_________________NA
___________HALIMA K/MASHI
Haka suka fita jiki babu karfikowa ya nufi gidan
shi suka nufi nasu da safe na gama yiwa yarona
wanka kenan sai gashi ya shigo sanye da
kananan kaya sai yaune ma na kalleshi yadan
rame yayi duhu natabe baki sannan na bata rai
Iya ta fita siyo mana biredi na gama na kwantar
dashi kan kujera zan fita da ruwan sai naga yakai
hannu zai dauke shi da sauri na dauki yarona na
sashi a bayana na kwance zanin jikina wanda
dama na dora ne a saman dogon wando na
goyeshi sannan na dauki ruwan, yako ji haushi
cikin zafin rai yace me kike nufi? Nace duk
abinda kake nufi ,na kalleshi sama da kasa yace
nufinki bazan dauki yarona ba? Nace au shima
danka ne? Na zata inda nake zuwa na yoshi yace
karfa kiga Iya na daure miki gindi ki zata har kin
kai matsayin da zakiyi min rashin kunya dan
kinga na kyaleki ban dauki mataki a kankiba, nace
don Allah kaini kotun musulunci yace bani yarona
in ganshi? bazan bayarba,Sallamar Iya tasa
yazauna kan kujera nima nazauna, na kwantoshi
nasoma shafa masa mai Iya tashigo dakin
ganinshi sai ta daure fuska tace lafiya me kuma
yakawoka? Yace Iya gurinki in gaisheki tsaki taja
sannan tafita zuwa kicin Yakalleni Nan gidan
ubanane ba mai hana ni zuwa. Nima na
harareshi ina ruwana Allah yasa nima ina da
gidan uban. Kafin yayi magana sai ga Iya ta shigo
da ruwan zafi takalle ni zo ki karya cikin jego,
kawo shi in sa masa kayan. Nace to, bayan na
karasa sa masa pampers din na mika mata shi.
Ina zama yayi caraf ya mika hannu ya dauke shi
a hannun Iya na kalleshi cikin tsana nazauna
shima yaharareni sannan yazauna yana kallon
yaron, banzaci ya san sunan shiba sai naji ya ce
Iya Sadiq ma dani yake kama sosai yanda ban
tankaba itama bata tankaba. Yarungumeshi tsam
a kirjinshi, sai kurum nafita tsakar gida ina
karyawa. Ashe Iya ma ta shige uwar daka dan
haka yadauki kayan yana sa masa yagama
yamike yafito da shi ganin zai yi waje nabishi da
gudu a ganina zai tafi da shine, ina fadin Iya
zaitafi dashi nasha gabanshi,bani yarona dasauri
Iya tace kyaleshi yatafi dashi din seme? Nasoma
kuka shikuma sai hararata yake yi yaja tsaki
yawuce nace Yaya inka tafi dashi saina tona
asirinka tsam yatsaya sannan yawaiwayo yakalli
Iya itama shi take kallo sannan takalleni na isa
gabanshi namika hannu Bani yarona.Sai yamiko
minshi sannan yafita da sauri naje kan kujera
nazauna ina cika,Iya ta iso gabana wane irin
asirene zaki tona masa?yaken dariya na kakaro
birgace kawai nayi masa babu komai Iya. Tayi yar
dariya haba Sadiya shi mahaukacikane bayan ba
wani sirri jikinsa yayi sanyi haka? In dai da wani
abu kifadamin,Nace ba komai iya tace oho miki in
ma dashi, shiyasa wani lokacin banasan shiga
shirginku.Ni dai sim sim nayi daki.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Hudu da ashirin ina kwashe tuwo naji sallamar
shi ciki ciki na amsa, banyi tsammanin ma zaijiba
na dago nadubeshi cikin tsana, sai naga
hankalinshi yana kan yarona wanda nashimfida a
tabarma akan katifar shi nakwantar dashi akofar
daki Iya tana zaune kusa dashi. Dagudu na aje
tuwon dake hannuna nafito har ina tsallaka iya
nasuri dana nasa a baya naja zanina a igiyar
shanya nagoye shi sannan nakoma kicin ina jin
tsakinshi a raina nace kadai karata can.Daga inda
nake ina jiyo shi yana gaida Iya, dakyar ta amsa.
Yace zantafi zaria dama wani ayki nazoyi Kaduna
akwai wani malami ne da ake zaton kasurgumin
dan fashine to kan shi nake aiki,rahotanni sun
same mu cewa ya koma Zaria acikin satin nan
kafin inzo dan wata na biyu kenan ina nemanshi
tun daga Maiduguri nake biye dashi har zuwa
nan ina son Iya kitaya ni da addu'a Allah
yataimake ni. Iya tace Allah yabada sa'a. Yace
amin. Tace malami kuma dan fashi in banda son
duniya? Ay irinsu suna da yawa Iya kuma yana
siffatuwa ne da malai manyan malamai yana da
ilimin, sai dai shi dan fashine ga tsafi ,sama da
shekaru goma ankasa kamashi,kingako kamashi
nasarace. Iya tace Allah yataimaka yace amin
yaciro kudi gashi Iya. Tace a'a ai na fada maka
bamu da bukatar komai,yasake tausasa murya
Iya wannan fa tsakanin mune ni dake in baki
amsaba sai inga tamkar kin cire ni a tsatsonki,
Ya'ajiye gefenta. Iya kiyafemin natafi.,Bata ce
komaiba kuma bata dauki kudinba yazo bakin
kicin yajeho min wasu mukullai ga mukullin
gidanki nan kije ki dauki motarki aciki. Nadubeshi
fuska daure cikin harara nace bani da gida bare
mota in kana nufin motarka to bana so,tsaki yaja
sannan ya wuce batare daya dauki mukullanba.
Nafito gurin Iya rai a bace nace Iya naga har
kulashifa kikayi kuna hira har yana wani baki kudi
kina karba? Iya tace kin san shi naci zai tayimin
shiyasa narabu da shi ya aje kudin dan yatafi
yabamu guri sannan ina zulumin yanayin aykin
nan nashi wannan malamin kuwa dan fashi
tunkararsa hadarine ina tsoron karya halakashi.
Gadanga shiba mutumbane mai son neman tsarin
kai, da kaikayi koma kan mashekiya,da kai
magana zaice yana addu'a an san dai ita ce
dama kan gaba. Don haka itama Iya ban tanka
mataba wato ma tausayin shi takeji.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Aliyu yayi masauki unguwar Mazan Gudu gidsn
limamin unguwar da sunan cewa shi bakone
matafiyi ne. Hannu 2 aka karbeshi kwanansa 2
yace a nema masa daki na haya yana son yadan
kama sana'a yafada musu cewa rani yake Zuwa
garin Kaduna daga Hadeja yake,Liman har yayi
masa tambaya game da wasu unguwanni a can
Hajejan Allah yasa garuruwan da Aliyu yasani ne
ya kuma fada masa cewa ya sani. Liman yace sun
zauna sun danyi karatu a garin shekarun baya
lokacin suna yawon neman ilimi. Liman yace Aliyu
yazauna ga daki nan a zaure a gidansa na
dansane dake karatun boko a jihar sokoto a
jami'ar shehu dan fodio. Cikin sati daya yasaba
da makota. Akwai wani dan dandali da mazan
unguwar ke zama ko in ce majalisa. Tuni Aliyu ya
saba da yan majalisar in da ake zama ayi ta
labarin wane da wane ko duk wanda yagifta.
Anan yasamu labarin wannan malami daya sauka
gidan sarkin malaman kusfa ance yanda ilimi
sosai kuma yana bada fatawa. Aliyu yace dan
Allah wanda yasan gurin yayimasa rakiya don
yana son daukan karatu. Kullum 'yan majalisar
nan suna mamakin Aliyu duk irin shigar dayakeyi
ta kaya marasa kyau amma fatar jikinsa bata
nuna cewa daga kyauyen hadeja yakeba kamar
yanda yafadamusu. Akwaima wanda yakecewa
shifa yana wa fuskar Ali kallon sani.
Cikin sati 2 sukayi sabo da Malamin wanda yasaki
jiki da Aliyun amma sai dai Malamin ya fadawa
Aliyu shifa malamine mai yawon yada da'awa
don haka daga nan zai wuce Katsina ne tafi tafi
har Nijar. Aliyu yace in ba damuwa zaibi shi,Aliyu
ya lura da yanda malamin ke daga waya akai-
akai sannan ya lura da irin kudin da malamin ke
rabawa jama'a sadaka. Duk binciken dayayi ya
gano cewa malanin ne wanda yake nema sai dai
dama yana da labarin matsawar malamin yana
cikin daki bazai kamuba. Ana gobe zasu bar garin
kamar yanda suka shirya har da shi Aliyu
shikuma ya daura aniyar kama shine aranar
jajiberen tafiyar. Karfe 2 sun taso daga sallar
Azahar Aliyu hankalinshi tashe burin shi yanzun
idan sun iso kafin su isa gidsn malamin ya sauke
yashige daki. Aliyu yakalli malamin. Allah
yagafarta malam naga jama'ar wannan garin
suna alhinin rabuwa dakai shin bazamu dan kara
kwanakiba? Malam yakalli Aliyu ina da dalilin
barin garinnan asubahin gobe.Aliyu yace Allah
yasa haka shine mafi Alkairi. Malam yace ameen.
Sai dai kai ina mamakin yanda kake son bina ban
cika sakewa da mutaneba amma kai raina ya
kwanta dakai amma daganinka ka taba zaman
cikin birni? Aliy yace e duk cikin gari nayi
rayuwata ban zauna gidaba, Malam yayi
murmushi toh Aliyu sai dai kayi hakuri ina zaton
bazanje dakaiba. Aliyu yace saboda me malam?
Malam ya gyara tsayuwar wato malam Ali an
sanar dani cewa duk inda zan shiga kada in shiga
da mutumin cikin gari domin shine zai zamemin
hadari cikin rayuwata. Aliyu yace Allah gafarta
malam an fada maka kamannin shine munyi
kama? Yace ko kusa an dai ce min zai shiga jikina
sosai kuma zai cutar dani a rana irin ta gobe
shiyasa duk lokacin dazan bar gari nakan barshi
tun asubahi. Aliyu wanda ya kosa yaga isowar
jami'an tsaro yace toh Alagafarta yaya zaka yarda
da irin wannan kila ba gaskiya bane. Malam
yadafa kafadar Aliyu inayimaka fata nagari Allah
yasa zamu hadu wata rana amma wanda yafada
min zancen nan yasha fadamin zantuka suna
tabbata ina ji ajikina zamu sake haduwa da.....
Jiniyar motar 'Yansanda ce tasa malam bai karasa
zancenba sai Aliyu yaga malam ya daga kafada
yasa gudu cikin azama da kwarewa Aliyu yaciro
bindiga daga bayan wandasa ya harbi malam a
kafa take malam yafadi amma burinshi yakai daki
dan haka ya yunkura Aliyu yayi azama yacafkeshi.
Mutanan gurin sun cika da mamaki harma suka
taso da nufin jin ba'asi sai dai kafin suji dalili tuni
yan sanda sunyi zobe a gurin sun kuma cafke
wasu daga cikin makarraban malamin sannan an
samu muggan makamai cikin kayan malamin da
kudin kasar Amuruka(Dollar) da irin namu na
gida. Mutanan unguwar suna ta al'ajabin lamarin
yayinda wasu ke mamakin Aliyun wanda suka
zata shima yana cikin mukarraban malam. Ta
gidan lima suka bi mai masaukinsa,Aliyu yayi
musu sallama yadauki yan kayan shi tare dayi
masa alheri haka ma yen majalirarsu yatafi yabar
su da labarinshi tare da jinjinawa aykin shi.
Cikin wata hudu da aka damka aykin hannun
Aliyu ya samu nasara ya fara bibiyar malamin
tundaga maiduguri har kawo Kaduna sannan
Zaria inda yayi nasara sakamakon haka ya samu
lambar yabo tare da karin girma zuwa
mataimakin kwamishina na can Abuja haka nan
nasarar taja masa farin jini inda akayi ta haskashi
gidajen talabijin. Ina kallon Iya tunda Aliyu yazo
da batun aykin nan kullum cikin yimasa addu'a
take tare dayawaita sadaka. Araina nace da da
mahaifi sai Allah. Dubi duk haushinsa datakeji be
hanata yimasa addu'ab. Inzanje aiki yanzu gida
nake barin Sadiq sabida yana shan kamu. Iya
tasani gaba tana min fada wata ranar Litinin na
shirya zantapi aiki. Sadiya! Dan Allah shekarunki
nawa? Nace me yafaru Iya? Tace fadamin. Nace
26 Tace dubi duk yanda kika koma ba wani ado
ba kwalliyar da kikeyi ada, ki dage ko dan ki ba
Gadanga haushi,amma kullum sai kina yawo
kamar me takaba,Nace ni banima da kayan
kwalliyar,tace inzaki dawo ki tsaya kasuwa ki saya
in ma baki da kudi in baki,nace ina dashi a cikin
account dina,tace to.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ina zaune bayan na sallami daliban ajina sun fita
break nazabga tagumu ina tunanin zancen Iya
gaskiya ta fadamin bazan tsaya in tsufar da
kainaba tilas in nafita in shiga banki sannan in
shiga kasuwa. Shigowar alert ne ya tsaida
tunanina na dauka na duba kudi ne naira dubu
saba'in sannan yaya ne ya turo min. Haushi da
bakin ciki kamar inyi kuka don haushi. Dakyar
nabari aka tashi na nufi banki na ciri kudin daya
turomin naira dubu 70 na maida masa cikin
account dinsa sannan naciri dubu 20 dan yin
siyayyata acikin account dina. Nashiga cikin
kasuwa nasiyo mai na perpect nasiya duk kayan
shafawa, sannan nasai turaruka na har da kayan
humra dan dakaina nake hada humrata nasai
mayafai da takalma har atamfa na kara. Iya na
gani tace ko kefa. Nanfa nashiga gayuna kafin
wata daya na komo da farina da gayuna, sai dai
ban maida kibata sosaiba, ba wanda zai ganni
yazata ina da yara har 4. Wani abin dariya sai ga
mutane sun soma yin sallama dani.
Ranar wata juma'a ne sunan wata malamar da
muke koyarwa tare nayi kyau cikin leshi mai
ruwan madara ni kaina nasan nayi kyau taku dai
dai nake yi na tsallaka titi zan hau abin hawa sai
mota ta tsaya a gabana na waiwaya zanyi masifa
sainaga yaya Usman ne cikin dariya na isa gurin
shi. Yaya ashe kaine? Yace to na tsaya kafin inyi
magana sai naga za'syi min masifa nayi dariya ka
san mutane wai dasunga mutum ya tsaya sai
suce zasu dauki mutum. Yace hakane sai ina?
Nace nan Askulaye zani suna watace da muke
koyarwa tare ta haihu. Yace muje. Nace a'a
dakaje kada in batamaka lokaci yace hanya tace
ni gaba naci don kurmin mashi zanje. Nace ok.
Nashiga muka hau titi nace ina su Auntyna da su
Ummul? Yace duk suna lfy shine bakya son fita
da Sadiq koh? Nace shima ya saba da Iya baya
son bina. Yace ya huta da shan rana. Nace
wallahi. Naji cewa abokina yasamu karin girma
kwanaki? Nabata rai ina ruwana. Yayi dariya da
ruwanki mana koba dangantaka akwai su Kausar
nace harsu duk na barmasa na yafesu. Yace
bacin raine. Nace wai ya batun binciken? Yace
ina kan binciken kiris yarage in kammala. Murna
ta cikani cikin zakuwa nace kun gano kowane ne?
Yace eh toh na dai yi nasarar gano cewa mutum
dayane a abu uku Sulaiman din daya kawowa
aboki gulma shine malamin makarantarku kuma
shine Sadiya Abubakar mun gano hakan ne ta
hanyar lambar MTN Din dayayi amfani da ita
gurin cike form na account din da ya bude. Nace
a'a duk lamba daya yayi amfani? Yace a'a daban
daban ne sa'ar da muka ci duka na MTN ne
kuma duk yayi musu rijista taimakon dayayi
mana kenan. Nace Alhamdulillah. Muka danyi
shiru nawasu yan dakiku sai Usman yayi gyaran
murya yace, Sadiya! Nadube shi irin kallon
dayayimin yasa gabana faduwa nayi ta maza
nadauke kaina. In tambayeki mana? Nace
eh...ina...jinka. Nafada cikin in ina yace in
abokina yaji gaskiyar batun nasan zaku sasanta
koh? Nakalleshi da sauri nan take raina yabaci na
sunkuyar da kaina yaya Usman dan Allah na roke
ka kadaina yimin zancen yaya nayi rantsuwa
bazanyi kaffara ba,Muka danyi shiru na wani
lokaci,sannna yasake yin 'yar gyaran murya
"Sadiya nasan kisoma tsayawa da masu sonki
ko?"
Nadubeshi "banajin zan bata lilacina gurin kula
su,domin al'amarinsu sai su."
Yayi dan murmushi "karkiyi kudin goro"
Nan nanunamasa layin muka shiga,gabana yana
ta faduwa sabida irin kallon da yaya Usaman
yake yimin. Nace ga gidannan.ya tsaya ya
dubeni.
"Zan dawo in daukeki"
Nace a'a kayi hakuri daga nan zanwuce wata
unguwar,nagode.
Yace "ina zaki!"
Nadubeshi "Gidan kawata"
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Yace "Ok! Shikenan, kila zan dawo nanda anjima
inna zaton zamu tattauna wata magama mai
muhummanci
Nace to sai kazo.
Jiki babu karfi nashiga gidan sunan,duk da irin
shewa da wasa da dariya da abokan aikina keyi
ni nakasa ko murmushi.
Malama Bilkisu ta dubeni tace wai Malaman
sadiya kodai baki da lafiyane?nai dan yake kaina
ciwo yake Sukayimin sannu mai jegon har dacewa
ke kam tunda kika haihu shi kenan kika zama
sarkin ciwo. Nace aykam gashi nan na kasa maida
jikina. Adaddape nayi minti 40 agidan nafito na
nufi gidan Ayshata sai taganni kamar an jeho ni
ta tashi tare dapadan lfy? Nace Uhm wata
sabuwace tasamu. Tace kuma, to zauna kisha
ruwa kin taki sa'a yau alalar gwangwani nayi.
Naja tsaki ni wallahi yau ko nama kikayi zalla
bana zaton zan iya ci. Tace meyafaru? Nan na
bata lbrn duk yanda mukayi da yaya Usman
itama dai ta damu amma tace balallai yace yana
sonaba wai kila zuciya tace kawai ta zargi hakan
nace toh shikenan. Sai bayan magariba na yimata
sallama ta rako ni na hau mashin ina hanya naji
wayata na ruri, ina dagawa iya ta rufe ni da fada
ina natsaya ga Sadiq yana ta ihu? Nace gidan
Aysha nawuce gani nan tafe. Ina shiga yaya naci
karo dashi zai fito dashi a kafada yana ta kuka,
duk da darene na raya cewa fuskar shi a daure
take ranshi kuma a bace yake, nashige nazauna a
falo ina ninke mayafina sai gashi. Kin tafi yawon
banzanki kin bar yaro yana ta kuka ko? Ina
kikaje? Naki ko dubanshi nagama ninke mayafina
na mike zan shiga uwar daki yace baki amshe
shiba yana kuka? Iya ta sallame sallah tace ki
daukeshi mana ya jima yana kuka, nace to. Saida
nakai mayafina na ajiye sannan nafito fuska
daure na isa gurinshi namika hannu cikin harara
yabani shi sannan yayi kwafa. Kisani in zaki tafi
yawon banzanki ki daina ajiye min yaro a gisa
yana kuka banda shashanci me zai sa mace tafita
har magriba. Na zaci acikin zuciya nake magana
ashe tafito fili ina ruwana da kukan shi zan kiyin
harkar gabana ne saboda shi? Sai muryar Yaya
naji yace Iyee haka kikace? Nayi shiru. Tozan
dauki yarona in hada shi da yan uwansa in yaso
ke kije kiyi ta gantalinki. Nazauna nasoma bashi
nono ina jijjiga nace Tabdi Ay wallahu bazan bada
dana ba koh gaban Alkali Za'a,Iya dai tana jin mu
bata tankaba yace basai Alkaliba ahannunki zan
amshe shi kicika baki kigani. Nakalli iya don na
soma fargabar zantukanshi tsaf zai iya,Nace iya
kifada masa yafitga harkata yadaina cemin ina
gantali. Iya tace ki kyaleshi yazo yadauki dan
nasa gantali kuwa ai kin isa yine. Yatausasa
murya Iya kidena dauremata gindi tanamin
rashin kunya. Yakalleni. Zan targadaki in kika yi
wasa. Namike nashige daki shi kuma yawuce.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Haka suka fita jiki babu karfikowa ya nufi gidan
shi suka nufi nasu da safe na gama yiwa yarona
wanka kenan sai gashi ya shigo sanye da
kananan kaya sai yaune ma na kalleshi yadan
rame yayi duhu natabe baki sannan na bata rai
Iya ta fita siyo mana biredi na gama na kwantar
dashi kan kujera zan fita da ruwan sai naga yakai
hannu zai dauke shi da sauri na dauki yarona na
sashi a bayana na kwance zanin jikina wanda
dama na dora ne a saman dogon wando na
goyeshi sannan na dauki ruwan, yako ji haushi
cikin zafin rai yace me kike nufi? Nace duk
abinda kake nufi ,na kalleshi sama da kasa yace
nufinki bazan dauki yarona ba? Nace au shima
danka ne? Na zata inda nake zuwa na yoshi yace
karfa kiga Iya na daure miki gindi ki zata har kin
kai matsayin da zakiyi min rashin kunya dan
kinga na kyaleki ban dauki mataki a kankiba, nace
don Allah kaini kotun musulunci yace bani yarona
in ganshi? bazan bayarba,Sallamar Iya tasa
yazauna kan kujera nima nazauna, na kwantoshi
nasoma shafa masa mai Iya tashigo dakin
ganinshi sai ta daure fuska tace lafiya me kuma
yakawoka? Yace Iya gurinki in gaisheki tsaki taja
sannan tafita zuwa kicin Yakalleni Nan gidan
ubanane ba mai hana ni zuwa. Nima na
harareshi ina ruwana Allah yasa nima ina da
gidan uban. Kafin yayi magana sai ga Iya ta shigo
da ruwan zafi takalle ni zo ki karya cikin jego,
kawo shi in sa masa kayan. Nace to, bayan na
karasa sa masa pampers din na mika mata shi.
Ina zama yayi caraf ya mika hannu ya dauke shi
a hannun Iya na kalleshi cikin tsana nazauna
shima yaharareni sannan yazauna yana kallon
yaron, banzaci ya san sunan shiba sai naji ya ce
Iya Sadiq ma dani yake kama sosai yanda ban
tankaba itama bata tankaba. Yarungumeshi tsam
a kirjinshi, sai kurum nafita tsakar gida ina
karyawa. Ashe Iya ma ta shige uwar daka dan
haka yadauki kayan yana sa masa yagama
yamike yafito da shi ganin zai yi waje nabishi da
gudu a ganina zai tafi da shine, ina fadin Iya
zaitafi dashi nasha gabanshi,bani yarona dasauri
Iya tace kyaleshi yatafi dashi din seme? Nasoma
kuka shikuma sai hararata yake yi yaja tsaki
yawuce nace Yaya inka tafi dashi saina tona
asirinka tsam yatsaya sannan yawaiwayo yakalli
Iya itama shi take kallo sannan takalleni na isa
gabanshi namika hannu Bani yarona.Sai yamiko
minshi sannan yafita da sauri naje kan kujera
nazauna ina cika,Iya ta iso gabana wane irin
asirene zaki tona masa?yaken dariya na kakaro
birgace kawai nayi masa babu komai Iya. Tayi yar
dariya haba Sadiya shi mahaukacikane bayan ba
wani sirri jikinsa yayi sanyi haka? In dai da wani
abu kifadamin,Nace ba komai iya tace oho miki in
ma dashi, shiyasa wani lokacin banasan shiga
shirginku.Ni dai sim sim nayi daki.
Hudu da ashirin ina kwashe tuwo naji sallamar
shi ciki ciki na amsa, banyi tsammanin ma zaijiba
na dago nadubeshi cikin tsana, sai naga
hankalinshi yana kan yarona wanda nashimfida a
tabarma akan katifar shi nakwantar dashi akofar
daki Iya tana zaune kusa dashi. Dagudu na aje
tuwon dake hannuna nafito har ina tsallaka iya
nasuri dana nasa a baya naja zanina a igiyar
shanya nagoye shi sannan nakoma kicin ina jin
tsakinshi a raina nace kadai karata can.Daga inda
nake ina jiyo shi yana gaida Iya, dakyar ta amsa.
Yace zantafi zaria dama wani ayki nazoyi Kaduna
akwai wani malami ne da ake zaton kasurgumin
dan fashine to kan shi nake aiki,rahotanni sun
same mu cewa ya koma Zaria acikin satin nan
kafin inzo dan wata na biyu kenan ina nemanshi
tun daga Maiduguri nake biye dashi har zuwa
nan ina son Iya kitaya ni da addu'a Allah
yataimake ni. Iya tace Allah yabada sa'a. Yace
amin. Tace malami kuma dan fashi in banda son
duniya? Ay irinsu suna da yawa Iya kuma yana
siffatuwa ne da malai manyan malamai yana da
ilimin, sai dai shi dan fashine ga tsafi ,sama da
shekaru goma ankasa kamashi,kingako kamashi
nasarace. Iya tace Allah yataimaka yace amin
yaciro kudi gashi Iya. Tace a'a ai na fada maka
bamu da bukatar komai,yasake tausasa murya
Iya wannan fa tsakanin mune ni dake in baki
amsaba sai inga tamkar kin cire ni a tsatsonki,
Ya'ajiye gefenta. Iya kiyafemin natafi.,Bata ce
komaiba kuma bata dauki kudinba yazo bakin
kicin yajeho min wasu mukullai ga mukullin
gidanki nan kije ki dauki motarki aciki. Nadubeshi
fuska daure cikin harara nace bani da gida bare
mota in kana nufin motarka to bana so,tsaki yaja
sannan ya wuce batare daya dauki mukullanba.
Nafito gurin Iya rai a bace nace Iya naga har
kulashifa kikayi kuna hira har yana wani baki kudi
kina karba? Iya tace kin san shi naci zai tayimin
shiyasa narabu da shi ya aje kudin dan yatafi
yabamu guri sannan ina zulumin yanayin aykin
nan nashi wannan malamin kuwa dan fashi
tunkararsa hadarine ina tsoron karya halakashi.
Gadanga shiba mutumbane mai son neman tsarin
kai, da kaikayi koma kan mashekiya,da kai
magana zaice yana addu'a an san dai ita ce
dama kan gaba. Don haka itama Iya ban tanka
mataba wato ma tausayin shi takeji.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Aliyu yayi masauki unguwar Mazan Gudu gidsn
limamin unguwar da sunan cewa shi bakone
matafiyi ne. Hannu 2 aka karbeshi kwanansa 2
yace a nema masa daki na haya yana son yadan
kama sana'a yafada musu cewa rani yake Zuwa
garin Kaduna daga Hadeja yake,Liman har yayi
masa tambaya game da wasu unguwanni a can
Hajejan Allah yasa garuruwan da Aliyu yasani ne
ya kuma fada masa cewa ya sani. Liman yace sun
zauna sun danyi karatu a garin shekarun baya
lokacin suna yawon neman ilimi. Liman yace Aliyu
yazauna ga daki nan a zaure a gidansa na
dansane dake karatun boko a jihar sokoto a
jami'ar shehu dan fodio. Cikin sati daya yasaba
da makota. Akwai wani dan dandali da mazan
unguwar ke zama ko in ce majalisa. Tuni Aliyu ya
saba da yan majalisar in da ake zama ayi ta
labarin wane da wane ko duk wanda yagifta.
Anan yasamu labarin wannan malami daya sauka
gidan sarkin malaman kusfa ance yanda ilimi
sosai kuma yana bada fatawa. Aliyu yace dan
Allah wanda yasan gurin yayimasa rakiya don
yana son daukan karatu. Kullum 'yan majalisar
nan suna mamakin Aliyu duk irin shigar dayakeyi
ta kaya marasa kyau amma fatar jikinsa bata
nuna cewa daga kyauyen hadeja yakeba kamar
yanda yafadamusu. Akwaima wanda yakecewa
shifa yana wa fuskar Ali kallon sani.
Cikin sati 2 sukayi sabo da Malamin wanda yasaki
jiki da Aliyun amma sai dai Malamin ya fadawa
Aliyu shifa malamine mai yawon yada da'awa
don haka daga nan zai wuce Katsina ne tafi tafi
har Nijar. Aliyu yace in ba damuwa zaibi shi,Aliyu
ya lura da yanda malamin ke daga waya akai-
akai sannan ya lura da irin kudin da malamin ke
rabawa jama'a sadaka. Duk binciken dayayi ya
gano cewa malanin ne wanda yake nema sai dai
dama yana da labarin matsawar malamin yana
cikin daki bazai kamuba. Ana gobe zasu bar garin
kamar yanda suka shirya har da shi Aliyu
shikuma ya daura aniyar kama shine aranar
jajiberen tafiyar. Karfe 2 sun taso daga sallar
Azahar Aliyu hankalinshi tashe burin shi yanzun
idan sun iso kafin su isa gidsn malamin ya sauke
yashige daki. Aliyu yakalli malamin. Allah
yagafarta malam naga jama'ar wannan garin
suna alhinin rabuwa dakai shin bazamu dan kara
kwanakiba? Malam yakalli Aliyu ina da dalilin
barin garinnan asubahin gobe.Aliyu yace Allah
yasa haka shine mafi Alkairi. Malam yace ameen.
Sai dai kai ina mamakin yanda kake son bina ban
cika sakewa da mutaneba amma kai raina ya
kwanta dakai amma daganinka ka taba zaman
cikin birni? Aliy yace e duk cikin gari nayi
rayuwata ban zauna gidaba, Malam yayi
murmushi toh Aliyu sai dai kayi hakuri ina zaton
bazanje dakaiba. Aliyu yace saboda me malam?
Malam ya gyara tsayuwar wato malam Ali an
sanar dani cewa duk inda zan shiga kada in shiga
da mutumin cikin gari domin shine zai zamemin
hadari cikin rayuwata. Aliyu yace Allah gafarta
malam an fada maka kamannin shine munyi
kama? Yace ko kusa an dai ce min zai shiga jikina
sosai kuma zai cutar dani a rana irin ta gobe
shiyasa duk lokacin dazan bar gari nakan barshi
tun asubahi. Aliyu wanda ya kosa yaga isowar
jami'an tsaro yace toh Alagafarta yaya zaka yarda
da irin wannan kila ba gaskiya bane. Malam
yadafa kafadar Aliyu inayimaka fata nagari Allah
yasa zamu hadu wata rana amma wanda yafada
min zancen nan yasha fadamin zantuka suna
tabbata ina ji ajikina zamu sake haduwa da.....
Jiniyar motar 'Yansanda ce tasa malam bai karasa
zancenba sai Aliyu yaga malam ya daga kafada
yasa gudu cikin azama da kwarewa Aliyu yaciro
bindiga daga bayan wandasa ya harbi malam a
kafa take malam yafadi amma burinshi yakai daki
dan haka ya yunkura Aliyu yayi azama yacafkeshi.
Mutanan gurin sun cika da mamaki harma suka
taso da nufin jin ba'asi sai dai kafin suji dalili tuni
yan sanda sunyi zobe a gurin sun kuma cafke
wasu daga cikin makarraban malamin sannan an
samu muggan makamai cikin kayan malamin da
kudin kasar Amuruka(Dollar) da irin namu na
gida. Mutanan unguwar suna ta al'ajabin lamarin
yayinda wasu ke mamakin Aliyun wanda suka
zata shima yana cikin mukarraban malam. Ta
gidan lima suka bi mai masaukinsa,Aliyu yayi
musu sallama yadauki yan kayan shi tare dayi
masa alheri haka ma yen majalirarsu yatafi yabar
su da labarinshi tare da jinjinawa aykin shi.
Cikin wata hudu da aka damka aykin hannun
Aliyu ya samu nasara ya fara bibiyar malamin
tundaga maiduguri har kawo Kaduna sannan
Zaria inda yayi nasara sakamakon haka ya samu
lambar yabo tare da karin girma zuwa
mataimakin kwamishina na can Abuja haka nan
nasarar taja masa farin jini inda akayi ta haskashi
gidajen talabijin. Ina kallon Iya tunda Aliyu yazo
da batun aykin nan kullum cikin yimasa addu'a
take tare dayawaita sadaka. Araina nace da da
mahaifi sai Allah. Dubi duk haushinsa datakeji be
hanata yimasa addu'ab. Inzanje aiki yanzu gida
nake barin Sadiq sabida yana shan kamu. Iya
tasani gaba tana min fada wata ranar Litinin na
shirya zantapi aiki. Sadiya! Dan Allah shekarunki
nawa? Nace me yafaru Iya? Tace fadamin. Nace
26 Tace dubi duk yanda kika koma ba wani ado
ba kwalliyar da kikeyi ada, ki dage ko dan ki ba
Gadanga haushi,amma kullum sai kina yawo
kamar me takaba,Nace ni banima da kayan
kwalliyar,tace inzaki dawo ki tsaya kasuwa ki saya
in ma baki da kudi in baki,nace ina dashi a cikin
account dina,tace to.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ina zaune bayan na sallami daliban ajina sun fita
break nazabga tagumu ina tunanin zancen Iya
gaskiya ta fadamin bazan tsaya in tsufar da
kainaba tilas in nafita in shiga banki sannan in
shiga kasuwa. Shigowar alert ne ya tsaida
tunanina na dauka na duba kudi ne naira dubu
saba'in sannan yaya ne ya turo min. Haushi da
bakin ciki kamar inyi kuka don haushi. Dakyar
nabari aka tashi na nufi banki na ciri kudin daya
turomin naira dubu 70 na maida masa cikin
account dinsa sannan naciri dubu 20 dan yin
siyayyata acikin account dina. Nashiga cikin
kasuwa nasiyo mai na perpect nasiya duk kayan
shafawa, sannan nasai turaruka na har da kayan
humra dan dakaina nake hada humrata nasai
mayafai da takalma har atamfa na kara. Iya na
gani tace ko kefa. Nanfa nashiga gayuna kafin
wata daya na komo da farina da gayuna, sai dai
ban maida kibata sosaiba, ba wanda zai ganni
yazata ina da yara har 4. Wani abin dariya sai ga
mutane sun soma yin sallama dani.
Ranar wata juma'a ne sunan wata malamar da
muke koyarwa tare nayi kyau cikin leshi mai
ruwan madara ni kaina nasan nayi kyau taku dai
dai nake yi na tsallaka titi zan hau abin hawa sai
mota ta tsaya a gabana na waiwaya zanyi masifa
sainaga yaya Usman ne cikin dariya na isa gurin
shi. Yaya ashe kaine? Yace to na tsaya kafin inyi
magana sai naga za'syi min masifa nayi dariya ka
san mutane wai dasunga mutum ya tsaya sai
suce zasu dauki mutum. Yace hakane sai ina?
Nace nan Askulaye zani suna watace da muke
koyarwa tare ta haihu. Yace muje. Nace a'a
dakaje kada in batamaka lokaci yace hanya tace
ni gaba naci don kurmin mashi zanje. Nace ok.
Nashiga muka hau titi nace ina su Auntyna da su
Ummul? Yace duk suna lfy shine bakya son fita
da Sadiq koh? Nace shima ya saba da Iya baya
son bina. Yace ya huta da shan rana. Nace
wallahi. Naji cewa abokina yasamu karin girma
kwanaki? Nabata rai ina ruwana. Yayi dariya da
ruwanki mana koba dangantaka akwai su Kausar
nace harsu duk na barmasa na yafesu. Yace
bacin raine. Nace wai ya batun binciken? Yace
ina kan binciken kiris yarage in kammala. Murna
ta cikani cikin zakuwa nace kun gano kowane ne?
Yace eh toh na dai yi nasarar gano cewa mutum
dayane a abu uku Sulaiman din daya kawowa
aboki gulma shine malamin makarantarku kuma
shine Sadiya Abubakar mun gano hakan ne ta
hanyar lambar MTN Din dayayi amfani da ita
gurin cike form na account din da ya bude. Nace
a'a duk lamba daya yayi amfani? Yace a'a daban
daban ne sa'ar da muka ci duka na MTN ne
kuma duk yayi musu rijista taimakon dayayi
mana kenan. Nace Alhamdulillah. Muka danyi
shiru nawasu yan dakiku sai Usman yayi gyaran
murya yace, Sadiya! Nadube shi irin kallon
dayayimin yasa gabana faduwa nayi ta maza
nadauke kaina. In tambayeki mana? Nace
eh...ina...jinka. Nafada cikin in ina yace in
abokina yaji gaskiyar batun nasan zaku sasanta
koh? Nakalleshi da sauri nan take raina yabaci na
sunkuyar da kaina yaya Usman dan Allah na roke
ka kadaina yimin zancen yaya nayi rantsuwa
bazanyi kaffara ba,Muka danyi shiru na wani
lokaci,sannna yasake yin 'yar gyaran murya
"Sadiya nasan kisoma tsayawa da masu sonki
ko?"
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Nadubeshi "banajin zan bata lilacina gurin kula
su,domin al'amarinsu sai su."
Yayi dan murmushi "karkiyi kudin goro"
Nan nanunamasa layin muka shiga,gabana yana
ta faduwa sabida irin kallon da yaya Usaman
yake yimin. Nace ga gidannan.ya tsaya ya
dubeni.
"Zan dawo in daukeki"
Nace a'a kayi hakuri daga nan zanwuce wata
unguwar,nagode.
Yace "ina zaki!"
Nadubeshi "Gidan kawata"
Yace "Ok! Shikenan, kila zan dawo nanda anjima
inna zaton zamu tattauna wata magama mai
muhummanci
Nace to sai kazo.
Jiki babu karfi nashiga gidan sunan,duk da irin
shewa da wasa da dariya da abokan aikina keyi
ni nakasa ko murmushi.
Malama Bilkisu ta dubeni tace wai Malaman
sadiya kodai baki da lafiyane?nai dan yake kaina
ciwo yake Sukayimin sannu mai jegon har
dacewa ke kam tunda kika haihu shi kenan kika
zama sarkin ciwo. Nace aykam gashi nan na
kasa maida jikina. Adaddape nayi minti 40
agidan nafito na nufi gidan Ayshata sai taganni
kamar an jeho ni ta tashi tare dapadan lfy?
Nace Uhm wata sabuwace tasamu. Tace kuma,
to zauna kisha ruwa kin taki sa'a yau alalar
gwangwani nayi. Naja tsaki ni wallahi yau ko
nama kikayi zalla bana zaton zan iya ci. Tace
meyafaru? Nan na bata lbrn duk yanda mukayi
da yaya Usman itama dai ta damu amma tace
balallai yace yana sonaba wai kila zuciya tace
kawai ta zargi hakan nace toh shikenan. Sai
bayan magariba na yimata sallama ta rako ni na
hau mashin ina hanya naji wayata na ruri, ina
dagawa iya ta rufe ni da fada ina natsaya ga
Sadiq yana ta ihu? Nace gidan Aysha nawuce
gani nan tafe. Ina shiga yaya naci karo dashi zai
fito dashi a kafada yana ta kuka, duk da darene
na raya cewa fuskar shi a daure take ranshi
kuma a bace yake, nashige nazauna a falo ina
ninke mayafina sai gashi. Kin tafi yawon
banzanki kin bar yaro yana ta kuka ko? Ina
kikaje? Naki ko dubanshi nagama ninke
mayafina na mike zan shiga uwar daki yace baki
amshe shiba yana kuka? Iya ta sallame sallah
tace ki daukeshi mana ya jima yana kuka, nace
to. Saida nakai mayafina na ajiye sannan nafito
fuska daure na isa gurinshi namika hannu cikin
harara yabani shi sannan yayi kwafa. Kisani in
zaki tafi yawon banzanki ki daina ajiye min yaro
a gisa yana kuka banda shashanci me zai sa
mace tafita har magriba. Na zaci acikin zuciya
nake magana ashe tafito fili ina ruwana da
kukan shi zan kiyin harkar gabana ne saboda
shi? Sai muryar Yaya naji yace Iyee haka kikace?
Nayi shiru. Tozan dauki yarona in hada shi da
yan uwansa in yaso ke kije kiyi ta gantalinki.
Nazauna nasoma bashi nono ina jijjiga nace
Tabdi Ay wallahu bazan bada dana ba koh
gaban Alkali Za'a,Iya dai tana jin mu bata
tankaba yace basai Alkaliba ahannunki zan
amshe shi kicika baki kigani. Nakalli iya don na
soma fargabar zantukanshi tsaf zai iya,Nace iya
kifada masa yafitga harkata yadaina cemin ina
gantali. Iya tace ki kyaleshi yazo yadauki dan
nasa gantali kuwa ai kin isa yine. Yatausasa
murya Iya kidena dauremata gindi tanamin
rashin kunya. Yakalleni. Zan targadaki in kika yi
wasa. Namike nashige daki shi kuma
yawuce.......Zandakata a nan, acigaba da hakuri
dani.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
Darajar Yayana4-03
Posted by ANaM Dorayi on 10:47 PM, 13-Apr-16
Under: DARAJAR 'YA'YANA
_________________NA
___________HALIMA K/MASHI
Mama natawasan ruwa a karamin fanfon cikin
bandakin,Khausar ta kalleshi cikin fargaba amma
bata tashi daga inda takeba,jiratake yafara
yimata fada kamar yanda in Mujidat taci Zalinta
sanna tayimata karya gurin Abbanta cewa Tayi
kaza-tayi kaza, yayi mata fada amma sai taga
yamaida kofar ya rufe kuma yamaida
mukullin,dan tajiyo kara,sabon kuka tasoma
Mama ta juyo tan kallonta.
Cikin zafin rai Aliyu Yayi dakin Mujidat,turo kofar
dayayi da karfi shiyasa ta tura wayar a karkashin
pillow sanna ta mike zubur, ya kalli pillon sannan
ya kalleta,rashin gaskiya ya bayyana fuskarta.
Sanna tace, "My Dear sannu da zuwa."
Ya dauke kansa daga kallonta sannnan yace, "ina
yarana?"
Gabanta yabadi sakamakon tinowa datayi ta
kullesu a bandaki,cikin inina tace sun..suna falo
kokuma dakinsu bari inkirasu,yadan kauce ta
wuce shikuma yabi bayanta. Cikin takun isa
tashiga cikin dakin sannna tafito tace, "ina
yarannan suka shiga?" Nahanasu Khausar
yawonnan amma sunki,bari induba gidan maman
Markus,
Aliyu yace,"kinsan inda suke dan haka nunamin"
Tace, "ni bansab inda suka shigabafa a falo na
barsu"
Yace, "yaya basu tafi da yaronkiba sai sukadai"
Tace, "Amma dai kasan Abdul bashi yarda
dakowa"
Yace, "bansaniba, kin rufemin yara a toilet?"
Ta zaro ido "suna Toilet?" Ta nufi bandakin da
sassarfa,Aliyu yabi bayanta,ta bude mukullin
hannunta na rawa,zunmbur Khausar ta mike
hannunta na rawa tana cewa yi hakuri Aunty
nadena kar ki dokeni.
Tace zonan Khausar me kukeyi a nan?
Tadaga Al'amin tana cigaba da cewa, "haba
Khausar"....
Aliyu yana tsaye cikin takaici da bakin ciki, domin
ko karamin yaro zai fahimci cewA kawo yarantayi
ta rufe amma tana nema ta raina masa hankli.
Sai da tayiwa yaran wanka tana cewa haba
yarana karku kara ba'a wasa a toilet. Saida
tagama musu wankan suna fitowa zata fito ya
hankada ciki ta koma da baya tafadi,ya maida
kofar ya kulle sannan ya zare mukullin yabi yaran
zuwa dakinsu, yazauna bakin gado yana
kallonsu.kausar ta dakko musu kaya,hawaye ke
zuba daga idanunshi, yaranshi duk sun lalace ba
wata cikakkiyar tsafta,yaran da mutane ungwa
suke labarinsu a makaranta suke amsar kyautuna
sabida tsafta dubesu duk sunyi baki, gashin su
khausar ya lalace, kayansu duka bakula. A fiili
yace, "Sadiya kin tarwatsamu," yasake kallon
yaran yaga suna kallonshi yamike yaje ya hadasu
ya rungume yana cewa, "Kuyi hakuri yarana, ba
laifina bane laifin mamankune" sunfi minti daya
haka sannan ya sakesu yace, "inkaiku gurin
wasan yar ko?
Skace, "e"
Yace, "to,kokuma kuna jin yunwane."
Nanma sukace, "e"
Yace, "to bari inyi wank"
Yace, "ina sababbin kayan dana siyo muku."
Khausar tace, "suna dakin anty"
Yatafi dakin ya hau bincike har ya binciko kayan
yazo yasamusu,sannan shima yaje yayi wanka
yafito cikin wani yadi mara nauyi me ruwab
siminti, sannan takalmin da hular wadanda suka
dace, har zai wuce sai yaleka dakinta, har yanzun
danta na bacci, yadaga fillon sai ga waya BB ya
dakko ya zura a aljihu yafice ya kwashi
yaran,yanajinta tana buga kofa tanacewa, "My
Dear dan Allah ka budeni."
Yace, "kiji abinda sukaji"
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
yafice yazuba yaranshi a mota suka wuce.
Ranar dai yaran sunji dadi duk da Khausar ta
kasa walwala amma fuskarta a sake alamar taji
dadi, yaymusu siyayya sosai
Basu dawo gidanba sai da yayi sallar isha.
Yasamu Abdul yatashi yayi kashi da fitsari a gado
da kasa, yaje ya budeta tayi kuka ta gaji dan tana
jiyo kukan danta badamar ta je gunsa,
tasakarmasa harara sannan taja tsaki ta wuce,
dariya yayi don turamata haushi.yana ta re da
yaransa har sukai bacci sanna yaciri wayar
yasoma binciki amma hakan ya faskara saboda
security datsa, yamike yatafi dakinta yatara da ita
tana waya da karamar wayar da kullum yake
tsammanin ita kadai ke gareta ya tatsuramata ido
dan son fahimtar da wa take wayar amma sai
tayi sallma tare sa cewa, "momyi sai anjima."
Ya dago ya nuna mata wayarta dake hannunsa
yace, "wannan wayar waye?"
Tace, "tawace" cikin gadara yace, "ina kika samu
kudin siyan wannan wayar dubu sittin?"
Gabanta ya fadi amma sai ta dake tace, "ni ba
haka na siyaba second hand na siya."
Yace, "gurin wa kika siya?"
Tace, "gurin kawata."
"Wacece kawar taki?"
Tace, "Azima"
Nawa kika siya?
Tace, "dubu ashirin"
Yace, "a ina kika samu kudin?"
Cikin kosawa tare da daga murya tace, "Auncle
yabani,
Wai sata nayi da kasani a gaba da wadannan
tanbayoyin?"
Ya mika mata, "ciremin scurity"
Ta amsa ta cire tana kokarin shiga wasu guraren
ta goge wasu abubuwan ya fisge wayar yafita, ta
biyoshi tana cewa ni kabani wayata ba kai
kaseminba,
Afalo yazauna sanna ya kalleta kallon zargi, "karki
karso min nan, inbadan kinsan baki da gaskiyaba
menen dan mijinki yadauki wayarki?"
Tace, "nadamune dan zaka duba wayata meye a
ciki?
Kayi ta dubawa nidai nace kabani a buna tinda
bakaine kaseminba"
Baisake tankamataba, yayi iya bincikensa baiga
wani abu ba amma cikin inbox dinta na message
yaga wani sako da yadauki hankalinsa cewa
akayi,
"Malama ki aikomin da cikon kudin aikina inba
hakaba zanyi miki rashin mutunc daga Jamilu."
Yaduba ranar da aka turo sakon ya lissafa kwana
tara kenan,ya tura sakon zuwa wayarshi sannan
ya aje wayar a hannun kujera tazo ta dauka ta
wuce. sam bata tinanin wannan sakon
damuwarta karyashiga group dinsu yaga abinda
sukeyi,dan in hirar da sukeyi da mazane tasan
bazai ganiba tinda tana gogewa shikuma bai
tsaya wani shiga group ba.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Sunfi kwana uku suna gaba,tafita lamarinshi da
yayanshi,shinma yafita shirginta,sai hidimarsa
yake da yaransa.Nazari tayi taga suke
cutuwa,don haka ta sauke girmankai tare da
samunshi a dakinshi tsakar dare inda tabashi
hakuri,tare da yimasa alkawarin bazata karaba.
Cikin kwanakin da suka biyo baya tana kokarin
dannar zuciyarta dan ta kyutatawa yaran,sabida
ubansu ya yarda ta canja,saidai yaran sunki sakin
jiki da ita, data lura yasaki jikin sai takoma
halinta,yanzu bata rufesu a bandaki saidai duka
kamar jakuna, dan kuskure kadan na yaro sai
takama tayita duka.
Cikin haka wata ranara litinin su Khausar sun
dawo daga makaranta dauke da yunwa,sunfi
minti talatin sannan ta tashi daga chatting din
tabasu abinci,wanda ko Al'amin sai yacinye.
Kausar tace, "Anti Wannan fa bazai ishemuba,"
Ta watso mata wata harara ta nufi dakinta tana
cewa, "Dama ni nace ku koshine?"
Khausar ta Mika musu tace, "kuci," sun cinye
Amma basu koshiba, Don haka khausar tace
kibari in ta dan dade zanje in debo muku nima in
debo nawa,Don ka dayushe dama idan basu
koshiba takan dan lababa ta debomusu.
Kamar kullum ta taka kujera tana cikin zubawa
sai taji kamar motsin Auntynsu ashe
Mamace,tana kokarin sakkowa kujerara ta gurde,
Kausar ta fado, shi kuma plate din yayi sama sai
yafada kan wasu plates din 'yan uwanshi na
tangaran,nanfa kakejin tartsatsi yana tashi,da
gudu Mujidat ta fito.
Khausar ta mike jiki na bari tsoma cewa , "Anty yi
hakuri tana kka."
Mujidat tace, "ok! Allah yakamaki dama kece me
satar abinci kullum inna tanbaya kice bakebace
ko?"
Cikin rawar muraya khausar tace, "zasu karane,ni
ko cima banyiba."
Tace, "Ina ruwana,dole inzaneku yau, kizo ki
gyaramin kitchen bari innemo wayar wuta."
Ai tana juyawa khausar tafita da gudu inda tadau
takalmansu suka gudu,Mujidat tafito bata
gansuba,tace "oh! Kunguduko?zaku dawone."
Duk da cewa barikin 'yan sanda da tsaro amma
sai Allah yakauda idon kowa basu gansuba har
suka fice.
Al'amen yace, "yaya Khausar ina zamuje? Ko
mutafi Office grin Baba?"
Khausar tace, "inmunje zai dawo damune ko Yayi
mata fada,in Yayi tafiyrs Sai ta dakemu,"
Al'amin yace, "emana , kawai mu tafi gurin
Momy."
Khausar tace, "zamu iyane? Kadunafa?"
Mama tace, "nima zanje Momy kinji Yaya
Khausar"
Khausar tace, "to mama zaki iya Zuwa a kasa?"
Mama tace e
Almen yace, "in tagaji sai ki goyata"
Khausar tace, "muje to kila mugane.'
Sunyi ta zagaye cikin garin Abuja har duhun
Magriba yasoma shigowa,inda suka Isa kusa da
wani Store na saida kayan shaye shaye na
zamani, suna son su sha ruwa, ga yunwa,in
mama tayi kuka sai Khausar tace, "yi shiru mun
kusa"
Khausar ta Isa gurin wani mutumi dake tsaye
yana shan kankanar gwangwani, tace, "Baba dan
Allah kasammana ruwa."
Yakalleta ya kalli su Mama yace, "kai inazaku?"
Khausar tace, "Kaduna"
Yace, "Inna zuwa"
Yaje yafito da ruwan gora yabasu suka sha
sannan yakirasu gefe yanayimusu tanbayoyi har
mutane suka taru,nanfa akayi ta shawarwari
wasu suna Cewa akaisu makaranarsu inyaso su
can sai su kira iyayensu,tunda ansan
makarantar,jin haka yasa Khausar tashiga kuka
tana cewa, "Kutaimakamana wallahi antynmu
zata kashemu,kukaimu kadna gurin Momynmu."
Suma su Al'amin kuka sukeyi dan haka sai
sukace, "tinda shi wanna daya saimusu ruwa
direban motane sai yatafi dasu Kadunan indai
sunsan unguwarsu." Dayake daga gurin babu nisa
zuwa tasha dan haka sai suka tafi..
Mujidat bata tina da cewa yarannan basa gidanba
saida Aliyu yakirata a waya yace ta shirya
yarannan zaizo yakaisu Islamiyyar dayayi musu
register,firgigit ta mike tana cewa ai saita dokesu
babu fashi.saidai me?tayi Neman duniya cikin
gidan da makota basanan,nanfa hankalinta ya
tashi,makota suka firfito,kafin wani lokaci
ankarade rukuninsu da neman yaran,amma babu
wanda yagansu, saidai masu cewa tabbas
sungansu da takalman makaranta a
hannusu,wasu kuma suce da kayan makaranta.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Mujidat taci kuka ta koshi,gashi ta kasa kiran
babansu dan tsoro.makotansu kuwa da suka San
abin da takeyi wa yaran cewa suke Allah yakara,
saidai munafukn dake bin bayanta ne ke tayata
damuwa.
Yana shirin zuwa don kaisu sabuwar islamiyyar
da yasasu saiga wayar makocins wai bafa aga
'ya'yansaba, cikin tashin hankali yanufo gidan.Sai
yasamu gida dankam da mutne,ya kalli Mujidat
"Ina Yayana?"
Tace, "bangasuba sunyi barnane a kitchen suka
gudu."
Baice kalaba ya nufi gidan,sannan yafito yakira
"yansanda suzo gidan shi,sanna yace kowa yatafi
yagode.
Kafin wani lokaci "Yansanda sun karaso nan yasa
sukama Mujidat sai ta fadi inda takaimasa yara.
Cikin dare 'yansanda sai faman neman yara suke,
duk inda yakamat asanar an sanar, hanklin Aliyu
yatashi Karshe.karshe yakira Usman yafada
masa,amma yace yabar zancen a tsakaninsu dan
bayason su Iya suji,Usman yace Allah ya
bayyanasu.
Abu kamar wasa har cikindare babu labarin
yaran. Daidai wanna lokacin suna can akan
hanya,inda direban yasasu a bayan Mota yakashe
kujer daya kusa da wata mata inda yace "Don
Allah ta lurar masa dasu," duk da tsare motocin
da 'yansanda sukeyi suna haskawa sam babu
wanda yagano yaran,shiko direban bemasan
yaran ake nemaba balle yayi wani bayani.
Sunyi isowar dare,don haka yagama da fasinger
yanufi gidansa da yaran,wadanda harsunyi bacci,
matarsa tanada fahimta,baisha wahalaba wajen
fahimtar da itaba, nan yaran suka kwana.
Washgri akayi Tayi musu tanbayar Sunan unguwar
ta momynsu Amma suka kasa tunawa,gidan me
unguwarsu ba nisa,don haka sai yaje dasu
gurinsa,suma dai sunyi iya tanbayoyinsu
ba'aganeba,Sai matar me ungwar tabasu
shawara suje gidan TV da yaran,aikuwa basuyi
kasa agwiwaba suka nufi gidan DITV inda ake
gabatar da wani shiri na gari ya waye.
Daidai wanna lokcin inna zaune agaban TV inna
kallon shirin domin dama baya wuceni,innayi
innashan Tea. Iyama na son shirin sosai,don haka
tana ta kokari tafito daga kitchen ta iso.Kamar
daga sama sai akace ga wasu bayinAllah suna
bada Cigiyar iyayen wadannan Yara, mai
sanarwar yafada, ganin an hasko fuskar Khausar
cikin daga Murya nace Iya Iya zo kigani,da
tuntube tafita tana fadin lafiya? Itama nan
tazauna dabar.daidai lokacin ana tanbayrsu
sunayensu suka fada,dan Jaridar ya haska
Khausar
"Yarina yakikace Sunan ki?"
Tace, "Khausar Aliyu Tukur Hadeja"
"Daga ina?"
"Abuja"
"Ina Zaku?"
"Kaduna gurin momynmu"
"To can Abujan gurin wa kuke?"
"Gurin antynmu"
"Ina bbanku?"
"Yana gurin aiki."
"Me akayi muku zaku dawo gurin momynku?"
"Dukanmu Auntynmu keyi,kuma bata bamu
abinci muna kosh,jiyama naje zankaro aboye
batasaniba,zan krawa su Momy dama ni banciba
duka nabarmusu,shine nafadi,dataji karar
fashewar abu tafito,shine taje dakko wayar wuta
sai muka fito Muka kwashi takalmanmu Muka
gudu."
Yace, "to kinsa unguwar da momynku take?"
"Da nasani yanzu namanta."
"To yasunan mamanku?"
"Sadiya"
"Babankufa?"
"Aliyu Tukur Hadeja"
"Meye sana'arsa?"
Tace, "dansadane"
Nantake dan jaridar yace badai Aliyu Tukur din
danasaniba,in shine kuwa ai sanannene,yataba
rike kakakin rindinar yansanda alokacin yana ASP.
Mai unguwa yace shekarun baya ko.
Ai tini na jike shrkaf da gumi da hawaye har da
majina, yaranane wadannna ? Sai ga Habu
yashigo da sauri yace Aunty Ku kunna TV,Sai
yasamemu cikin kuka,yace iya kutaso muje gidan
me unguwa,na dauki lanbar wayar dayabayar,
gidan sa kuma hayine layin yandinki,dakyar
namike wayata tana ta ringi amma nakasa
dagata,nasan kawyenane dasukaga yaran,tin
kafin mutafi mkota dai shigowa suke suna mana
jaje gami da barka da arziki.
Munshiga gidan,sashin matar me unguwar, Mama
tana wasa,khausar da Al'amin suna ta zantuka
kasakasa,mukayi sallama yaran suka dubemu, da
karfi kausar tace Momy! Se rige rigen tahowa
gurina,na hadasu su ukun na rungumesu
jikina,inna kuka suma suna kka, duk mtanen
gurin suma kuka suke.nadauki Mama inna
kallonta,nadubi Iya cikin kunci
Nace, "dubi yarana yanda suka llce,"
Iya tace, "su da Allah sun cuci Kansu,menene
riba don ka cuci karamin yaro?" Nandai akayi abin
dayakamata muka dauki yara muka nufi gida.
Gidan cike da makota Sai barka da arziki
akeyimana,Allah yasa sunfada hannu nagari.har
lanbar direban na karba dan yimasa godiya ta
musamman sabida taimakon dayayimana.
Tini Habu yafesawa Yaya cewa abga su Khausar
anan Kaduna.Habu yabashi labarin komai,shi
kansa yasan tinda yarannna sukazo gurin iya dole
ya hakura dasu,amma yaji dadin ganinsu.yanufi
office dinsu yasa asaki Mujidat,ta fito tayi wujiga
wijiga, yace to bafa gidanshiba sai ta nemi gurin
zuwa,tace ina Abdul? Yace ai ba yaronkibane
yaronane na amshi dana.
Tace, "kana zaton dan ka boyemin Yaro zanki inje
infadawa iyayenka? ai dole su Sani."
Yace, "kekisani,saidai kisani zakikoma Kadunane
bayan kinkoma gidan Ubanki Lagos."
Aikuwa yasa aka kaita har garin da 'yan
kayanta,ko gani Abdul din ya hana tayi,yakaishi
gidan wani abokinsa a Asokoro.Mujidat ta
jinjinawa wulakancin da Aliyu Yayi mata,Amma
tace indai itace yaci Bashi,sannna tinda be
saketaba da sauki.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ya nufo kaduna cikin fargaba. Nikam na tsefe kan
yarana na wanne,akaje akayi musu kitso nayi
musu lalle. Munsha labarin irin wuyar da suka
sha a baki Khausar ni da iya, aikuwa munsha
kuka sabida tausayinsu.
Karfe uku ina zaune da 'Ya'yana cikin farinciki
inna yanke musu farce,Mama nakeyiwa magama
yiwa sauran.Khausar na dauke da Sadiq
tanayimasa wasa tace "Momy Sadiq dinki wallahi
dariya Yake yimin damun hada ido ya sannine?"
Nace, "kullum sainabashi labarinku, yasanku
dukkanku...."Sallamar yayace ya katsemu,sainaga
Khausar ta mike da gudu ta nufi daki Al'amin ma
yabita,Mamace kawai naga ta nufi Yaya tanamai
Oyoyo oyoyo,na hade raina tamkar zan saki
kuka,sanna na kauda kai nadauki wayata inna
latsawa. Yanufi cikin daki gurin iya, su Khausar
duk sun makale a bayanta tana Cewa, "lafiya
kuke boyewa?" Sai kuwa Yaya Yayi sallama,tsaki
Iya taja takasa amsa sallamar, yazauna tare da
sunkuyar dakai yace, "ina yini"
Ta kauda kai tace, "lafiya,"
Yace, "nazone inbada hakuri kan laifin danasan
za'a gani nawa,duk dacewa bansan fitarsuna
tinda ni bama na gida,laifin Mujidat ne kuma
nayi mata hukunci."
Iya tace, "can da matsalarku, sai dai abinda
zanfadamaka yarannan sunzo kenan,kuma abin
da kukayi musu Ku da Allahnku,"
Aliyu yace, "Dama ni bawai zan Koma dasubane."
Iya tace, "ai nazaci takardara sammaci kazo
kawomana." Ya mike yasake fadin aymin afuwa.
Ya dubi Khausar, "bazaku gaisheniba?"
Tace, "ina wuni Abba,"
Almin kuwa cewa Yayi, "mudai bazamu bikaba,"
Yace dama badaku zan tafiba.
Ya iso gurin su Khausar ya dauki Sadiq yafita.
Bai zaci zai samu sauki a guri Iyaba,yasandai
damuwar dama kar yakuma daukan yaran, kuma
dama ya yanke hukuncin barinsu fishintama na
yaune.
Yakira Usaman a waya suka gaisa samasama yace
,"Aboki kana gidane in iso ? Yunwa nake ji,gidan
su Iya kuma babu fuska."
Usaman yayi 'yar Dariya sannnan yace, "ka isa
gidan zan sameka a can."
Aliyu yace, "kayi nisane?"
"Inna Office din 'yansanda na nan unguwar."
Aliyu yace, "lafiya me kake a gurin?"
Usam yace, "wani dan case ne."
Aliyu yace, "shine bazaka sanar daniba, bari
inzo."
Ciki yakoma yamaida Sadiq, a cinyata ya ajiyeshi
ya fita,yana Isa office yansanda suka soma
kamewa suna sara masa, Oga yana ciki.
Agaban DPO yasmu yaron tare da Usama, DPO
ya mike ya kame sannan suka gaisa. Aliyu ya kalli
Usman, "Yaya, me yafaru aboki,"
Usaman yace, "irin yarannanne masu bude
account da Sunan mutane su kullamusu sharri."
Aliyu yace, "to shi wa yayi?"
Usma yace, "shine yayiwa Sadiya,"
Aliyu yace cikin sauri, "wace Sadiya,"
Usman yace,"wadda nake neman aurenta."
Kan Aliyu ya kulle yace, "dama zakayi aure?"
Yace, "Eh,bamuyi zancen dakaiba ko?"
Ya kalli yaron, "kasan Wannan?"Yanuna masa
Aliyu, yaron yace, "a'a,"
Daga nan Usman ya kalli DPO; "yanzu ni zan tafi "
Aliyu ya zauna, "bangane zaka tafiba, wai yaya
case din yafaru?"Nan aka umarci Jamilu yayi
bayani kamar yanda Yayi dazu.
Jamilu yace, "nidai wani yarone kanin Aunty
Ramatu ya kirani inzo zanyiwa wata Auntynsu
wani aiki,dama yana zuwa Cafe dinmu yana
Browsing, danazo sai tace inbudemata wasu
account guda biyu,zata yiwa kishiyarta sharri,
kawai Sai na yarda sabida ta yarda zata bani
Dubu5,nikuma dama inna neman dubu 5 din
sabida zanse JAMB Form dan shiga Jami'a.shine
nayi mata har yau kuma bata cikamin dubu
biyunba,sunma tashi daga garin."
Aliyu ya dinga kallon Jamilu tamkar yanason Yayi
tajin labarin kokuma labarin ya burgeshi. Usman
yace Jamilu sakamakon wanna hada Chat din
danayi nafada maka kasan aure yarabu? karaba
uwa da 'Ya'yanta? yanuna Aliyu Kaga mijinsu
nan,wadda kayiwa sharrin da wadda tasaka kayi
aikin."
Mamaki Yakama DOP yace, "Dama abin yafaru ne
a gidan Oga?"
Aliyu dai hannu a cikin aljihunsa yarasa me zaice,
Jamilu kuwa zubewa Yayi gban Aliyu yana
rokonshi cewa a yafemasa, shi dama wannanne
karo na farko da yasoma kuma bazai karba.Aliyu
yamike yakalli Jamilu, "Ayimaka hukunci daidai da
lefinka sabida masu hali irin naka." Har waje DPO
ya rako Aliyu, sam Yakasa magana sai zufa
yakeyi, zuciyarshi nata fadin kayi wauta.
Suna tafe shi da Usman shiru babu mai magana
saidai shi Usman ranshi Fes yaji dadi komai
yafaru a agaban Aliyu.
Koda sukaje gidan Usman din Aliyu Yakasa yin
tinanin komai,yamaji cewa yakoshi,duk da irin
yunwar dayakeji, idanunshi sunyi jazir.
Usman yace,"Aboki bisimillah"
Aliyu yace,"haba aboki, yakake tinanin zan iya cin
wani Abu a halin danake ciki? Don Allah kaima ka
ajiye muyi magana."
Usman Yayi murmushi, sannan yasake cika
cokalinshi ya tura baki yace, "wace magana
zamuyi."
"Ta Sadiya mana , gaskiya nayi wauta danaki
natsaya nayi bincike,kuma saida tace inbincika."
Abida dake jiyosu batasan sanda dariya ta
subucemataba, saidai taji Aliyu yana cewa "au!
dariyama nabaki Madam?"
Abida tace, "yanda kake maganar ne yabani
dariya."
Usman yace, "ai abin dariyarne,ni yanzu bazan
saka bakinaba cikin wannan lamarin, Sadiya
Alkawari nayimata zanyi bincike ingano masu
hannu cikin wannan lamarin kuma Allah ya
taimaka nasara tasamu,daga nanma sai can gidan
sabida insanar da ita,saikuma mudora daga inda
muka tsaya kan maganar auranmu."
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Aliyu yakalli Usman cikin tsananin bacin rai
yace,"kai nalurafa ba kasan kawaiciba ko?"
Usman yace, "kamar yaya?"
Aliyu yace, "wallahi dan kaine kunnuwana suka
jure jin kanacewa zaka auri Sadiya."
Yamike tsaye,"Wato damacan kanason matata tin
muna aure ko?"
Usman yace, "sam karkayi wannan tinanin,
hasalima ka manta kaine kabani shawara in
aureta lokacin danake lallabaka kamaida ita? Kace
ai bai haramtaba inna aureta, katuna? Shine
kawai mukayi shawara da Abinda,kuma
Alhamdulillah zance yasoma bisa...."
Aliyu ya harari Usman, sannan yaja tsaki yanufi
waje yanacewa, "Kadakatar da Neman aurenka."
Usman yace, "Sabida me?"
Aliyu wanda yakai bakin kofa, "najanye shawarar
dakace nabaka,inkuma kaki ji kada ka zargeni
akan abin dazaibiyo baya."
Usman yace ," aboki kazo muyi magana a zaune"
Tsaki Aliyu yayi tare da bugamusu kofa yayi
waje,ranshifa yayi zafi.,dama Habu yagayamishi
Usman ke zuwa gurinta duk kwana uku,saidai
sam bai tsammaci yanazuwa don sontabane.
Yashigo gidanmu inna shirin fita zuwa Isalamiyyar
'ya'yana tada domin inmaidasu, yanda naganshi
yashigo a sukwane nadan tsorata.yace, "ina iya?"
Nayi masa banza,yashiga daki tare da cewa, "zo
Sadiya!" Yayi maganarne cikin taushin murya.
Nashiga.
Yace, "Sadiya don Allah kinyafemin nayi
kuskure,ashe Mujidat ce duk ta kullamiki Wannan
Sharrin?"
Iya dake cikin daka tace, " Usman yakira waya
yayimana bayani yanzunnan,binciken da kakasayi
shi yayi kuma Allah yatoni asirinsu."
Aliyu yace,"Usman ai ba don Allah yayiba,yayine
don manufar kanshi,kuma wallahi Usman inbai
kiyayeniba za'ayi danyen aiki"."
Iya tace, "kai Gadanga da girmanaka kakeyin
wannan zancen,duk taimakon dayayi baka
ganiba?"
Aliyu yace, " Bansaniba". Yanunani.
"Kekuma zanfadamiki wallahi bake bashi."
Namike, "baruwanka da rayuwa ta don ni yafimin
kai."
Iya tace, "sau dubuma,kuma wallahi innaji wani
abu tsakaninka dashi Sai ranka yabaci,tsakaninka
dashi sai godiya."
Yace , "Iya matata fa yakeso,banda cin amana
yazaice yanason Sadiya?"
Nace, "Ok! Sabida bakasona shikenan kar kowa
yasoni ko?inkaga ban auri Usaman ba saidai
inbansoba kokuma shi yafasa....."
Ban ankaraba sainaga yatasomin zai
dokeni,nagudu nayi bayan iya innacewa, "Wayyo
Iya zai dokeni"
Yatsaya yana huci, "ni kike gayawa zaki auri
Usman?"
Iya tace , " tafada , hauka kake kadoketa?"
Yace, " inna tacigaba da yimin irin wanna zancen
bashakka zan jimata ciwo,kuma Usman zaisha
mamakin abin da zanyi masa."
Nace, "karkaga wani kana dansanda,inkatabashi
baza'a barka ba."
Yace, "kimin shiru,karkibari inzonan wallahi zan
ballaki." Yajuya fuuu! Yafice rai a bace.
Nasauke ajiyar zuciya,nace, "wallahi natsorata
ban manta da irin fishinnan ba,irinshi yayi lokacin
da akayimin wannan sharrin,jikinshi har rawa
yakeyi, Allah yatemakeni badan keba da yau naci
duka."
Iya tace, "tinanina yanzu Usman,ko kiranshi zakiyi
yanzu kicemasa inna nemansa?"
Nace , "to , bari inkirashi."
Tace "kishin banza ne ke cinsa a rai.
Nace , " Dama yabar Usman,danni ba auranshi
zanyi ba, na fadamasa hakane don kawai yaji
haushi.shima Usman din ina zaton dan yaturawa
Yaya Haushine yace yana sona."
Iya tace, "banda matar shi dake tsakanin ai
Usman mijine."
Daidai lokacin kiran yashiga, yadaga ,nace,"Yaya
Usman wai kazo inji Iya"
"Lafiya?" Cikin daga murya.
Nace "lafiya,kodai ba kalau ba."
"Ko Abokinane?"
Nace, "eh, ai yacene wai kace kana sona,a ina
yaji?"
Nina fadamasa,Kice iya karta damu, ni dashi
babu a binda zaifaru,nasan dama dole yayi
haka,ni dama hakan nakeso."
Nace, "to shikenan,sai anjima" nakalli iya bayan
nakashe wayar nace, "yace babu abinda za'a
faru." Nandai mukayi ta tattauna zancen.
Shikam yaya police yakoma yasake bincika Jamilu
ya tabbatar da gaskiyar lamari,sannana yawuce
Zuwa Abuja cikin damuwa. A daki ya kulle kan shi
yana tinanin tsantsar rashin kyautawar da yayiwa
Sadiya,baimasan ya zaiyiba.ya daga waya yakira
layin Usman har takatse yana kallo bai dagaba,a
karo na biyu ma saida takusa katsewa sannna ya
daga.
Aliyu yace, "Usama nakirakane ince kafita harkar
matata,zan dawo da Ita dakinta."
Usman yace, " innaki fa?kawai Mallam ka shiga
layi zawarawa nima inna ciki mai rabo
Yasamu,kuma banda abunka wannan baikamata
yashafi zumuncinmuba."
Aliyu yazo iya wuya,ranshi yakai matuka gurin
baci,yace, "ok! Haka kace? To shikenan kajira a
abin dazai faru." Yakashe wayar yanata kai kawo
a dakin,zuciyarshi tagama sakamasa abinda
zaiyi,kawai zuwa zaiyi yasa akama Usman, baza'a
fito dashiba har Sai anmaida auranshi da
Sadiya,inyaso saiyaga da wanda zaija.
Mujidat tasauka a garin kaduna kai tsaye
unguwar Mu'azu ta dosa,muna tsaka da cin
abinci kwanonmu daya da Yayana,tire ne dan
babba nazubamana,Danwake mukayi munaci
muna hira,Iya kuma tana gefe tanacin sauran
Tuwon Masara da Miyar Kuka.
Kwatsam sai mukaji sallama,zunbur namike ganin
Mujidat nace, "me kikazo yi gidanmu?"
Tace, "Ba gurinki nazoba,gurin sirikata nazo."
Iya tamike itama,"karki shigomin gida,juya."
Su Khausar kuwa tini sun ruga daki sun rufo
kofa,nace ," azzaluma kinje kin cutarmin da yara
duk da irin taimakon Dana yimiki."
Mujidat ta sheke da dariya sannan tace, "kikadai
taimaki mijinki,yanzu kuwa nazo na kwance kullin
da kukayi ke da mijinki."
Nace, "Ina ruwana,yanzu mijinkine ba
nawaba,inkinso ki tona,inkinso ki rufa."
Iya kawai ta tsaya tana kallonmu tare da sonjin
asirin da ake cewa za'a tona."
Mujidat ta kalli Iya tace, " Tsohuwar ba zama
nazo ba, nazone in fadamiki gaskiya tsakanina da
danki."
Gabana yashiga faduwa,tamkar in tashi in toshe
bakinta kar ta sanar da Iya taji bacin rai,banason
'ya'yana suji abin da ubansu yayi.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Mujidat tace, "Danki Aliyu ciki yayimin tin a
Ilori,yace inna yarda dashi zai aureni.Yayi min ciki
ya taho, nikuma na biyoshi,shine sukace inyi
shiru kar ince haka zasuce mijinane ya mutu
yabanni da ciki,kisani Abdul jikankine."
Na kalli Iya wadda takasa magana, na iso gurin ta
na kamata nace, "Iya zauna karki damu."
Iya ta fincike hannuwanta tace,"Sakar min
hannu."
Ta nuna mujidat "fita tinda kinfadi sakonki."
Mujidat tace,"Yanzu kuwa zan tafi burina yacika
tinda kinsani."
Nace , "To me yadame mu? Saiki fita ai ko?"
Ta saka dariya, kidena min korar kare,domin ko
bana auren yayanki uban 'Ya'yanki inna da yaro
daku."
Nace, "naji jeki."
Kafin insake magana Iya ta isa bango ta dafa,na
isa gurin ta,sannan nadauki wayarta na kira Yaya
Usman , nacemasa, "dan Allah kazo in kana
kusa,Mujidat tazo ta dagawa iya hankali."
A zaton ta Yaya Aliyu nakira,don haka saitafice da
sauri.Allah yasa Yaya Usman yana kusa ya iso
mukayi ta bata baki. Tace, " Ashe dake za'a hada
baki a rufeni?"
Nace, " Iya kiyi hakuri, alokacin ko anfadamiki
babu abinda hakan zai kareki dashi sai bacin rai."
Usman yace, " Iya lokacin abin da zaifaru yariga
yafaru."
Sai ga hawaye yasoma zuba daga idanunta, tace,
"Wato shi Aliyu ko yaushe shi zaidinga sani zubar
da hawaye "
Usman yace , "sai hakuri iya"
"Nagaji da hakuri da laifukan da Yake
aikatamin,ya batawa zuri'a ta suna,ya
gurbatamin zuru'a yabani mamaki."
Kukana ya tsananta,nace, "Iya kiyafemasa."
Tace,"kema ai a gurina me laifice balleshi,kike
cemin inyafemasa."
Usman yaciro wayarsa yakira laying Aliyu, lokacin
yagama shirya yanda zaisa a kama masa Usman
din domin bazai yuwu a kamoshi batare da wani
laifiba,dolene a nemi laifin da za'a
joganamasa,kamar kada yadaga layin, saikuma
yadaga cikin isa yace.
"Malam Lafiya?"
Usam yace, "kana inane yanzun?"
Cikin jin haushi yace, "menene kake son jin inda
nake? Innaso fa ka manta kasan ni."
Yace, "kafin in manta nasanka din kazo ga
matarka nan tazo ta kunce kullun da Kuke ta
boyonsa yanzu haka Asibiti zamu kai Iya."
Tace, "daina kiransa Usman, na yafeshi cikin
Yayana,ya nemi wata uwar shi ba zuri'a ta
bane..." Ta fashe da wani kuka mai ban tausayi.
Aliyu duk yaji wadannan kalaman dama wasu,don
Usman sam ya manta bai kashe wayar ba,sabida
wata irin sheshsheka da Iya tasoma.
Yace, "Sadiya dakko mayafinki da nata muje
Asibiti."
Ta dakko,suka kama iya zuwa Mota.
Sai da Sadiya tace zamu bar yaranne ? Sai yaciro
wayar tare dacewa, "bari inkira Abida tazo ta
kwashesu," a lokacinne yaga bai kasheba don
haka sai yakashe,sannna yasake kiran Abida.
Aliyu yanata kai kawo cikin ofishinsa gumi yajika
rigarsa sharkaf,ya balle duk botiran gaban
rigarsa, ana kallon singiletinsa,Sam bazakace da
Akwai AC a cikiba.
Kiran wayane yasashi isa gurin
wayar,kawimishinane ke nemansa wai zasuyi
wani dan meeting, a isa ofishin yana balle botiran
gaban rigarsa,sai kwamishinan yabukaci daya
zauna.
Bayan ya zauna be suka gaisa da sauran
mutanen daya gani ciki,fuskarsu ba boyayyabace
'yan siyasane na gwamnati me ci a wannna
lokacin,wasu masu neman tazarce wasu kuma
masu son sababbin mukamai.Aliyu fa ya hade rai
sabida ya lura 'yan siyasan nanfa sun raina
jami'an tsaro.
Wanda suka wakilta yayi magana shine ya
gabatar da kudirinsu na Neman goyon baya daga
jami'an tsaro,su zama suna bangarensu.
Kwamishina ya kalli Aliyu tare da bashi izinin
magana.
Aliyu cikin isa yace, "Ranka ya dade mu ba 'yan
siyasa bane,bazaiyuwu mu cusa kanmu cikin
harkar siyasaba,mu jami'an tsarone dole yazama
muna tare da kowa ku da 'yan adawarku,bai
kamata gwamnati maici dan kawai tana ganin
tanada madafan ikon a hannunta tayi anfani da
hakan gurin tursasamuba,mun San aikinmu,kuma
inshaAllahu in zabe yazo zamu tsay kai da fata
ayi zabe a gama lafiya.......zandakata anan
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
Darajar Yayana4-04
Posted by ANaM Dorayi on 07:27 PM, 16-Apr-16
Under: DARAJAR 'YA'YANA
_________________NA
___________HALIMA K/MASHI
Wakilin siyasa yace, " amma mu muke daku tinda
muke da gwamnati." Ya kalli kwamishina.
"Ranka ya dade kai yakamata kace wani
abu,sabida wannan mataimakin naka ya nuna
karara baya tare damu."
Yace,"zantukanshi suna kan hanaya,sai dai
zamuga taimakon da zamuyi muku."
Sai suka mike tsaye suna zantuka,wani harda
Cewa, " kujerarku tana rawa,domin kunsan akwai
nasama daku,kuma su namune inkunce Ku ba
namu bane."
Aliyu ya lumshe Ido,baiyi wani mamakiba domin
yasan su basu da wani buri sai son kansu,amma
indai yana nan da yardar Allah sai ya hana
ruwansu gudu,zai dawo da martabar 'yan sanda.
Bayan tafiyarsu kwamishina ya kalli Aliyu yace,
"kamin dai-dai,shiyasa nakiraka."
Gida Aliyu yanufa,sintiri yakeyi tare da kai kawo
daga falo zuwa dakinshi,yarasa ta ina zaibi kuma
wa zaikira yabashi shawara? Yazauna yaciro
wayarshi yanabin lanbobin daya bayan daya
yanason yaga wa yakamata ya canja abokin
shawara madadin Usman. Yaduba har karshe
baisamuba,wata zuciyar tace dole dai Usman ne
zaibaka shawarar data dace.
Tsaki yaja,sannan yabi shawarar zuciyarsa
yasoma kiran layin Usman,duk dacewa shi yafi
tsana a halin yanzu.Ringing biyu Usamna ya
dauka,yace,"Aboki ya akayi?"
Cikin tsana yace,"bawani zancen
Aboki,nakirakane inji ya jikin mahaifiyata?"
Yace,"da sauki,amma zaifi kyau kazo kadubata."
Yaja tsaki ,"bayan kaje ka shishshige a gurinta
don tabaka matata."
Usaman yasa dariya,"Aboki ka aje kishi a gefe
guda,muyi magana me muhimmanci, Sadiya
allurace cikin ruwa,kaga kenan me rabo
kadauka."
Aliyu ya runtse ido,jiyake maganganun Usman na
sukarsa cikin rai,amma dayake shawara yake
bukata sai ya danne yace, "InshaAllahu matatace
ni Daya." Yacigaba da Cewa.
"Kana ganin inzo gurin ta ko Yaya?"
Yace,"zaufi kyau kazo din don kabata hakuri."
Yace, "kana ganin inzo yau ko gobe?"
"Kabari sai jibima,domin lokacin ta dan huce," inji
Usaman.
Aliyu yace, "to shikenan zamudinga yin waya."
Iya ta tara sauran 'ya'yanata tafadamusu abinda
Aliyu yayi,kuma tace musu ba'ita babu
shi,tacireshi daga sahun 'ya'yanta,nima da kyar
na wanke kaina daga zargin datakemin wai na
rufeta.
Yaya Sulaiman yakira Aliyu yamasa Nasiha kan
abin da yayi,Aliyu yabashi labarin yanda
abubuwan suka faru,yakuma yimasa rantsuwar
cewa yanzuma yadena.Yaya Sulaiman Yayi masa
fadan girma sannan yace yaje yanemi iya
gafara,don tadau zafi dayawa.Kwananmu Daya a
asibita aka sallamemu,Yaya Usman da sauran
'ya'yanta sunbata kulawar data kamata.
Na idar da Sallar La'asar na nufi kitchen domin
dafawa Iya wake da Alayyahu sai naji sallamar
Yaya, na amsa amma ba lallai yajiba,bankuma
kalleshiba nacigaba da harkar gabana.Bakin
kitchen din yazo ya tsaya,kamshin turarensa
yacika kitchen din,nakalleshi cikin tsana.
"Lafiya?"
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Yace, "in ina cikin damuwa da nakalleki sai inji ta
yaye."
Naja tsaki, "dan Allah kabani guri kaje kaji da
kalubalen da yake gabanka."
Yace, "Don Allah kitayani bawa iya hakuri nasan
zaki iya shawo kanta."
Nace, "eh, dama bakasan daniba sai matsala ta
sameka wadda kake ganin nice zan iya yima
maganinta." Najuya baya.
"Malam kaje da matsalarka,Yanzu ni babu wata
alaka tsakaninmu dazan iya yimaka wannana
arzikin.jeka da kanka,innace mahaifiyarkace?"
Ya tausasa murya, "Don Allah kizo muje innason
muyi zancen gabadayane harda batun auranmu."
Naji tamkar ya watsamin wuta,Nace,"Allah ya
kyautamin,." Naja tsaki tankashima bata
lokacine,don haka yagaji da surutunsa da
banbakinsa ya kyaleni.
Inna jiyoshi yanatayiwa iya magana tayi banza
dashi,nasaka kujera bakin kofa na zauna,yayi ta
bata hakuri,amma kala bataceba,sai datagaji
sannan tace, "Don Allah kafitar min daga gida,
Innaso insanar dakai tini nacireka daga sahun
'ya'yana, bana koson ganknka."
Yace, Don Allah iya kiyi haku...."
Ta katseshi, " inkanaso inyimaka baki to kacigaba
da zama a cikin dakinnan "
Tsam yamike yafito yanufi waje cikin damuwa,
baifi minti 5 da fitaba yayomin text wai in yara
sun dawo daga Islamiyya inshiryasu zasuje shan
Ice cream,tsaki naja na aje wayar gefe.
Shida da mintina,suna shigowa yana shigowa,
saikace dama yana wajen yana jiransu,jin
muryarshi duk yaran sukaje suka makalkaleshi
harda Sadeq dake koyon rarrafe,sai daga hannu
yake wai dole yagane babansa.Ina Mamakin
yaron.
Yace, "kuje kucire kayan makaranta kuxo muje
shan Ice cream." Yarannan sai suka hau murna
da tsalle.
Khausar ta nufi iya tana murna tana cewa, "Iya
zamu fita da babanmu."
Wata tsawa da iya tayiwa Khausar ni kaina saida
na tsorata,tace,"Ku tashi sama mana da Baban
naku me yadameni?"
Karshe dai da kayan makaranta ya tattarasu suka
tafi harda Sadeeq.
SaKu ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347i Tara saura suka
dawo,lokacin sadiq yayi bacci,ni da iya wai har
tsaraba yayimana don neman gindin zama.
Yanda iya bata kalli ledarba, haka nima nayi
saida Iya tafita sannan nace dasu Khausar Su
dauka su hada datasu.
A daren ne Alhajin nan yasake zuwa karo na
uku,biyun ban fitaba,nace ace bana nan,Amma
yau sainafita sabida nasan Yaya yana
nan,tayiwu yazo zanso ya ganmu. Kwalliya nayi
sosai, sannan nafita.
Cikin wata dankareriyar Mota yazo sai kamshi
Yake,na kwankwasa motar sai gashi yafito daga
gidan baya yace, "ranki ya dade yau dai naci
sa'ar samunki,amma naji Dadi."
Nayi murmushi sannna na rage tsawo nace, 'ina
yini?"
Yace, "Lafiya kalau," Bayan mungaisa yace,
"Mama tana ciki?"
Nace, "Eh"
"Inna son mugaisa."
Tofa!,bani da zabi,dole saidai inkaishi din.
Na shiga nagayawa Iya za'a shigo gaidata,tace,
"toh"
A gaban iya yazube ya gaisheta,itako Iya harda
fadamasa cewa; ni marainiyace,dan Allah in
aure ya hadamu yarikemata ni amana, saboda
na wahala a gurin mijina na farko,shi kam sai
yace ,yaji komai game dani, tinda ya ganni
yasan innada tarbiyya sabida naki yarda inhau
motarshi, mata yanzu da zakaga suna tare mota
da kansu wai dan a ragemusu hanya! Yacigaba
da cewa, "Sai danasa akaimin bincike akanta,
kuma naji sakamako me kyau don haka nashigo
da karfina zan aureta."
Iya tace, "InshaAllahu, yanzu kaima yakamata
insanka."
Yace, "Sunana Alhaji Badamasi Yunusa,ni dan
asalin jihar katsinane karamar hukumara
Bakori,inna nan gwamna road da iyalina,matana
biyu,yarana goma,ni ma'aikacine a matatar man
fetir dake nan Kaduna."
Iya tace, "to shikenan,Allah ya tabbatarmana da
alherin dake ciki."
Yace, "Ameen."
Kan ya wuce saida ya ajiyewa iya daurin yan
dari biyar guda daya. Nafito daga uwar daki dan
innajinsu,iya tace, "da alama yanada
mutunci,nace, "nalura tin farkon haduwarmu."
nakoma gurinsa inda yacigaba da yimin zancen
aure,shi bayason adauki lokaci,sannan yanason
muma muyi bincike a kansa,bayan nan zai turo
tinda yanzun mu ba yara bane da zamuyi ta
doguwar hira,nace , to! Yabani lokaci nayi nazari
da tinanin kafin ya turo din,Yace to yabani,nima
haka yacikani da kudi,nayi nayi yabarshi yace
Sam; dole nakarba. Yataka zai shiga Mota kenan
Aliyu yayimana sallama,shine ya amsa nikam
gabana sai faduwa yake. Yace, "Alhaji nazone
inyimaka gargadi."
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Alhaji Badamasi yace, "name fa?"tare da
dawowa da kafarsa.
Aliyu yace," wannan matatace, dan Allah
karkasake zuwa."
Alhaji Badamasi yadubi gurin danake Yace,
"Wannan ne?"
Koda bansan meyake nufiba Sai nace, "Eh! Shine
Alhajina,shiga motarka kayi tafiyarka sai munyi
waya."
Tamkar me jiran umarnina sai kurum yashiga
mota tare da cewa, "sai kunjini ginbiya."
A hankali motar ta silala ta dauki hanyar barin
layin. Cikin zafin rai yasha gabana, "wato harma
labarina kike bayarwa ko? gani dan iska!"
Nace, "Eh!" Nacigaba da tafiyata."
Yace kinsan Allah zakijamasa bala'i,zan tono
laifukansa inmasa tarko yafada hannunmu,ai
nasan shi."
Tsaki naja nacigaba da tafiya inna cewa dadinta
baka isa kayimasa abinda Allah baiyimasaba.
Innashiga zaure shima yashigo, "Sadiya dan
Allah tsaya kiji." ya tsare hanyar shiga gidan ya
tausasa murya, "Sadiya dan Allah ki rabu da
mutuminnan, yawancinsu suna ta'ammali da
matan banza."
Nasaki dariya cikin izgili Nace, "wannanfa shine
shege! Yi da me zina," nanunashi da yatsa,
"ashe har kai zaka dinga zargin wani cewa yana
bin mata? Kamanta da naka laifin ko? har
sakamako ka ajiye." Nayi murmushi, "bani hanya
in wuce."
Yace, "Naji dai,duk abin da zaki cemin
Kice,amma zan nunamiki cewa nidai nine
mijinki."
Na ratsa ta gefensa na wuce,bansan yabiyoniba
sai da namikawa iya kudin inna cewa "nayi-nayi
yabarsu yaki."
Ta ciro nata tace, "kingansu dami guda, Allah
yashi albarka,tinda yafadi inda yake zansa
yayanku babban a bincikomana,in bashi da wani
aibu shikenana."
Kurum sai Yaya yafado dakin, "Dama sabida
kudi kike sonshi ko Sadiya? Sannan kuma kisani
bazakiyi aureba har sai kin yayemin yarona."
Nace, "ina ruwanka dani? Yaro kuma dashi zanyi
aure a can zan yayeshi."
Yasake daga murya, " kinyi kadan."
Da hannu iya tayimin alama wai inyi banza
dashi, don haka na shareshi Yakara masifarsa
ya nufi waje.
Ranar Aliyu yaga tashin hankali,yanzun yanda
zai shawo kan Sadiya da Iya yake nema.nikam
dan So banson Alhaji,amma zan iya auransa da
in auri Aliyu ko Yaya Usman, in anyi bincike zan
amince muyi aure kawai in huta.
Aliyu fa yadage kullum yana kan hanyar gida
daga Abuja,yana gida yana bawa iya baki,ya
turo wannna ya turo wancan,rokon gafara har
dasu mahaifina. Andau tsawon wata biyu a
haka,lokacin zancen aurenmu da Alhaji yasoma
nisa,dan batun har yakai Zaria. Yaya Aliyu kam
yadan rame duk da juriyarsa. Saifa yadauki wani
sabon salon kamun kafa da yaransa,kawai sai
mukaga yara sun canja ba kamar Khausar, in
Alhaji yazo ta dinga kunci kenan harda
Kuka,dana tanbayeta dalili wai inkoma gidan
Babanta,ranar har marinta nayi, iya tayimin
fada wai indena dukanta,ammafa baza'a
komaba. Ko Yaushe zaizo yakwashesu zuwa
yawo yanatayimusu hidima. In Iya kuma tayi
maganarsa sun dinga kunci kenan,har Mama.
Wata ranar Juma'a muna zaune iya taje
Masallacin Juma'a Yaya yayomin waya inshirya
yabiyamin kujerar maka ni da Iya zamuje,duk
da farincikin daya girgizani amma sainace nikam
nagode bazaniba zamuje da Alhajina,
( Lallai Sadiya kin burgeni,ANaM Dorayi
hhhhhhh)
Bantabaji Aliyu yayi babban zagiba sai yau,ya
kudundumawa Alhaji zagi, da sauri na kashe
waya
Yaya Sulaiman yazo da daddare cikin murna
yana gayawa Iya wai Aliyu yabiyamusu Hajji shi
da Iya da Mahaifina,ga mamakina sainaga tahau
murna harma tasoma kiran 'yan uwa a waya,
saidai banji ana kiran sunana a 'yan tafiyaba
Alhalin ya cemin yabiya ni da iya.washegari
makota sukai ta shigowa taya murna iya tana
yaye baki, amma da yamma da yazo sainaga
tayi kicin kicin,musamman nazo nazauna inji ko
zaiyi batun tawa kujerar, sai naga iya ta tubure,
"Naji sakon, nagode, amfa kasani karkazata zan
hakura da laifin dakayi,hajji kiran Allah ne koba
ta hannunkaba indai an kirani Sai naje."
Yace, "hakane Iya,innadai neman afuwa,kuma
dama kujeru hudune yanzu saura daya shine
nace kowakikaga yadace abaiwa? Har na bawa
wani sai yace bayaso."
Iya tace, "kai wannan wane mara rabone? To kai
kajene?"
Yace, "a'a zanje wata shekarar,sabida Siyasa
datake bullowa a daidai lokacin aikin
hajjin,kasarnan tana bukatar Irina."
Iya tace, "Allah yataimaka "
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Nashiga daki cikin takaici, bakina ya
cuceni,da'ace nasan Iya zatayi saurin yadda da
batun da bance banasoba,gashi tace yabawa
kawunmu kaninta na Hadeja.
Aliyu yasamu sassauci gurin iya da yan'uwanshi
sanadin wadannan kujeru da yabiyamusu yanzu
burinsa kawai ya shawo kan Sadiya, amma ta
yaya bayan tabawa wani dama har ankawo
sadakinta.
Daya Isa Abuja kai tsaye Office yawuce sai wajen
shabiyu yaje gida, abinda yabashi shi mamaki
yanda yaga ankulle kofar falon ta ciki maimakon
ta waje, yasaka Key yaki shiga sabida akwai
wani ta ciki,don haka sai ya kwankwasa don
yaga ikon Allah,jim kadan aka bude. Mujidat
yagani, tayi kyau iya kyau,kamar farkon
haduwarsu, ta rungumeshi; Oyoyo Mijina,ya
yakiceta ya tureta yadaga murya, "Wayace
kidawo gidana?"
Tace, " to inna can zaune bakazoba"
Ta nufi ciki ya shiga, ta nunamasa tebur da
hannu; " ga Abinci."
Yace, "bana ci."
Ya nufi dakinshi ta bishi, bandaki ya fada ya
watsa ruwa, yafito yayi shirin kwanciya yana
hawa gado itama ta fada,Yace, "kifita,kuma
nabaki zuwa da safe kibar gida na."
Tace, "Gidanmu dai, dan Allah Honey kayi
hakuri bazan sakeba."
Yace, "kina takama da aurene ko? To ni zan
ball....." Ta katseshi ta hanyar manna bakinta a
a cikin nasa,hmm Mujidat yar duniya, sai datasa
ya manta komai,yashiga shawagi cikin duniyar
Ma'aurata. Haka ya hakura ya barta sannan ya
dakko mata danta daga inda yakaishi Ajiya
bayan taimasa alkawarin bazatasake
sabamasaba,kuma zata mutunta kowa nashi.
An ajiye lokacin bikinmu nan da wata
biyar,lokacin na yaye Sadiq,Alhaji Badamasi
nason yin dawainiya damu danma iya tana
hanashi,su Khausar sun tsaneshi,har shidakansa
ya fahimci hakan,har yataba cemin, meyasa
yarananan ko yakirasu basason Zuwa? Nace
haka suke basu da sabo.
Cikin yan kwanakin da suka biyo baya Yaya
banda kyautatawa dangi baya komai,ya
kammala gidanshi dankarere yace Iya takoma
donshi ba shiga zaiyi ba,namu nada kuma Yaya
Sani yakoma.
Nadauka Iya zatace a'a,sainaji tace zatayi
shawara, Nace, "to iya komawa zamuyi?"
Tace, "Eh,ai abinda baifaruba shi ake gudu
Sadiya, wanda ya faru saidai a kiyayi gaba.Aliyu
yariga yanemi afuwa ta yaya zanyi? Sai addu'a
inna nunamasa fushi nane don ya kori gaba
yakuma gane yayi ba daidaiba."
Nace, "yanzu dai za'akoma gidan kenan?"
Tace, "to waye bayason cigaba yarnan?"
Natabe baki cikin takaici nace, " to saidai
kukoma kubarni a nan, ko kujira in nayi aure ku
kuntare." Iya dai banza dani tayi. A raina nace
wato da da Mahaifi sai Allah,yanzu iya har
tamanta da fishin datakeyidashi.
Wata ranar asabar yazo har da Abdul su
Khausar suna ta murna ganin dan'uwansu nidai
beganeniba yaron,lokacin iya na makota.
Yaya Yace, "gabar harda danki?" Nidai ban
tankashiba, Allah-Allah neke iya tashigo naga
irin warwarar dazataimasa amma tana shigowa
sai naga ta hau washe baki.
"Ai harda Abdul din kazo."
Al-amin yakamomasa hannu, "gashi Iya."
Ta daukeshi tanacewa Khausar ta debomasa
ruwa a firij,Yaya ya kalleni harda yin wani
murmushi,wato inganidai bashi da wata
matsala, nima dan inkular dashi nadauki wayata
nakira Alhaji Badamasi mukagaisa,nace, "Alhaji
zanje unguwa kozaka aiko akaini."
Cikin murna Yace, "dole inbar komai inzo inkaiki
"
Nakalli fuskarshi kamar zai fashe da
kuka,murmushi nayi na tashi na hau yin
kwalliya, minti shabiyar saiga kiranshi,
"Na'iso ranki ya Dade "
Nace, "dama kana kusa kenan,to ganinan
fitowa."
Nadinga yiwa jikina aman tirare har saida ya
time,yace,"wai ke ina kike shirin zuwa haka?"
Nace, "Sai kaji? Ba matsalarkabace."
Ya kalli iya, "haka take yawo kamar mara
mafadi?"
Iya tace, "shi zata aurafa."..
Nazo fita ina wucewa ina cewa, Iya zanje gidan
Aisha,tace, "ki dibarmata kwai."
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ya kara kulewa,sai yatare bakin kofar, "To Koma
ki dauki Sadeeq bazakibarshi ya tashi yadinga
kukaba."
Dariya ke nema ta kufcemin,Nace, "Kasan Allah
yayi kukan jini inyatashi nikam bazani dashiba."
Yayo kaina, nayi bayan Iya inna fadin, "Dukana
to zakayi?"
Yace, "bakin rashin kunyar zan buge."
Nace, "Aiko daka amsa tanbayoyin Alhaji,domin
matsayin matarshi nake." cike da rashin kunya
nayi maganar.
"Inma matsayin uwarsa kike be
dameniba,amma daukarmin yaro aje duk inda
za'a dashi."
Na kalli iya wadda tinda tayi magana dazu bata
kuma yin maganaba, sai nagama dariya take
kunshewa dan abin dariya itama yabata.
Nace, "kifada masa yadena zargin mijina." Sai
naji jifa a kafadata da wayar shi, nashiga uwar
daki inna sosa gurin domin naji zafi,bakina bai
mutuba innacewa, "Ba inda zanje dashi kome
zakayimin."
Iya tace, " ina ruwanka da sune? Yaza'ace
saitafita da yaro dole?"
"Iya amma inyatashifa yanason nono?"
Nace, "nawa kake biyana kudin shayarwa?"
Yace, "kifadi kudin nonon gabadaya a biyaki."
Iya tadaure ta hade rai tace, " to tinda ban
isaba kacigaba."
Yazauna tare da fadin, "shiyasa tagama
rainani,domin kankomai sai a nunamata tafini."
"Au, hakama zakace?"
Sai kuma cikin sauri Yace,"iya kiyi hakuri." Nidai
nafi to na debi kwai kawai nayi gaba.
Tin bayan fitata kai yadafe, baisan ta ina zai
bullowa lamarinaba,abinda dai yayiwa kansa
alkawari shine , bazai taba bari Sadiya ta auri
waninsaba,yadogara ga Allah ta hanyar
tsayuwar dare tsananta addu'a,Allah baya bacci.
Nikam a gidan Aisha inna fadamata yanda
mukayi munata kwasar dariya,Aisha tace Sadiya
nidai bazangaji da fadamiki da Aliyu kadai kika
daceba,shima dake yadace, nace tabdi, ni yanzu
nacire batun wani so ko dacewa a cikin raina,
nafiso inyi aure inda za'a ga mutuncina,insamu
tsabtataccen miji mara aibu,tace ai bari
infadamiki Sadiya a wannna zamani da wuya
kisamu mara aibu,sai dai wani yafi wani,ni
innagudun kar kiyi gudun gara ki afkawa zago,
amma shi din kinbincika halinsa?
Nace, "iya ta bincika ba matsala"
Tace, "shikenan Allah yazaba mafi alkhairi."
Aliyu yacewa iya yagama zubamusu kaya a
wancan gidan sati me zuwa zasu tare.
Iya tace, "Ai nazata sai mundawo aikin hajji anyi
bikin Sadiya don batason tarewa a gidan."
Yace , "a'a, tafiyarku saura wata Daya da
kuntare kawai,"
Tace, "ko a barshi mutafi daga nan inmundawo
lafiya sai musauka a can."
Ranar tafiyarsu iya har kuka nayi, nace yanzu ni
kadai zan zauna a gidannan sai yara, gashi
zandinga tafiya makaranta, iya tace, "bana
fadamiki matar kawu Hauwa tana nan tahowaba
daga Hadeja tare zaku zauna,in Allah yadawo
damu lafiya sai sutafi tare da kawun naku ko?"
Nace, "shikenan,"
Amota Daya Yaya yadaukesu wata kuma aka
debi 'yan rakiya, nidai dama nafadawa Alhaji
kuma yaturo direbansa yakaini, Aliyu ya hana
yaransa shiga motar, nace ohodai.
Bayan tafiyarsu Iya da sati daya sai ga yaya
sunshigo da Habu, na daure fuska muka gaisa
da Habu,dama alokacin zantafi gurin aiki, sai
kawai nafita.
Aliyu yasa Habu yayi ta jidar kayan yana kaiwa
gidansu, irinsu kujeru,TV harma da fringi,Baba
Hauwa tace lafiya? Aliyu yace dama zaku
tashine,kayan nabaiwa uwar yaron nanne
mokatanmu."
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Tace, "harda firingin? Amma danasani na
tanbayi firing din innasonshi,Aliyu yace, "inzaki
tafi sai insemiki wani"
Tasoma godiya yace ai ba komai,nidai addu'ar
dazakiyimin Allah yasa Sadiya ta yarda tadawo
gurina.
Baba Hauwa tace, "Ai dama kanasonta baka
yunkuraba?"
Aliyu yace, " Ai babu irin yunkurin da banyiba
amma yarinyar nan taki yarda dani,yanda
kikasan inyi hauka."
Baba Hauwa tace, "shikenan zan tayaka
addu'a,sannan zan dinga dan cusamata ra'ayi."
Yace, "nagode, nikuma zanmiki alkhairin da
bazaki mantaba indai kika shawomin kanta."
Nadawo naga gidan wayam, yarana da
murmushinsu suka tareni da batun wai Abbansu
yace yau zamu tashi,tsaki naja tare da cewa dan
Allah kukauce kubani guri,raina yabaci daganin
hukuncin da Yaya ya yanke, na dinga zaga dakin
inna kallon jakunkunan kayanmu a kasa anfito
da komai sai gashi yashigo, "kufito Habu yayi
gaba damu nikuma zantaho da jakunkunan, ko
bata dawoba?"
Baba Hauwa tace, "tadawo tana ciki."
Yashigo cikin dakin, "Sadiya" nakalleshi cikin
bacin rai,har saida yayi in'ina kafinyacemin,
"kizo Habu yakaiku" Nace ina? Yace sabon
gidanku, na girgiza kai gami da tabe baki,
gidanka dai bazaniba.yashigo tare da tausasa
murya yace , Sadiya wai bazaki yafeminbane?
najuyamasa baya, "wai me zanmikine kiga
haskena Sadiya?" na waiwayo na dubeshi,
"rabuwa dani kawai za'ayi kadena shiga harkata
sai inyafemaka." Ga mamakina sainaga yazube
gabana gwaiwa biyu biyu yanacewa, "Sadiya dan
Allah na rokeki ki yafemin kidawo aurena wallahi
ke kadai nakeso,kanki nasoma sanin wacece
mace, dake kadai nake samun nutsuwa, Sadiya
ki amince kiyimin takaba."
"Takaba kuma?"
"Inna nufin kikoma gidan har inmutu kiyimin
takaba."
Na tabe baki,"ga Mujidat can zatayimaka takaba
ni bazan iya zama dakaiba," nasake juya baya,
sainaji muryar Khausar, "Dan Allah Mama dan
girman Allah mamanmu," nace nifa bazan koma
wani sabon gidankaba bare aurenka inkamanta
abindakayimin to ni banmantaba, yamike, "ke
wace irin zuciya gareki bayan na kaskantar da
kaina na rusuna a gareki akan kiyafe kidawo
kince a'a to bari kiji dole nema ki Koma gidan,"
nace, "bazan komaba" Yace, "to ai nanma gidan
ubanane,meye banbancinsa da nawa?" Na
kalleshi cikin bacin rai, "dadin abin nima ubana
yanda gidan, kuma zankoma yanzunnan."
Nasoma hada kayana, da sauri yafito yana
fadawa baba Hauwa wainace zantafi gidan
banana, sai gata tashigo, "haba Sadiya, me yayi
zafi haka,"
"Gorin gida yayimin, dan haka zan tafi gidan
ubana,"
"inkinyi haka kuwa iya bazataji dadiba," nasoma
kuka to Baba Hauwa duk yatakuramin, ina
ruwansa dani? gara intafi abuna." Tace, "ba inda
zakije, kuma yanzunnan zamu tare a sabon
gidan idan na isa dake, inkuma taurin kan zaki
nunamin ina yabinki to bisimilla."
Shiru nayi dan babu abinda natsana a duniya
irin babban yaga na raina shi, banson ayimin
shaidar rashin kunya, inna kuka riris Muka shiga
Mota zuwa gidan da yaya ya ginamana.
Sam barka,gaskiya gidan ya tsaru. Abin mamaki
can Muka samu makotanmu sunje kallon gidan,
inna zaton Yayane yasa Habu yasanar musu
zamu tashi. Anzuba komai sabo, tafkeken falo
da dakuna hudu, nawa dana Iya dana yara,sai
na baki. Can gefe ga wani gini, dana tanbayi
Habu sai yacemin na megidanne in yazo hutu,
"muje kigani." Nace bazaniba. yara kuwa sai
murna suke suna tsalle ga kayan wasansu nan
kala-kala. Bayan kowa ya watse na daga waya
nakiraki Aunty Abida inna gayamata yanda
mukayi, tace zatazo, A'isha ma haka.
Inna kitchen dinmu mai dauke da kayan girkin
zamani, inna yiwa yara abincin tafiya
makaranta, dayake da safene, zani na daura
akan rigar baccina,Sai hula akaina, sai naji
maganar Yaya a bayana.
"My choice, me kikeyine.? Nadafe kaina cikin
takaici,na kalli jikina, yaci ace da hijabi a jikina,
sabida kirjina yafito, dayake rigar tana da katon
wuya, nace, " Lafiya?"
Yace, "lafiyalau, nazo ingaishekine "
Nace, "nagode, jeka."
Ya iso daf dani, "kintashi lafiya?"
"Don girman zati kafita, mufa musulmine, bai
dace kazo inda nake cikin kowane yanayiba."
Yace, "Ok! Hakane, sai anjima,amma
ataimakamin da abin kari." Sabida yafita nace, "
toh."
Banyimasa abin karinba,ina sallamar yara
nakoma na kwanta. Baba Hauwa tashigo gurin
sha daya ta tasheni.
"Kin karyane Halimatussa'adiyya?"
Nace, "a'a"
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Alhajima yana ta shigowa, wai kin hadamai abin
kari. Nace, "bazan hadaba Baba Hauwa, ni
matarsace?"
Tace, "amma Kanwarsace ko?"
"Eh, amma banason wata alaka ta hadamu."
"Aiko da alaka ta hada, 'Yaya hudufa, don haka
kibar batunnan,abin karidai nayimasa, shine ma
ya kunna kayan girkin."
Nace, "ni bamanajin yunwa, sai anjima zanci na
rana gaba daya."
Tace, "to shikenan, Allah yakaimu."
Can saiga Aunty Abida wajen karfe daya muna
kitchen muna girki. Gaskiya tayi santin gidan,
muna cikin hira sai mukaji sallamar A'isha, nan
muka yini muna hira, dan ko dakko yara a
makaranta Baba Hauwa ce ta dakkosu.
Aisha tace, "Kyan gidannan kunmaida aurenku."
Na daka mata duka a baya, "aniyarki tabiki."
Abida tace nidai ba ankimuba, mene aibun
mijina? Kin gwammace mai mata biyu da yara."
Nace, "Haka nake sonshi."
A'isha tace, "kikoma gidan mijinki Hajiyar Allah
Ku rungumi yaranku."
Nace, "Zanje in haifi wasu a can." Tace,
"shikenan."
Sun yini har dare sannan suka tafi,nakira Alhaji
a waya nace mai muntashi har yakemin korafin
Cewa bandaukeshi da muhimmancibane sai
bayan muntashi sannan nafadamai? Nace masa,
"tashinne yazomana cikin bazata, Yayane ya
uzzura."
Yadanyi dif, sannan yace, "nifa duk lokacin da
kikace Yaya dinnan sai gabana ya fadi gani
nakeyi kamar har yanzu kinasonsa ."
Nace, "dan Allah adaina maida hannun agogo
baya, ni bazan Koma gidansaba."
Yace, "to zaibari inshigomasa gida?"
Nace, "tinda yakawoni dole inshigo dakai."
Yace, "a'a, bazan shiga gidansaba, in nazo kya
fito. Ina kikacema gidan Yake?"
"Nan unguwar mu'azune,Amma sabon gurine."
Yace, "to zamuyi waya, anjima zanzo."
Nace, "Allah yakawoka."
Washegari yashirya zaitafi Abuja inna kwance
kan gadona na saki A.C inna Karanta wani littafi
maisuna Yayana safara na Asma'u Lamido
sainaji sallama,kafin na amsa har yashigo, naja
hijabi na rufe jikina, fuskata a hade na dubeshi.
Dan murmushi naga yanayi, sannan yace,
"menene Bako ake rufe-rufe?" Cikin zolaya yayi
maganar.
Nace, "aidai haramunne ka kalleni cikin wannan
yanayin."
Yace, "to nidai zantafi." Nacigaba da
karatuna,kudi ya ajiye a gefena, bankalleshiba
ballantana kudin, har yakai bakin kofa sai yajuyo
yace.
Karkijawa wani kato duka dan nacewa 'yansanda
dake gadi su daki duk wanda yashigo gidan.
Tsaki naja tare da cewa, "Dadin abin nasa gidan
yafi Wannan." Bai tankaba yafita yabani ina ta
fada.
Kamar ance ya wai waya, Aliyu yaga Mujidat
cikin mota tare da wani Mutum,kasancewar bata
ganshiba, sai kurum yabi bayansu,dayake mota
ukuce tsakaninsu, amma yaga Hotel din da suka
shiga, shima yabisu, ga alama ba lokacin zasu
kama dakinba,sun kama tuni, don baigansu nan
gurin karbar bakina.(Reception)
Yashiga kai tsaye yanuna katin shaidarsa ta
zama Dansanda, sannan yayi tanbaya game da
dakin da suka kama, yayimusu kwatance da
motar da yagansu, har dakin aka kaishi, ya
kwankwasa shiru, sai ya murda kofar, baizaci
zata budeba,amma sai ta bude.Irin kamun
dayayimusu ya kazanta,domin haihuwar uwarsu
suke, sannan maimakon saduwa irin ta mace da
namiji, sai yakamasu yana saduwa da ita ta
dubura,wato luwadi.
Wa'iyazubillah! Allah yayimana tsari da mugunji
da mugun gani, Ameen.
Salati Aliyu yasaka,Mujidat tayi wuki-wuki,Alhajin
yasoma yiwa Aliyu fadan meyasa yashigo?
Mujidat tace mijinane, juyawa yayi batare
dayace kalaba.
Ni naga yasake dawowa washegari da Abdul da
kaya niki-niki,ko kallonshi banyiba,Baba Hauwa
itace ta tare shi,itacema ta bawa Abdul
abinci,nabar falon nakoma dakina, sai gashi
cikin raunanniyar murya yace,"Sadiya inna
maikara nemana afuwarki, jiya naga abin
dayaban tsoro bayan komawata daganan, wai
ashe har yanzu Mujidat tana bin maza, dumu-
dumu na kamata da aurena akanta wani kato
yana luwadi da ita."
Na kalleshi cikin zaro ido,ban tankaba yacigaba.
"Don Allah ga Abdul nan na rikeki kisakashi cikin
'ya'yanki, kodadai yazone ba tahanyar data
daceba jinine, nasani bashi da gadona amma
baidace inbarshi ya wulakantaba,donshi ba
ruwanshi." Ya aje kudi a gefena.
"Kisashi makarntar Isalamiyya da Boko wadda
'yan uwanshi keyi, nasan zaki iya."
Duk bantakamasaba, har sai dayace "zakuyi
kwanaki baku ganniba akwai aikine a hannu na
kila ya daukeni lokaci, kiyimin addu'a."
Na tabe baki, "Allah ya tare ."
Yace, "nagode."
Haka kuwa cikin kwnaki uku Abdul yasoma bin
'yan uwanshi makaranta.
Aliyu wani course yaje na wata biyu
India,Yasamu Wannan damarne daga gwamnati
me ci a yanzu,yasan sunyi hakane Don ayi zabe
baya nan,tinda yanuna baya goyon bayansu suyi
yanda suke so, shikuwa ya karbi wannan dama
da zuciya daya, dankuwa ba kowane
dansandane ke samun wannan damar ba.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Su Iya sun dawo, muna ta murna,kullum
gidanmu sai yacika da Iyalai da abokan arziki,
anata rabon tsaraba, abakinta nakejin inda Yaya
Yake.
Baba Hauwa daki daya muke kullum sai tayimin
zancen Yaya tayi ta kwarzantashi tana bani
shawara har abin ya isheni nagudu dakin yara,
suma suka isheni da tanbayar ina Abbansu,
nace bansaniba kuma kada wanda yasake
tanbayata. Iyace kurum ke goyon bayan aurena
da Alhaji, ni dama tsarabar zannuwan gado
yayomin sai Jallabiyya.
Kwanci tashi saiga Yayay kamar daga sama,duk
dacewa natsaneshi bankasa ganin kyawun
dayakaraba, har da dan haske, a raina nace
anje course ko anje Hutu?......zandakata anan,
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
Darajar Yayana4-05
Posted by ANaM Dorayi on 02:28 PM, 20-Apr-16
Under: DARAJAR 'YA'YANA
__________________NA
___________HALIMA K/MASHI
Assalamu'alaikum, kuyimin afuwar shiru da
kukajini, hakan yafarune sakamakon tsaiko dana
samu sabida wasu dalilai,saidai yanzu nayi
yunkurin kawomuku Babi na karshe fatan kuna
tare dani, inna kuma fatan kuna sane da inda
muka kwana...
Tsarabar daya kawo dan gulma harda ni,banki
karbaba, Pakistan yakawomin kala shida masu
kyau sosai, zanyi gayuna a gidan Alhajina, ga
turaruka masu tsada. Yara kam ba'a magana
harda yaran Usman.
Ba'ayi wataba sai karin girma zuwa matakin
kwamishina 'yansanda na jihar Kaduna, anyi biki
tare da duk wani abu dayakamata,. Tuni yatare
a gidan kwamishinan yansanda dake kaduna. Sai
naga antilomana wasu yansanda wai masu
tsaron lafiyarmu.
Tinda Yasamu wannan matsayin saikuma
ganinshi yayi wuya,baya zuwa gida ya kwana
kamar da, sai da daddare jefi-jefi yazo yagaida
iya yatafi. Hidima kuwa baifasaba, saima karawa
da yayi. 'Ya'yansa yana aikowa a daukesu ranar
da babu makaranta su yini can, ko zama yakeyi
dasu, komenene bantaba tanbayarsuba.
Daidai wannan lokacin na yaye Sadiq, kuma
muka tsaida lokacin aurenmu. A lissafi yau saura
kwana ashirin da takwas,inna ta shiryeshiryen
gyara jikina da duk wani abu nasha wanda zan
rike mijina,dan kuwa Aunty Abida zugani kawai
takeyi indage innada kishiyoyi,cikin dan lokacin
ni dakaina nasan nayi zam-zam.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Direban dake zuwa daukan yara yakaisu gun
Babansu nagani tsaye nadawo daga makaranta
yace, "Madam ance in kaiki Gida."
Nace, "Inji wa?"
Yace, "inji mai gida,"
Tsaki naja nace, "bazanjeba."
Kasancewar layin shiru sai tsoro yakamani, yace,
"Kishiga kawai da arziki Madam, sabida kalli
can." Yanunamin Karshen titin, motar
'yansandace. Yacigaba dacewa.
"Zasu daukeki da tsiya."
Nace, "ai da kukuke kaini gidan?"
Yace, "Umarni akabamu daga yau, shiga muje
kawai."
Nace, "Innakifa?"
"Hakuri zakiyi ranki ya dade,sabida kare
lafiyarkine." Nace, "Allah ke Kare lafiya ta."
Yace, "To kitemakeni kar inrasa aikina." Cikin
muryar tausayi yayi maganar.
Nace, "zanshigane don aikin naka,amma badan
isar wanda yaturokaba. Yace, " Nagode ranki ya
dade."
Tinda muka hau titi 'yansandannan suka
dafemana baya, haushi duk ya isheni. Munyi
tafiya me tsayi kafin na fahimci cewa ba a
hanyar gidanmu muke tafiyaba, Nace, "ina zaka
kaini?"
"Gida mana."
Daidai lokacin naga munsha wani round about,
kafin nasake magana muka shiga wani layi muka
hari wani babban gate, Nace, "Mallam ina zaka
kainine?" Yansanda dake kofar gidan suka bude
muka shiga.
Gidan yanada dogayen bishiyoyi, dankuwa
girman gidan bazan iya musaltashiba,inna cikin
motar naki fitowa, wayata tasoma ringing,
Bansan lambarba, na daga, muryar Yaya naji
yanacewa.
"Karki zubar da kimata kishigo magana zamuyi
kitafi abinki."
Ban musaba nabi bayan direban kamar yanda
ya bukata. Cikin wani kayataccen falo nasameshi
Zaune kan kujera daya daga kujerun falon na
Alfarma, Laptop ce a kan wani tebur a gabanshi
yana latse latse.jikinshi sanye da wata shadda
ruwan kasa wadda haske da kyanta suka tona
asirin tsadarta,kamshinsa na yau da kullum
yacika gurin.
Batare da yadubeniba yanunamin kujera da
hannunsa Yace min cikin harshen turanci,
"Zauna." Ba musu na zauna, saidai raina a bace
Yake, Jira nake yayi magana insoma zubar da
bala'i.
Yanata danne dannenshi, na dubi agogon dake
falon nace, " Gaskiya innada abinyi, innason
intafi."
Ya dago ya dubeni kibani minti uku kacal in
kammala muhimmin aikina."
Naja tsaki tare da kauda kai. Wayata tayi
ringing, nadauka A'isha ce,nace, "ya akayi?"
Tace, "ga Humra ankawo me kyau," nace, "cikon
nawa zanbada?" Tace, "dubu ukune, namabada,
dama gudun mowar dazanbakine."
Nace, "a'a A'isha zanbaki kudinki, nasanfa
yanayin garin."
Tace, "Kin raina kenan?"
Nayi 'yar dariya, "wallahi ni banrainaba Nagode
Allah yabar zumunci, zanfadawa Alhaji
kokarinki." Mukasa dariya.
Tace, "kina inane?"
"Oho! Ni banmasan inda nakeba, kibari
innakoma gidazamuyi zancen."
Na kalli agogo, minti ukun tacika, yature na'ura
me kwakwalwar dake gabansa yamike a hankali
yazago gefen danake, kafafunsa babu takalmi.
Yazauna a kujerar dake daf dani ya karkato.
"Sadiya!" Yakira sunana cikin lallausar muryarsa,
nasake tsuke fuska, yacigaba.
"Sadiya meyasa kika zabi ki auri wanina? Bayan
nasan cewa ni kikeso"
Da sauri nace , "a daba, lokacin da bansan inda
kemin ciwoba,amma yanzu gaskiya bana wani
sonka."
Yayi dariyar yake, "nasan kinfadane amma in
gaskene ki kalli cikin Idona kice bakyasona."
Cike da rashin kunya na kalli idonshi, "Aliyu
bana sonka, bana kaunar......"
Yadagamin hannu tare da rintse ido , " naji
nayarda bakyasona,amma kiduba wasu
abubuwa. Nafarko, 'ya'yan dake tsakaninmu,
kinfiso kije ki kula da nawasu kibar naki? Bansan
wace mata zan auroba, ke nifa tinda Mujudat ta
wahakar da yarana na janye batun aure indai
bakebace."
Nace, "wannna ra'aynka kenan, ni nawa ra'ayin
na auri wanda yasan kimata da darajata, wanda
zaimin adalci akan komai."
Yace, "Sadiya dan Allah kitaimakamini, wallahi
inna sonki, haka zaki tafi gurin wani kibarni?
Kinsandai yanayina kullum cikin Azumi nake,
sabida tsoron fadawa barna."
Nace, Aliyu kayi hakuri, kanemi wata, gaskiya
bana sonka,tini kagama fita daga raina."
Namike.
Sai kawai naga yazube gwiwoyinshi a kasa,
"Sadiya kitaimakeni bandamu cewa kowa
yaganni a gaban ki a hakaba, indai zaki amince.
Sadiya inkincire soyayyar Allah da manzonsa, sai
mahaifiyata kece kike bayanta, don Allah
kitaimakeni kisake bani dama, zanrikeki da kyau,
namiki alkawarin zanzama tamkar bawanki."
Nace, " kai bame cika alkawaribane, akwai
alkawurra dakayimin tun a baya wadanda baka
cikaba, nifa gaskiya banajin zan kara rayuwa irin
ta aure da kai, muyi zumunci kawai na 'yan
uwantaka."
Sainaga kwalla tasoma sakkowa daga idanunshi,
ya mike tare da juyamin baya, "
Matsayina,mukamina da Shekaruna duk na
karyardasu na durkusa miki, amma kin kunyatar
dasu."
Nace, "Kaine kaja."
Ya isa kan tebur yaciro tissue ya goge
hawayenshi, yadaga waya yakira direban, ya
dubeshi, "kaita gida." Na mike na fuce, sam
banji tausayinsaba ko kadan a cikin raina.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Shi kuwa sintiri ya dinga yi cikin falon cikin
tsananin damuwa, duk yanda yazaci zaisha kan
Sadiya abin yaci tira, saidai bayajin zai iya
hakura da ita. Zumbur ya mike yayi hanyar fita
yakira direbansa, yasa takalmi da Hula ya debi
kudi ya zuba s cikin aljihu yafita.
Zari'a yanufa, yaci sa'ar samun Baba a gida.
Suka gaisa, Baba yayi ta murna da zuwan Aliyu,
'yan uwansa sukazo suna kara yimasa godiya
game da aikin hajjin da sukayo, Aliyu yace
bakomai. Yakalli Baba yace "Baba dama nazone
in nemi wata alfarma a gurinka."
Yace, "Kamar mefa?"
Yace, "Innson in maida Sadiya mu rike yaranmu,
nabi ta iya, yarinyar kuwa har durkusawa nayi a
gabanta amma taki."
Ya karonto masa irin azabar da yaran sukasha a
hannun Mujidat, da matsalolin da suka shiga
sakamakon rashin kasancewarsu tsakanin uwa
da Uba, har yanda Mujidat ta shiga harkar
banza da irin kamun da yayi mata, yakara da
cewa, " nayi mata saki biyu, don na tanbayi
malamai sunce yin uku babu kyau."
Baba yace, "dama kanason maidata kayi shiru
aka karbi batun wani? Amma kabari InshaAllahu
dakai za'ayi domin dama ni mutuminnan bai
kwantamin a raiba, saboda bai taba zuwa
yagaisheniba, tinda yaturo wakilabsa, bawai inna
neman wani abun hannunsa bane, amma mai
son auren yarka yakamata yakawo kansa
gurinka ku gaisa, kodon haduwa a hanya.
Karkadamu kakoma zanzo gidan gobe."
Aliyu yacikasu da kudi yatafi zuciya fal murna.
Nikam inna ta shirina, iyace kurum me tayani,
amma Khausar ko zancen bataso.
Washegari Lahadice, inna kwance daki yara suna
hadda, najiyo muryar Baba cikin Falo, sama
sama yake magana, nafito da sauri nashigo
falon, daidai lokacin dayake cewa.
"Don ni indai ni na haifi Sadiya to takoma gidan
mijinta shine albarkata, ta rike yaranta, ai
banzaci yana ta bintaba da yaushe zan amshi
batun wani, wanda ma ban isa yazo
yagaidaniba, matsayin mahaifinta."
Cikin sauri na zube gabanshi, "Baba wallahi
dama gobe zamuje yagaidaka."
Iya tace, "nima zanfiso suna tare da 'yan
yaransu, amma Aliyu yasaki damarsa tin farko,
don haka ni duk abinda Sadiya takeso nima
innasonshi,"
Na mike nakara kusanto Baba, "don Allah Baba
ka taimaka."
Yace, "inni na haifeki to kikoma kirike yaranki."
Ya mike.
"Ranar da akasa ta auranki babu fashi, amma
da Aliyu za'a daura."
Na kalli Iya, "kinfayi rantsuwa akan bazan
komaba."
Iya tace, "Mahaifinki ya nuna ikonshi natsaya
inyi ta jayayya? In takasance yanda yakeso zanyi
azumin kaffara guda uku."
Fuuu! Nayi daki,wato iya madai danta takeso
baniba. Nakira Aunty Abida a waya inna kuka na
fadamata, nace yanzu anyimin adalci kenan?
Tace, "Eh!, wannan shine adalcin, ki zauna ki
rike yaranki shine daidai, kiyi hakuri da rayuwa
duk inda kikaje shine jagoran zama ballanatana
tsakanin kishiyoyi ." itama na kashe waya kafin
takarasa abindatake cewa. Bankira Ayshaba dan
nasan ita yar partyn Aliyu ce.
Na kira Alhaji inna fadamasa cewa Aliyu yaje ya
zuga Babana bansan me yafada masaba. Sai
kawai mukaga yazo wai inkoma gidana.yayi shiru
yanaji har nagama,bayan kusan minti biyu
sannan yace, "Shikenan Allah yasa haka shine
mafi alkahairi." Nasaka sabon kuka , "Haka
zakace kaima? Dama ba sona kakeba?"
Yace, "Inna sonki mana, ammafa ni ba yaro
bane da zan tsaya inna jayayya, sannana tini
jikina ke bani gidanki zaki koma, Allah yasa haka
shine mafi alkhairi."
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ranar yini nayi kuka har yara suka dawo,
Khausar da Al'amin suka tsareni da tanbaya ,
haushinshi yasani jin haushinsu suma, nace, "Ku
fita ko inyu muku dukan tsiya," suka fita sukaje
suna tanbayar Iya.
Iya tace, "wai dan kakanku na Zariya yazo yace
takoma gidan Babanku." Sai iya taga yara sun
soma murna, Khausar me wayon tsiya sai ta
saci wayar iya ta nufi dakinsu ta kira layin
Babansu, Cikin murna tace, "Abba innayimaka
murna, ashe Momy zata dawo gidan ka?"
Yace, "Eh, Babyna. Ina Maman naku yanzu?"
Tace, "gatacan daki tana kuka,dan Allah kada ka
karayimata abinda zaisa kuyi rigima."
Yace, " To Khausar zan kiyaye, kije ki lallasheta,"
Tace, "To." Tana aje wayar yayi murmushi,
yarinya yar shekara tara da rabi wayonta kamar
na manya.
Yashigo, "Momy inji Abba wai yana gaisheki,yace
kiyi hakuri kidena kuka."Tsawa na dakamata ta
tashi, ga mamakina sai naga tana dariya.
Cikin dare naga sakonsa, wai: Saura sati uku ko?
Nakosa inrike lallausan hannunki, My choice ya
kike ganin darenmu na farko zai kasance? Inna
jiran amsa.
Tsaki naja na goge sakon.
Shida na safe naki tashi infita,sabida inna fishi
da kowa na gidan, wayata tasoma ruru na duba,
koda banyi saving number shiba nasan yayane,
don haka naki dagawa. Kiranshi goma inna
lissafawa, sannana sako yashigo.
My choice kiyimin addu'a zantafi wani daji
dakaina zan jagoranci yarana don cafke wasu
barayin dana gano suna tare da tsohon
kwamishinan da aka canza daga Kaduna.
Nafadamikine ba dan wani abuba sai dan kila
bazan dawo ba, nafitane a bakin raina.
Shiru nayi, dan kalaman sun tsirka zuciyata
kadan, amma duk da haka sai na tabe baki na
ture wayar.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Tamkar almara karfe goman dare na jiyo muryar
Usman a dakin iya, can sai naji tana salati na
fito ina tambayarta lafiya? Tace, "Aliyu ne wai
yan fashi sukai masa harbi uku, amma dai anyi
nasarar kama wasu, sannan aka harbe wasu."
Take zan tukan da ya turo min dazu da safe
suka fado min, na zauna kan kujera nace, "Iya
yanzu yana ina?" Usman yace, "an tafi dashi
Abuja babban asibiti."
Kai gaskiya hankalina yayi mutukar tashi, cikin
daren nayi ta kuka amma bazance ga dalilin
kukanaba.
Washe gari su Usman da sauran yayyanmu su
yaya Sulaiman suka kwana acan sannan suka
dawo, sunce an cire masa harsashin amma ba'a
bari ma anganshiba saboda tsaro. bance
zanjeba amma zuciyata tana can. Satin shi daya
iya ta matsa zataje ta dubo shi, ya samu sauki
sosai sannan hankalin iya ya kwanta.
Data dawo nace, "ya jikin?"
Tace "da sauki,ana dai bashi kulawa ne."
Nace, "masha Allah."
Ban ko kirashi ta waya ince ya jiki ba harya
dawo gida, satinshi biyu da kwana biyu wanda
ya rage saura kwana biyar aurenmu, nan gidan
aka kawo shi can shashinshi. Su Baba Hauwa
sunzo duba shi shine yake bata labarin ban taba
ce masa ya jiki ba, tazo tana yi min fada. Su
Abinda da Aisha kuwa gaba suka dauka dani. Iya
dai bata taba ce min inje ba niko zuciyata ta
kekashene ina saran zaice ya fasa tunda na
nuna masa kiyayya karara.
Washe garine ya tako zuwa ban garen mu ina
zaune a falo ina kallon T.V ya shigo, yadan rame
kuma yayi haske, yace, "ina kwana?" Na kalle
shi cikin jin kunya nace, "lafiya, ya jiki?" Yace,
"au ashe kinji, koda yake nasan kinso ace na
mutu ko?"
Nace, "duk wanda lokacinsa ya yi babu kari,
harni din." Bai sake magana ba ya shige wajen
iya, ina jiyo muryar ta tana cewa na zaci za'a
daga bikinne,shi kuma ya ce a'a jiya su Yaya
Sulaiman sunje Zaria sunyi magana da Baba,
sunkai sadaki ya ce yau zaizo gurinki
Tace, "to Allah yasa albarka," wani abin haushi
wai ashe ya ba Usman sun hado min setin
akwatuna cike da kaya masu tsada harda yara
duka, nidai ina ta kallon ikon Allah za'a yimin
auren dole.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ranar daurin aure kuwa kwanciya nayi abina,
gida cike da dangi, su A'isha suna tamin tsiya
wai inaso ina kaiwa kasuwa, jin haka naki
wanka, sai dare nayi wanka dan naji iska. Ina
sallar isha'i sai gasu Baba Hauwa tace, wai na
fito a kaini gidan mijina, sai da nai kuka mai
isata sannan na fita, wai inje gurin iya taimin
fada, "nace ba zuwan da zanyi, ni yanzu meye
ban sani ba sai kace wata yarinya? bayan itama
Iyan ta daina sona." Ashe Iya tana jina sai
kurum tace, "ni dai da kike fishi dani Allah ya
bada sa'a, fadan ku da Aliyu ba'a shiga kwanan
nan za'a jiku shuru." Haushi ya sake kama ni na
saka sabon kuka, dan wulakancin sai aka samin
dariya.
Gidan shi aka kaini, dakina yayi kyau mutuka,
sai dai ba kayan gadon dana zaba bane
wadannan sunfi su kyau da tsada. Sha biyu ya
shigo dakin, cikin fushi nace, "indai kana wa
girman Allah ka fita in kuma nizan fita to in
fita." Sai yace, "Asuba ta gari."
Tin daga ranar bai sake shigowa daki naba,
kullum shine yake min magana amma bana
kulashi. Ya siyo wannan ya siyo wan can inya fita
zai kirani yafi sau biyar naki dagawa.
Satina biyu ya debo yara, niko yaranma Sadiq
kurum nake kulawa kuma yaki zama shi sai
gurin Iya, nace a sauka lafiya, itama Iyan ta
sami dan tayin hira tunda ita daya ce, danma
da masu aik.
Ranar wata Alhamis ina xaune bayan isha kusan
tara saura Khausar ta shigo, "momy kizo inji
Abbammu yana dakinsa," nadanyi shuru nasan
ya hada da Khausar ne dan yasha kirana kullum
dare ta waya inki zuwa, ta zauna bakin gado,
"Momy yace kije fa," ta katse min tunani, nace,
"ke karki dame ni, kije zanje," data fita taga
shuru ban fito ba sai ta shigo da takardunta
tahau tsakiyar gado na wai zatayi home work,
nace in gani in tai maka miki tace, "a'a kije Abba
na kiranki ko kinje?" Dole tasa na mike, acikin
dakunan bansan wannene dakinsa ba sai da
Abdul ya fito nace inane dakin Abba? ya nuna
min nace meya fito dakai yace ina neman yaya
Khausar ne bata yimin Home Work ba, nace ka
shiga dakina. Na murda kofar dakin ta bude na
shiga yana sanye da jallabiya mai gajeran hannu
kamshi da sanyin A.C suka buge ni na ji sanyi
yana ratsani sabida yanayin sanyinne ake ciki
nace "lafiya?" Yace, "Shigo mana ciki," Na shiga
tare da maida kofa na rufe, ya tako ya kama
hannuna ya zaunar dani a bakin gado shima ya
zauna ya lalubo hannuna ya matse cikin nasa ya
sauke wata irin ajiyar zuciya, na kalli fuskarshi
idon shi a lumshe, Yaya mutum ne da yayi dai
dai da kowanne zamani yana da kyau abin son
kowacce mace amma ni sam bana jin sonsa a
zuciyata, ya bude ya kalli cikin ida nuna, "nasan
kin tsaneni koh?" Nima na cigaba da kallon cikin
idanunshi, wata siririyar kwalla ce naga ta taru a
cikin idanunsa yace, "duk da haka ina neman
alfarma ki bani hakkina,wallahi ina cikin wani
hali sai dai bazan matsa mikiba, babu matsala
in kinga cewar da takura kije abinki karki damu
kiyi baccinki," nayi shiru ban motsaba, ya cire
hijabin jikina, rigar baccina ta bayyana, Sky blue
ce mai santsi, ya soma shafa min gashin kaina
hawaye suka soma zubo min, bansan ko na
menene ba,sai na tsinci labbansa saman nawa,
jikinsa kuwa bari yake sai kace tsohon daya
dauki budurwa, ni kaina ban san ina muradi ba
saida abubuwa sukai nisa. ranar dai mun kwana
muna aikin lada cikin wata duniya da masu
auren sunna ne kurum suka santa.
Wannan karon yaya bai dauki al'amarina da
wasaba, ji yake dani kamar yar yaye Ko laifi
nayi baya yi min fada, inna ce ina son abu baya
ja ko aiki da nake nace zan daina yace a'a in
kina son dai nawa na daina jayayya dake, nace
to zan daina dan dan nasan bakaso, yace
nagode.
Haka nan tun ina dari dari da shi na saki jikina
da shi nima ina nuna masa kulawa, zamammu
yafi na farkon aurenmu, 'ya'yanmu sun
warware, damuwarsu ta yaye, sun ganmu a tare
cikin aminci sun zama cikin farin ciki da walwala
karkashin kulawarmu.
Wurin shi na sami labarin Mujidat ba lafiya tana
asibiti wai bata rike kashi da fitsari, yace, "kinga
illar zina da Luwadi ko?" Nace, "Allah ya bata
lafiya," yace, "yanda nake samin labari gwara
mutuwarta da rayuwarta, Allah yasa mufi karfin
zuciyarmu." Nace, "ameen ya rabbi........"
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Tammat bi hamdullahi taku Halima Abdullahi k/
mashi kecewa kusaurari littafinta na gaba,
SAUYIN RAYUWA........
Alhamdulillah yaudai cikin ikon Allah gamu
mumkawo karshen wannan labarin da muka dau
tsahon lokaci muna yi, fatan zamu anfani da
dukkanin anfanin da yake ciki sannna mu kiyayi
kusakuran cikinsa. Inna neman afuwarku idan
na sabawa daidaikunku kokuma jamhuri.
Nagode sai kunji daga gareni.
Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100
